Chapter 4 Reading Turmin Danya Book Compelet BY Hilfat Arewa Novels

Turmin Danya Book Compelet BY Hilfat

Author :  Hilfat Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   4 / 19

9K to 12K   out of 54.7K words

ya isa wurinsu "Me ta muku ina za ku kai ta? Wai babu jama'a a kusa ne a kawo mana ɗauki" Ya fara ihu. Kafin ya rufe baki suka buga masa kan bindiga aka, take ya silalo a wurin, su kuma suka fizgi motar tasu suka bar wurin da matsanancin gudu.

A can wurin aikin nasu kuwa Zaitun ke ta jiran zuwanta amma shiru, tuni ta shirya tunda ta ce mata da wuri za su fita su dawo amma ga shi har an shafe awa ɗaya tana zaman jiran ta ba ta zo ba.

Ganin an doshi awa biyu sai ta cire waya ta kira ta, sai dai wayar a kashe, tsaki ta ja ta koma ta zauna cike da takaici, wasa-wasa lokacin ya cigaba da ja, tun tana saka ran zuwan nata har ta fitar da rai. Cire mayafin jikinta ta yi ta yi ta jefar ta yi alwala ta tada sallah, tana idarwa ta koma kan kujera ta zauna ta hau aikinta cike da takaicin jirga ta ɗin da ta yi ta ɓata mata lokaci, haka ta gama aikin da za ta yi na ranar cike da ƙunci tuni ta ƙudurta sai ta biya ta gidan su ta nuna mata ɓacin ranta kafin ta tafi gida.

A hankali ya fara buɗe idanunsa jin hayaniya a kan shi, har ya yi nasarar buɗe su gabaɗaya. "Yawwa ya farfaɗo, sannu bawan Allah" Ya tsinkayi muryar wani a kan shi. Kan shi ya ji ya masa nauyi sai ya mayar da idon ya rufe. "Daure ka tashi bawan Allah nan kan titi ne dama shirin ɗauke ka muke yi" Ya kuma ji an faɗa. Ƙara buɗe idon nasa ya yi sai ya shiga ƙarewa wurin kallo take ya tuno abin da ya faru, sai kuwa ya miƙe a zabure yana faɗin "Nuratu, ina Nuratun, shike nan sun tafi da ita. Innalillahi wa inna ilaihirrajiun!" Ya fashe da kuka "Kwantar da hankalinka bawan Allah ka mana bayanin abin da ya faru. "Muna cikin tafiya zan kai ta wurin aiki kawai suka tare mu, bindiga suka buga mini suka saka ta a mota suka tafi da ita."

"Su wanene?" Wani ya tambaya "Ban san su ba ni ma sun rufe fuska. Ya kuma saka kuka "Ka ga kwantar da hankalinka in sha Allahu babu abin da zai sami ƙanwarka, yanzu ka samu a sanar da gida abin da ya faru" Ba musu ya ciro waya ya kira mahaifin nata, da ya ɗaga kuma sai ya kasa magana. Wani dattijo ne ya karɓa ya fara yi masa bayani.

Take hankalinsa ya tashi kuwa, cikin ɗimuwa ya hau faɗin suna daidai ina yanzun? Ana faɗa masa yace ga shi nan zuwa. Ba a fi minti talatin ba kuwa sai ga shi ya iso wurin a ruɗe yake kuma tambayar abin da ya faru, bai ɓoye masa komai ba ya kwashe ya sanar masa.

"Shike nan sun sace mini ƴar, magauta sun fara sako ni gaba, to ina suka kai mini ita, kai kana kallon me har suka tafi da ita ba ka taɓuka komai ba?" Ya mayar da tambayar kan shi "Wallahi Alhaji na yi ƙoƙarin dakatar da su suka buƙa mini bakin bindiga daga nan na faɗi ban jima da farfaɗowa ba."

"Ai zama bai kama ni ba, shiga motar ka wuce gida ni bari na je police station na sanar musu abin da ya faru, idan ka je kar ka faɗa mata ka jira na zo gidan tukunna." Daga haka ya faɗa mota ya fige ta ya bar wurin. Shi ma motar ya shiga ya tayar da ita, nan ya bar mutane na mayar da yadda aka yi. Daga nan kai tsaye can ɗin ya nufa ya shigar da rahoto, suka ce ya koma gida za su yi iya ƙoƙarinsu akai. Isar shi gidan ya tarar da Mamyn a birkice, tana ganin shigowarsa ta tashi da sauri ta nufe shi "Ina take? Ina Nuratun na gan ka kai kaɗai?" Maimakom ya ba ta amsa sai kawai cikin ɓacin rai ya ce "Wai sai da ya faɗa miki maganar nan? na ce masa fa ya bari na yi miki bayani a nutse saboda na san ki da ruɗewa" Ya faɗa cikin fushi "Tun kafin zuwan lawwali Zaitun ta zo gidan nan tana tambayar ina take na ce ai tun safe ta fita aiki sai ta ce wai ba ta je ba ga wayarta ba ta shiga. Ina kiranta ɗin nima ban same ta ba. Kuma katsam sai ga lawwali cikin yanayi mara daɗi na tambaye shi ina take shi ne ya faɗa mini abin da ya faru" Ta kuma fashewa da kuka. "Kin ga ki kwantar da hankalin ki, daga wurin ƴan sanda nake yanzu na faɗa musu komai, in sha Allahu za a same ta." Cikin damuwa yake maganar shi ma.

"Kai innalillahi wa inna ilaihirrajiun! mu kuma abin da muka waye da shi kenan yau, ba a tada sani ga Allah da na san haka za ta faru ba zan bari ta fita ba wallahi." Ta zauna kam kujera tana cigaba da goge hawaye. Zaitun ta ƙarasa ta zauna kusa da ita kafin ta kai hannu ta dafa ta "Ki yi haƙiri Mamy in sha Allahu tana cikin ƙoshin lafiya babu abin da zai same ta ai tana azkar mu yi addu'a."

"Tabbas kam Nuratu na da addu'a ba na jin wani mummunan abu zai same ta ina da wannan yaƙinin game da ubangiji. Amma kin san dole hankalina zai tashi musamman jin yadda abin ya kasance, fatana kar su cutar mini da yarinya" Ta ƙarasa cike da rauni, daidai lokaci ya shigo gidan da ƴar waƙarsa da ya saba da ma idan ba waƙa ba to sababi wani ya taɓo sa a waje.

Turus ya ja ya tsaya ganin su zaune jigum-jigum. "Me kuma ya faru a gidan na gan ku haka ko an yi mutuwa ne?" Ya tambaya, babu wanda ya kula shi "Yanzu babu mai iya amsa ni ina magana? Shike nan idan ta yi wari ma ji." Ya doshi ɗakinsa, yayin da Mamy ta maka masa wani kallo na takaici ta kasa magana "Nuratu ce aka ɗauke ta" Ji ya yi maganar ta daki kansa, juyowa ya yi yana kallon Zaitun da ta yi maganar "Ban gane aka ɗauke ta ba kamar wata ɗan tsako, mutum sukutun da guda kuma sai a ɗauke shi?" Ya kama haba "Eh a hanyarta ta zuwa aiki wasu suka tare su suka tafi da ita." Ta kuma ba shi amsa "Laaa'hailahaillallahu muhammadu ɗan Abdullahi, yau na ji abin da ya ishe ni, to wallahi ta Allah ba ta mutum ba, duk uban da ya ɗauka mini ƙanwa ma zai yi gaggawar fito da ita ne tun kafin rayuka su ɓaci, kawai an ga yarinya Allah ya fara ɗaukaka ta sai a fara saka ta gaba? To nan gani nan bari wallahi." Ya ƙarasa yana hararar gefe. Harara Zaitun ta maka masa don ta fara zargin kamar magana yake faɗa mata "To yaya ko kana zargi ne na ga kana jirwaye mai kamar wanka."

"Oho duk wanda ya tsargu ma da shi nake ehe." Kallonsa kawai take yi cike da talaici "Kai wuce ka ba wa mutane wuri a nan ka bar mu mu ji da abin da ya shafe mu, tunda kai dai har gobe baza ka nutsu ka yi hankali ka san ka girma ba." Daddyn nasu ya ce masa a fusace. Bai kuma magana ba ya tura ɗankwali gaba ya nufi ɗakinsa.

"Mamy bari na tafi gida ni na ga magriba ta kawo kai kar su ji ni shiru, don Allah da an samu wata alama ta inda take a sanar mini, don na san ni dai yau ba zan iya runtsawa ba."

"To Zaitun ki gaida ƴan gidan, mun gode Allah ya ba da lada." Ta amsa da amin tana ficewa jiki a sanyaye.

Kamar jiran fitar tata ake yi wayar daddyn ta hau ruri, da sauri ya zaro ta ya duba sai ya ga baƙuwar lamba ce,kasa ɗagawa ya yi ya dinga bin lambar da kallo gabansa na ɗan faɗuwa......"

[6/23, 7:16 PM] ~HILFAT~: WOW

TURMIN DANYA

NA

FATIMA UMAR KAS

(Mummyn Mihal)

(7)

A lokacin da suka jefa ta motar figarta suka yi da gudu suka bar wurin, fizge-fizge take yi tana dukan motar da ƙarfi tana faɗin "Ina za ku kai ni? Ku buɗe mini mota na fita, wayyo Allah ɓarayi." Mari na kusa da ita ya zuba mata. Duk da haka ta cigaba da ƙoƙarin kai hannu domin ta buɗe motar amma ta kasa, wani marin aka kuma zuba mata sannan ya buga mata tsawa kan ta yi musu shiru. A tsakiyar su suka saka ta, ɗan kwalin kan ta ɗaya ya fizge ya ɗaure mata ido da shi, bayan ɗayan ya riƙe mata hannuwa ta baya tamau, sam ta kasa motsi sai bakinta da ya ƙi shiru tana ihun kiran taimako. Sai dai babu wanda zai ji ta kasancewar motar a ɓame take kuma gilasanta masu duhu ne

Tun tana ƙoƙarin ƙwatar kanta har ta haƙura domin ta galabaita. Sun ci tafiya sosai kafin suka iso sansaninsu. Tsayar da motar suka yi sannan suka fito da ita suka tunƙuɗa ta ciki. Ɗaya ya saka makulli ya buɗe ɗakin suka tura ta ciki da ƙarfi sannan suka mayar da ƙofar suka rufe.

Da sauri ta cire ɗankwalin da aka ɗaure mata ido tana ƙare wa wurin kallo. Tashi ta yi tana jijjiga ƙofar gami da dukanta da ƙarfi amma ta ji ko motsi ta ƙi yi alamun a ɓame take. Kuka ta fashe da shi tana faɗin "Hasbunallahu waniimalwakil! Abin da nake ji a wai yana faruwa yau ga shi ya kasance da ni, ina ne nan suka kawo ni to? Allah ka kare ni daga sharrin waɗannan azzalumai." Ta cigaba da zagaye ɗakin tana yi tana jijjiga ƙofar amma shiru ko motsin wani ba ta kuma ji ba.

Sai can da rana ta ji ana buɗe ƙofar, kallonta ta yi tana jiran ganin wanda zai shigo. Abinci kawai aka ziro mata da ruwa aka mayar da ƙofar aka rufe. Ko kallon abincin ba ta yi ba, ruwan kawai ta ɗauka ta ɗaura alwala ganin biyu saura lokacin da ta kalli agogon da ke ɗaure a tsintsiyar hannunta. Tana gama wa ta ɗauki ɗankwalin ta yafa ta tayar da sallah anan wurin duk da tana tantama ko wurin zai yi sallah, amma dai da babu gara ba daɗi. Ko bayan ta idar addua ta yi sosai kan Allah ya kuɓutar da ita daga wurin nan.

Gefe ta koma ta rakuɓe tana tunanin halin da iyayenta za su shiga idan suka samu labarin ɓatan ta. Tuno wa da Zaitun da ta yi da shirin fitar da suka yi a ranar ya kuma karya mata zuciya, domin ta san tana can tana jiranta. Wani kukan ne ya kuma kufce mata ta fige ɗankwalin ta yi jifa da shi

Haka ta kasance a wurin cikin zullumi ta haɗa kai da guiwa har ta ga lokacin sallahr laasar ya yi. Da alwalarta don haka ta miƙe ta tayar da sallahr laasar ɗin ta koma inda take. Sai can ta ji an kuma buɗe ɗakin, ko motsawa ba ta yi ba balle ta ɗago.

Ya shigo idon shi a kan ta da ta haɗe kai da gwiwa sai hakan ya ba wa yalwataccen gashin kan ta damar zubowa. Kujera ya jawo gabanta ya zauna ya yin da yaran nasa su biyu ke tsaye a gefe da gefensa. "Ke ɗago" Ya ce cikin kaushin murya, tana ji ta masa banza "Ba dake nake magana ba, ki ɗago da kan ki na ce" Cikin tsawa ya mata maganar da ta saka ta ɗagowa ba shiru. Karaf suka haɗa ido ita da shi.

Ɗan kallon sakanni ta masa ta mayar da kan ta yadda yake bayan ta maka masa wani mugun kallo, kuma baza ta ce ga kamanninsa ba tunda ya rufe kansa ruf da wata ƙatuwar hular sanyi da ya janyo ta har goshi, kuma ya saka takunkumi a fuskarsa iya idon shi kawai take gani.

Sai da ya ƙare mata kallo har ya lura da shatin yatsun dake kan fuskarta kasancewarta fara sannan ya ce "Me yasa ba ki ci abincin da aka kawo miki ba?"

"Ba na ci ba zan ci ba, kuma ba zan taɓa cin ko me za ku ba ni ba" Ta ce a tsiwace cike da jin haushi ba tare da ta ɗago ba. "Keee ya ishe ki haka ki iya bakin ki ki san da waɗanda kike tare ba sakarkaru ne mu ba." Cewar goje yana zaburowa. Hannu kawai ya ɗaga masa alamun ya rabu da ita, sai kuma ya ɗage kafaɗa irin ko a jikin nan nasa, kafin ya ce "Kar ki ci wa kika yi wa? Cikin ki ko na wani? A miƙo mini wayar nan tata", na gefen damansa ne ya miƙa masa. Amsa ya yi yana faɗin "Karɓi ki nemo mini lambar mahaifinki." Sai lokacin ta ɗago ta kalle shi da jajayen idanunta. "Kuna nufin garkuwa kuka yi da ni za ku karɓi kuɗin fansa? To ku sani babu wanda zan kira muku domin ba zan taɓa bari a ba ku wasu kuɗi ba, azzalumai macuta kaw..."

Tasss ya ɗauke fuskarta da mari, ya kuma ƙara mata a ɗaya kuncin. Ko ɗigon hawaye bai kuma zubowa a idonta ba, cike da dakiya take kallonsa. Idonta a buɗe "Ki karɓa ki kira mahaifin ki aka ce" Ya kuma daka mata tsawa. "Wallahi sai dai ku kashe ni amma ba zan taɓa kira muku babana ba, saboda kuɗin da ake biyanku ya sa kuke cigaba da yin taaddancin, da ana hana ku da kun daina tunda ba riba, kuma abin takaicin karɓar ba ta saka ku saki mutum da rai sai kun kashe shi turr da halinku, ƴan wuta kawai." Wannan karan Maiyagi ne ya nufo ta gadan-gadan amma ya kuma dakatar da shi. "Ku rabu da ita da alamu kan ta ke hayaƙi kuma mu ba a mana iskanci da ɗanyen kai a nan, zan saita mata zama ne." Daga haka ya kunna wayar ta kawo haske, sai ya cire ta a jirgin da suka saka ta. shiga wurin lambobinta ya yi yana dube-dube har ya samu wadda yake nema. Ba tare da ɓata lokaci ba ya kwafe lambar a wayar a tashi watar sannan ya kuma kashe ta ya miƙa masa.

Kira ya danna take kuwa ta shiga. A lokacin ne kuma daddyn da suke zaune jigum-jigum a falo kiran ya shigo wayarsa har ya kasa ɗagawa. "Ka ɗaga mana Alhaji" Mamyn ta faɗa "Ai baƙuwar lamba ce ban san wanene ba" Ya ba ta amsa ƙirjinsa na cigaba da bugu. "Ka sani ko kiran ya danganci Nuratu? Ɗaga da bissimillahi kawai mu ji." A lokacin kiran ya katse ma, sai ya samu kan shi da bin kiran. Kamar baza a ɗaga ba sai kuma aka ɗaga.

Abin da aka fara cewa shi ne "Yarinyarka na hannunmu, mu muka ɗauke ta muna neman kuɗin fansa naira miliyan ɗari kacal." A zabure ya miƙe tsaye "Kuna nufin Nuratu tana hannunku yanzu haka? Ku haɗa ni da ita don Allah, na roƙe ku kar ku cutar mini da ita don Allah" Ya ce cikin roƙo, itama tuni ta miƙe jin ya ambaci Nuratu. "Ba doguwar magana muka kira mu yi da kai ba, wannan dai shi ne, ƴar ka na hannunmu ka biya kuɗim fansar ta ka karɓe ta, idan ba haka ba ka yi bankwana da ita kenan har abada domin za mu kashe ta bayan mun keta mata haddi mu kuma turo maka bidiyo ɗin, kwana uku muka ba ku, za mu kuma kira domin faɗa muku inda za ku kai kuɗin. Ba zan ce kar ku sanar wa ƴan sanda ba, ku bada himma." Daga haka aka katse kiran, da sauri ya kuma bin lambar amma a kashe.

Juyowa ya yi suka haɗa ido da ita "Alhaji yi mini bayani kai da su waye?" A ruɗe "Innalillahi wa inna ilaihirrajiun! Kidnapers ne suka ɗauke ta, yanzu ma su suka kira ni, wai tana hannunsu kuma suna buƙatar kuɗin fansa miliyan ɗari sun ba mu kwana uku.

"Miliyan ɗari? Wannan ai kuɗi ne maƙudai masu yawa? Ta ina za mu samu waɗannan kuɗin? Ta faɗa cikin tashin hankali, jagwab ya koma kan kujera ya zauna ya riƙe haɓa yana wani nazari da lissafe-lissafe, itama zaman ta yi dirshan a ƙasan capet tana cigaba da sallallami, falon ya yi shiru an rasa me magana.....

[6/23, 7:16 PM] ~HILFAT~: WOW

TURMIN DANYA

NA

FATIMA UMAR KAS

(Mummyn Mihal)

(8)

Daga can yana ƙare kiran ya cire layin ya miƙa wa Maiyagi, sai kuma ya miƙe ya fice. Rufa masa baya suka yi, suna fita suka mayar da garƙamemen kwaɗon suka rufe ɗakin wanda hakan ya kuma ƙona mata rai ta bi ƙofar da kallo cike da takaici.

Tsaf ya fito cikin shirin fita aikinsa kasancewar ya fi jin daɗinsa da dare magriba zuwa goma na dare. Wurin da yake ajiyewar ya nufa, ya karɓi makullin ya shiga ya tada shi. Wuta ya ba shi ya fice a layin ya hau titi. Waƙa ya kunna yana bi cike da nishaɗi. Duk wanda ya gani ya kan tambaye shi inda za shi, idan zai je ya ɗauke shi idan ba nan ya yi ba ya girgiza kai ya yi gaba.

Tana tafe tana waige-waigen rashin gaskiya sai zabga

4 / 19