Zafin Rana Book Compelet Novels By Aysha Alto

Author :  Aysha Alto Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   24 / 28

69K to 72K   out of 81.6K words

 in mukai fa?

Yace  in kukai abinda nace zan barku a matsayinku sannan zan yafe muku.

Kallan zargi waziri yama Junaid dan bai yadda da wannan maganar ba.

Junaid ya kalleshi yace  Ruwanka ne ka yadda ruwanka ne kaki yadda sanda karkai tunanin nazo

"nan a san rai nane bayan nasan laifin da kuka aikata, zansa ido inga abinda zakai. "

Yana kaiwa nan ya mike ya fito bai jira ko Waziri ya tattaro tunaninsa ba.

Yana fita waziri ya zauna yai shiru.

********

Ana kawoma Abdulsalam karin kummalo ya kalli Jakadiya dake basu umarnin inda xasu ajiye

yace  Jakadiya a aika a kiran Waziri.

"Da sauri tace to, kallo daya zakama Sarki kasan yana cikin wani hali ko dan yanda yanayinsa gaba"

daya ya canza.

"Sam ya kasa cin abinci har dan aiken ya dawo, sanar dashi yai wai Waziri baya gida, nan ya aika a"

"kira Shamaki, sai dai shima akacemai wai Shamaki bashida lafiya, bai hakura badai ya aika a kiramai Galadima, nan ma aka dawo akacemai wai ya je ganin gona."

"Nan ya fahimci zuwa ne basa sanyi wanda hakan ya kara daga mai hankali, dan har tsoronsa ya"

"fito karara dama yana tunanin in su Waziri suka bi bayansa tabbas zai samo mafita, wato suma sun yada shi kenan ko me?"

Hankali a tashe yace  Akira Azeema.

"Kallansa dan aiken yai yace to, haka nan ya dawo ya sanar dashi wai tana bacci."

"Gaba daya Abdulsalam ya fara neman zaucewa, yace  banda kowa kenan ko me? "

Dan aiken yace  ko na kira Hajjo?

Hajjo? Me zatamin wannan?

"Tausayinshi ne ya kamashi ya mike zai fita, Abdulsalam yace  kiramin hajjo. "

"Nan ya fita, Hajjo na zaune ranta duk a dagule, ga Zubair a gefenta, nan aiken Sarki yazo mata."

Mamaki ne ya kamata da sauri ta mike ta zura alkyaba dinta ta fito.

Sarki sai safa da marwa yake a daki haryanzu ko abincin da aka jera mai bai kalla ba.

"Hajjo ce ta shigo, mamaki ne ya kamata yanda ta ganshi duk a rikice."

Tace  Takawa mai ya sameka?

"Abdulsalam ya juyo da sauri, hannunta ya kamo ya zAunar da ita, kallanta yai yace  Hajjo ki"

"taimakamin, gaba daya na rasa yanda zan shawo kan matsalar dake gabana. "

Matsala? Kai da kake neman ba Dan Azeema mulki saboda soyayya wace matsala ce dakai?

Abdulsalam ya kalleta yace  ke yanzu a yanda nake din nan kina tunanin har zan iya ba ko dana

na cikina ne mulki balle dan da ba nawa ba?

Cikin rashin fahimta Hajjo tace  bangane ba?

"Kallanta yai yace  Junaid ne duk ya shirya wannan abin, kuma a gobe yake so ya kwace mulkin"

"nan, sam na rasa yanda zan shawowa matsalar. "

Wata dariyar rashin yadda tai tace  har Junaid yakai girman da zai saka kai abunda bakai niyya

ba?

"Abdulsalam yai shiru, kallan zargi tamai tace  ko yasan wani sirrinka ne? "

Kallanta yai yace  kema kinsan sirrin nawa ai.

Tace ni? Ta tambayeshi cikin rashin fahimta.

Kallanta yai yace  Yayana Zubair.

Baki ta hangame ta bude tace  da gaske kana da hannu a ciki? Amma sanda na tambayeka

kacemin bakada hannu harda min fada.

"Shiru yai, can yace yanzu duk ba wannan bane matsala yanda zan kwaci mulkina na koreshi ko"

na halakashi nake nema.

Mijin yar taka?

Kallanta yai yace  da dan me na bashi ita? Ai dan kome ya faru ya yafemin ne a matsayin

mahaifints.

Hajjo ta kalleshi tace  da can bakasan dani ba sai data keabe muku kai da matarka ta so?

Sannan yanzu bani ba neman ruguza rayuwar yarka kake?

"Yace  shawara na kiraki muyi, kinsan dai in komai yai daidai Zubair danki ne zai gajeni wannan"

alkawari na miki.

Kallansa tai tace ka tabbatar?

Da sauri yace eh

Tace ka kwace yar ka kace sai ya hakura da abinda yake shirin yi zaka mai data.

"Wani kallan takaici ya mata dama can shiyasa bai san yin shawara da ita gaba daya bata da lissafi,"

a kufule yace  dama can santa yakeyi? Da har in muka dauketa xai bar abinda yake?

"Tace  eh mana, ka bari na gwada ka gani, ai namiji ba sai yana san mace kadai ba da zaran ya"

"dandana zumarta magana ta kare, nasan yanda na shirya  yata. "

Cikin takaici yace  to jeki.

Mikewa tai tace  zan aiwatar yanzu zakaji sakamako mai kyau. Haushi yasa ma bai kulata ba.

"Jakadiya ce ta shigo da sauri bayan fitar Hajjo ta zube tace  Takawa, sarkin Zazzau da sarkin"

Kano sun aiko tayaka murnar ba surukinka mulki da zakai.

Idanu ya zaro yace  mene?

Jakadiya tace yanzu dakarun dake kula da kofar gari suka aiko a sanar yanzu zasu shigo kofar

garin.

Jikinsa ne ya kaure da rawa.

Wannan yaro anyi tsinane

******

Ayusher

* ZAFIN RANA *

......................

*Hask e  W rit e rs Ass o ci a ti o n*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*K A$ f[ fV *

{45}

Hajjo ta fito daga bangaren mai martaba kai tsaye ta nufi bangaren Zeena.

"Zeena na zaune ta gama cin abinci kenan, haka kawai tun jiya takejin dadi, a kalla tasan Junaid ya"

"damu da ita, a hankali takai hannunta kan kafadarta inda ya dafa ta jiya, wani lalausan murmushi ta sake cikin jin dadi."

"Fure ce ta kalleta tace ""Gimbiya kalau dai ko?"""

"Kallanta Zeena tai, Fure tace ""naga kina dariya ne kamar "" sai kuma tai shiru."

"Zeena ta kalleta cikin takaici, tace ""wlh fure na kusa koraki gun Hajjo can kika fi dacewa ba nan"

"ba, wato nice mahaukaciya kenan?"""

"Da sauri Fure tace ""Gimbiya ba haka nake nufi ba wlh."""

Zeena tace ko?

Da sauri tace eh.

"Alama ta mata data matso, da sauri ta matsa kusa da ita da jan gwiwa."

Zeena ta daga hannu da sauri Fure ta runtse ido tana jiran saukar mari.

"Jin shiru yasa ta bude ido daya kafin ta bude dayan idan, Zeena tace ""nama fasa aikaki gun Hajjo"

"hada kayanki ki koma gun Binta, can itace zata iya da haukarki."""

"Fure tace ""tuba nake Gimbiya wlh bazan iya zaka gun kowa ba in bake ba."""

"Hannu ta kara dagawa, da sauri Fure da sake rufe ido, Zeena tasa hannu ta dungure mata kai tai"

"baya, tace ""tashi kije can waje cikin rana ki tsaya, nama fahimci duka da hannu batawa kaina lokaci ne."""

"Fure tace ""Haba Gimbiyata, kin manta yau kwananki ne? Ai yanzu zamu fara shirin kwana."""

"Murmushi Zeena tai tace ""kin wanke kanki, me zamu shiryama Ya Junaid yau?"""

Fure zatai magana Hajjo ta banko kofa.

"Baki a sake Zeena ta kalleta, Hajjo tace ""tashi."""

Tashi? Wa? Ni?

"Hajjo tace ""a'a ni."""

"Zeena tace ""meya kawoki dakin sirikinki? Bayan ko gaisheki baizo ba tukun?"""

"A kufule tace ""suruku, kin tashi kin fito mun tafi ko sai na sa an ja ki?"""

"Zeena fuskarta dauke da mamaki tace ""wai ni za'a dauka ko kuwa wata? Na tabbatar kinsan halina"

"da abinda zanyi da wanda bazan ba."""

"Hajjo tace ""yau kuwa dole kiyi abinda nakeso, kin tashi mun tafi ko sai na ci mutuncinki, aure ne"

"na raba ya kawo miki takardarki, ya dau uwarsa da matarsa su koma kauye."""

"Da fuskarta alamar mamaki ta fara nunawa kafin ta sa dariya tace ""lalai Hajjo ni yau Allah yasa"

"lfy kike?"""

"Kin wuce ko kuwa?"""

"Gyara zamanta tai ta kalli Fure tace ""dubo in Ya Junaid na nan kece mai Hajjo tazo zasu gaisa."""

"Fure data tsaya a kofa tun zuwa Hajjo tai waje da sauri, Hajjo tace ""uban wa yace ina nemanshi?"

"Balle har mu gaisa?"""

Zeena bata ce mata komai ba sai kallan gefe ma datai.

******

"Binta ce ta gaisheda Sabisu cikin sha'awa ya kalleta yace ""Masha Allah kece matar Yariman?"""

"Binta ta kalli Junaid cikin kunya sannan tai kasa dakai."""

"Sabisu yace ""kai lalai Yarima kayi sa'a na tabbatar da Sarki nadarai da ya kasance mai alfahari da"

"zabinka."""

"Junaid ne ya kalli Binta wace ganin bai dawo yaci abincin safe ba yasa ta bi bayansa yace ""nayi"

"laifi amim afuwa."""

"Dan kallansa tai ta kasan ido tamai alama da zata wuce, dan wata kunyace ta rufeta datasan"

akwai babban mutum a can da bazata taso ba.

"Junaid yace ""Baba tun kafin inyi laifim da za'a dakeni bari naje."""

"Dariya sosai Sabisu yai yace ""waya isa tabaka Yarima? Ko 'yarnan?"""

"Binta tace ""zolayarsa ne wlh."""

Da sauri ta mike cikin kunya ta fita.

"Dariya Junaid yai, Sabisu cikin sha'awa ya kalleta sannan ya kalleshi."

"Junaid ne ya canza yanayin fuskarsa yace ""Baba kana tunanin abokin naka zai kai takardar"

"wasikar Gayyatar?"""

"Sabisu yace ""ai inaji yanzu ma ya kai, amma me kake nufi da aika takardar gayyata dakai?"""

"Junaid yai wani murmushi sannan yace ""daga jiya zuwa yau kana tunanin ya isa masarauta"

"nawa?"""

"Sabisu yace ""matsalar dansa ne ba shi din bane, amma shi a lokacin Sarki Zubair in aka aikeshi kai"

"sako kwana daya yakeyi ya je masarauta hudu."""

"Junaid cikin jinjina yace ""masha Allah, to d'an nasa musamai ran daga jiya zuwa yau yaje uku"

"kenan?"""

"Sabisu yace ""eh."""

"Azi dake bakin kofa yana neman izini ne Junaid yace ""shigo."""

"Nan Azi ya shigo ya gaisheshi, sannan yace ""Yarima ance Masarauta biyu na kano da Zazzau sun aiko da sako kyaututuka da taya murnar Murabus din sannan da jinjinama Sarki, wasikar yanzu za'a shiga da ita fada."""

"Junaid ya kalli Azi yace ""Alhamdulila komai na tafiya yanda ya dace."""

"Kallansu yai yace ""bari naje na dawo."""

Mikewa yai ya nufi bangaren Binta.

Tana zaune akan kujera ta cika ta batse ya tura kofar tare da dan gyara kafadarsa.

"Kauda kanta gefe tai cikin nuna alamar fushi, zama yai kusa da ita sannan yadan bige kafadarta"

da kafadarsa.

"Kara kauda kai tai, turata yai daga inda take ta matsa ya kara turata, mikewa tai zata bai gun, da"

"sauri ya maida ita ta zauna yace ""Bintalo na tuba."""

Kara hade fuska tai.

"""Laaaa har na tuno wata rana, muna zaune a waje ana hira cikin hasken farin wata, wata ta. """

"Da sauri ta toshe mai baki tace ""Na hakura ya isa ba sai ka fadi me nai ba."""

Yana dariya yana kokarin yin magana bakin nasa a rufe.

"Dan cizo ya mata a tafin hannun nata, sakeshi tai tana cewa ""yaya Allah na hakura."""

"Yace ""inaaa ai sai na karasa."""

Batasan sanda ta sake rufe bai baki ba ta daddane shi da jikinta tana girgiza mai kai.

Idanunta yake kallo yana dariya sannan ya daga kai alamar ya daina.

"Sakeshi tai tare da cewa ""Allah Yaya gaskiya ka gama dani, ka gama sanin komai nawa ina yarinya"

"nasan haka zakai ta zolaya ta."""

Dariya yai zai sake magana sukaji ana magana a waje.

Baiwarta ce ta shigo ta sanar da ita sakon Fure.

"Junaid ne ya kalleta fuskarshi dauke da mamaki, kallan Binta yai yace ""bari na dawo yanzu."""

"Bangaren Zeena ya nufa, Hadimansa na biye dashi."

"Yana kokarin shiga yana Hajjo rike da Hannun Zeena ita kuma tana zaune, ta rike kujera da daya hannun."

Hajjo ko da ganin Junaid bai sa ta bar abinda take ba.

Zeena na ganin Junaid ta warce hannunta da karfi ta nufi kusa da Junaid ta tsaya a bayansa tare

da rike rigarsa ta baya.

Hajjo ya kalla alamar karin bayani.

"Fuskar Hajjo a turbune tace ""ka gaida ni ne?"""

"Junaid yace ""jira nake ki zauna."""

"Haushi ya kamata tace ""ba zama nazo ba tafiya da yar Abdulsalam zanyi tunda bakaga darajar yarsa ba kake neman wulakantashi."""

"Kallansa Zeena tai cikin rashin fahimtar kalaman Hajjo, Junaid ne ya kalleta yace ""babu"

"wulakantace a duniya sai wanda ya wulakanta kansa, sannan duk wanda ya wulakanta mutum da saninsa to lalai cikin dayam biyu ne kodai wanda aka wulakanta baisan kanshi ba ko kuma bashida daraja."""

"Hajjo ta cika da bacin rai tace ""bamu 'yarmu."""

"Junaid ya kalleta yace ""gatanan in zata biki."""

"Da sauri Zeena tace ""Ya Junaid?"""

"Sannan ta kalli Hajjo tace ""ba inda zani."""

"Junaid Hajjo ta kalla tace ""bata takardarta, na tabbatar inka saketa dole ta tafi."""

"""Takarda?"""

"Hankali Zeena ne ya tashi tace ""Hajjo baki da. """

Kallan da Junaid ya mata ne yasa tai shiru ranta yayi matukar baci.

"Junaid yace ""wannan kuma banga mai sani inyi abinda banyi niyya ba."""

"Sannan ya sake kallanta yace ""ki huta lafiya."""

Ya juya ya fita.

Hajjo kam kiris take jira ta fashe da alama.

*******

"Isowar masu aiken sarakunan nan ba karamin hargitsa kwakwalwar Abdulsalam akai ba, yana"

"makale a kasa a lungun gado kamar zautace yana cewa ""a'a ba wanda ya isa ya kwacen mulki."""

Nace sai mugani ai

* ZAFIN RANA *

......................

*Hask e  W rit e rs Ass o ci a ti o n*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*K A$ f[ fV *

{46}

"Gaba daya Azeema banda kwanciya a daki ba abinda takeyi, zazzabin ya barta amma abinda ke"

"zuciyarta ya kasa sakinta, a duk sanda ta tuno abinda ya faru sai taji kwalla na neman kawo mata, ba shakka tasan tama Zubair babban laifi amma inta tuna ta bada kofa anyi amfani da ita ne sannan yanzu hankalinta ya kaimata ai shi Abdulsalam din shine ya kaita gun mai maganin, kenan dama ya gama shirinsa?"

Duk sanda ta tuno hakan wani hawaye ne ke zubo mata.

"Barira kam ta rasa abinda ke mata dadi, gashi Azeema tace karta sanar da ko Safiyah."

Inta gaji da kwanciyar ta mike tai tasbihi da hailala.

*******

Gaba daya shi kadai ne a cikin tangamemen kilisarsa yana zaune a lungu hankalinsa a tashe.

"Jakadiya ce ta sake shigowa tace ""Takawa ana jiranka a fada."""

"Abdulsalam ya kalleta hankalinsa a tashe, sannan yace ""to."""

Da kyar ya daure hadimansa suka shigo suka tayashi shiryawa.

Junaid yana zaune falan Binta amma gaba daya hankalinsa nakan Azi akan ya dawo ya sanar

dashi ko Sarki ya shiga fada.

"Binta ce ta fito daga daki ta kalleshi tace ""Yaya!"""

"Kallanta yai yace ""zuwan zakiyi?"""

"Tace ""tunda kai bazaka ba gwara ni naje, dan Allah yaya kazo muje Allah Umma batada lfy."""

"Yanda ya kalleta tasan bazashi ba, fuska ta hade tace ""shikenan."""

"Ta fita, murmushi yai tare da kara jiran Azi."

Binta ko minti biyar da fita batai ba Azi ya dawo.

Junaid na ganinshi ya mike yace  ya?

Azi yace ya fito daga sashensa.

Nan Junaid yace muje.

Tare suka fito hadiman sa suka bi bayansa suna tafe ya kalla Azi yace  Zeena fa? Tabi Hajjon?

Yace  a a tana bangarenta.

Su Waziri fa?

Sun iso yarima.

Junaid ya jinjina kai sannan yace  Zubair fa?

Haddashi?

Junaid yadan kalleshi kadan yace  haddashi.

Nan Azi ya amsa aike sannan ya juya.

Junaid fada ya wuce daga nan kai tsaye.

"A fada kuwa Sarki na zaune bayan ya amsa gaisuwa ne, kallan Waziri yai wanda kansa ke kasa, ya"

"kalli Shamaki shima kansa na kasa, ya kuma kalli Galadima."

"Daurewa yai yace  banyi tsammanin taran gaggawa haka ba, Allah yasa komai dai lafiya. "

Turaki cikin mamaki yace  Ranka ya dade ai mu sako aka iso mana dashi akan kana neman

nemanmu a fada.

"Nan kowa ya amsa da hakan ne, Sarki yai shiru kenan Junaid ne? Uban me yake nema dashi?"

"Zagi ne ya sanar da isowar Wakilan da aka turo, Sarki ya basu izini cikin dakewa, duk da yanda"

gabansa ke faduwa.

Suna shigowa Zagi ya sanar da isowar Junaid.

Ba Sarki ba hatta su Waziri sai da gabansu ya fadi.

"Junaid ne ya shigo cikin isa da takamarsa, ya gaida sarki sannan ya zauna."

"Wakilai suka kalli Junaid sannan suka kalli Sarki, wakilin sarkin kano ne yace  wannan sako ne"

"daga mai martaba sarkin Kano, tabbas yana kara jinjina maka yace mu tafin masa da ranar yin"

nadin shi da kansa zaizo.

"Sarkin Zazzau ma abu daya ya fada, ajiye kayan kyautar da suka kawoma Junaid sukai sannan suka"

gaisheshi.

Gaba daya Abdulsalam ya kara rikicewa kafafunsa kawai yake matsewa ta cikin kayansa.

"Junaid ya amsa tare da yin godiya, sai da suka fita, Turaki yace  ai Sarki wannan lamari kowa"

"yana bashi mamaki, duk da muma ba san murabus dinka muke ba amma in muka tuna namijin"

kokarin dakai gun yanke wannan hukunci sai musan bakuda bakin magana.

"Nan kowa ya fara tofa albarkacin bakinsa, Abdulsalam ji yake kamar ya saki wani ihu a gun da"

yake.

Junaid ne ya kalleshi cikin mamaki yace  Takawa ina tafe ina fatan Allah yasa ba abinda kake

shirin fada yasa ka taramu ba?

Abdulsalam ya kalleshi me yake shirin yi?

"Zubair ne ya shigo ya zauna, Turaki yace  Mai Martaba badai ? "

Sai yai shiru suna kallan Juna.

Wale yace  Takawa bai kamata ayi abu cikin gaggawa ba.

"Junaid yace  sosai ma kuwa, komai ayishi a hankali, dan Allah ka janye alkawarin nan naka na"

yau zaka ajiye mulkin nan.

"Bai san sanda ya bude baki ba, Waziri cikin tsoron Junaid ya kalli Sarki anya wannan zai barsu"

suma kuwa?

Turaki yace  au yau? Indai Alkawari yai ba yanda zamuyi.

Junaid ya kalli Abdulsalam sannan ya kalli Zubair wanda ya kumbura fam.

"Abdulsalam idanunsa ne suka canza kala, ya daure ya kallesu yanzu kam yasan bashida wata"

"mafita, inba so yake komai ya fito ba, an gama daureshi ta ko ina."

"Wale ne yace  da alama Sarki sauri yake ya baka mulki a matsayinka na sirikinsa kuma dansa,"

yafisan yai jika yana gefe.

Dariya sukai dukansu wanda dariyar ta kasance kamar arsashi ne ya dira a zuciyarsa.

"Zubair ya kalla wanda ya gama bata rai, Junaid ya kalla wanda ya kalleshi shima."

Mamaki me ya kamashi dayaji yace  to Mai Martaba.

"Kafin ya fara tunanin me zaiyi kawai yaga ya taso yazo inda yake ya tsuguna, ya dukufo kusa da"

kunnensa.

"Yace  idan har baka sauka ba a wannan lokacin yanzu kuma, duk abinda ya biyo baya a wannan"

"lokacin karkaga laifin kowa sai naka, ga danka ga fadawan ka nan, kowa yaga mumunan halinka da"

"kake boyewa a cikin fara arka, sannan kar ka manta ina da shaidar laifukanka, kana batamin rai komai xai tarwatse a gun nan. "

Murmushi yai bayan ya dago ya

24 / 28