Auren Wata Uku Book Complete By Sameena Aliyu.doc

Author :  Sameena Aliyu Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   4 / 52

9K to 12K   out of 153.1K words

gaba da zagaye katafaren parlorn nasa.

Furzar da huci Hajiya Kwaise tai, tana mai kuma dialing layin Haidar amma shiru bai d agawa.

Dad ya kuma dubanta  He s not answering right..?

D an lumshe idanu tai had ida mik ewa tsaye  Engr please calm down.

Ya kuma katseta  Seriously Kwaise..? Are you asking me to calm down.? Ko bakiga babban abun kunyan da wann shashashan d an naki yai bane.. Kwaise, I m a highly respected person. A well known businessman. I have a reputation to protect.. Bazan bari wann d an naki ya ruining d ina ba.

Izuwa lokacin cikin ta tunzura itama  Aw laifin Haidar kake gani..? Kai bakaga laifinka ba.. Kan wani dalili zaka cakume kwalan d anka a bainar mutane.. Cameras all over ba dole masu Neman ganin bayanmu suyi amfani da wann damar ba.. Yanzu sai ka yarda da maganan Haidar da yace maka akwai mai maka zagon k asa cikin mutanen da ka aminta dasu..

Katseta yai cikin b acin rai  This is natural in a business world. We ve business rivals and competitors. So ba abin mamaki bane idan sunada spy cikin Kampaninmu.. Amma babban abun takaicin shine yanda muka gaza handling such situations.. And this is all your Son s fault.. He s weak, idiot.. A pathetic loser.. Yana can ya saka mata a ransa.. What do you expect..?

Ya kuma jinjina Kai yana sakin huci sai yarfe gumi yake kai kace ba sanyin AC ne ke circulating cikin parlorn ba.

Isowar Haidar k ofan gidan mahaifin nasa yai tozali da dandatson  yan jarida. Ai kuwa kaman jira suke suka nufosa suna jefo masa tambayoyi ta ko ina.  Yallab ai Aliyu. Da gaske ne mahaifinka ya tareka da fad a bayan cecekuce da ya kaure tsakaninku cikin Kampanin mahaifin naka..? Engr Maitama ka amsa mana..

Da kyar ya samu ya kutsa cikin gidan sabida tambayoyi da kalaman da manema labaren keta jefo masa.

Yana dosowa parlorn Daddy ya nufesa a zafafe kaman zai shak o sa Mommy tai saurin shiga tsakani cikin k ok arin dannar mijinta.

Sosai yake huci kaman zai kifa k asa yana nuni da Haidar hannunsa har rawa yake.

 You.. You and your entire existence is a disappointment..! Kai kayi kad an ka lalata mun suna da sunan Company.. You better find a way to fix this mess kafin business rivals d inmu su samu abun yawo damu kaji na fad a maka.. Bazan tab a bari bak in cikinka yayi ajalina ba.. I will make sure to cut you off kafin hakan ta kasance.. Yatsanshi na rawa yaci gaba da nuna Haidar  So Kar ka sake kayi abinda zaisa na haramta maka amfani da sunana..! Daga haka sa Kai yai ya haura sama dan a halin yau fita ma bai ganshi ba  Yan jaridu ta ko ina. Dan yasan K iris abokan adawansu na kasuwanci Ke jira. Har yayi step biyu ya kuma juyo ya dubi Haidar da idanunsa suka kad a sukai jazir  Kaje ka sallami mutanen can da ka tara mun kof ar gida.! Yasa kai yaci gaba da haurawa.

Furzar da huci Haidar yai yasa kai zai shige. Dan yasan mahaifinsa bazai tab a sauraransa ba. Momy ta dakatar dashi

 Mom please not now.! Ya katseta da fad in haka.

Cikin rawar murya take furta  What s wrong with you Haidar.. Why are you doing this to us to yourself.. Meyasa ka maida iyayenka Abokan gabanka.. Why can t you open your eyes and see my son.. Your Dad is only trying and struggling to make a proper man out of you..

 Oh really Mom.! Is he really trying to make me become a better person by pressuring me to meet all his expectations..? Muryarsa ya soma rawa sanda yake furta  Na gaji.. Na gaji.. I m fed up with everything around here..! Bai kuma tsayawa sauraronta ba yasa kai ya fice yana haki da huci ga wayarsa da ta gaza yin Shiru. Kira ne keta shigo masa.

Saiga Mommy ta koma gefe tana hawaye. Meke faruwa da rayuwar ahalinta.. Meke damun Haidar.. Dik yanda akai something is wrong a wani wajen.. Zama bai ganta ya zama dole ta tashi tsaye. Da wann tunanin ta nufi nata b angaren duk jikinta a mace kaman dai ba Mommy ba. Mace mai zafi da jajircewa.

Jiki a sanyaye Anisa ta k araso rik eda waya ta mik a ma Mommyn tana fad in  Ammi Ke son magana dake tana ta kiran wayarki bata samu.

Mommy tana amsar wayar ya fashe da kuka tana fad in  Asshe ba lafiya.. Asshe gidana a hargitse yake..

Jin haka yasa Anisa komawa dan ta baiwa  yan uwan waje su tattauna. Sosai hankalinta ya tashi da ganin yanayin Mommy dan tinda take bata tab a ganin  Yaruwar mahaifiyar nata cikin irin wann yanayi ba.

**

KANO

K aton parlor ne mai d aukeda kekunan d inki kusan guda biyar. Yafi kama da wajen koyon d inki.

Wata mata ce da ta d an data a shekare tsaye cikin babban zauren tana duba kekunan.

Ummulkhairy ce ta soma halarta cikin d aliban nata. Dama ita d in da wuri take zuwa kafin lokaci yayi dan ta taimaka da share share da gyare gyare.

Sallama saman bakinta ta shigo.

Matar ta fad ad a murmushinta  Wa slaikissalam uwar alkhairi. Dan haka take kiran Ummul d in a akasarin lokuta.

Ummulkhairy ta risina ta gaidata. Ta amsa kaman ko yaushe da sakin fuska  Uwar alkhairi kece dai kullum akan gaba kina masu wayo kina kwashe ladan. Wataran bazaki huta ba.. Jiki da jini Ummul kink i ayi maku roster da kowa tasan ranan nata aikin.

Ta murmusa  Hajja ai nafi son na tara ladan da albarkan ni kad ai ne..

Hajja Fannah ta murmusa  Ai kuwa da izinin Allah albarka na bibiye dake.. Kinci sunanki uwar alkhairi..

Murmusawa ta d anyi kad an jikinta na kuma yin sanyi da kalaman Hajja sakamakon tuno tashin hankalin da ta baro a gida. Ta mik e da sauri gudun kar Hajja ta fahimci yanayinta ta d auko tsintsiya zata soma shara Hajja da tuni ta karanci yanayinta ta dakatar da ita.

 Zo nan Ummul, zo ki zauna magana zamuyi kafin sauran d aliban su k araso. Bar sharan nan. Tai mata nuni da gefenta saman tabarma.

Jiki a sanyaye Ummulkhairi ta isa ta zauna.

Hajja ta gyara zamanta  Fad a mun me Ya faru.? Hajja Fannah ta jefo mata tambayar dan dama tana sane da halinda Ummul d in ke ciki. Gidanta na bayan layin su Ummul layin da ke babban kwalta. Hajja Fannah tanada shagon d inki da yara maza masu d inki a shagon ta dake gaban gidan nata yayinda take koyar da  yanmata sana ar d inkin a cikin gidanta. Sunyi sabo mai tsafta da Ummul tin sanda ta soma koyon d inki wajenta. Tana bata shawarwari had ida kwantar mata da hankali hakan yasa Ummul ke samun sanyi wajenta, takan kai mata damuwarta su zauna su tattauna ta kuma bata shawarwari masu amfani a gareta had ida nitsa zuciya.

Ummul ta d an share hawayen da suka gangaro mata  Hajja wllhi na gaji.. Harga Allah na gaji.. Ita fah Umma ko wanne irin mutum so take na aura babu ruwan ta ko ina san wann mutumin ko bana so.. Ita burinta kawai nai aure da farin ciki ko babu. Ni kuma a halin yanzu wllhi batun auren nan ya fita kaina ni sana ar nan da nake nafi samun kwamciyar hankali cikinsa fiyeda komai. Shin wai ita mace ba a mata uzuri ne a rayuwar nan..? Hajja ba biye biyen maza nake ba.. Allah shine sbiadana ina k ok arin tsare mutuncina.. Sann azumin litinin da Alhamis duk basa wuceni ba wai dan na Gaza rik e kaina ba sai dan sabida nasan shi azumi garkuwa ne Hajja.. Amma ita Umma duk fah bata ganin wann. Ita kawai damuwarta mutane da abinda suke Fad i.. Shin Hajja menene laifin wacce Allah ya jarabceta da JINKIRIN aure..? Ta k arashe damuwa fal fuskarta hawaye na kuma gangaro mata.


Girgiza kai kad an Hajja Fanna tai, cikeda tausayi. Ta kuma gyara zama tana duban Ummulkhairy  Ummul, shi fah d an Adam a koda yaushe bai rasa abin Fad i.. Sann har abada bazaka tab a Iyar masa ba.. Mutum sai Allah.. Ta kuma gyara zamanta  Wato muna cikin wani irin Al umma ne da k addararka take iya zama zunubi a gareka.. Mai nake nufi da k addararka tana zama zunubi a gareka? Macece Allah zai jarabceta da JINKIRIN aure sai kiji mutane suna cecekucen cewa ta zauna a gida tak i aure. Idan wacce take karatu ne sai kiji ance ta rungumi boko tak i aure.. Idan ma Sana a take dan ta rufa ma kanta asiri sai kiji ana cewa maza ke bata kud i ta Kama Sana a ne dan ya zame mata garkuwa kar a zargeta.. Ita dai mace wai bazata rayu ba saida tallafin namiji. Mace ce Allah zai jarabceta da mutuwar aure sai kiji ana cewa ta kashe aurenta ta dawo gida bazaki tab a Jin ance miji ya kashe mata aure ba sai k alilan a a itace dai Sarkin laifi. Kuma babban abin takaicin mutanen da tafi kusanci dasu Sune mutanen da take soma fuskantar k alubale daga wajensu. Kowa sai ya tsangwameta a cikin gidan baga iyayenta ba baga  yanuwanta ba a wasu lokutan. Kinga a nan k addararta ya zama kuskurenta. Ta d an numfasa kafin taci gaba  Ummul ba ina fad a Miki haka bane dan kiga laifin iyayenki ko wani abu mai Kama da haka. A a ko d aya, burin ko wasu iyaye shine da zaran  yarsu ta isa aure su ganta a d akin mijinta. Kuma babu iyayen da zasu so suga auren  yarsu ya Mutu. Toh amma idan jarabawan Ubangiji ya shigo ciki sai ayi hak uri a fawwala masa lamuran. Ka tsara rayuwarka yanda kake burin Ubangiji ya tafiyar maka da ita tareda fatan mafarkan ka su cika ba laifi bane hasalima Wanda baya planning rayuwarsa baisan ina ya dosa a rayuwar ba. Toh amma wasu lokutan yanda muka tsara ba haka rayuwar take zuwa mana ba. Dalili kuwa shine ba muke da hakkin tsara rayuwar ba iyakacin namu mafarkai da burika had ida fata na gari. Ubangijin duka shike tsara mana rayuwar yanda yaso. Kuma tsarinsa a koda Yaushe shine daidai. Idan ya amsa mana addu anmu ya tabbatar mana da burinmu da fatanmu sai muyi farin ciki mu kuma gode masa. Sann idan ya jarabcemu ya janye wann fata daga garemu bamu samu abinda muke mafarki da buri ba shima sai mu masa godiya sabida shi yasan abinda yasa ya hana mu kodai abin mai cutarwa ne a garemu. Ko kuma ya mana tanadin Wanda yafi wann. Ta kamo hannun Ummulkhairy cikin nata  In every delay, I believe there s khayr.. Just like your name Uwar alkhairi. In sha Allahu JINKIRINki zai zamto cikeda d imbin alkhairi.. Babban abinda zan Miki wasiya dashi shine biyayya ma iyaye. Kar ki kuskura koda wasa ki fasa musu biyayya matuk a bazasu ce ki sab i mahaliccinki ba.. Idan kika rik e biyayyan iyaye alkawarin Allah ne rayuwarki zai cika da d imbin alkhairi kinji ko..

Ummulkhairy ta jinjina mata Kai a hankali kyakkyawan murmushi saman kyakkyawan fuskarta. Hak ik a tana samun relief da kalaman Hajja Fannah. Inama Ummanta zata kasance mai fahimta kamar haka. Sallaman wasu daga cikin d aliban yasata k ok arin saita kanta Hajjah Fannah na fad in ta kwantar da hankalinta komai zai shige ya zama tarihi da izinin Allah. Ta mik e tana amsa gaisuwan  Yanmatan da suka shigo tana fad in yau dai Ummul d inta zata huta Sune zasuyi shara su gyara waje.


Daga can bakin Layi Alhaji Kamilu Ya aje motarsa Mama na biye dashi tana fad in  Kai dai muje ka bama idonka abinci Alhaji.




SameenaAleeyou=???

*AUREN WATA UKU..!*



*06*







*??Sameena Aleeyou&
'



K ofan gidan Hajja Fannah Mama ke nuna masa  Yauwa Alhaji. Nasan Kai mutumin kirki ne. Ance matanka ma ko fita unguwa basayi tsaban yanda kake kaffa kaffa da iyalanka. Toh kaga can yanda kaga mata da maza suna safa da marwa.

Alhaji Kamilu ya kuma duba k ofan gidan wanda shaguna suka saka a tsakiya ga samari sai kai komo suke tsakanin shagunan can gefe harda shagon aski ga  yanmata masu sana an koyon d inki suna Kutsawa suna shiga gidan Hajja Fannah.

Mama taci gaba  Toh wann gida dai dake gani Ummul tana ciki da ita ake wann kai komo tsakanin wad ancan samari marassa tarbiya masu aski irin na shed an. Idanun Alhaji Kamilu ya sauk a samarin da Mama Ke nuni dasu wanda suka fito shagon Aski gana ganinsu kaga samari marassa tarbiya ga wani aski da aka musu an kwashe gefe d aya an bar d aya. D aya saurayin ma harda sark a a wuyansa.

Alhaji Kamilu yai Shiru kaman mai nazari. Sai kuma yace  Da zaran na aureta ta dena fita ko k ofa dan mata na ko taron biki da suna basa zuwa babu yanda suke zuwa sai asibiti da ya zama dole.

Mama tai  yar bazaurar murmushi  Toh ai Alhaji ba a nan gizo Ke sak an ba. Ta kuma gyara tsayuwarta  Kaga wann gida da Ummul Ke zuwa da sunan koyon Sana a. Matar gidan ba kowa bace face gasunk umar kawaliya. Wllhi nake fad a maka Alhaji ta addabi kowa ta fitini kowa a unguwar nan. Mata take tarawa cikin gidanta maza kuma suna daga waje a shago. Maza take had awa waje mata kuma cikin gidan ayita aikata masha a ana aikata alfasha. Kuma ba zallan  yanmata harda matan aure a wann bad ala da take had awa. Na tabbata bazaka so ka auri yarinyar da ta gama watsewa wajen wann hatsabibiyar Matar wacce ko aure bata dashi zaman kanta take zaman daduro.. Wann shago da koyar da sana a da take cikin gidanta ba komai bane face rufa rufa gudun idon mutane. Amma mu da mukaga jiya mukaga yau a unguwar kowa ya kwana da sanin Kawaliya ce. Amma idan baka aminta da abinda nake fad a maka ba zaka iya tare mutanen unguwar nan ka tambaya Kaji idan ba zaman kanta take ba. Ko aure bata dashi babbar Magajiyar karuwaice. Kaf  yanmata da matan aure dake zuwa wajenta da sunan koyon sana a, karuwanci suke fitowa su fake da san a. Meyasa Ummul tak i aure..? Kai bakai ma kanka wann tambayar ba. Mace har mace kyakkyawa irin Ummulkhairy ta gaza samun mijin da zai aureta.. Ai kaima kasan da walakin wai goro a miya.

Ganin Alhaji Kamilu ya kifa kansa had ida maida hannayensa baya irin yanda manya suke idan suna tunani yasa Mama ci gaba  Ni wllhi ganin mutuncinka ne kuma ganin Malam zai yaudareka ya lik a maka  yarsa da ta gama yawon ta zubar a kororo yasa nai wann shahadar nace bari dai na sanar dakai gaskiya ka gane dalilin da Ke sa ko wani namiji mai kamala da mutunci Ke guje ma aurenta. Malam bai dubi amanar dake tsakaninku ba. Ba kalan suturan da baka masa ba amma ya zab i ya maka lumbu lumbu dan dai kawai shima ya rabu da alk ak ai.. Yo shima ya gaji da ita.

Birki tai da kalamanta ganin Hajja Fannah ta fito biyeda ita Ummulkhairi ce rik e da kayan d inki suka shige shagon d inki ga wani matashi ya fito daga cikin shagon ya gifta ta gefen Ummulkhairi.

Mama tai kabbara tana hamdala  Ka gani ko.. Ka tabbata ba sharri nake ba. Wai ance gani ya kori ji.. Kana nan kanata rawar k afa zaka angwance toh aikin banza kake wai rufin d aki da b arawo dan k artai bila adadi sun rigaka.. Ta numfasa had ida gyaran murya  Toh Alhaji ni na gama nawa, Allah ya gani na fita na sanar dakai. Kuma ka gani ma idanunka. Ya rage maka ka amince ka sai ma kanka da iyalanka tikitin mutuwa dan k anjamau ne zai maku sallama. Ka taimaki kanka kaman yanda saura suka taimaki kawunansu. Ni na Barka lafiya Alhaji..

Tana ida fad in haka tasa kai ta shige zuciyarta fari tas.

Alhaji Kamilu kuwa sai kallon k ofan shagon yake yana jira yaga ko Ummulkhairi zata fito amma shiru. Zuciyarsa sai tafarfasa take haka yaja k afafunsa yana sab a babbar rigarsa da take  yar duk unaso ya nufi motarsa.
**

Mama tana shigowa gidan ta cire mayafi ta soma zuba ruwan bala i

 Iyi.. Kan wani dalili za a tare ni a hanya ana mun cin mutunci kan laifin da banji ba ban gani ba.. Babu wanda ya huta a gidan nan duk akan rai guda.. Baga yarana dake gidan mazajensu ba yanzu abun har ya tsallako kaina& Toh wllhi bazan d auki cin mutunci daga kowa ba kan  yar da ban haifa ba..!

Umma ta fito daga kitchen afujajan tana goge idanunta da hayak i ya sanya mata su hawaye  Yaya lafiya.. Meke faruwa..? Wani abu ne aka miki..?

Mama taci gaba da tururi  Yo uban meye ma ba a mun ba.. Gashi can Alhaji Kamilu yake ko ya tareni a hanya ta yanda yake shiga ba ta nan yake fita ba saikace alhakin tarbiyan Ummul a hannuna yake.!

Cikin Umma ya bada wani irin sauti k uuuu  Wani abu ne Ummul d in tayi Yaya.?

 Meye kuwa batayi ba bayan ganinta a gidan Matar nan da yayi wacce kowa ya kwana da sanin

4 / 52