Chapter 26 Reading Zafin Rana Book Compelet Novels By Aysha Alto Arewa Novels

Zafin Rana Book Compelet Novels By Aysha Alto

Author :  Aysha Alto Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   26 / 28

75K to 78K   out of 81.6K words

Zeena wacce gaba daya hankalinta da tunaninta rabi makan tasan

abinda ke faruwa.

"Hannunta ya kamo ya rike, da sauri ta kalleshi cikin sanyin murya yace  Zeena! "

"Jikinta ne gaba daya yai sanyi sai idanu data zuba mai, Junaid yace  Ga Binta nan, inaso ki kula"

"da ita, kece uwar gida sannan matsayinki a masarautarnan mai karfi ne, yanzu komai na rayuwa zai canza, bakoda yaushe zan samu damar kula daku ba dan haka ina rokonki da ki ajiye duk wani halaye naki da kikasan basu da kyau, ke yanzu uwa ce ga mutane dayawa dolene ki zama abin koyi"

"ga mutane, bazan yadda da sakarci da cin zarafi ba kamar yadda kika saba a baya. "

Hawaye ne suka zubo mata ta daga kai alamar to.

"Junaid ya saketa sannan ya kalli Binta wacce gaba daya jikinta yai sanyi, yace  Binta! Kallansa"

"tai ya rike hannunta yace  kece karama, banasan wani abu daya danganci rashin kunya ko wani batanci daga gareki, duk da nasan halayenki sai dai inaso ki kiyayi kanki daga biyewa mutanen da"

zasu kawo miki gulma da kuma hadaku da mutane.

A hankali Binta ta daga kai alamar fahimta.

Murmushi Junaid yai sannan yace  muci abinci?

Zeena ce ta kalleshi tace  Abba yama laifi ko?

"Yanda tai tambayar ne yasa ya kalleta, saboda tambaya ce da aka yishi cikin shakkar amsar da"

zataji.

"Yanda take kallansa yasa yasan a tsorace take yace  karkisa irin wadan nan abin a ranki,"

"Abdulsalam mahaifinki ne ki daukeshi a fuskar da kika sanshi, nima zan daukeshi a fuskar dana"

sanshi.

Kallanta yai sannan ya kalli Binta yace  Bismillah!

***

Ayusher

* ZAFIN RANA *

......................

*Hask e  W rit e rs Ass o ci a ti o n*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*K A$ f[ fV *

{49}

Kasancewar ranan kwanan Zeena ne bayan sun gama cin abinci Binta ta musu sallama ta nufi

sashenta.

"Zeena tasa su Fure suka kwashe kwanuka, kallan Junaid tai wanda yasashi kallanta yace  me"

kike san cewa?

Tambaya nake sanyi kuma bansan ta yanda zanyi ba? Kasan haka na taso magana ina fadarta ne

"daga raina, sai dai yanzu nasan dole ne na dinga sanin abinda zan fada kafin ya fito daga bakina. "

Cikin jin dadin kalamanta yace  menene?

Idanunsa ta kalla wanda ke mata kwarjini ga so da take masa har cikin jikinta tace  Hajjo 

"ta kasa kuma karasawa sai kasa da idanunta datai, jitai kwalla tana neman zubo mata, haka kawai"

jikinta ke bata laifin Abba mai karfi ne tunda har ya iya ajiye mulkinsa saboda shi.

Idanunta a runtse tana kokarin maida kwallarta ne taji hannunsa akan fuskarta gaba daya jikinta

"ne ya amsa, a hankali ya dagota ta kalleshi, da kyar ta kakaro murmushi ta mai wanda suka kara bayyana kwallarta dake neman zubowa, yanda ya zuba mata ido ne yasa kwallar suka gangaro a kan hannunsa."

"Idanunsa ya lumshe sannan ya sake kallanta, murmushi ta sake yi na dauriya tace  Yaya na sani"

"ni mai laifi ce, ma taso ba ruwana da halin da wani zai shiga a dalilina, wannan banzan halin nawa ya ja mutane dayawa sun shiga wani hali ciki hadda kai, banda bakin da zan nemi ka saukaka ma"

mahaifiyata da mahaifina. 

"Wasu kwalla ne suka sake gangarowa akan hannunsa, wannan lokacin shine karo na farko dayaji"

"Zeena har ransa, ya aureta ne saboda burinsa ma auran Binta, san Binta a jininsa yake tun baisan kanta ba take da babban matsayi mai karfi a ransa, sai dai a wannan lokacin ya fahimci Zeena ta samu guri a ransa, dan tabbas tausayinta yakeji sosai, ya sani yanzu shi kadai ne da ita, dole ko dan haka ya boye abinda mahaifinta ya aikata in ba haka ba mutane ma kinta itama zasuyi."

"Hannu ta dago tana neman share hawayenta, hannunta ya rike da daya hannunsa, jitai zuciyarta"

"na kara raunana, kallansa tai tana san sake magana kuka ya kwace mata."

"Jawota jikinsa yai ya rungumeta, sai datai kuka sosai sannan ta daina, ba tare da yace mata"

"komai ba, sai data gama sannan yace mata  Karki damu komai zaizo da sauki insha Allah, sannan in har kika canza halayenki komai naki zai canza, kada ki manta na fadamiki kece ido na nacikin"

"gida, dole ne ki dinga sanin abinda zaki dinga yi daga wannan lokacin. "

Kai ta daga tana kwance a jikinsa tace  insha Allah bazan taba baka kunya ba.

"Murmushi yai, dagowa tai a hankali ta kalleshi sannan itama tai murmushi tace  nagode da ka"

bani dama.

"Mikewa yai sannan ya mika mata hannunsa, wani irin dadi ne ya kamata ta mika masa nata"

hannun cikin wani irin jin dadi da ita kadai tasan yanda takeji.

"Hannunta ya kama suka shiga daki, a bakin gadan ta zauna cikin kunya, tana cewa  yau na fara"

shigowa dakinka.

"A hankalinya taka zuwa inda take ya zauna a gefenta, hannunsa dataji ta ratsin cikinta ne yasa ta"

dan rike numfashinta tare da saukeshi a hankali.

Kansa ya sako ta kafadarta yace  garin ya ya?

"Gaba daya ta kasa magana saboda wani irin yanayi data tsinci kanta a ciki, dan juyowa tai ta"

"kalleshi, hannu yasa yai baya da ita a hankali ta kwanta akan gadon, idanunta na lumshe sai gabanta dake wani irin faduwa."

Bakinsa ya sa a cikin nata................

**********

Washegari!

"Cikin tsananin kunya ta tashi, bakowa a dakin hakan yasa ta dinga tuno abinda ya faru jiya tana"

"dariya tare da rufe fuskarta, da alama da sukai sallar asuba tare ta koma bacci lokacin ne ya fita."

"Mikewa tai zuciya daya, jin zafin datai ya ratsa ta ne yasa cikin kunya ta koma ta kwanta."

Junaid kam bayan ya gama karatunsa yana ganin gari yayi haske ya mike ya nufi bangaren

Azeema.

"Gaba daya ba kowa a hanyar dan duku dukun safiya ne, ita kanta Azeemar tayi sallah kenan"

"tadan kishingida a inda ta kwanta din, barira ce ta leko ta sanar da ita isowar Junaid."

"Mamaki ne ya kamata matuka, jitai baccin idanta ya ware ta kalleta tace  ya shigo. "

"Da sauri ta gyara zamanta, gabanta na faduwa."

"Junaid ya shigo ya zauna sannan ya gaisheta, kallansa tai cikin wani irin yanayi mai wuyar"

fassarawa tace  Junaid!

"Kallanta yai bai amsa ba, murmushi tai tace  banyi tsammanin ganinka ba. "

"Fuskarsa a hade take babu alamar fara a a tattare dashi, kallanta yai yace  nazo ne na sanar"

dake abubuwa guda biyu.

Jikinta a sanyaye ta kalleshi tace  inaji!

"Nasan kinsan abinda ya faru kin kuma san jiya Sarki ya ajiye mulkinsa, daga yau har zuwa sanda"

"xa ai nadi bazan sake cewa komai ba, sai dai ina so kisan daga wannan lokacin zan yanke hukunci akan abinda kika aikata a dalilin san zuciyarki."

Azeema ta daga kai cikin dana sani tace  nagode Junaid.

Bai amsa ba yace  mijinki nace ya bar masarautar nan shida matarsa yace sai dake zai tafi.

Fuskarta ta hade tace  ni?

"Junaid ya mata kallan eh, haushi ne ya kara rufeta tace  zan dau matakin wannan, ma tabbatar"

"wannan me kadai abinda zan iya na taimakeka, ko da kuwa hakan ya kasance na bi shi ne to lalai"

zan tafi dashi dan samun sauki da kwanciyar hankali a masarautar nan.

Kallanta yai yace  Ta yaya kika bari san zuciya ya rufe miki ido? Kinsan yanda nake ji a duk sanda

"na sa abinci a bakina? Ina tuna ina ci ne a maimakon mahaifina, ko me nakeyi abinda nake tunani"

"kenan, taya a cikin mutanen duk duniya ace ke? Ta ya.  "

Idanunsa ya runtse cikin takaici.

"Azeema ta share ta kasa cewa komai, idanunsa ya bude yace  ina sauraran yanda zaki sa ya bar"

masarautar nan.

"Kallansa tai cikin wani yanayi, mikewa yai ya mata sallama ya fita."

"Da kallo ta bishi har ya fita, tace  Abban Zubair da ace kana da rai na tabbatar da sai kafi kowa"

"alfahari da yanda danka yake, wannan shine halin cikaken Sarki, karya kuskura ya karaya kar kuma"

ya ragawa duk wani mai laifi koda kuwa mahaifiyarsa ce.

Murmushi tai tana mai jin haushin kanta.

******

Dare........

Junaid wanda ya dawo daga fada sunyi karamin zama akan wata shari a wacce yau ya fara aikinsa.

"Daga nan sukai sallah ya taho, kallan bangaren Binta yai sannan yai murmushi yace  Azi bari na"

dan lekata.

Azi ya matso yace  Ranka ya dade zatazo anjima ai.

 Cewa nai bazata zo ba? Ya tambaya yana san jin me Azi zai sake cewa.

Da sauri Azi yace  gwara mu leka kam kafin tazo.

Bai amsa mai ba ya nufi bangarenta.

******

"Binta na zaune tana gyara jikinta, yau tun safe ita da Hari suke hidimar gyara jikinta, ita har"

kunya ce ta isheta ganin yanda ake ta hidima.

"Harira ta tafi ita kadaice a daki tana tufke gashin kanta, jin bude kofa yasa ba tare da ta juyo ba"

tace Hari kin dawo mu tafi?

"Jin shiru ne yasa ta juyo, Junaid ne ya kalleta tare da harde hannunsa a baya ya fara takowa a"

"hankali yana kallan dakin, yace  baki ganni bane? "

Binta wacce bakinta ke bude ta kalleshi tace  Ya j. au Takawa mai kake anan?

Hade fuska yai yace  me? Bakya nemana anan?

Mikewa tai da sauri tazo kusa dashi sannan ta wuceshi zuwa kofa ta tura kofar ta rufe ta dawo

gabansa a hankali tace  Yaya ka manta yanzu kai Sarki ne? Cikin irin radar nan tai maganar shima cikin rada yace  sai akace Sarki karyazo yaga matarsa?

Tace  ba a ce ba tunda nima yanzu zanje.

Murmushi yai cikin rada ya sake cewa  in koma kenan? Ya fada yana nuna kofa.

"Kai ta daga alamar eh, harararta yai ya hade fuska ya juya, dariyarta ta guntse harya fita sannan"

ta kara shafa humra.

"Yana fita Harira na isowa, nan suka fita."

Junaid rai a bace ya koma bangarensa yana zama ya harde hannunsa ya kalli Azi yace  daga yau

"ko nace zani lekota kacemin na tuna, daga ka fadi haka zan gane. "

Dariya Azi ya dane yace  to Yarima.

"Jin sanar da isowar Binta da akai ne yasa ya mike ya shiga daki, Azi yai dariya ya rasa me yasa"

Junaid ke komawa yaro inda akai Binta ne.

Binta ce ta shigo ta kalli Azi tace  yana ina?

Daki Azi ya nuna mata yana murmushi tare da jan kofa ya fita.

"Tura kofar tai ta leka, ganin ba kowa yasa ta bude sosai ta shiga tana kallan dakin."

Daga gefe ta ganshi a zaune akan kujera ya harde kafafunsa.

Murmushi tai sannan ta nufi gun tace  Ranka ya dade ashe nan ka boya.

"Hade fuska yai yana kara kallan Littafin daya dauka wanda bude wa kawai yai, zama tai ta"

"kalleshi sannan ta kalli littafin, dariya tai tare da zuwa kusa da kunnensa tace  a juye littafin yake. "

Kallan littafin yai da sauri sannan ya hade fuska yace  a haka nake san karantawa.

Dariya ta sa tace  Hmmm na manta ashe ana iya yi a haka.

"Harararta yai, hannu tasa ta riko hannunsa tace  Ya Junaid! "

"Kamshin da take ne yasa ya dan lumshe ido, kallanta yai tace  nice fa Bintalo! "

Dariya yasa yace  Bintalo?

Tace  tunda nasan shikadai zai saka dariya ba dole na fada ba.

Dariya ya sakeyi sannan ya kalleta.

"Kallansa tai itama ta sakar mai murmushi, hannu yasa ya jawota jikinsa, kan cinyarsa ta zauna"

tadan sauke idanunta kasa.

Dagosu tai ta zubamai tace  Yau zanta cewa Ya Junaid saboda yaune rana ta karshe da zan

kiraka haka.

"Junaid ya kalleta yace  ban yadda ba, na fisan in muna tare mu biyu ki fadi hakan. "

Kai ta daga cikin amincewa sannan ta sake murmushi.

A hankali ya sa hannu ya matso da fuskarta ya sa bakinsa cikin nata.........

********

"Shiri ake sosai na nadin sarauta, sai dai duk wannan shirin Zeena da Binta ke yinshi, Hajjo na"

"kwance ciwon bakin ciki ya kamata, komai nata masifa ne, sau uku Zeena na zuwa tana cewa ta koma batasan ganinta, Zubair kam gaba daya ya zama sauna, shikenan da yawo a gari yana neman abin da zai daukemai kewa ya rage mai bakin ciki."

"Azeema kam ita ke aikawa Binta tazo ta nuna mata abinda zatai, duk wani abin masaruta ta koya"

mata sannan ta nuna mata yanda xata zauna da mutane ba tare da ta bari sun cuce ta ba.

Sosai Binta ta ke daukan darasi take kara sanin yanda al amura ke tafiya.

"Sarki kam gaba daya abin duniya ya isarsa, duk ya rame ya jeme a yan kwanakin nan, haka ya"

koma daya bangaren aka hau gyarana Junaid bangarensa.

Zeena sau uku shima tana neman iso a gunsa yana maidata wannan abu ya dameta sai dai data

fadawa Junaid yace  karta damu zai sa tagansu.

Azeema yau da kanta ta nufi bangaren Abdulsalam.

"Yana zaune a kasa akan dadduma, duk abin duniya ya dameshi yaji isowarta."

"Da sauri ya mike ya taho jikin kofa, tana shigowa ya rumgumeta, Azeema!"

"Abinda ya fada kenan cikin tsananin farin ciki yace  ban taba tunanin zaki zo ganina ba, nagode"

sosai Azeema nasan kema bazaki iya rayuwa ba ni ba.

"Dan matsar dashi tai daga jikinta sannan ta kalleshi, kallanta yai sannan ya jawota ya zaunar"

"sannan shima ya zauna, Yace  Azeema! "

Kallansa tai sannan tace  yaushe zaka bar masarautar nan?

Fuskarsa ya canza ya gumtseta yace  bangane ba?

Tace  sai yaushe zaka daina wannan abin daka daurawa kanka? Har yanzu bakai dana sanin

abinda ka aikata bane? Na tabbatar da kayi ba sai na tako na ma magana ba da kanka zaka ce

zaka tafi.

 Zan tafi amma sai dai in har zaki bini.

Wani murmushin takaici tai tace  in bika in ma me? In bika na ma kallan cutar dani dakai ko na

bika na ma kallan makiyi?

Fuskarsa sosai ya canza yace  ko zan mutu sai dai na mutu dake amma wlh bazan daga kafa na

"bar nan ba sai dake, inko ba haka ba na mutu a cikin dakin nan. "

Kallansa tai tace mene?

"Yace  nayi rantsuwa kin kuma jini, in har kinaso na bar masarautar nan da Junaid to ki hada"

kayanki a gobe ma zan barta in dai zaki bini.

"Kallansa kawai take, tari ne ya kwace mata wanda take ta fama dashi, da sauri ya riketa yana"

cewa  baki da lafiya ne?

"Ture hannunsa tai tana kallansa, yace  Azeema mu tafi tare na rokeki da Allah, bani da lafiya ni"

"kadai nasan jikina na tabbatar bazan dade a duniyan nan ba, ki taimaka ki bini na mutu kusa"

dake.

"Kallansa kawai takeyi, yace  Azeema ki taimakamin dan Allah. "

*****

Ayusher

* ZAFIN RANA *

......................

*Hask e  W rit e rs Ass o ci a ti o n*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*K A$ f[ fV *

{50}

"Junaid dake durkushe gabanta ta kalla, tamai murmushi jin dadi sannan ta kamo hanunsa ta rike."

Kallanta yai cikin tausayawa yace  Hajiya Inna!

Cikin maganar tsofafi masu shan wahala ta kalleshi tace  Bazan bar godewa Allah ba dayasa kai

"dan Zubair ne ba, ina kaico da lokacin da zuciyata ta rayamun Azeema amanar Zubair taci ita da"

"Abdulsalam aka sameka, saboda hankalina ya tashi sanda naje duba d ana naga halin da yake ciki sannan na taho ina tafe ina tausayinsa kawai na hango Abdulsalam ya nufi ta baya, ina ta binsa"

"saboda ina san naji halin da Zubair yake ciki ne naganshi ya nufi kango, abin mamaki naga"

"Azeema a cikin kangon, wannan lamari yasa na fara kawo shirme a raina sai dai kafin Zubair ya rasu ya fadamin ba haka bane, Duk  ya yan Azeema nashi me, wannan ne yasa na cire hakan a raina sai dai na san tabbas da wani abin a kasa."

"Kwatsam sai gashi yana rasuwa ta auri Abdulsalam, tun daga wannan lokaci ne gaba daya na canza musu, nan na kira Abdulsalam ina mai magana akan auran dayai ban sani ba sai cemin yai ai dama can shi da Azeema ke san juna na aurama Zubair saboda d a nane, sannan ya daukemin"

kai.

"Kallan Junaid tai saboda wahalar datasha gun magana, tace  tundaga lokacin na yanke"

tsakanina da Azeema da kuma Abdulsalam!

Junaid ya kalleta sannan yadan yi murmushi mai tattare da tausayinta yace  kiyi hakuri Hajiya ki

"yafe musu, sannan Marigayi ne yasa a kaini can ba shi bane. "

"Kallansa tai duk da idanunta basa Kai ta daga tace  nayafe musu Junaid banda wani buri a yanzu,"

"balle nasan dakyar ko gobe in zan kai, nagodema Allah dayasa zanga wannan rana. "

Kallanta yai cikin tausayi yace  zaki kai insha Allah.

Haka ya zauna a gunta kafin ya fito.

********

"Bangarensa ya koma saboda shirin yana shiga yaga masu shiryashi sun hallara, gaba daya"

"masarautar cike take taf ta ko ina, shiyasa yai shigar burtu dan zuwa gun Hajiya Inna."

Shiryashi aka farayi.

"Daga can cikin gida kuwa Binta da Zeena hidima suke ta ko ina, Azeema ma ta zake

26 / 28