Author : King Boy Isa Category : My Hausa Novels
star *****
π5β£STAR ONLINE WRITER'S ASSOCIATION π Β©5SWA
***** 5 star *****
...
.
bayan yan grp sun danyi shiru suna nazari kuma sai suka ce al ameen 70% dursum 60% al ameen kalamai yayi amfani da su zallah dursum kuma yasa ka kirari a ciki bayan kuma nan dandalin soyayya ne.
dursum yaji haushi sosai domin a lokacin left yayi daga grp din. kursiyya ta saki yan kawuna luv tana farin ciki nan fa ba bata lokaci tace a daura aure. al ameen da ya dau abun wasa gashi dama da jan fada a whatsapp ga zolaya da san wasa da nishadi. nan aka shiga shirye shiryen aure a grp.
shi ba ruwansa baisan ko suwaye ba baisan ko yan wane gari bane ba sunnayen su ma ba tambaya yayi ba sai wanda akasa a login nan fa aka daura aure kursiyya da al ameen ango cikin barkwanci. abunda ya lura kawai shine suna matukar bawa kursiyya girma.
to ko prvt baibi kursiyya ba bayan sun gama hirar su a grp ya sauka cikin farin ciki yayi barcin sa mai dadi bai sake hawa whatsapp din ba sai ynz. da ya bude yaga kursiyya ta biyo sa.
ynz bata onine murmushi yayi tukun ya mata reply kmar hk.
wa'alaiki slm amarsu ta ango amarya bakya laifi ai ba matsala in kin shira ko ynz ni a kawo min amaryata. yayi sent abun mamaki yana turawa kawai sai ganin ta yayi a online oyoyo ta fara mishi tukun tace to shikenan ango na yau za'a kawo maka amaryar ka kuwa. ka dai tana di kaza ko?
icon din dariya yasa tukun yace kwarai akwai kaza. ...
sauka yaga kursiyya tayi daga online murmushi yayi tukun shima ya kulle data ya jona carji ya kwanta.
Yasmeen barci take abunta nan fa ta shiga mafarki. zaune take cikin shiga ta alfarma a parllo nan fa ta fara jin goda yirrri,! yrii! gabanta ya shiga faduwa ga gudar kara nufo gidan akeyi.
bude kofa aka yi nan ta zurawa kofa ido tana kallan ikon allah.
wasu fararen yan mata ne maso kyau kamar larabawa suka dinga burarowa gidan tana kallan fuskar kowa sai wata ta tsakiya da fuskanta ke rufe da wani gyale mai duhu.
bata ce da su komai ba ido kawai take binsu da shi. kujerar da ta kalli Yasmeen a nan aka zaunar da amaryar sauran yan matan kuma suka zagaye ta.
wata tsohowa ce Kyakyawa fuskanta duk furfura ta zo ta zauna kusa da amaryar nan fa ta fara cewa
to uwar gida ga abokiyar zama mun kawo miki duk da dai ta girme ki yanzu tanada shekara 600 amma hakan bazai sa aki kiranta da kanwarki ba domin ke muka iske a gidan kece uwar gida ki tauke ta kamar kanwarki kinji.
Yasmeen gyada kai tayi abun ya daure mata kai . tsuhuwar ta juya ta kalli amaryar tace to kursiyya ga yayarki nan uwar gidan ki ki bita sau da kafa kinga ita mutun ce yar adam tana da rauni dan haka duk abunda zata miki kiyi hkr ki kyale..
ta karfinku ba daya ba. nasiha akawa amarya sosai nidai kallo ne nawa. tsohuwar ce ta juyo ta kalle ni tace inane dakin amaryar.
banyi gardama ba na nuna wani bangare inda ba kowa a ciki na nuna da hannu. tashi sukayi suka nufi gun. har sun kusa shiga.
amaryar naga ta tsaya ta cire mayafin da ke kan nata. sai da na fado kasa daga kan kujera dan tsabar tsorata fuska lafiya lau kyakyawa rabin fuskanta kuma abun tsoro kamar an toya shi idan kuma ja gashi ya wani zazago kanta kuwa ba gashi sai wasu irin bakaken macizai duk a mimike suke kamar gashin suna wani bude baki..
da wata irin kausasar murya tayi magana : ki shirya fada dani na shigo gidan mijina kenan ba abunda zai fitar dani kuma nasha alwashin sai na fidda ke daga gidan nan hahahahaha ta saki wata dariya da tasa duka parllon girgizawa. .
firgigit na tashi na farka. tsoro ne ya shige ni na juya gefe naga al ameen nata sharar barcin sa. ni fa al amarin nan gaba daya ya fara bani mamaki miyake shirin faruwa dani ko dai aljannune ke san su rikita ni ko kuma mayune dazu nayi mafarkin kishiya aljana kuma ynz ma hk kai wllh bazai yuyuba bari gari ya waye wllh sai na dau mataki inaga mayu ne kawai.
tunani take a zuciyarta ko taje wancan bangaran ta gani. sakkowa Yasmeen tayi daga kan gadon ta nufi kofan fita parlllo wai sai taje ta gani domin ita mafarkin ya tsorata ta. a wankali take bude kyauran bedroom din me zata gani kuwa. nadis da gudu tayo baya wai ita ta tsorata barata iya bin bayan Yasmeen taga me zai faru ba nace dama aiki ai sai maza daka kuma sai mata ban takardar in bita......................................
king boy β₯ nadis
ππΏβ MIJIN ALJANAH β ππΏ
page 13 - 14
|
|
na king boy isahπ
|
|
__________________________
π5STAR MAR 2017 π
|_________________________|
***** 5 star *****
π5β£STAR ONLINE WRITER'S ASSOCIATION π Β©5SWA
***** 5 star *****
...
.
parllon ta gani duhu rudum an kashe goluluwan bango ta shiga lalube har ta dai ci sa'a ta lalibo switch din ta kuna wutar tukun ta yi aji yar zuciya tukun ta nufi step din.
a tsorace take tafiyan a hankali kamar marar gaskiya kofan dakin ta murda a hankali duhu rudum dakin nan ma tayi lalube ta kunna kwan wayam ba komai a dakin sai da ta shiga ta duduba har toilet da ko'ina na dakin tukun ta fito.
bata kashe wutan ba zata jawo dakin kenan taji wata irin guda ayyirii yirriii da sauri ta saki kofan ta ruga da gudu kofan dakin ta ta kusan zuwa ta dan juyo gani tayi dakin duhu rudum kaman yadda ta iske sa.
wutar parllo taga ta fara farfari can jumawa kuma sai ta dauke. wajen kunnawa ta lalubo ta kunna. juyowar ta ke da wuya sukayi ido hudu da wasu kalar hallitu cike da parllo zazaune a kujeru.
cikin daki tayi da gudu har tana tuntube. ko rufe kofa batayi ba ta fada kan gado ta wani kudundune duk ta makalkale al ameen. ta dan juma a hk tukun barci ya yi gaba da ita.
sis zeesa na tambaya wai wancan halittun fa na parllo.? tace ai yan kawo kursiyya amarya ne πππ
kursiyya nagani sanye take cikin wata doguwar riga baka fuskanta ba kyan gani domin rabi na mutum rabi aljan.
hannunta dauke da plat a ciki da katuwar gasasar kaza. ta nufi dakin Yasmeen . kan mirror ta ajiye kazar tukun ta nufi gadan da suke kwance.
saitin Yasmeen ta tsaya tsugunawa tayi ta dan shafi fuskan yasmin da hannun nan take naga ta rikide ta dawo Yasmeen sak.
(ni da zeesa sakin baki mukayi muna kallan ikon allah ga Yasmeen biyu π¦)
chamak ta dauki Yasmeen ta bace da ita bata dade ba sai gata ta dawo ita kadai ba Yasmeen din
kayan jikinta ta cire daga ita sai pant ta bude Wadrop din Yasmeen wata yar share sharen riga tasaka wadda tasan lalai zata tadawa al ameen sha'awa bayan tasa rigar ne
plat din kaxan ta dauko ta ajiye a kan carpet tukun tazo ta hau jijiga al ameen ta tada shi. cikin barci ya bude ido da niyar yayi mata fada. suna hada ido da ita naji kuma yayi shiru baiyi mgn ba.
cikin wata sasanyar murya irin wacce Yasmeen take yi mai tace sweetyna kaxa na dafa maka sauko muci. ido kawai ya tsira mata domin gaba daya ta tafi da imaninsa wata irin sha'awar ta yake ji.
saukowa yayi takama hannunsa suka nufi toilet sanda ya yi brush tukun suka dawo bayan sun zauna yake ce mata. "Yasmeen amma me yasa tun da wuri baki dauko kazan ba sai ynz wajen karfe 1:30 fa.
wani mugun bakin kishine ya zo ya tsaya mata a makoshi jin ya kirata da yasmeen amma ba yanda zatayi dole tayi hakuri ya dinga kiranta hakan in har tana san zaman lfy.
murmushi tayi tukun tace wannan wani plan ne da na shirya ta fada lokacin da ta yanko wata tsokan nama ta ce bude bakin ka masoyina.
daga bakin yayi lokacin da yake kallan fuskanta. wow gaskiya baki taba soya kazar da takai wannan dadi ba tunda mukayi aure.
murmushi kursiyya tayi a xuciya tace au ashe dai duk da tana mutun na fita iya girki ma. nan fa suka shiga ciyar da juna tsakanin su saida suka kusan cinye kaxan duka sannan kowa yace ya koshi.
wanko hannuwan su suka je yi tun a ban dakin al ameen ya fara rikice mata domin duk shashafa tan da yake bai isa ba sai faman cire mata rigan da ke jikinta yake.
da kyar ta samu ta jawo shi zuwa kan gado nan fa suka shiga salan so. al ameen yaga canji sosai irin salon da kursiyya take mishi.
kursiyya dadi take ji sosai domin yaune daranta na farko ta cika burin ta ta xama cikakiyar matar aure ynx. nan fa tasha alwashin ba wanda ya isa ya rabata da al ameen mutun ko al jan.
duk da tasan ba aure tsakanin mutun da aljan amma ita tayi kuma ba wanda ya isa ya hana. sai wajen karfe 3:40 al ameen ya samu yayi barci kursiyya ma yi tayi kamar tana barcin.
sai da ta lura yayi barci tukun ta mike juyewa tayi ta dawo kursiyyar ta ta asali. batt ta bace
zeesa zata ruga na riko ta lolz.
...........................
king boy nadis
ππΏβ MIJIN ALJANAH β ππΏ
page 15 - 16
|
|
na king boy isahπ
|
|
__________________________
π5STAR MAR 2017 π
|_________________________|
***** 5 star *****
π5β£STAR ONLINE WRITER'S ASSOCIATION π Β©5SWA
***** 5 star *****
...
.
ba'a dade ba naga ta dawo da Yasmeen kamar yanda take dai har ynz barcin ta take yi.
karfe 4:30 ta farka nan ta fara tashin al ameen ya tashi yayi shirin masalaci. tashi yayi yana mika my Yasmeen wllh kin gajiyar dani sosai jiya amma ke naga alamun ko a jikin ki ko. wai har kinyi wanka kenan? ya fada bai jira amsa ba ya tashi ya nufi bathroom domin yayj wanka.
Yasmeen kuwa nan ya barta maganganun sa nayi mata yawo a kai to me yake nufi ne. dora hannunta da zatayi taji lema da sauri ta kunna fitila duk gadan a bace yake. nan fa abun ya kara daure mata kai.
to wai yaya al ameen ko dai mafarki yayi. to kuma ai in mafarki ne baici ace ya bata gadan nan har haka ba. nan dai tq tashi tana ta tunane tunane.
kafin ya dawo ta cire zanin gadan ta canza wani ta feshe dakin da turaruka masu kamshi domin irin wani wari wari da taji yana tashi. zuwa tayi ta dauro alwala. tukun ta dawo ta canza kaya ta tsaya jiransa domin shi yake jinta sallar asubah.
ba'ajima ba ya fito nan suka tada sallah bayan sun gama. nan ya koma barci ita kuwa ta nufi ketchin domin hada musu breakfast.
sai da ta gama komai tukun taga ynz ai karfe 6:30 lokacin tashin al ameen baiyi ba hakan yasa ta koma itama ta kwanta barci yayi gaba da ita.
karfe 7:30 kursiyya ta bullo a dakin daidai Yasmeen nan ta sake sauyawa zuwa Yasmeen ta kuma dauke Yasmeen din. tada al ameen tayi suje suyi break ya tashi nan ta durkusa ta gaida shi. yayi mamaki domin kuwa yau ne karan farko yasmeen ta gaida shi.
( zeesa tayi dariyar mugunta tace malam kursiyya dai ta gaida ka ba Yasmeen ba. dankwashin ta nayi nace kaji muguwa)
amsawa yayi tukun ta kama hannunsa ta ja sa har dinner inda Yasmeen din gaskiya ta jera abincin. a baki ta dinga bashi yana ci. wani irin san Yasmeen ne ke kara shigar al ameen.
domin shi tun jiya ta yi matukar canza mai. " Yasmeen amma dai kwanan nan kina amfani da mgnin mata ko. baisan lokacin da wannann tambayar ta kubce mai ba.
kursiyya tayi murmushi tace kwarai kuwa ango na me ka gani ne.? ina fatan dai kaji dadin hakan.
sosai ma ya fada lokacin da ya jawo ta jikinsa ya dorata a kan cinyar sa bakinsa ya hade da nata ya fara tsotsa. kursiyya ta ga ya fara wuce gona da iri yana neman zarcewq cikin sigar wayo ta kwace jikinta.
haba my sweety ango na ka bari sai ka dawo mn ni fa taka ce ina nan ina jiranka ynz zaka makara kaga har 8:00 fa.
al ameen da duk ya wani rikice ya canza kamanni da kyar ya iya sarrafa kansa ya mayarda sha'awarsa ciki ba dan yaso ba. jakan sa ta miko mai ta raka shi har mota saida ya shiga mai gadi ya bude mai gate tukun ta dawo.
dakin Yasmeen ta bullo ta maido da ita tukun ta bacce bat.
Yasmeen bata tashi ba sai karfe 8:30 tashi tayi taga al ameen baya nan ta tashi tana murzar ido ta nufi ban daki duk ta duduba bata ji motsin sa ba.
haka ta fito parllo shiru dinner ta hanga alamun anci abinci. da sauri ta karasa gun ta tarar anci abinci hmm wato yaya al ameen shine ya taso yaci abinci ba tare da ya tayar dani ba ko.
zaunawa tayi tayi break din itama tukun jawo wayanta ta kira al ameen da sauri ya dauka ganin ita ke kira. kai my wife gaskiya kina ji dani ba yanzu muka rabu ba amma har kin kira ni ko wani abun ne?
chakwakiya....,............................
king boy nadis
ππΏβ MIJIN ALJANAH β ππΏ
page 17 - 18
|
|
na king boy isahπ
|
|
__________________________
π5STAR MAR 2017 π
|_________________________|
***** 5 star *****
π5β£STAR ONLINE WRITER'S ASSOCIATION π Β©5SWA
***** 5 star *****
...
.
*_WANNAN PAGE NAKI NE KAWAR KURSIYYA NASMAT. NA GODE DA KULAWA ALLAH YA KARA BASIRA SANNAN MUNA JIRAN NEXT BOOK DINKI DUK KINGAM MU NAN CIKIN JIRA. WE LUV U TOOOOO MUCH*_
kan Yasmeen ne ya kara daurewa. "dawa kuka rabu ynz din?
ke din mana fatan dai za'a min tanadin abincin rana mai dadi kamar na safe domin naji dadin abinci sosai my.
lokacin ta dan ji sanyi amma fa har ynz hankalin ta ba kwanciya yayi ba wai me ke shirin faruwa ne a gidan nan ita ga baki daya kwalwarta ta juye ma. katse wayan tayi domin ta dan samasasauci.
kursiyya da ke tsaye a gaban yasmeen saidai a wannan karan yasmeen bata gani ta kishi ya cikata wai ana waya da mijinta. hararen yasmeen tayi a zuciya tace wai ke nan kishiyata ce hmm to ai kuwa zaki sha wuya domin kin daina moran duk wani dadi daga gun al ameen sai ni nan kursiyya yar sarkin aljan amarya al ameen.
Yasmeen abubuwan fa sun fara yawa amma tace baza ta fada a gida ba tukun.
kofan dakin kursiyya ne ya fara bodewa yana rufewa da kansa a hankali ya farayi har kuma ya farayi da sauri ya bude gam ya kuma ya kuma rufe. tashi tayi a dan tsorace ta nufi kofan. cikin sanda ta je kofar dakin ta leka. ba kowa. motsi taji cikin bathroom.
hakan yasa ta nufi gurin tana budewa kuwa taga wani dan jariri cikin bath jini ne cike da bahun wanka dan jaririn sai fachali yake cikin jini yana kallan ta yana dariya. iho ta saki ta yo baya a guje ta futa a dakin bata xamie a ko'ina ba sai dakinta.
kullo dakin tayi tana karkarwa ta lalibo number mai gadi tayi calling. da sauri ya dauki wayan ganin mai kira. hello hajiya me ake bukata. malam lawali dan allah kayi sauri ka shigo gidan nan ba lafiya pls kazo ka gani.
to hajiya gani nan wayan yana yankewa ya shiga daki ya dauko wata sharbebiyar ada ya nufi cikin gidan da gudu. assalamu alaikum hajiya miye ne a hankali ta bude kofa ta leko saida ta tabbatar da shine tukun ta fito.
yauwa malam lawal wllh aljanune a cikin gidan nan dakin ta nuna mai shiga kaga ni malam lawal wllh aljanu mgnr take a wani firgice. aljanu kuma. mu ai ba tsoran su muke ba su din ma inji man lawal kursiyya dake gefe tana kallan su ciza lebe tayi jin ciki baki gurin mai gadin. a hankali ya nufi kofan dakin cikin tako irin ya san aiki da kafa ya tura kyauran.
ya lalaka ba kowa hakan yasa ya shiga ko'ina baiga komai ba. ya dawo ya sanarwa Yasmeen ba kowa a ciki. tace ka duba cikin bathroom fa.
eh na duba banga komai ba. Yasmeen tace muje inga. gaba ya shiga ta bishi baya. ya bude bandakin wayam bataga kowa ba. hakuri kawai ta bashi tace tsorata nayi ashe.
lawal yacr ba komai wannan makeken gida ke kadai ai dole ki dinga tsorata dan idan wata ce wllh baratq iya ba. godiya tayi mai ya fito ya tafi. Yasmeen tq dade a gun tana mamaki ita da taga abun kirikiri ba mafarki ba yanzu kuma gashi taga wayam ba komai.
kursiyya aljannah tsaye take tana kallan Yasmeen amma ita Yasmeen bata ganinta. ta wani murtuke wata yar kwalba dake saman wani dan bench ta taba. ta fado kasa. da gudu Yasmeen tayo waje.
ita kuwa kursiyya me zatyi in ba dariya ba. haka nake sanki bakya addu'a ni kuwa zan sakata in wala a gidan nan yarinya yau aka fara wasan zamuga waye matar al ameen tsakanin ni da kuma ke.
dr al ameen bayan ya gama duba mararsa lafiyan dake karkashin kulawansa ya dawo office yana yan dube dube. wayarsa ce tayi kara. kursiyya yagani. murmushi yayi yace kai gaskiya nima shege ne har na sace zuciyar wannan yarinyar haka daga haduba.
(nida nasmat dariya mukayi nace kinji fa baisan tuni ya aure ta har sunci amarcin su jiya ba.lolz...............................
king boy
ππΏβ MIJIN ALJANAH β ππΏ
page 19 - 20
|
|
na king boy isahπ
|
|
__________________________
π5STAR MAR 2017 π
|_________________________|
***** 5 star *****
π5β£STAR ONLINE WRITER'S ASSOCIATION π Β©5SWA
***** 5 star *****
...
.
in dedicated to you oll members of hausa novels by king
cikin sasanyar murya tayi mai sallama. shiru yayi na dan seconds domin