Author : Jeedderh Lawals Category : New Hausa Novels 2026
naci gaba da daddaga kayan.
Ina cikin fito da kayan Janan ta kirani, ni sai lokacin ma na tuna babu wanda na kira, na daga wayar cikin dariya saboda nasan korafi ta kira ta min. Illa kuwa, ina dagawa ta fara, "haba baiwar Allah, dokin sabon gida har yasa kin fara mantawa da mutane ne?".
Nayi dariya nace "don mantuwa kam na manta dake, sai dai ba santin gida bane yasa na manta dake wallahi, gajiya ce da yunwa, gashi tunda muka sauka bamu zauna bane shi yasa".
Tace "to sannunku. Nima tun dazu naji Yaya yana fadawa Ummah kun isa lafiya, shine na zauna ina jiran a kirani sai kuma naji shiru, shine na biyo baya. Kun sauka lafiya?".
Nace "lafiya lau, ya su Ummah?".
Tace "lafiya. Ya gidan naku?".
Nan na mike kafa na fara labarta mata labari, har sai data fara cewa in dan saurara sannan na dakata ina dariya, "Allah don baki ga gidan bane Jan, ya hadu fiye da tunaninki. Bana tunanin duk shige-shigenki kin taba shiga gidan daya kai wannan wallahi".
Tace "ai in Allah ya yarda zamu zo ganin gida ni dasu Yaya kila satin sama, tunda Yaya ya gama ginin kusan shekara nawa yanzu, babu wanda ya taba zuwa sai dai su Yaya Auwal da naji suna fadin haduwar gidan".
Nace "haba? Dama ba'a taba zama a gidan nan ba?".
Tace "wa zai zauna? Shi kadai yake zaune a gidanshi. Anty Ameerah dama bata taba zama a gidan ba saboda lokacin da aka yi aurensu tana karatu, kuma yana cikin yin ginin ne, bayan ya gama kuwa taki komawa. Ita kuma Anty Raheemah dama bai taba cewa zai kawota nan ba, don't know why though!".
Na jinjina kai, "lallai yayi kokari ba kadan ba. Zama a gidannan kai kadai duk girma da fadinshi?".
Tace "to yanzu ba gaku nan ba? Dagewa zaki yi ki fara sauke mana yan digwi-digwi yadda zaki ga gidan ya cika nan da dan lokaci, sai ku daina ganin girmanshi".
Wani abu ya dan ratsa zuciya da tace haka, amma sai na dake, na saki wata sarkakkiyar dariya nace "ke fa baki da kunya wani lokacin Jan, duka-duka yaushe aka yi auren?".
Tace "tunda aka yi sati kuwa, ai lokaci yayi babe, yakamata zuwa yanzu ace koma menene ya gama shiga. Kin fara jin canje-canje a jikinki kuwa?".
Na sake fashewa da dariya, wani lokacin haka take kamar wata sintacciya. Ina shirin bata amsa, naji alamun shigowar kira, na duba naga 'Zhaujee', kamar yadda ya kawo min wayar da wannan sunan a jikin lambarshi yana tsalle, nace "you are nuts wallahi. Bari in dauki wayar Yaya ya kira, ki gaida su Ummah".
Ban jira ta gama fadin abinda ta dauko fada ba, na katse kiran tare da amsa na Yaya. Ina dagawa yace "ke da waye ne kuke yin waya tun dazu?".
Nace "Janan ce Yaya".
Yace "ok, ki fito mu ci abinci".
Nace "to". Na kashe wayar na tashi.
Wani tattausan silifas pink, na dauka a cikin kayana na saka. Na dauki turare na kara fesawa a jikina, na dauki wayar hannuna naja dakin na fita.
Suna zaune akan dinning table, da kwanukan abinci a gabansu na same su. Na musu sallama suka amsa, tare da jan kujera kusa da Yaya na zauna, ita kuma Raheemah tana kan wadda take fuskantar shi. Fuskar nan tasha make up har da na hauka.
Yaya yace mana "bismillah ko?".
Na ga Raheemah ta ja plate ta bude ta zuba abinci a ciki macaroni ne aka yi jallop, an zuba kifi da nama a ciki. Maimakon in ga ta mikawa Yaya wanda ta zuba, sai naga ta ja shi gabanta zata fara ci.
Na kalli Yaya naga yana fama da cokali da plate, sai na dan matsa, na karbi plate din hannunshi na zuba mishi abincin, na tsiyaya ruwa a cikin cup shima na ajiye mishi, sannan na fara zuba nawa nima. Ya kalleni cikin dan murmushi, tare da furta "jazakillah", a can kasan makoshinsa. Na maida mishi martanin murmushin.
Ina daga kaina, naci karo da idanun Raheemah tana watso min harara, ni kuwa na daga kafadata sama na fara cin abincin bayan nayi bismillah.
Ban wani ci da yawa ba, na ture kwanon gefe na ajiye. Ban taba cin girkin Raheemah ba tunda nake, don haka ban taba sanin yadda girkinta yake ba sai yau. Kodayake, zata iya yiwuwa yau din rana ce ta kufce mata abincinta yayi gishiri da yaji ya kuma dafe.
Na ci gaba da zama anan duk da cewa na gama, har suka gama cin nasu abincin. Yaya ya tashi ya wuce dakinshi, itama ta mike tayi nata dakin, ta bar kayan abincin anan, suka barni ina zare ido.
Da nima nawa dakin zan koma, sai na jiyo sautin karar talabijin a falon Yaya, don haka na karasa can. Baya cikin falon ma, na zauna tare da daukar remote na latso tashar mbc action na kunna, suna hasko film din Furious 7 kuwa, na gyara zama sosai don ina kaunar film din kwarai.
Ban yi nisa a kallon ba, sai ga Raheemah itama ta shigo. Tana zama, ta dauki remote ta canza tasha, na dan daga kai na kalleta kadan, sai kuma na dauke na maida kan tvn da take ta latse-latse da canza tasoshi. Idan tayi zaton magana zan mata akan haka, zata sha mamaki kam. Daga karshe ma sai na kunna wayata na bude wani document akan pregnancy issues ina dubawa.
Muka cigaba da zama a haka, babu mai ko tari sai sautin wakoki dake fita daga wata tasha data kunna. A haka Yaya Bilal ya fito ya same mu.
Ya umarceta data kashe kallon, yana so yayi magana damu. Nima sai na kashe wayata, na maida hankalina kan shi.
Yayi gyaran murya, ya fara da kara yi mana nasiha da kuma dokoki daya kafa. Yace babu yan aiki a gidanshi, daga maigadi, sai mai ban ruwan fulawa, sai kuwa wata mace da yace zata dinga zuwa tana tayamu da share-share da wanke-wanke, amma bai yarda da girkin yan aiki a gidanshi ba, mun fahimta? Muka ce mishi eh.
Sai kuwa zancen girki, ya tambayemu kwana nawa muke ganin zasu fi zama convenient a wajenmu? Ni dai nayi shiru ina jin suna muhawarar kwana daya ko biyu shi da Raheemag, har sai daya jiyo ya kalleni, Ya tambayeni ya nake gani? Nace ni duk yadda suka yanke daidai ne a wajena. Nan ma na kara karbar wata hararar dai, na nuna kamar ban gani ba. Daga karshe dai suka kare akan kwana biyu.
Yace tunda ita Ameerah bata da ranar dawowa, zamu cigaba da raba girkin a tsakaninmu har zuwa lokacin da zata dawo. Ya kara da cewa bai yarda da fada ba a gidanshi, babu fada kuma babu cece-kuce, yace duk wadda take da matsala game da wani abu, mu tunkari junanmu mu warwareta a tsakaninmu, ko kuma mu fada mishi, sai yasan yadda zai warware matsalar, muka ce to.
Daga nan muka cigaba da kallonmu har dare yayi, sannan na tashi na musu sallama na wuce dakina.
Kayan da ban gama gyarawa ba, na gyara. Na ciro kayan barci na ajiye akan gado, sannan na shiga wanka. Wanka nayi, na wanke bakina da mouth wash mai kamshin berries, na daura alwala na fita.
Yaya Bilal yana bakin gadona a zaune da wayata a hannunshi yana dannawa, ya daga kai ya kalleni lokacin dana fito. Har naja kujerar da aka ajiye a gaban dresser na zauna, idanunshi suna kaina.
Na kauda kaina kamar ban san yana yi ba, na dauki lotion na fara shafawa a jikina. Ta cikin mirror na sake tsintar idanunshi a kaina, wayar ma ya ajiyeta a gefe guda, ya karkato da hankalinshi kaina kacokam. Naji gabadaya na fara takura da kallon kurillar da yake yi min, a gaggauce na karasa shafa man, na mike tsaye da niyar dauko kayan barcina dana ajiye.
Babban tawul ne a jikina wanda ya sauka har kasan gwiwata, na karasa gaban gadon na janyo kayan, ganin har lokacin yana zaune yana kallona yasa na juya na koma bandaki na sanya kayan.
Wannan karon dana dawo, yana tsaye a bakin gadon, hannuwana saye cikin aljihun sweat pant dake jikinshi, idanunshi kyam akan kofar bandakin yana dan murmushi.
Yace "meye na wani guduwa bandaki kuma? Menene ake boye min ne, wanda ban riga na gani ba?".
Na kalleshi blankly kawai ban ce komi ba, na wuce kan gado kawai na ja bargo na rufa.
Ya matso ya janye bargon daga fuskata, "uh uh!! Shariyar menene ake min haka, baby na kamar baki gane ni ba?".
Na sake yin banza na kyaleshi. Bai san tunda na baro su shi da Raheemah a falon nan ba wani haushin shi ya cika ni ba taf? Ji nake kamar in koma in janyeta daga kusa dashi, in jefata dakinta in kulle don ma kada tayi tunanin sake fita ta koma wajenshi, haka nan dai na danne zuciyata na dawo daki.
Yanzu kuwa da nake ganinshi a gabana, tunanin wajenta fa zai koma ba wajena zai dawo ba, naji wani irin matsanancin kishi ya rufe min idanu, kishi irin wanda ban taba jin shi ba.
Ya shafo gefen fuskata daga bayan kunnena zuwa kan lebuna na, cikin nuna damuwa yace "wani abu yana damunki ne? Ko baki jin dadi ne?".
Wani haushin shi ya kara tuko ni, to ko ina ruwanshi ma da wata rashin lafiyata? Koma dai menene, daga karshe dai tafiya zai yi wajen matar shi ya kyaleni anan.
Nace "wai ina ka baro matarka ne ka taho nan? Ta ma san kana nan kuwa?".
Ya daga gira cikin alamun mamaki, kafin wani murmushi ya subuce mishi, ya zauna sosai a gefen gadon.
"a'ah, bata sani ba, na taho yiwa baby na kuma amaryata sai da safe ne. Ko kuwa nayi laifi ne?".
Nace "to ni sani zan yi? Sai ka bari sai ka tambayeta, sai kaji ko?".
Yace "haka ne, bari inje in tambayeta inji kuwa".
Bai jira ya sake cewa komi ba, ya duko ya bani peck a kumatuna, ya mike tsaye yana kallona cikin murmushi, "sai da safe baby na, kiyi barci mai dadi".
Bai jira na amsa ba, ya juya ya fita daga dakin bayan ya kashe min wutar dakin. Na sauke ajiyar zuciya a hankali bayan fitar tashi, ina ji wani irin abu yana mintsinin can kasan zuciyata. Daga karshe dai nayi addu'ar kwanciya barci, na shafe jikina.
Cikin yan kwanakin nan shida, ba karamin sabo nayi da kwanciya a jikin Yaya ba, ban san nayi sabo da jikinshi sosai ba sai da barci ya nemi ya gagareni. Na dinga juyi ina karawa akan gadon, Allah kadai yasan iyaka tsawon lokacin dana dauka, kafin da kyar barci yayi awon gaban dani.
o
Kamar yadda ya saba a Zaria, da asuba ya leko ya tasheni inyi sallah, shi kuma ya tafi masallaci.
Bayan na gama sallar barci na sake komawa. Bani na tashi ba sai daya leko kafin ya tafi wajen aiki, lokacin karfe tara saura. Bayan munyi sallama dashi, na bishi da addu'ar Allah ya kiyaye hanya, na tashi na shiga bandaki nayi wanka. Na fito na shirya cikin riga da siket na paper lace. Dinkin ya matukar karbata kamar yadda ya bi jikina ya zauna sosai kamar second skin. Ni kaina nasan cewa ba karamin gogewa jikina da fatar jikina suka yi cikin dan lokacin wannan ba.
Na fita zuwa falo, babu kowa sai kuloli da flask ajiye akan dinning table. Naje na fara dagawa, indomie ce zallarta da ruwan shayi a cikin flask. Na girgiza kaina cike da tsananin mamaki, Allah dai yasa ba abinda Yaya yaci kafin ya fita ba kenan.
Dama can indomie ban maida ta abinci ba, na maida kular na rufe, na wuce kicin na lalubo gwangwanin oats na fara damawa.
Ina tsaye ina jiran ya dahu, Raheemah ta fado kicin din kamar an jefo ta. Ta bude firjin ta hau dube-dube, da kamar in kyaleta, na dai daure nace mata ina kwana?.
Ta wani dago ta kalleni a dage, taja tsaki ta kara tura kanta cikin firjin.
Abin ya bani haushi ba kadan ba, nace "maida wukar mana baiwar Allah! Sai kace na roke ki wani abu?".
Daga gani dama a wuya take, kiris take jira, ta kalleni, "to na roke ki gaisuwar ne dama? Kaji wani aikin banza ma, har ki wani daga baki ki gaida ni? To an ki a amsa din, ko kina da abinda zaki yi ne?".
Ni da tsabar mamakinta ya kawo ni wuya ma, kasa maida mata martani nayi, ita kuwa tayi tsamnanin ko tsoro ne yasa na kasa magana ko kuwa wani abu? Ta ciro lemun exotic ta maida firjin din ta rufe garam! Tace "ya dai fi miki kiyi shiru din don baki da karfin gwabzawa dani. Masu kwacen miji kawai, idan ma don kinga Haleemo ta kwacen miki miji ne kika yi haka, to ita build taci, kuma nan da watanni biyu zamu je mu sha bikinta mu rakashe, ehe! Ke kuma sai mun ga takamar kwacen miji, zamu ga abinda hakan zai tsinana miki. Da kanki zaki nemi takardar ki wallahi, ko kuma ki kare a haka!". Ta fita daga kicin din fuu!! kamar guguwa.
Na bita da kallo cike da tsananin mamaki, me hakan yake nufi ne? Kuma ma daga maganar arziki sai ta koma ta tsiya, akan me? Naja tsaki lokacin da naga har oats din dana dora ya dahu ya dafe. Na sake jan tsaki lokacin dana zubar dashi na sake dora wani. Cikin tsananin tunane-tunane da saka da warwara na gama hada oats din, na juye a cikin mug na cicciba na wuce dakina.
Bayan na karya, na dauko wayata na kira su Fatsu muka gaisa, mun jima muna hira da ita, tana ta mij nasiha da nuna min muhimmancin hakuri, daga karshe ta ba Malam shima muka gaisa. Shi addu'o'i ya bani wadanda zan dinga yi safe da yamma na neman kariya, kafin shima ya dora da nashi waazin da nasiha, daga karshe dai muka yi sallama.
Ina kashe wayar na kira Sailu itama muka gaisa. Ranar dai wuni nayi kiran wayar yan uwa da abokan arziki. Bayan na gama kuma na dauko textbooks ina dubawa da yin bita, nan da sati biyu zan fara yin internship dina.
☆
Yau ma kamar jiya, sai da Yaya ya leko ya min sai da safe kafin mu kwanta.
Washegari na karbi girki, da safe zamu dinga karbar girkin bayan wadda zata fita tayi karin safe. Yaya yana fita na dauki makullin dakinshi daya ba kowaccenmu, na shiga na gyara mishi dakin tsaf. Na yaye zanin gadon dake kai na shimfida wani, shi kuma na hada shi da kananan kayanshi na wanke su tas, bayan sun bushe na goge.
Bayan na gama turare dakin da turaren wuta, na dauko kofi na tofa wasu muhimman addu'o'i da Malam ya koya min jiya, nabi lungu da sako da kowace kusurwa ta dakin na yarfa wannan ruwa. Sauran ruwan kuma nayi girkin abincin dare dashi. Kai hatta da ruwan da Yaya zai sha sai dana tofe shi da addu'a.
Sai dana tabbatar da komi ya hadu lafiya lau, lokacin har Yaya ya dawo daga wajen aiki, sannan na fada bandaki na tsalo wanka.
*☆⋆39⋆☆*
Satinmu uku da dawowa Abuja, na riga na saba da yanayin garin, gidana, mijina, da abokiyar zama na.
Tuni na riga na fara zuwa aikin internship dina, daga aikin safe sai na rana nake yi, bana yin na dare. Har yau dai babu bayanin uwargida Ameerah. Bata dawo ba, Yaya kuwa bai taba tado maganar game da ita ba, nima dai ban taba tada mishi zancen ba. Don haka muka cigaba da raba girkinmu a tsakaninmu ni da Raheemah, wadda har yau bata sake zaki ba, kamar ma kullum kara rura mata wutar masifa da neman magana ake yi kullum.
Kullum a shirye take da fada, kiris take jira taga gilmawata a tsakiyar gidannan, zaka ji ruwan habaici da bakaken maganganu ya fara tashi, malka-malka kuwa. Ban taba tanka mata ba, kai ban ma taba nuna mata na kula da abinda take yi ba. Illa iyaka idan na fito mun hadu da ita a falo, in mata sannu, ta amsa ko kada ta amsa, ni dai na fita hakkinta.
To sai ma ranar girkina ne muka cika haduwa, ranar da take yin girki wuni nake yi a daki abuna. Babu ruwana da ita, in wuni ina shan fruits da kayan makulashe, sai da dare idan Yaya ya dawo daga wajen aiki nake fita mu ci abincin dare, duk da dai shima ba kullum ba, don abincin matar nan is terrible Sam bata iya girkin azo a gani ba. Abinda zata iya dafa maka ya dahu, indomie ce, sai kuwa spaghetti ranar da sa'ar ta ta kai sa'a.
Don haka bata da damar gasa min magana a gaban Yaya, duk da cewa ta dauko hakan, sai da Yaya ya tsawatar mata sannan.
Da ta tsiro da maganar kin cin abincina, sai dai ta shiga kicin ta girka kayanta, a raina ni kam nace mata umma ta gaida assha. Sai da Yaya ya fatattaketa sosai, nan ma ta hau cewa wai ya daure min gindi, yana sawa ina raina mata wayau. Yace wani irin rainin wayau? Yace shi fa ya kula da take-takenta na rashin son sasanci da zaman lafiya, yace kuma ta kiyayi kanta don ba zai lamunci hakan ba. Abinci ne, ya hana wata ta girka nata daban, idan wata ta girka dayar taga bai mata ba, ta bar mata kayanta taje can ta karata ita kuma da yunwa. Da wannna aka tashi dai baram-baram.
Sai kuma lokacin dana fara zuwa wajen aiki. Ranar farko da zan je Yaya ne yayi jigilar kai ni da kanshi, washegari kuma direban gidan ya kaini, zai kuma cigaba da kaini da daukoni daga ranar. Ina daki sai jiyo tashin muryoyi na dinga yi, rigima suka yi sosai akan ya bada mota ana jigilar kaini wajen aiki.
Yace "kina nufin in barta tana kai da kawowa a cikin motocin haya ne, bayan ina da ikon da zan ajiye motar da zata yi jigilarta ne?".
Tace