Author : Yar Jingau Category : Romantic Hausa Novels
abinda zance sabo yanzu yafi karfin ganina naje da kaina danne mansa sai mugun gamo danayi agunnasa ,
ashe lokaci yayi da uwa zata haifi danta duk wata wahala Tasha da abunta baka nemi daukin waniba sai na Allah ameera anrabani da dana yazanyi ?
Ita dai batasan mezatace ba domin kwata kwata Bata fahimci me umman take nufi ba dan bata taba gaya Mata komai ba yo ma har yaushe tazo gidan itakanta batasan ame take a tasan dai an daura aure ansha biki daga bisani aka kawota Wanda har yanzu batasashi a idontaba,
Yau kwanansu biyar da dawowa daga asibiti anatashan shirye shorten suna Kuma harkawo yanzu baya tinanin zuwa gun umman tasa ,barna yakeyi ta kudi kamar bada jiki aka Nemo suba Dan yanzun ma kayan dayasiyo bmata nafutar suna suke gani suna shewa.
Mardiyya ce tazo sakamakon Kiran da umma tayi Mata tasanar Mata da haihuwar Dan uwannata,
Bayan hutawar datayine suka Dan taba hira da ameera dama kosanda suka rayu gu daya tasu tazo daya take zoki rakani Inga danmu sonake inga dawa yayi kama ,
Wuri wuri tayi da Ido Dan da lada in,akace ta koma gun mejegon bazataba Bata mance abinda akayi musu ba ita da umma Randa aka sallamosu da murna suka taryesu Ana Mata sannu da jiki itako da saurinta taje tana kokarin daukar babyn tsawa aka daka Mata bakowa bace Kuma sai sadiyar sannan yayarta takarbe dacewa Ashe kunsan ta haihu to ta Allah batakuba abunda kukaso yasameta Allah ya ketararta Dan haka umma tagaida ashsha,
Jiki a mace ta ja baya ,ita ko umma murmushi tayi take abani angonnawa nagani ,
Turbune fuska tayi alamar bazata bataba yitayi kamar batasan abinda takeba tasa hannu tadauki dan addu,a take tofa masa sai ga alhaji sabo Nan yashigo niki niki da Kaya bayansa megadi ne rike da wadansu ledojin,
Sallama yayi yashigo amma sai yasaki ledojin hannunnasa tare dayin baya dasauri Yana addu,a itama suman zaune tayi sannan cikin firgici ta saki dan Allah ya taimaka uwar nakusa tariko kafarsa ,
Kowa kallonsu Yake domin shidai maboya Yake nema itama hanyar futa take nema ameera ce tariketa suka futa tindaga ranar har yau dinnan fama take ta kanta ko sunansa bataso Taki an ambata .
Mardiyya ce ta katse Mata tinanin da take tace taso muje ,
Tace kije kidawo ni umma Zan Taya Hira haka tatashi tashiga gurin yayan nata
pls share
*INA BUKATAR COMMENT DINKU NA ROKEKU INHAR KUNASO NACIGABA*
🤝 *DAGA ALKALAMIN* *YAR MUTANAN* *JINGAU* 🙋
🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀
🤦♀
😨😨😨😨😨😨
🙏 *ABINDA KE FARUWA* 🙏
*LABARI DA RUBUTAWA*
*BY*
🤝 *FAUZIYYA AUWALU* *ALIN BABA JINGAU* 🙋
🅿 *21(U)*
🌈 *KAINUWA WRITERS* ✍🏾 *ASSOCIATION* 🤝
sallama dauke a bakinta tashiga gurin yayan nata bayan gaisuwar da tayiwa mutan gunne Wanda suka amsa bayabo ba fallasa takecewa Allah yasa matar yaya ta iya haihuwa Dan inba mekama Dani aka haifaba lekensa kawai zanyi bazan dauka ba dan bazan yarda kifara da kalarki ba garama kifara da kalarmu ,
Dagowa tayi shekeke ta kalle Aiko baki fadaba balallai ne yazam kingan shiba domin baccima yake ,
Yayarta ce tatashi ta dakko jinjirin ta Mika mata ,
Tace Kai Masha Allah kin iya haihuwa zarkadi duk Wanda yaganshi inba fada akaina sai ace ninayi nakudar tafada tana dariya,
Dake ba mutuncine yawada cetaba sai tace Kinga inzakiyi abinda ya kawoki ki wuce kiyi Ni banason kitifi Dan da badan Allah yasa da kwanansa gababa da tini mutan gidan daba imanine dasu ba sun kashe minshi,
Keeeee tadaka Mata tsawa tace inzaki ci kasa to kiyayi tashuri suwaye agidan?
nace suwaye a gidan badai ummata kike fadaba gara dayar ace kishiyarki ce to ko itadinma rainonn ummace bazatayi abinda Kika ceba balle sirukartaki ,
dannaga take takenki kodama bakida mutunci bansani ba naje nazauna Ina mutunta iyayan wasu nikuma tawa tananan a wulakance ,
to ahir dinki Rami nake sai dai aganni amma ba,asan abinda yake ciki ba , inma kalarki kenan toyi kokarin sauyawa Kan mijinki yadau mummunan mataki akanki,
Kebama mijinki nidinnan inmuka daura bazakiji da kyauba,
Watace afalon tace Yoshi wanna ki ai ba mahaukacibane da hankalinsa ai yasan meke faruwa inzaki iya zuba Ido tom inkuma bahakaba kema ....turo kofar dakinsa yayi yafito Yana mutstsika Ido hayaniya nakeji lafiya?
Tayi karaf ta amshe zancen mardiyya ce daga ana zancan arziki shine ta maidashi tashin hankali kamar wata yarinya Kuma har hakuri muke bata amma kamar bazancen Wasa ba ta maidashi fada.
Ya kalli Yar uwar tasa cikin salama da kauna yace Koma kizauna bansanki da tashin hankali ba abar zancan ya isa haka.
Zama tayi suka Shiga hirar zumunci daga bisani datakeson su tattauna tace yaya kozamu Dan fita saboda akwai wani personal issue Dana keson mutattauna,
Mikewa sukayi zasu futa ta kalleshi tace alhaji ka rabuda ita ta tafi nima inason zamuyi magana ,
Kamar bada umarni haka yajuya zai koma cikin zafin nama mardiyya takamo hannunsa tajashi suka fita kokarin jansa part din umma takeyi yaja ya tirje,
.yace karki Jani Nan banason zuwa musamu wani gun muzauna amma bananba kicikani ,
Data kafe sai sunshiga sai ya fuzge hannunsa zai juya da gudu Tasha gabansa tace Yaya meyake faruwane tinda nazo nake ganin difference abubuwa agidannan anya ko lafiya?
Shiru yayi domin bashida abinda zaice sai jikinsa dayakara mutuwa,
Tace yaya gurin umma nefa nan zamu Shiga bafa wani gun zamujeba ,
Tinda nace Miki bazani ba toki rabu dani banason naganta tsoro take bani kuma ko kinsan batason sadiya agidannan ko kadan batasonta nikuma duk Wanda bayason iyalina wall... .ya Isa nace ya Isa sai hawaye sharrrr sai Kuma tadurkushe kasa tafashe da kuka dagota yayi tare da Jan hannunta domin sizaga bayan dakunan gidan ,
Tinani tayi tace mushiga dakin ameera sai mutattauna acan ,
Yace wace ameera ?
Dafe Kai tayi tace innnalillahi wa Inna ilaihirraji un sai takara ruko hannunsa yazame Mata wani soko haka suka tura kofar dakin ameera suka shiga,tagama fahimtar komai lamarin Yana bukatar addu a shikansa auran anmantar dashi take Yaya dan Allah karkatafi jirani nazo,yace Ina jiranki kiyi sauri kar sadiya tabiyo mu .
Dasaurinta tashiga gurin umma ameera take kwalawa Kira cikin sauri ta fito tana cewa lafiya kywa wannan kira ?
Lafiyar kena kedai zo zasu fita sukaji umma na magana Ina fatan dai bawata maganar zaku dakko minba tace bakomai umma inmuka
dawo Zan Miki bayani yayane Yake kiranta,
A hanya take tambayarta yanayin cikin gidan yadda taganshi it's abinda tasani tagaya mata Dan batasan komaiba Akan gidan,
tace to Kuma sai Naga kamar Yaya baisan dazamankiba a gidannan amma fa karki damu abubuwane danake tinaninsu nakeson tabbatarwa hadin kanki Kuma shine zaisa komai yatafi dai dai sannan Kuma sai kinsa juriya zadai mutattauna bayan mundawo amma kidan jinkirta Inna Shiga dakamar mintina saiki biyo bayana,
.sunci gaba datattaunawa anan take sake fahimtar duk wata hira da zatayi mar indai ta umma ce baya bukatarta,
Suna cikin hirar ne ameera tayi sallama tashiga da tsokana take amsa sallamar tana matar yaya sai yanzu Kika ga damar biyo bayana gashi har Ina Shirin tafiya to ai sai kizo kiyimin taki taryan Naga wadda tafi it's Taran bako inba hakaba insa yakaro wata .
Dariya sukayi gaba daya sannan ta durkusa har kasa tagaisheshi amsawa yakeyi Yana me Kare Mata kallo yace ameera yaushe kikazo gidan ankwan bitu ba,a haduba ya Kika barosu take kowa lafiya,
. Mardiyya ce tace yaya bakasan ameeran bace amaryarka kake tambatar Ina tabarosu ai tadade rabonta dasu,
Ya rike baki Yana murmushi yace kice kanwatace amaryar aini bansan was aka auraminba wallahi namanta dazancan auran kwata kwata ,
Sukayi dariya amma Banda ameerar wadda Tasha kunu kamar tafashe ,tofa Yaya kayi laifi wayake mantawa da amaryarsa gaskiya yau kazo kabada hakuri ko aci tararka,
Dariya yakumayi yace kaina bisa wuya na amarsu Ina Nan tafe in anjima zanzo bikoe ayimin afuwa kannawane ba dadi sai a hankali.
Itako sadiya sanda suka fita ranta inyayi dubu yabaci tinani take inhar tabari yarinyarnan tana Mata katsalandan tokuwa aikinta akwai gyara akai , shewar mutanan gun e tadawo da ita daga tinanin datake sukace Anya ko sadiya haka kikabar mutumin nan wannan bada umarni haka sai kace da da uwa bamason muna muna agaya Mana sirrin,
Ta juya Kai cike da damuwa tace in ma wani abunne ai gashinan nasami wata tana Shirin rusamin amma zataci ubanta Zan maganinta haka daibsukayi ta tattauna wa daga bisani suka tashi suka tattafi sai yazama daga sadiya sai yayarta rahane matsowa tayi kusa da it's kamarunafu ci tace kenima fa tin randa Naga sun furgita da sukaga juna nayi wannan tinanin kodai wani abun kikasa akayi musu,
Tayi dariya tace ke badan nasa anyi min aiki akansu ba ai dakema bakizo gidan kin dandali arzikin da kike cikiba yanzu da wannan sittirar daya dinkamiki kusan guda hudu gasuna harda mayafi da baki samesuba nikaina da agida Zan haihu saboda takurarta shiyasa wata amiyata tayi min hanyar arziki
Pls share
*INA BUKATAR COMMENT DINKU NA ROKEKU INHAR KUNASO NACIGABA*
🤝 *DAGA ALKALAMIN* *YAR MUTANAN JINGAU* 🙋
🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀
🤦♀
😨😨😨😨😨😨
🙏 *ABINDA KE* *FARUWA* 🙏
*LABARI DA RUBUTAWA*
*BY*
🤝 *FAUZIYYA AUWALU* *ALIN BABA JINGAU* 🙋
🅿 *22(V)*
🌈 *KAINUWA WRITERS* ✍🏾 *ASSOCIATION* 🤝
Yo amma kinsan haka Kika barni gida zaune bawani dan temako da Zaki bani Nima inkoma gidan nawa mijin kinaganin inda nake fama da babanmu nazame mata kamar kishiya Kan zaman gidannan danake..
Takatseta tare tintsirewa da dariya tace anti Wannan gigicewa haka kwantar da hankalinAInsha Allah gobe aminiya zata dawo tayi tafiya ne ai da tini kunsan juna,
zata rakaki kuwa indai wannan teacher dinne kamar kinkoma kingama kikuma jashi inda ranki keso,
Baishiga takofar dazata ganshiba sai yashigata kofar baya tinani yakeyi wai meyashiga kansane sai yayi wasu abubuwan sai yazo yayi ta tinanin hujjar yin hakan,
ummansa ce ta wado Masa da sauri ya Mike domin zuwa gunta jiyayi wani abu ya gilma takansa Wanda yasashi dafe kannasa Zama yayi yarasa meke Masa dadi wani abu yaji yatokare Masa kirjinsa dafe gun yayi Yana Kiran sunan Allah a hankali yaji Yana samun sassauci. ajiyar zuciya yasaki da yatuno wai ameeara umma ta aura Masa amma har kawo yau wai baije yaga kalar amaryarba sai da mardiyya tajashi gun dazu tsaki yayi yace yo Ni inbanda ma ta tinamin ai shaf namanta rigingine yayi Dan yafijin dadin tinanin sannan yakara murmusawa yace lallai yau ango nake akwai shagali kenan ,
tinawa yayi da sadiya zumbur ya Mike Yana lekenta ta taga kwarjini takara yimasa wani irin tsoron tane yadirar Masa sai wata uwar zufa datake kwaranyo Masa.
Yanzu umma kinsan da wannan matsalar Amma baki taba gayanba kema ameera aikya bugo kisanar Dani kome akwai Koda bazanyi maganin matsalar ba aikwaji dadin kunsanarwa da wani,
To mardiyya abinda yafi karfinka ai sai kamarshi wasa abin ya wuce tinanin me tinani sai dai Mika Al,amarin ga Allah Dan Haka karki tada hankalinki muyi addu,a akwai Allah akwai kuma lokaci dukkanin abinda mutum yayi domin kansa kedai fatana kirike Taki uwar mijin kamar itace ni Inka mutunta uwar wani kaima sai amutunta taka Kuma shi tsoho daraja ce dashi balle wannan zamanin bakayi ba ma anmaka Allah dai yasa mudace.
Hajiya Taji jiki gaskiya domin masassarar datayi takwana biyu tabata wahala Haka nasha jinyarta harta warke Dan makaranta ma sai da nadau excuse din kwana biyu saboda inkula da ita taji Dadin hakan shima megidan yaji dadi sosai ,
A wannan kwanakin datayi kawai Ina lallaba wane tasami lafiya nikuma insami nutsuwa domin kamar akwai son zuciya cikin lamarinsa yadda nake fama da dawainiyyar yarana inbasu da lafiya nice siyan magani nice sewa yaro abinda zaisa abakinsa yaji dadi Kai duk wata hidima ta asibiti nice sai dai yayi min godiya,
to Haka ma yabarmin hidimar hajiya ko kudin mota Bai bamu ba Dana matsa masane ma ya dakko dari biyu yace muyi kudin mota abinda nasan yahadani dashi kenan shiyasa nakeso tagama warwarewa nadau mataki Dan bazai yiwuba da innayi hidimar gida nasan Babu ne yanzu ko nasan akwai sauyi ba abinda ma Yake bani mamaki sai inzai bani kudi da yakan juyemin abinda Yake dashi har sai nadau wani abin aciki nabashi yayi kudin mota yanzun ko inzai bani kudi sai yashiga bandaki ya kirga sabida karnaga yawan kudin dake gareshi wato nidin Yake neman ya manta alherina gareshi,
ko Kuma inyaga nagane shi sai yajuya bayansa sannan ya kirga abinda zai bani badai zai Bari naga kudinba sabida San zuciya irin nada namiji Dan haka nakeson nadau mataki danni bazan jure irin wannan ba yazama kamar cin fuskane agareni to meyake nufi shinakeso nafara ji sannan Kuma into Masa tini da nauyin dayake kansa bani Allah yadorawa nidin wani yanki ne natemako da aka sani gareshi Dan Haka lallai komai sai an sauya Nima macece bakuma matar wahala ba inda najure yanzu Nima gashin kaina nake nema.
pls share
*INA* *BUKATAR COMMENT DINKU NA ROKEKU INHAR KUNASO NACIGABA*
🤝 *DAGA ALKALAMIN* *YAR MUTANAN JINGAU* 🙋
🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀
🤦♀
😨😨😨😨😨😨
🙏 *ABINDA KE FARUWA* 🙏
*LABARI DA RUBUTAWA*
*BY*
🤝 *FAUZIYYA AUWALU* *ALIN BABA JINGAU* 🙋
🅿 *23(W)*
🌈 *KAINUWA WRITERS* ✍🏾 *ASSOCIATION* 🤝
toke yanzu duk hakurin da baiwar Allahnnan tazo tabayar bemikiba mekikeso Kuma tayi miki Aiko bada gaske take ba kyayi hakuri kikoma kigani insun tuba da gaske Kuma ita rayuwar aure tagaji haka bakowa ce, mace ce take dacewa da abinda takeso ba Kota dace din akwai kalubale dasuke biyo baya ,
Umma wallahi tariga tace batasona gara muhakura Allah yahada kowa da rabonsa na alhairi shikansa tayata yakeyi abinda takemin Dan Haka kikyalesu kawai zasuga in inada Rana in ma banida ita zasu gani,
Haba zainaba Aiko sungama ganin ranar da kike da ita tinda gashi ita takasa jiyyarsa har tana kukan kitemaka Mata ki koma kodan kiyi jiyyar mijinki Aiko ranarki tagama fitowa,
Kije gidan aure ne, ai kome Kika ci Karo dashi ladane, lada kuwa me tsoka, Kuma dama masu iya magana sunce fini da gidan uba nafiki da gidan miji , fini da gidan miji nafiki da gidan uba ,
Dan Haka kitattara kayanki kikoma nikuma zanbiki da addu,ar neman sa,a ta gidan aurenki Allah ya doraki akansu ko Dan kuzauna lafiya,
Baki ta zunbura tace to ni nace yaje ya karye dazasu ce sai nayi jiyyarsa wayasani ma ko alhaki nane Allah ya Kara ma da ya karye din,
Alhakinki dan kunyi fada Kuma ya karye sai kice alhakinki ne ,
Wallahi alhakina nane banace Miki har marina yayiba ,Niko danaji zafi nace Allah yasakamin ko a tsokar jikinsane Aiko gaba yakuma wallahi inkarayi Masa wata addu,ar.
Hannu tashiga tafawa , tace niyasu dama bana hanaki yiwa mutum irin wannan addu,ar ba dama baki denaba Aiko ko kinaso ko bakya so sai kinyi jinyarsa tinda ke kikaja masa Allah yashirye ki yarabaki da wannan baki naki,
Haka ta tattarata tasa aka rakata gidan ranta baisoba Dan ita tagama da Yan kayansu, tana da hakuri da juriya amma inta botsare abin bakanta,
Sanda sukaje gidan dagashi sai baban ,
tana ta kiciniyar dagashi zata dorashi afo takasa,
dama takan leka waje ne inyana bukatar temako irin wannani tasami irin masu zaman majalisa su temaka Mata tosuma ganin tana damunsu yanzu sundena zama shiyasa yanzu Kan ta daga shi sai ta wahala,
Sannu suka Shiga yimasa itako dauke kanta takuma yi gefe Saida kanwar babanta tace tashi kitemaka Mata Mana Kika zuba musu ido bamu mukulin dakinnaku sai mu Shiga kafin kifito,
Mika musu nayi suka tafi domin bude dakinnawa,
Niko Dakar cikin bacin Rai nadoshe su duk yarame sai ido dama shi Abu tibar kalla gwaragwara,
Haka badan naso ba nakama matashi ta zare Masa wandon nikuma na turo Mata fodin ta daidaitashi ,
Ruwa ta tafi ebowa na tsarki ta barni dashi,
Ahankali ya kalleni yace Zainab abin har yakaimu ga haka kikasa yimin sannu da jiki,
O sannu ko to madallah,
dakasamu nadawo kaga in matsamin zakayi da magana wallahi sai na koma dama tilas akayimin nadawo sai kace Nina karyaka,oh Ashe fa alhakinane gara ma Haka wallahi duk Randa kakuma sa hannu ka mareni adduar da zanma tafi wannan ,
Na murguda Mai baki,
Kallonna kawai Yake yace Zainab ko me nayi Miki yakamata kiduba halin da nake ciki ki tausayamin ninasan abinda nakeji inhar wannan radadin danakeji alhakinkine toko nadandana kiyi hakuri badan niba kuskurene nariga nayi bazan sakeba lokacinma sharrin shedanne amma nasan bakida laifi duk laifinane Dana baba,
Hhh Allah sarki Ashe kasani katake ai shikenan inkun gyara magyara inba hakaba daidai nake Dana bar gidannan inyaso wadanda kake kaiwa zumar taka sai suzo ku hadu kuzauna agidan ,
Tashi nayi natafi dakina Daman a dakinta take jiyyar tasa tararwa nayi suna Shirin tafiya Nan mukayi sallama dasu suka tafi nikuma na haugyaran dakina inajinta tana kwalamin kiran inzo ayi Mai tsarki Niko nayi banza da it's nabi lafiyar gado,(illar takura kenan Tin mutum naganin mituncinka har sai kakoma dakai da Babu duk daya wasu surukan kenan ).
Damisalin karge takwas ne nadare dukkaninmu muna zaune atsakar gida har da hajiya wacce take cikin nishadin kasancewarta da jikokinta cikin koshin lafiya gefe daya nanace da su saddiku zaune tana koya musu homework can gefe shimfidar babansuce wacce najere Masa kayan abincinsa akai har da su lemo na hada Masa daga gefe cikin abincin kuwa dankwa leliyar jelace takifi tare da kwai guda daya aciki ,nikuma tawa shimfidar tana tsakanin tasa data hajiya,
Suna cikin homework dinne sun bude littafin maths sai ga takarda tawado daga ciki aminullahi ne yayi sauri ya dakko🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀
🤦♀🤦♀
🤦♀
😨😨😨😨😨😨
🙏 *ABINDA KE FARUWA* 🙏
*LABARI DA RUBUTAWA*
*BY*
🤝 *FAUZIYYA AUWALU* *ALIN BABA JINGAU* 🙋
🅿 *24(x)*
🌈 *KAINUWA WRITERS* ✍🏾 *ASSOCIATION* 🤝
Aminullahi yayi sauri ya dakkota yace ,laaa gatakardar da aunty ross