Author : King Boy Isa Category : My Hausa Novels
saki kawarta taga haka sai ta kwada iho ta nufi hanyar fita da gudu tana iho tana fadin aljana. Aljana. Basmah kuma tashi tayi zaune har yanxu hannun budurwar na rike a hannunta kuma ta wani zura mata ido. Ita kuwa yarinyar kuka kawai take yi. Gata a hannu ba damar ta tsere bata yarda su hada ido domin idan kawa basmah kallo daya dole ne ka tsorata duk rashin tsoranka. Dayar budurwar haka ta fita tana iho tana kirqn aljana aljana.
Habawa yan matan makarantar gaba daya suka firgice duk aka fara guje guje da iho irin nasu na mata.( na kalli nasmat nace ai kaji irinta ga tsoro ga cika baki ji yanda suka tsorata daga ance aljana bayan ko ganinta basuyi ba. Tace to dai kaima nasan halin ka da tsoro kuma in ba tsoro ba je ka kwaci budurwar can a hannun basmah mana. Nace yo ai ba aiki na bane ni aikina kawai kwaso labari.lolz.)
Ihon da suke yi na yajawo hankalin malaman nan wajen malami biyar ne ya fito. Suka fara tambaya lafiya lafiya. Wacce aka rike kawarta tace malam wllh aljana ce ta rike farida ni na ganta da idona aljana ce. Wani dan gajeran malami yayi dariya yace kaji shirme wai aljana tana ina. Yarinyar tace tana room din mu. Ta rike farida.
Dan gajeran malamin yace da sauran malaman ku tsaya in shiga in gamo muku shiga irin nan ai sai mu yayan gado. Domin kakana ma ruk-yah yake yi. Basu ce dashi komai ba. Ya fada dakin can ya hange su su biyu ga farida a gefe har ta gaji da kokarin kwace hannunta da take yi kuka kawai take. Basmah kuwa kanta a sunkuye yake duk gashi ya rufe fuskarta kanta kuwa yayi wani iri ba kyau duk gashin tsaitsaye. Malam dan ladi yayi Murmushi yace a zuciyarsa wai basmah ce aljanar. A lokacin da ya tunkare su yace basmah sakarta mana
Yaji shiru ya kara cewa ke basmah sakar mata hannun mana habawa nan ma shiru bata ko kula da shi ba. Tsawa ya daka mata ke basmah wane irin iskanci ne wannan ina miki magana kin yi wa mutane shiru. Dago kai tayi ta kalle shi yana hada ido da idanunta sai naga ya fara karkarwa karatun ma kasa yi yayi sai ya jawo wannan ayyar ya bai karasa ba kuma sai ya yanko wata. Da wata irin murya tace mishi kaine marar kunya ko harda zaka ce in sake mata hannu to kai zo in rike naka hannun. Jin wannan muryar mai tsoratarwa gata tana fita uku uku.sai gani nayi fitsari ya fara tsiyaya daga wandan malam dan ladi. Nan ya farq cewa innahu-sulaimanu. Kuma sai ya canza yace kulluhiya- illayya. Nan dai ya ta jawo ayoyi rabi rabi. Cikin rudadar murya tace zo mana. Habawq da gudu yayo baya ina kofar dakin nasmat dama kasa shiga tayi. Ganin ya rugo da masifafqn gudu nima nq yarda kayqn rubutun nayi waje
Malamai suka tare shi suna tambaya malam danladi lafiya. Habawa waje ya samu ya zauna baice da su komai ba sai cewq yayi ku shiga ku gani. Fitsarin da aka gani a wandan shi duk ya jika yasa mutane aka fara dariya ciki ciki.
Malaman nan su hudu suka kutsa kai suka shiga dakin suma da sukayi arba da fuskar basmah saida duk suka firgita harma wasun su suka yi shirin guduwa kuma sai sukayi ta maza. Suka karasa. Suka mata magana amma shiru duk wanda yayi mata magana saidai ta zuba mishi idanunta 2color. Daya daga cikin su ne ya karanta ayatul qursuyy a zuci ya tofa mata habawa sai tq saki farida ta kwala kara. Farida na ganin haka sai ta tashi tayo waje a guje malaman kuma baya baya suka fara yi. Domin basmah tsaye ta mike tana yi musu wani kalan magana.
Koda dai ta faki idan su sai ta falfalo a guje ta kaiwa wanda ya tofa mata addu'a mari. Habawa nan ya zube kasa sumame kansa ya fashe jini ya fara zuba.
Koda suka ga haka sai suka ce kafa me naci ban baki ba ranar nan gudun da basu taba yi ba sukayi shi. Suna fita suka ci sa'a kafin ta karaso suka rufe dakin. Basu san sun garkame dani a ciki ba ihoo na fara yi ina cewa wayyo mamanaππa lokacin aka sama wani dan arziki ya bude ni har na fara fitsari a wando but dan kadan nayi lolzπ.....................................
karku so kuga yanda nasmat ke min dariya wai an kulle ni a ciki.
ππΏβ MIJIN ALJANAH β ππΏ
page 61 - 62
|
|
na king boy isahπ
|
|
__________________________
π5STAR APR 2017 π
|_________________________|
***** 5 star *****
π5β£STAR ONLINE WRITER'S ASSOCIATION π Β©5SWA
***** 5 star *****
π₯ wanga page din naku ne masoyana ina tune daku ban manta daku ba π love u tooo mucch oll fansπ
Kulle basmah akayi a dakin lokacin ta wani dinga makar kofan allah yasa kofan ba ta wasa bace amma da sai ta balla ta malamai suka je suka samo samari matasa guda shida har su hudun sun zama goma kenan. Nan suka zo suka ce ma malam dan ladi ya taso a je a kamo basmah. Yace dawa aka ce da kai mana yace wllh ba abinda zai kaini.
Dariya sukayi suka wuce. Tunda aka je bakin kofar aka fadawa kowa ya kama yin addu'a nan fa suka fara karanta ayatul kursiyu da aka bude gate din da gudu wasu marar tsoro suka jesuka ririke basmah tana neman kwacewa wasu suka kara ririkw ta wajen mutun goma ne sukq rike ta. A mota aka sata nan ma saida akq samu marar tsoro suka ririke ta tukun wato zasu maida ita gida.
Bayan anzo kofar gida nan ma kokowa aka sha domin wani irin karfi ne a jikin basmah sai da akq karo matasa abokan nuhu tukun suka tura ta daki. *_asalin labarin basmah kenan_*
A nan basmah ta tsaya a labarin ta umma ta girgiza kai tace tabb ikon allah nasiha tayi matq sosai a kan kawayen banza da kuma san zuciya nan dai na barsu tana yi mata nasihi.
A daidai nan marsiyya ta tsaya a labarin kursiyya ta kalle ta tace sis manyan gari ashe a gun basmah aka labe. Marsiyya tayi dariya. A daidai lokacin ne sukaji motsi a dakin yasmeen wannan ya tabbatar musu da sun tashi a barci. Marsiyya ta nufi dakin zata shiga sai kursiyya ta riko hannunta tace ina zaki?
Marsiyya tace aunty yarinyar nan zan fara tsoratar wa domin bata sama gurin zama bq wllh a gidan nan.kursiyya tace gaskiyan ki sis domin hada kishi damu ba karamin bala'i bane duk wanda yayi to gobe fa bazai karq ba. Tace amma ba yanzu ba zaki fara aiki ki bari mijina ya fita tukun. Marsiyya bata so ba amma haka tayi hkr ta dawo.
Yasmeen bayi ta shiga ta hadawa al ameen ruwan wankq tukun ta dawo ta tayar da shi ta kama hannunsa suka shiga har bathroom din tukun ta juyo ta barsa yayi wankansa. Kursiyya ta tashi ta shiga dakinta. Saura marsiyya kadai a parllo ita kuwa tacr to wllh sai na fara aiki tun yanzu.
Yasmeen na zaune tana kallan mirror tana jiran al ameen ya fito itama ta shiga tayi wankqn. Nan fa ta fara tuno abun da ya faru jiya a mafarki wato kadan garu. Nan fa taji duk ta tsorata hakan yasa ta fara waige waige. Ba'a dade ba sai ju tayi wani jirdeden kadan gare ya fado mata daga sama a kan zane. Wani uban tsalle tayi hade da iho wanda ko kudi aka bata in lafiya lafiya barata iya irin sa ba.
Ban dakin tq nufa da gudu tana kara tana kakabe kakabe. Kamar saban shigar hauka.
Ban dakin ta shiga tana zazage zazage al ameen cikin kaduwa yq ce minene tace kadan gare tana dube dube a jikin ta domin a tunanin ta har yanzu kadan garen bai sauka ba yana jikin ta. Yar dariya yayi yace matsoraciya kawai kin saka abun a ranki ne shi yasa kike yawan ganin sa ni yanzu tube muyi wankan yi sauri kizo ki cuda ni ya fada lokacin da yake kara hada kumfa a sosan. Bataji kunyar komai ba dake daman sun saba wanka tare. Tubewa tayi taje suka yi wankqn tare.
Bayan sun gama wankan ne a cikin su bq wanda yayi maganar sallah balle a karanta kur'an ta nufi kicin shi kumq ya lalubo wayarsa domin duba massages na whatsapp da Facebook da sauran su.
Whatsapp ya fara bude wa sai kuma ya fito ya shiga Facebook kafin mAssages su gama shigowa. A facebook notification yaga kursiyya ta tura mai frndreqst yayi accept yana murmushi tare da cewa kai amma fa yarinyar nan ta kamu da sona da yawa bata san halina ba ne. tukun ya fara duba messages din da aka aiko mishi nayi mamaki domin a cikin friends dinsa maza daya-daya ne abun mamaki kuma wai duk tilin yan matan nan soyayya suke yi. Ni nama rasa ina yake samo su.
Wata kyakyawar yarinya ce a dp din a jikin kuma sunanta fatima sadiq ta aiko mishi da messages har biyu.
" assalamu alaika ya abun kaunata lantarkin zuciyata abun tunanina me yasa zaka min haka banyi tunani ba bayan mun riga mun saba da kai ka koya min zama da kai shine kuma zaka guje ni.
2 " dan allah yah al ameen karka min haka zaka jefa zuciyata cikin kunci da matsi. Pls ka fada min address dinka inzo in sameka har gida mn number da ka bani bata aiki. Ix switchoff ant tym.
Murmushi yqyi yace wannan fa da gaske zata iya zuwa har nan ko. Hmm yarinya kenan ai bazan taba gayawq wata wace muka hadu a net address dina ba ko na bawa mutun ma sai dai in bashi fake! ( ni kuwa nace kaji dadin abu su su kursiyya basa bukatan dressπ)
yan karyayaki yayi wa fatyma ya tura mata kuma yace zai turo mata da number sa. tukun ya fita. nan ma yan matan na gani da yawan su duk sun aiko mai da sako domin rasa wanda zai bude ma yayi. tsaki yaja ya fito daga Facebook din ya shiga whatsapp.
hmm mai hali baya canxawq a ko'ina domin a nan ma numbobin yan mata ne kawai birgik kuma abun haushi a numba ba sona kawai yake sawa ba sai yasa wani abun a gaba. numbers kamar haka suke. ni'mah baka. sadiya mai katan baki. asmau mumuna. rashida mai muryar gardawa. safeenah yar lukuta. kareeme mai gwiguyayan gashi. nafisa mai bilicin. zainab siririya. fauxiya yar wahala. a number kursiyya ce kawai banga an rubuta wani abu a gaban ba. nayi Murmushi nace in ba tsoro ba a rubuta mnπ
haka ya shiga mayar musu da reply din karya daga wacee dai cewa....................................................
good morning fans have a nice dayβ
β
β
π§ππ΄π΄π΄π΄π΄π΄π΄
little of writer's
π KING BOY π
Shiga nan ka/ki yi like kai tsaye a page mu domin samun farkon lbrn
https://m.facebook.com/bigboyisahfans/
ππΏβ MIJIN ALJANAH β ππΏ
page 63 - 64
|
|
na king boy isahπ
|
|
__________________________
π5STAR APR 2017 π
|_________________________|
***** 5 star *****
π5β£STAR ONLINE WRITER'S ASSOCIATION π Β©5SWA
***** 5 star *****
I miss u dear jiya nayi mafarkin ki munyi aure har mun haihu. Haka ya turawa zainab siririya. Ya fito ya shiga ciki massages din yar wahala. icon din Kuka yaga tasa my life kana ina ne haba al ameen san gaskiyar kenan da zaka barni wajen 12 hour baka neme ni ba kuma ka kashe wayoyin ka. Ko kasan irin kuncin da na shiga na rashin ganin ka a on da kuma rashin tafiyar wayarka.zuciyata ta kamu da ciwo al ameen cewan kuma mai tsanani wanda kai kadai ne maganin sa al ameen.
Dariya yayi wace har saida ta fito waje yace kan uba. Lalai yarinya iska na wahalar da mai kayan kara. Amma nasan maganinki ai. ""srry dear na wllh an dan sama matsala ne jiya wayana charji ya kare min kuma na nema aran waya in kiraki but ban samu ba. Sanin kanki ne ke kadai ce wacce nake so ke kadai tillo fauziya bazan barki ba bazan guje ki ba ki rike ni amana. I love u i luv u fauzi na idan kin hau ki min flash.
Yayi tsaki ya fito. Mtseww idan mutun yasa kansa soyayyar net ma ya shiga uku shikenan mutun ba dama ya dan huta bai hau on ba kamar wani dole. Massages din da suka shigo ne ya tsaida sa daga surutun da yake yi. Ganin kursiyya ce ta turo yasa shi sauri ya shiga massages din.
" hmm to kai yanzu al misali idan pics dina ne wannan daka ce baka sona ne?
Hantar cikin sa ce ta kada kuma sai ya fuske yace haba wasa take taya ma xa'ayi ace pic dinta ne bayan wannan aljanah ce. Hakan yasa yayi Murmushi ya aika mata massage kmr haka.
""Haba sarauniyar mata kursiyya ai nasan ma bake bace kuma ina so in tabbatar miki da cewa koda ace kece wannan to ni ina sanki a hakan balle nasan ba ita bace.
" Kursiiyya ta ce na gode amma in tambaye ka mana me yasa kace kana sona har ka shiga gasa a kaina bayan baka san ni kowacece ba baka ma taba ganina ba ko zan iya sanin dalili.?
Jibi ne ya fara keto wq al ameen domin wannan tambayar fa mai rikitarwa ce kuma nan ya tabbatar da cewa wannan fa bakanwar lasa bace domin da yawa yan mata a grp yakw fara cewa yana sansu bayan bai gansu ba ko yaji muryarsu sai daga baya tukun su turo mishi. Idan yaga kinyi mai yaci gaba da soyayya dake idan baki mishi ba kuma ya share ki ya bar kula ki. amma ba wacce ta taba yi mai tambayar nan sai kursiyya. Ya dan jima yana tunanin me zaice mata tukun can sai ya aika mata text kmr hk:
"A gaskiya ne nace ina sanki ba tare da na sanki ba to karki manta shifa so gaman jini ne idan allah yayi niyar hada sa sai kiga ya hada ta wata sigar wacr baka tunani to kinga ni. Ni kuwa ina ganin sunanki naji ina sanki domin sunan ya hadu shine dalili na.
Kursiya tace
to na gode sahibina bari in turo maka pic din. Mamaki ne ya cika sa ganin pic din da ta turo kusan guda goma uku daga ciki rabin fuskar ba na mutane bane sauran kuma sai yaga rabin wacan fuskan ne cikaken ba rabi aljani ba. Shifa ya fara tsorata da lamarin yarinyar nan ya data dinga tsorata shi. To su kuma wannan masu rabin mutun rabi aljana fa bari in tambaye ta.!
"Amaryata gaskiya kinyi mugun haduwa kinyi kyau sosai kafin a sama mace mai kyawanki a zamanin nan sai ansha wahala wajen binciki sai dai in tambaye ki mana ya naga pic uku daga ciki rabi mutun rabi aljan ko kinfi so ki ta tsoratar da angon naki ne?.
bata basa wata gamsasar amsa ba tace "haba angona ni taya zan yadda in tsorata ka just editor ne angona me kake so in dafa maka yanzu na breakfast ne.? ta basar da maganar
" al amin yace amarya kenan yanzu har kin fara girki da kanki du du du yau kwananki nawa ne a gidan ki bari ki kwana biyu mn ya tura mata hk.
Ba fi secon biyar ba ta dawo da rply kmr hk; " haba angona baka so in sama ladar aure ne ni gaskiya idan baka bari nayi mk girki ba bazan je shin fidar ka ba har na tsawan kwana uku. Dan hk kawai ka xayyano min abunda kake bukata kaci in girka maka yanzun nan.
Al ameen abun ya bashi dariya sai da ya danyi mai isarsa tukun ya kalli wayar yace rigima kenan soyayyar net kawai kwalele ne fa zaki min in ma na fada wato ki turo min pic. Yace amma ai ba komai bari in zayyano mata.
Nan fa ya shiga zayyana mata yace. " yanzu dai abunda nake bukata in kirya da shi soyayen kwai sai tea mai kauri. Yau ina marmarin masa da miya. Sannan sai dan kali soyayye da doya. Idan aikin baiyi miki yawa ba ina bukatar indomie ma. Dariya yayi yace bari muga karshen rigimar ki kursiyya ai idan kinada pic din wasu baki da na wasu a cikin nan.
" kursiyya na ganin massages din ya shigo ta karanta tace ohh dan wannan ai mai sauki ne ango na just 3 mints kaji. Daidai lokacin ne Yasmeen ta gama jera abinci a dinner tebur ba wani abu bane tayi sai tea da indomie bata sama damar dafa mishi komai ba sai wannan domin karya makara. Dakin ta shigo ta iske shi yana chat. Taje ta fada kanshi hade da cewa Darling taso muje na kammala breakfast din. Yace ok dan jira.In dan maida wasu reply masu muhimmanci.
.kursiyya na daki ta murza hannu sai ga marsiyya ta bayyana.kursiiya ta kalleta tace sis bari in aike ki wane waje kika sani inda ake yin waina da miya mai dadi inda manyan mutane ke saya. Sannan kuma ina kike ga zamu sama dankali da doya soyayu da kuma indomie suma ba na kazaman mutane nake bukata ba. Marsiyya ta dan dora hannu a haba alamun tunani tukun tace.
" gaskiya a dai daura babu amma a bauchi nasan wajen da ake yin waina da miya da naman kai mai dadi kuma a duk wajen manyan mutane ne kawai ke zuwa saya domin manyan motoci ne a kofan gurin a kullu idan naje hucewa. Kursiyya tace yauwa ynz nake so ki dauko min nasan ki da gudu kafin 1 mint nake bukata domin angona ne zaici............................................................
Yawu ne ya fara zuba daga baki na sakamakon sakin baki da nayi ina kallan wannan dramar. Nace da nasmat wai me kursiyya ke nufi ne. Tace dallah malam yi min shiru lbr ya fara min dadi ka katse ni.
____________========________________
Muna bukatan sababin members a group din mu na whatsapp if u need.