Author : King Boy Isa Category : My Hausa Novels
kamar mutun bakinta wani dogo ne kamar bakin jaki saidai yafi na jakin tsini idanunta jajur sai jini dake futa a ciki gashi ne yabayaba a kanta baki kirin da shi. karin abun tsoran shine kafafunta sirarane kamar ka taba ta karye.
cikinta kuwa runbu guda tumeme da shi abun tsoro. waini bakin hayaki ne ys gauraye dakin kamar guguwa yana bacewa tsulum sai ga mace tsullum ta bullo a ciki. wata Kyakyawar budurwa ce sanye take da doguwar bakar riga mai wani adan kwarangwal a wuyan rigar.
ba abunda zai baka mamaki sai gashints da ya rufe duk bayanta yake jan kasa Kyakyawa ce ta gaban kwatance gata fara sall bakaken kayan sunyi mata kyau sai wata kwaliyyar hauka wace na rasa gane kangadanta domin duk wani bakin abu ne kamar kwalli aka zazana layi layi a fuskar sai dai kuma abun mamaki jikinta wajeje duk alamun kuna ne duk ta susulge.
na kalli ama nace amma wannan Kyakyawar fa anya kuwa za'a sama kamarta ko a india nace gaskiya da zata soni dana gwada sa'a ta. ama tace gaskiya dai kam wannan abu hk kmr aljanah. bamu gama mganar ba sai gani mukayi ta nufi kursiyya itama kursiyyar ita ta nufa suka rungume juna suna farin ciki...................................
https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarks
naku har kullum kingboy little of writer's
ππΏβ MIJIN ALJANAH β ππΏ
page 31 - 32
|
|
na king boy isahπ
|
|
__________________________
π5STAR MAR 2017 π
|_________________________|
***** 5 star *****
π5β£STAR ONLINE WRITER'S ASSOCIATION π Β©5SWA
***** 5 star *****
kursiyya na ganin yarinyar nan sai ta chanza sufa ta dawo yanda take da rabin fuska aljana rabi kuma na mutun abun mamaki duk da rabin fuska ne zaka iya gane sunyi kama da wannan yarinya.
rungumar juna sukayi cikin farin ciki ji nayi kursiyya tace haba marsiyya me nayi miki ne da zaki guje ni har nayi aure amma baki zo min ba ko sau daya. ina kika buya ne yar kanwata yama dai naga duk jikinki wani gu a kone me ya faru?
marsiyya tayi wata irin dariya tukun ta bata rai tace wato yaya bansan ke jaruma bace a cikin mu mu jinni sai ynz na kara tabbatarwa domin a cikin mu dadaya ne ke auran mutane yan adam suma kuma sai maza masu sakaci. da addu'a da kuma karatun qura'ani.
kursiyya tayi dariya hahHa tace kanwata da kinsan yadda nake jin dadin gidan nan da kema sai kinyi sha'awa domin gabaki dayan su jahilai ne bangaran addu'a basu iya komai ba ba abunda suka sani a Qur'an balle su nema kariya a gun allah ga mu.
taci gaba da cewa matsalata kawai matarsa. kan marsiyya naga yayi jajur idanunta sunyi baki. yaya miji fa kika ce kam buhu ai kuwa yaya bazan tafi ba sai kishiyarku tabar gidan nan me ma kike jira da ita ai da nice da tuni na hallakata wllh aunty ina take nuna min ita kiga aiki da cikawa badai kince bata yin addu'a ba.
kursiyya ta bazo wasu fukafuka ta tashi sama hahaha sis na ashe har ynz kina nan da muguntar ki da bala'i ki da shu'umancin ki da zalincin ki. to ina so in gaya miki cewa wannan ba ynz ba tukun bana ma so in wahalar da ita abunda nake bukata shine kawai ta tsorata ta bar min miji na ni kadai in koreta.
dajin haka na juya da niyar guduwa zeesa ce ta chaf ko min rigata wai ina zani nace aradu na ma fasa daukan labarin daga ganin wannan kanwar aljanar baratayi kirki ba karta gama da su yasmeen tayo kanmu.lolz.
hahahaha ta yi dariya aunty hk nake har ynz kuwa kuma indai hkn ma kike bukata to zamuyi kuma zamu kore ta cikin ruwansanyi yanzu tana ina a fara aiki. kursiyya tace barci suke. marsiyya tace aunty mu bita ciki a fara bata horo. kursiyya ta yi dariya hahaha tukun tace aa ke kiji da ita ni gun mijina zani allah yasa dai baiyi addua ba da zai kwanta. batt suka bace duk su biyun
yasmeen na barci ta shiga mafarki.........β
zaune take a parllonta ita kadai kanta a kunce yake ba dan kwali rigar ma yar shara sharace mai nuna tsirai ci.
( note pls yan uwana mata da maxa yayai da kannai a kula da irin suturar da za'a na sakawa karki yi wani tunanin wai ai a gida kike ko kuma kiyi tunanin a cikin daki ne kiki saka dan kwali to karki manta fa aljani ko'ina yawo yake kuma ko'ina akwai su kuma aljanu akwai masu naci wanda idan kayi musu laifi koda ace basu sama hanyar shiga jikinka ba a lokacin saboda to zasuta binka ne har sai lokacin ya dace ga kadan daga cikin irin lokutan.
1 lokacin da kake ko kike aikata saban allah
2 lokacin da kikayi shiga ta tsiraici.
3 lokacin da kake / kike jin kida da wake-wake
4 lokacin da ka manta da ambatan allah 5 lokacin da kake cikin kazamta domin aljani kazamai ne mafiyawancin su domin wasu ma kashi ne abincinsu
6 lokacin da kika bar kanki a bude ba dan kwali
7 ko lokacin da kake kake aikata zina ko mata masu lesbian mafi yawancin su suna da shafar iska ko ma bai bayyana ba in har basu tuba ba gaba zai bayyana allah ya kare mu ameen.
8lokacin da kuma kake cikin matsanan cin fushi nan ma aljani na samun dama.
wasu daga cikin lokutan kenan
wannan lokutan aljanu suna samun cikakiyar damar shiga jikinka. nasan wasu dasuyi la'akari da kafurai wato arna turawa ko bakar fata mutun zaiga ah to su wancan ai duk sunayi abubuwan da aka lissafo to su me yasa aljanun basa shigarsu.? eh idan kayi tunani zaka ga cewa mafi yawancin alanu masu shiga mutun shedanune. to suma kuma kafuran shedanune. to misali kanada customs ukuu a harkar kasuwancin ka to ga kuma wasu ukun ba custom dinka bane shin tambaya anan shine zakaje kayi invite din customs
kane ko kuwa zaka nema wasu to kagani abun lura a nan shine kafure su tuni suma shaidanune kaga kuwa aljannun zasufi bukatar wanda ba shaidani ba wato mai bautar allah idan yayi saka ci shima wato ya bar hanyar allah allah ya kiyashe mu ameen allah ka yafe min inda nayi kuskure a bayani na)
. tana jin kida a wayanta tana bibiyar wakar tana kuma gyada kai. knock taji anayi kofar shigowa parllon kamar za'a karya ta da karfi akeyi. waye? waye? ta shiga tambaya kuma sai taji andaina
can kuma bayan ta kuma ji anci gaba da kwankwasa kofan cikin fushi ta tashi da masifa ta nufi kofa tana fada.
wai uban waye wannan ana mgn yayiwa mutanw shiru to wllh koma waye zanyi mishi rashin mutunci wllh domin ni ba karamin aikina bane.
ba'ayi mgn ba aka kuma bugawa cikin fushe ta bude kofar a firgice tayo baya da gudu tana iho kadan garone da yawansa kamar tururwa sukayo kanta kala kala da masu katan kai da kuma masu jajayen kane
irin mazan nan kah harda mai irin kan nasmat ma lolz . ... ..
https://m.facebook.com/bigboyisahfans/?ref=bookmarks
naku har kullum kingboy little of writer's
ππΏβ MIJIN ALJANAH β ππΏ
page 33 - 34
|
|
na king boy isahπ
|
|
__________________________
π5STAR MAR 2017 π
|_________________________|
***** 5 star *****
π5β£STAR ONLINE WRITER'S ASSOCIATION π Β©5SWA
***** 5 star *****
*a gaskiya ina matukar jindadi yanda kuke karfafa mun gwiwa masoyan litaffin mijin aljanah idan nace zan zano sunayen ku page din sai ya kare amma dai zan iya cewa ina gaida ku yan grp din pharida khamshi. samee khaira.hausa novels by king. hausa novels. 3star hausa novels. hasnat novels and others fans. kursiyya ma tace a gaida ku but bani ta gayawa ba*
a rode tayo baya da gudu wani katan kadan garan taga yayi tslle ya shiga gabanta ya tare mata hanya. wani gefe na dakin ta sake yi da gudu tana kara.
kafin kace me kadangarun duk sun cika dakin zakiya suka sata juyawa tayi chan ta hange wani dan karfe cikin dakewa ta ruga da gudu ta dauka
wani karfe nan fa ta dingi kwadawa duk kadan garen da ya nufota tana iho tana dukan su abun takaici duk wanda ta bugawa wannan karfen mutuwa yake kuma sai biyar sun tashi a gun . nan fa kadan farun suka mimike suka fara tafiya da kafafu biyu kmr dai mutane.
nan fa abun ya .kara firgitata sukahau tsire ita da su tana zagaya kuje ru. da gudu wani kadan gare ya rugo bata ankara ba ya shige mata cikin zani ai kuwa tahau yin tsalle tsalle tana iho tana zazage zazage habawa sai ma kara yin gaba da yake yi. ji tayi wani ya kara duro mata a kai yana neman shigar rigarta. fabawa rikicewa tayi kamar mai hauka tahau zabure-zabure ta fadi tana ihu. ji tayi sunyi mata chaa! sun dabaibaye ta.
can taji wani yqna neman ya wuce mata haba wani iban ihooo ta kurma aaaahhhhhhhhh! firgigit ta farka karan ihun da yq fito har waje shine ya tayar da al ameen daga mafarkin da yake yi wato shi kuma kursiyya taje mai a matsayin watq tsaleliyar budurwa.
wash! wash shine abunda yasmeen ke furtawa. batyi ko a'uziya ba balle addu'ar mumunan mafarki.
magana yayi mata cikin tsawa tsawa " ke dake fa nake kin wani tsaya cewa wash wash meye.?
kadan garu..yace kadan garu kuma. eh dr wllh mafarkin kadangaru nayi cike da gidan nan. al ameen yace shirman banza kawai kinxo kin tashi mutun yana mafarkin sa mai dadi yaja tsaki mtsewww yaja blanket dinsa ya rufa Yasmeen kuwa ai gaba daya barcin ma ya tafi abunsa domin nemansa tayi ta rasa.
su kursiyya dariya suka hau yi hahahaha suka kashe da hannu wani tartsatsin wuta ne ya fita a tsakaninsu. tashi sukayi sama suka rabuda juna suka ce sai mu yayan sarkin aljan duk wanda ya tabo mu ya tabowa kansa. suka kuma fashewa da dariya can sai kuma kursiyya ta bata rai marsiyya da ta gano hkn tace auntyna me ya faru.
" kursiyya tayi murmushi tace ba komai yar kanwata kinyi min daidai saidai tashin al ameen daga barci ne ya ban haushi ya katse mu a duniyar so din da muka tsunduma. marsiyya tayi murmushi tace to Aunty ai zaki iya komawa waya isa ya hanaki keda kinsan ba addu'a suke ba balle su sa katanga a tsakaninsu damu.
kursiyya tayi wata shu'umar dariya tace hk ne fa sis kinsan mugayen jahilai ne basu iya komai ba sallahr ma bayi sukeyi ba daga ta asuba ba mai karayi a cikinsu da alamu basu wani riki addini nasu da karfi ba. marsiyya tayi dariya tace yauwa ai nafi san hkn kinga kenan zan yi duk abunda naga dama a gidan nan gidan auntyna ne.
kursiyya tace fadi da ihoo yar kanwata amma gaya min me ya faru ne dake naga duk an kokona ki. marsiyya tace wani mugun malami na hadu dashi lokacin da na shigi jikin wata amma kyale su zan koma bayan na huta aunty.
kursiyya tace to bani lbr mana. marsiyya tace mu sama gu mu zauna tukun.
waje suka samu suka zauna tukun marsiyya ta fara da ce wa.....
***
babban malami ne da charbinsa a hunnu. naga wani mutumi nayi masa iso zuwa cikin gidan. babban malami ne a garin dauran aikin sa ne ruk'iyya aljani duk taurin kansa saidai in bai hadu da malam nasir mai ruki'ya ba domin har ynz bai taba yin ruki:ya kuma aljanin ya dawo ba.
matar da take sanye da hijab sai sharar hawaye take dayar kuma da alamu babbar diyarta ce take lalashin ta. tana ganin malam nasir kuwa ta fara magiya. malam dan allah ka taimaki rayuwsr yata bata da laifi zasu kashe min ita malam dan girman allah kaa rabasu da yata. sun neman halaka min basmah. kuka yaci karfinta.
malam ya kalle ta cike da tausayawa yace kwantar da hankalin ki isha'allah wahalar yarki tazo karshe ki share hawayen ki. ina marar lafiyan malam ya tambaya. dakin suka nuna mishi malam ya juya ya kalli dakin a kulle yake. da kwado malam yace me yasa aka kulletaa daki ya kalli nuhu dake shine namiji babba a gidan yace maza jeka bude ta.
nuhu duk a tsorace yake domin basmah ta bashi mamaki matuka irin karfin ke tare da ita domin karti matasa majiya karfi kusan mutun ashirin ne ya kama basmah aka turata daki.........................
tofa ga marsiyya kun samu friends
kingboyn kune little of writer's
ππΏβ MIJIN ALJANAH β ππΏ
page 35 - 36
|
|
na king boy isahπ
|
|
__________________________
π5STAR MAR 2017 π
|_________________________|
***** 5 star *****
π5β£STAR ONLINE WRITER'S ASSOCIATION π Β©5SWA
***** 5 star *****
*this page dedicated to you my best friends hakika ku masoyanane masu san ci gabana husaini atk tanko - Prince abdullah - zainudeen zain. ina jijina gare ku masu gidana*
nuhu yace malam wllh akwai matsala gaskiya ina tsoran bude dakin nan domin basmah fa inaga aljanun dake jikinta sunfi dubu malam karfin nata yayi yawa. malam yayi.
murmushi yace kai dai ba umartar ka nayi ba jekaka ai watar da umarnin da na baka. basmah dake cikin daki lekowatayi ta windo tare da wata mahaukacinyan dariya hahahaha wai malami kuka kirawo ni kuwa zan gwada muku cewa ba mai rabani da basmah hahahahah kai malam ina baka shawara da tun kafin in fito kabar nan gidan domin bazaka iya ba zaka sha wuya ne a banza.
hahahahaha wata iriyar dariya ce mai fita wani ruwaruwa. .
ta kalli nuhu tace kai kuma ina jin haushin ka dama da kaine aka kamani Aka sakani wannan dakin ko wato kaine ma ja gaba to ina maka albishir da ranar gamamu da kai kuma ina fatan yaune.
nuhu cik ya tsaya a inda yake ya fara karkarwa jin maganar basmah din ko ince aljanar ta.
malam yace la'anana ni kike wa barazana shin kinsan ni ko wanene. hahahaha tayi darya hade da cewa to kai din waye bayan bil adama baka da komai kuma baka isa kaja dani ba idan kuwaka takura zakaga fushina hahahaha.
malam yace ni ba kowa bane kuma bani da komai sai ayar allah kuma da ita nake takama kuma da ita zan fitar dake a jikin wannan baiwar allah. ya kalli nuhu yace maza kaje ka bude dakin can ba abunda zai sameka.
nuhu yace malam wllh aljanun jikin basmah mugaye ne kaji irin su fa domin ita kanta ba barinta sukayi ba balle mu din .
nasmat ta kalle ni tace wacece kuma basma nace uhm muje zuwa zaki ji a gb ba ynz ba tukun..
sarakuwa ama tace in kaine ko kece nuhu zaki je???????? ni dai nace...
umma tace zo muje mu kamota hauwa. hauwa ta kalli basmah taga sai wani huci take hauwa"u kam cewa tayi maama wllh tsoranta nake ji baxan iya ba.
.
malam ya fahimci tsoro suke ji. nace tabb wuya tayi wuya kaga uwa na tsoran yarta.
malam ya kalle su yace bafa abunda zatayi muku domin ynz a daure suke duk wani aljani dake gadan nan yanzu na daure sa ba inda zaije. duk da haka hauwa kiyawa tayi.
malam ya kalli nuhu yace kai maharamin tane ku kamota kaida umnanta. tafiya sukayi duk su biyun a tsorace sukaje gun amma suka kasa kamota domin wani irin kallo da basmah din keyi musu idan ta ya wani juye ya dawo baki kirin bata ce musu komai ba saidai ido da take binsu dashi. domin ta galabaita sosai. saida malam ya kara musu mgn tukun suka kamota malam yace hauwa ta shinfida tabarma kuma ta kawo ruwa a kwano.
da sauri ts shinfida musu katuwar tabarmar nan su nuhu suka ajiye basmah malam yace su tayar da ita zaune. malam ys fara suburbuda addu'a yana tofa mata. sai jibi take.
kira yake zaki fita ko bazaki fita ba.2 amma shiru nan fa ya kara jawo wasu surorin ya tofa mata.
wani uban iho ta kwarara ahhhh! kuma sai tayi shiru tana wani irin nunfashi. malqm saida ya tofa mata ayoyi kusan sau biyar amma shiru marsiyya taki magana. .
malam yace ku samo min ruwa a kwano da barkono. hauwa ta zaro ido tace na shiga uku barkono kuma malam kamar za'ayi girki.lolz umma ta harari hauwa tace zaki jene ki dsuko abunda ake bukata ko kuma shirme zaki tsaya yi mana.
tace umma naga ai ba girki zamuyi ba kuma yace had...... ke ni ki wuce ki dauko ko ranki ya baci yanzu nan.
juyawa tayi ta nufi dakim da sauri ta dauko abunda akace ta kawo. malam yayi addu'a a barkonan ya tsoma a ruwa tukun ya yarfa mata.
ahhhh kana toyani ka toyani malam. naji na toyaki me yasa tun farko kika ki yin magana? shiru tayi. me yasa kikayi shiru nake tambaya. nan ma shiru tayi.
malam, yayi kmr yanda yqyi dazu nan ma iho tayi bayan hk batayi mgn ba.
ran malam ya mugun baci domin duk aljanun da yake ruk- yah bai taba haduwa da mai taurin kai irin wannan ba wai duk abunan da ake taki mgn chabb. nan take malam ya fara jawo wasu ayoyi yi yake yi ba tsatsayawa ita kuwa ba abunda take sai iho wayyyoo! wayyy! ahhhh!
malam baiko kulata ba yaci gaba da jawo aya.can fa dataji ba haza ta farq "zanyi magana kana toyani malam zanyi mgn fa nace. malam ya dan dakata tukun yace to yi mgn ya sunanki. shiru sukaji yasunanki nace. nan ma shiru taki magana.
hauwa da umma duk a tsorace suke domin ita hauwada duk ta wani makalkale jikin umma wai tsoro take ji
mΓ lam cigaba yayi da karatu ba kakaftawa domin kuwa ta fusata shi. ihoo take tana fadin zanyi magana wllh zanyi zanyi ahhh! wayyo jikina malam kana toyani fa zanyi mgn nace.
baiko saurare taba yaci gaba da karatu yana jayo aya dadai taji ba haza sai ta fara ihoo tana cewa sunana marsiyya. kabar toyani nace sunana marsiyya.
malam yace ke musulma ce ko kafura? shiru tayi yakara tambaya nace ke musulma ce ko kafura. shiru tayi malam ya kama baki