Author : Hilfat Category : Romantic Hausa Novels
ke tsakaninmu dole abin ya dame ni."
"To Allah ya bayyanata, karɓi wannan ka busa ka ji ta rage maka damuwa." Ta ce tana miƙa masa karan sigari guda biyu. Ba musu ya ƙarba ya kunna ɗaya sannan ya hau zuƙa yana fesar da hayaƙin......
[6/23, 7:16 PM] ~HILFAT~: TURMIN DANYA
NA
FATIMA UMAR KAS
(Mummyn Mihal)
(10)
Tana zaune ta haɗa kai da gwiwa cikin zurfin tunani na halin da ta tsinci kan ta a ciki. Tsawon kwana ukun nan ba ta cin abincin kirki, sai dai ta ɗan yafita shi ma sai da ta ji tana shirin mutuwa ne, ruwa kawai take moɗa da yake ƙulle mata ciki shi ma. Ta gaji da zaman wurin ji take yi tamkar akan ƙaya take. Gefe kuma fargaba da ta cika ta da ta wayi gari yau ɗin cikin wani irin yanayi na canjin da take ji a jikinta, gabaɗaya a tsorace take.
Ji ta yi an buɗe ɗakin an shigo, ba ta motsa daga inda take ba. "Ke fito yau kin yi free Allah ya tarfa wa garin ki nono" Da sauri ta ɗago sai dai har ya fice mai maganar. Ƙwafa ta yi tana miƙewa tsaye da ƙyar da niyyar bin bayansa. Ji ta yi ta taka abu mai tsini ba zato bare tsammani, ta ɗan yi ƙara jin yadda ya cakar mata ƙafa, ta ɗuƙa ta ɗauka tana dubawa. Ɗan kunne ne na mace guda ɗaya, take ta fahimci ba ita ce mace ta farko da aka kawo cikin akurkun wurin ba. Ta gyaɗa kai tana cije leɓe cike da wani ƙuduri a ran ta.
Ta tsaya a filin tsakar gidan tana rarraba idon ta inda za ta fita a wurin sai kawai ta ji ana ɗaure mata ido da ƙyalle, ta rintse idanunta da ƙarfi har ya gama. "Mu je" Ya ce da ita "Ta ya ya zan iya tafiya ka rife mini ido." Ta ce cikin takaici, sai kawai ta ji ya damƙar mata hannu, fizgewa ta yi da ƙarfi "Kar ka kuma taɓa ni tunda ba muharramarka ba ce ni ɗin." "Muharrama?" Sai ya sheƙe da dariya, ya kuma gimtse ta yana zaburowa kan ta "Ke ni sa'an wasanki ne kike mini kashedi na taɓa ki ɗin, na lura da ke fa ba ki da kunya, kar ki sake ki mini tsiwa yanzu sai na yi ƙasa-ƙasa da ke, kawo hannunki mu tafi" Ya kai hannu ya kuma damƙar hannunta sai kuwa ta ƙara fizgewa ta yi baya tana shirin faɗuwa sakamakon jirin da take yi, mari ya ɗaga hannun zai zuba mata "Ka buɗe mata idon idan kun fita sai ka mayar mata" Ya tsinkayi muryar babba ɗin. Wani kallo ya maka mata na za ki sani ya hau sassauta ɗaurin ya yi mata ƙasa da shi.
Ta watsa masa wani kallo ta nufi ƙofar dake gefenta wadda ta fi zaton ita ce hanyar fita. Fili ne sosai da bai yi kama da cikin gari ba, gidan kuma shi kaɗai ne a wurin, tana cikin nazartar wurin ta ji ya ce "Hau mashin ɗin nan mu tafi kina ɓata mini lokaci ba shiri ta kama za ta hau don ta matsy ta bar wurin itama. Ƙarar jirgin sama ne a hankali ke ratsa wurin, duka suka kai kallon su kan shi. A hankali ya sauka daga can nesa da su. Ƙaramin jirgi ne irin Helkwafta ɗin nan. Ga mamakin ta sai ta ga bayan ƙofar jirgin ta buɗe wasu sun nufi wurin jirgin suna gaisawa da waɗanda suka zo a ciki, kafin a hankali suka fara fito da makamai suna ajiyewa a ƙasa. Ido ta zaro ƙirjinta na bugu me kenan?
"Wai uban me kike kallon ne?" Ta ji ya daka mata tsawa, ta ƙarasa hayewa mashin ɗin tana murguɗa baki. Tana gama hawa ya fizgi ɗankwalin kan ta ya tamke mata ido tamau, sannan ya kama hannayenta ya ɗaure su ta baya da ƙyalken hannunsa, shi ma ya hau mashin ɗin ya fige shi da mugun gudu da ƙiris ya rage ta sullumo ƙasa jikinsa rataye da bindiga.
Ita dai ba ta san ina ake yi da ita ba kawai tafiya ta ji suna yi, sun yi tafiya a ƙalla ta mintina ashirin kafin ta ji an tsaya. Ji ta yi yana waya. "Eh na hango ka, ka ajiye jakar mu gani."
Shi kuwa daddyn sammakon ya doko kamar yadda suka ba shii umarni, ya dinga bin kwatancen da suka turo masa har ya iso bayan ya ci tafiya kamar mai shirin barin garin. Ya jima a wurin amma bai ga kowa ba, ya ciro waya ya kira duka lambobin da suka yi magana amma babu wadda ta shiga. Ya kusa minti talatin da zuwa har ya fara cire rai ya ji rurin wayarsa. Yana ɗagawa kuwa ya ji yace ya ajiye kuɗin suna kallonsa.
Buɗe murfin motar ya yi ya fito da jakar kuɗin a hannunsa. Ajiye ta ya yi yana waige-waige amma bai ga kowa ba. "Ka koma motar za a zo a ɗauka". Ba musu ya yi hakan, bayan minti goma wani ya zo a mashin ya ɗauke jakar ya bar wurin da shegen gudu.
Can wayar wanda ya kawo ta ɗin ta yi ƙara ya ɗaga "Sun cika kuma ba lakwayen a tare da shi." Aka ce masa ta wayar. Fizgo ta ya yi daga mashin ɗin zuwa ƙasa sannan, ya hau ya fige shi da gudu ya bar wurin ta cikin surƙuƙin bishiyu. Sai da ya koma can sansanin nasu sannan ya turawa daddyn cewa ya duba bayan bishiyun nan zai ga yarsa. Da wani layin daban. Daddyn har ya fitar da rai da ganinta ya ga saƙon nasu. Ya fito a motar yana dudduba ta amma bai ga bishiyun ba sai fetal ɗin fili. Gaba ya yi yana ƙwala mata kira "Nuratu!!!" Ya ce da ƙarfi amma shiru. Ya cigaba da zagaye wurin yana ji kamar ya yi kuka. Ita kam a hakan take tafiya tana harɗewa cike da ƙarfin hali tana neman hanya. Kamar daga sama ta jiyo an ƙwala kiran sunanta kuma kamar daddynta. Wurin da ta ji sauti take nufa katsam ta ji ta ci tuntuɓe da wani ƙaton dutse, ta rintse ido saboda azaba kwalla na zubo mata. a hakan ta cigaba da tafiya sai kuwa ta ji gif ta kuma karo da bishiya wannan karon ƙara ta ƙwalla sai kuma ta fashe da kuka "Daddy!!!!" Ta faɗa da ƙarfi itama. Jin abu na bin fuskarta ya sa ta durƙushe a wurin.
Kamar daga sama ya jiyo muryarta, sai da ya ɗan ƙura ido sannan ya hango bishiyun da suke nesa da shi cikin duhuwa, Motar ya faɗa ya tayar da ita ya nufi wurin. A bakin ya tsaya ya fita yana cigaba da dudduba ta. Sai kuwa ya ji ya ci karo da abu, yana dubawa ya gan ta kwance jini ya wanke fuskarta kamar ba rai a jikinta.
A zabure ya duƙa ya ɗago ta "Nuratu, ke Nuratu buɗe idon ki, don Allah kar ki mutu ki bar mu" Ya dinga jijjiga ta amma ba ta motsa ba, sunkutarta ya yi ya fice a wurin a miliyan. motar ya buɗe ya shimfiɗe ta a baya sannan ya bar wurin da mugun gudu.
Sai da ya ga ya hau titi sannan ya sauke ajiyar zuciya. Yana yi yana waigowa ya kalle ta cike da faɗuwar gaban kar su rasa ta. Asibiti mafi kusa da ya tarar a hanya ya tsaya ya nufa da ita. Asibitin ƙarami ne amma dai da babu gara babu daɗi, ya samu sun karɓe ta suka rufu a kan ta. Cikin ikon Allah ta dawo daidai da ma jinin da ya zuba ne ya dinga ɗibarta har ta fyaɗi, sun yi sa'ar tsayar da shi sannan suka mata duk abin da ya dace.
Sai bayan ta farfaɗo ɗin ne daddyn hankalinsa ya kwanta har ya samu bin kiran Mamyn da ya ga yana ta shigowa amma ba shi da nutsuwar ɗagawa. "Alhaji ya aka yi na ji ku shiru kuna lafiya ko?" Ta ce a ruɗe.
"Lafiya ƙalau muna hanya ma, amma zan tsaya da ita a asibiti a duba mana lafiyarta tukunna." Take ta ce za ta taho asibitin, ya ce ta bari ba jimawa za su yi ba ai amma ta ce sai ta zo ya gan ta hankalinta zai kwanta. "Shike nan amma muna hanya ba mu ƙarasa ba, idan mun isa zan sanar da ke. Daga haka suka yi sallama. Sallama ya buƙaci a ba su su tafi take kuwa aka sallame ta. Ya riƙo hannunta yana bin ta da kallon tausayi ya saka ta a motar.
Yana tuƙin yana waigowa ya kalle ta "Sannu" shi yake ta jera mata duk idon ta ya yi zuru-zuru har suka isa asibitin.
Gado suka ba ta sannan suka saka mata ruwa don tana buƙatar shi, ya kira ya sanar mata sun isa, ta tambayi asibitin ya faɗa mata take tace gata nan. Dama suna gama waya ta shiga kicin ta sama mata abu mai ɗan ruwa-ruwa, sai ruwan zafi a flask, ta riga ta yi wanka dama a shirye take. Take ta saka Nura (Ƴar dubai ) a gaba ya ɗaukar mata kwandon abincin suka fice. Direba ne ya kwashe su zuwa asibitin. Daddyn ne ya fito ya tare su zuwa ciki. Ai tana ganin ta ta ƙarasa gaban gadon ta rushe da kuka ganin yadda ta dawo cikin kwana uku kawai. Ta rame sai wani uban haske da ta yi fayau, ga ƙuraje duk sun ɓata mata fuska jikinta duk shatin cizon sauro. "Nuratu haka kika koma? Kai Allah ya isa tsakaninmu da waɗannan mutane. Wannan ciwon mene a goshinta me suka ce likitocin? Ta mayar da tambayar kan shi cike da fargaba. Shiru ya yi yana tunanin ta yadda ma zai fara faɗa mata.
"Ka faɗa mini Alhaji, kar ka ce mini sun keta mutuncinta?" Ta ce bayan ta miƙe tsaye tama kallonsa kamar yadda shi ma kallon nata yake da rinannun idanunsa. Shi ma Nuran kasake ya yi yana fargabar abin da zai fito daga bakin daddyn......
[6/23, 7:16 PM] ~HILFAT~: WOMENT OF WRITERS
Association
TURMIN DANYA
NA
FATIMA UMAR KAS
(Mummyn Mihal)
(11)
Wata wawiyar ajiyar zuciya Daddyn ya sauke yana samun wuri ya zauna sannan idon shi a kan su ya ce "Zazzaɓi ne ya mata kamun kazar kuku sakamakon cizon da sauraye suka yi mata, sai ciwon kai. Raunin goshinta kuma ina tunanin faɗuwa ta yi ko ta buge saboda idanunta a rufe suke haka hannayenta."
Ta hau girgiza kai idanunta a kan ta kafin ta ce "Yanzu sai yaushe suka ce za ta farka?"
"Eh to a kowanne lokaci ma za ta iya farkawa. Ni bari na je na dawo tunda kin zo, ki kula da ita." Kai ta gyaɗa tana neman wuri ta zauna shi kuma ya fice. Nuran ya ƙaraso ya sauke jakar kafaɗarsa ya zauna a bakin gadon shi ma duk suna jiran farkawarta.
Sai can yamma sannan ta farka, ji ta yi kan ta ya mata nauyi "Sannu Nuratu" Suka haɗa baki wurin faɗa. Kai ta gyaɗa tana dafe kan ta da ke sara mata. Kama ta ta yi zuwa banɗakin ta wanko mata baki. "Ina so na yi wanka Mamy" Ta ce a hankali" Mayar da ita ta yi ta zaunar sannan ta ɗauki filas ɗin shayin da suka zo da shi. Kasancewar ta samu bokiti a banɗakin ruwan zafin rabi ta zuba ta sirka mata don flask ɗin ƙato ne.
Banɗakin ta kama ta ta kai ta "Za ki iya wankan ne?" Kai ta gyaɗa alamun eh. Ta fita ta ja mata ƙofar. Kafin ta fito ta haɗa mata ruwan shayin. Sam Mamyn ta manta ba ta zo mata da kayan da za ta canja ba saboda hankalinta da ya yo gaba. Dole na jikinta ta mayar sannan ta zauna a bakin gadon tana kurɓar shayin a hankali. Farfesun kayan cikin da ta yo mata ta zuba mata a plate ta miƙa mata yana tururi. Ba musu ta karɓa don tana shaƙar ƙamshin ta ji ranta ya biya, take tsohuwar yunwarta ta taso mata.
Sai lokacin wani tunani ya faɗo wa Mamyn, waya ta zaro ta danna wa Zaitun kira. Kashewa ta yi daga can sannan ta kira ta. "An samu Nuratu fa, yanzu haka muna asibiti." Ta ce bayan ta ɗaga kiran. Tana jiyo murnarta ta cikin wayar take tace ta faɗa mata asibitin da suke gata nan zuwa. Bayan ta sauke wayar ta shiga kiran ƴan uwa da duk ɓatan ya dame su tana sanar musu an gan ta. Barister Sahabi ne kaɗai ya rage a waɗanda za a kira ɗin amma ba ta da numbersa. Dole sai da daddyn ya dawo sannan ya kira ya sanar masa. Bai yi ƙasa a gwiwa ba kuwa ya yi wa asibitin tsinke. Kan ka ce me duk sun hallara a asibitin kowa baki har kunne, sai ka rasa wa ya fi murna ma da ganin nata. Ita Zaitun tana zuwa ta je ta rungume ta ta fashe da kuka, itama duk ta yi wani zuru-zuru, yayin da mahaifiyarta da suka zo tare suke gaisawa da mamyn tana mata barka da arziƙi.
Shi kan shi Barister ɗin ji yake kamar ya je ya rungume ta tsabar farinciki amma ba dama, baya ga haka ma ɗakin a cike yake, sai dai bai ji daɗin ganin yadda ta zabge ba sai ƙashin wuya. Gefe ya ci alwashin idan ta sanar masa waɗanda suka ɗauke ta ɗin sai iya inda ƙarfinsa ya ƙare. A ranar da dare aka ba su sallama suka tafi gida. Nan da nan kuwa labarin bayyanar tata ya baza unguwa, tun a daren ake ta shigowa taya murna.
Tunda suka dawo ta zame ɗaki ta canja kayan jikinta ta watso su waje don ba ta jin za ta iya kuma saka su a jikinta. So take ta samu keɓewa ita kaɗai ta yi tunanin da take son yi. Abin ya tsaye mata a rai, ba komai ba ne face wannan makamai da ta gani an kawo su a jirgi, kuma duk tunaninta wurin son gano wanda ke da alhakin hakan abu ya ci tura. Fefe guda kuma tunanin ta yadda daddynta ya iya bayar da waɗancen uban kuɗin ya karɓo ta shin a ina ya same su? Wai ma wacce irin sana'a yake yi ne?
Sai da ta yi kwana uku da dawowa sannan ta warware sosai, tun a ranar ta so komawa aiki iyayen suka ce sai ta kuma warwarewa. A ƙalla ta samu wata guda kafin ta koma ɗin, kuma daddyn ya ce ta daina fita haka sakaka excort zai nemo mata masu kula da ita.
Zaune suke a katafaren falon da ya gaji da haɗuwa, su shida ne sai shi mai gayya mai aikin cikon na bakwai da ke hakimce kan doguwar kujera masu tsaron shi a gefe da gefensa. Gadanga ya juya ya kalli Goje da ke zaune a gefensa, ya fahimci me yake nufi, take ya janyo jakunkunan kuɗin guda biyu manya ya tura masa gabansa, inda shi kuma ya tura gaban na zaunen.
Janyo su ya yi ya zuge zif ɗin, take maƙudan kuɗaɗen suka bayyana. Rafa ɗaya ya ɗaga ya shinshina yana sakin wani shegen murmushi sannan ya mayar ya ajiye.
"Yanzu ya za a yi kenan?" Ya tambaya idanunsa kan Gadanga. "Yadda aka saba ɗin kawai za a yi shugaba." Ya ba shi amsa, wani murmushin ya kuma yi sannan ya ce "Wannan karon kiɗan ya canja dole ne rawar ma ta canja. Yadda aka saba kashe mu raba ɗin yau zai bambanta da na koyaushe, dole ni zan ɗauki kaso uku cikin biyar, sai ku kasafta kaso biyun saboda wasu dalilai." Ya ɗago ya watsa masa wani kallo jin abin da ya ce, sai kuma ya mayar da idanunsa ya lumshe ba tare da ya yi magana "Kai nake saurare Aliyu." Ya ce masa ganin ba shi da niyyar magana "Duk yadda ka yi daidai ne Shugaba." Ba tare da ya buɗe idanunsa ba.
Take kuwa ya kasa kuɗin inda ya ajiye nasan a gefe cikin jakar, ya tura masa nasu gabansa. Jin abu ya dunguri ƙafarsa ya sa ya buɗe idanunsa a hankali. Da ido ya yi wa maiyagi alama. Duƙawa ya yi ya ɗau jakar kuɗin ya shige ciki ya ajiye. Miƙewa baƙon ya yi ya saka yaran nasa suka ɗauki nashi kuɗin sannan ya kuma miƙa musu hannu suka ƙara gaisawa ya juya ya fice. Rufa masa baya suka yi. Shi ma miƙewa ya yi ya biyo su kamar ba ya son taka ƙasan. Har gaban motar suka rako shi, bayan ya shiga ya kuma leƙo da kan sa "Aliyu aiki na kyau ka ƙara kulawa dai" Kai kawai ya gyaɗa masa. Direban ya ja motar suka fice daga wurin.
Ciki suka koma su ma. Kuɗin ya sa suka ɗauko masa, ya ɗan ƙura musu ido da baza ka gane kallon me yake musu ba. Buɗewa ya yi ya kasa biyu ya raba musu rabin sannan ya ajiye rabin a gefensa. Ganin yawan kuɗin ya sa suka buga sowa gami da fito suna zabga godiya da yi masa kirari. Ya kuma ware wasu ya ce su kira matashin nan da ke musu aiki ya zo ya karɓa a ranar, shi kuma ya miƙe ya ɗau nashi kason ya juya ya fice a gidan. Motarsa ya faɗa ya tashe ta ya bar wurin.
Tunda ya shiga gidan yake bin