AZATONA COMPLET HAUSA NOVELS BY Jeedderh Lawals.txt

Author :  Jeedderh Lawals Category :  New Hausa Novels 2026

Chapter   43 / 52

126K to 129K   out of 155.4K words

da hasken fitilar wayata. Na kunna microwave din, na koma falo na zauna akan dinning ina jiran abincin ya dumama. Fitilar na kashe, naci gaba da zama a cikin duhu, a zuciyata ina ta saka da warwara akan wannan sabuwar matsala data tunkaro ni.
Zato zunubi, amma da sai ince ga wadda ta aikata min wannan danyen aiki, sai dai shi zargi bashi da kyau. Kawai dai yanzu zan dinga yin takatsantsan ranar girkina kawai, shine mafita.

A hankali naji an turo kofar daki an fito, na daga kaina daga zuzzurfan tunanin dana fada. Raheemah ta fito itama tana haska fitilar wayarta tana taku sadaf-sadaf kamar barauniya, ganin ta wuce kicin kai tsaye yasa na dan yi murmushi. Da alama itama yunwar ce ta korota.

Ban yi motsin kirki ba balle ta ganni, na kara yin kasa da kaina ina wasa da yatsun hannuna.

Dare da baya raina abin ji komi kankantarshi, duk wani dan karamin motsi da zata yi ina jin shi, zuwa can naji tashin murya kasa-kasa alamun tana waya, hatta da daya bangaren data kira ina ji.
Cikin barci wadda ta kira din ta fara cewa, "ke wani irin shashanci ne haka zaki wani hau kiran mutane da tsakiyar daren wannan?".

Tayi kasa da muryarta sosai, "Momcy, na manta yadda zan sanya wannan maganin ne. Kin san kuma Malam yace idan ya wuce yau ba zai yi amfani ba".

Na zare idanu sosai, amma sai na kara lafewa ina sauraronta.
Sai da tayi hamma sannan tace "wanne daga ciki? Na turaren ko kuma na ci?".
Tace "na ci dai, ai na riga nayi na turaren tun yaushe...", ta ja dan tsaki, "... amma ni har yanzu ban ga yayi wani abu ba, anya kuwa ba asarar kudi kawai muka sake yi ba?".

Tace "ina, shi mai nema ai baya gajiya. Ba zamu gajiya ba, balle ina da tabbacin wannan din zai yi. Kin san fa aikin malamin nan kamar yankan wuka, kin dai ga irin aikin da yawa Halima. Ke kanki ba da taimakonshi bane kika shigo gidan ba?".

Tace "haka ne, kawai naga kwata-kwata aikin baya yi ne yan kwanakin nan. Duk inda muka je sai dai suyi ta cinye mana kudi. Shima wanda nake zuba mishi a abinci fa har ya kare, amma kinga har yanzu shiru kamar an shuka dusa. Bai sallameta ba, bai juya mata baya ba kamar yadda suka ce. Ranar nan ma fa har tambayata yayi me yasa abincin yake wani warin magunguna? Nace mishi maggi ne. Kada fa mu je ya cafko mu Momcy".

Tace "ke ja can matsoraciyar banza da ta wofi!! Dan ubanki ke har kin fara sarewa tun kafin aje ko'ina? To arr dinki, ni cikin yayana babu matsorata wallahi, ki kiyaye ni. Kina ganin idan kika zauna a gidan wannan tsakanin wadannan matan nashi, zaki ganu? Shi komi ba dan hakuri bane? Da sannu, su duka zamu yi waje dasu. Yanzu abinda zamu kokarta muyi shine mu ga cewa mun karkato da hankalinshi kanki tukun. Yanzu kije ki zuba maganin a cikin danyen nama, ya kwana, gobe ki soya shi ki mishi girki yaci, zaki ga abin mamaki. Amma kada ki kuskura ki kara bari inji kalmar karaya ta fita daga bakinki, kina jina?".

Cikin sanyin jiki tace "ehh Momcy".
Tace "to madallah, maza je kiyi aikin gabanki". Ta kashe wayar.

Na dafe kai da baki a lokaci guda. Kaji fa wata irin tabewar basira. Kai Allah dai ya kara rufa mana asiri, ya kuma sa mu dace.

Ban damu da cewa har yanzu tana cikin kicin din ba, na tashi nima na shiga kicin din. Wutar kicin din na kunna haske ya bayyana, daidai lokacin tana maida danyen nama cikin firjin. Da sauri, kuma a tsorace ta maida firjin din ta rufe, ta juyo tana kallona cikin zare idanu. Ban ce mata komi ba, na bude microwave na ciro abincin ciki, na koma kan dinning na zauna na fara ci.
Ta zo ta wuce ni cikin sanyin jiki kamar kazar da kwai ya fashewa a jiki, tana yi tana satar kallona.

Nima a sanyaye na fara cin abincin hankalina ya kasu gida-gida, har na rasa da wanne zan ji. Da alama sai na kara zagewa da addu'a ba akan kaina kadai ba, har shi Yayan.
Ina gama cin abincin, na je na dauke gabadaya naman dake cikin fridge na zubar. Na koma dakin Yaya. Bandaki na shiga na dauro alwala na fito na fuskanci alkibla ina jero nafilfili.


Washegari da safe ba sai aka maimaita yar gidan jiya ba? Na hadawa Yaya abincinshi na kari ya fara ci cikin nutsuwa, ya kai shayin dana hada mishi, kawai naji ya furzar dashi, a dan zafafe yace "meye haka Na'ilah?".

Daga farko tsananin mamakin ya kirani da Na'ilah ne ya kama ni, kafin mamakin abinda ya faru da shayin ya biyo baya. Bai ma tsaya yi min karin bayani ba, ya tashi ya bar wajen. Ina nan zaune cikin rashin sanin abin yi, sai gashi ya fito dauke da brief case dinshi, da kyar ya iya cewa "sai na dawo". A Karo na farko, ranar ya fita ba cikin rakiyata ba, kuma cikin rashin dadin rai.
Sai daga baya na fahimci cewa, robar sugar aka juye gabadaya aka zuba gishiri. Wannan karon ma kadan ya hana ni inyi kuka.

Saboda haka da girki ya sake dawowa kaina, na dinga bin kwakkwafi. Idan na shiga kicin, bana lekawa ko nan da can har sai na gama girkina, idan kuma na gama, tunda nasan na Yaya ne ake hari, sai in shige daki dashi in kulle har sai ya dawo. Duk da nasan cewa da gangan ake min haka, amma ban shirya neman kowacece ba, bani kuma da zuciyar ramawa. Nasan cewa dai, rana dubu ta barawo ce, daya kuma ta mai kaya.



*



Yau da yake ba ranar girkina bace, kuma ina off saboda evening duty dana gama, ban fito daga daki ba sai karfe biyu na rana. Yau da su kayan marmari ma na karya. Kwana biyu yanzu mangawaro kawai nake sha kamar babu gobe, kullum sai in sha fiye da guda biyar.
Yanzu ma abinda ya fiddo ni waje kenan, saboda mangwaron dakina ya kare ne. Yaya da zai fita yace za'a kawo wani.

Ina shiga kicin kuwa, na ganshi an kawo shi har kwali guda. Wani irin dadi ya ziyarceni. Na dauki guda biyu manya masu kyau, na wanke su na yanka. Ina cikin yi, Raheemah da take yin girki ranar ta shigo. Tunda abin nan ya faru, kusan sati daya kenan, bata ko yarda mu hada idanu da ita. Ko hira suke yi, idan taga na shigo waje, haka zaka ji tayi shiru ko ta ma tashi ta bar wajen.

Sannu kawai na mata ciki-ciki, na dauki mangwarona na koma daki.
Na zauna na tada mangwaron nan tas, na bi da ruwa mai sanyi.
Komawa nayi na kwanta naci gaba da barcina.


Wajen karfe hudu, wani irin masifaffen ciwon ciki ya tado ni daga barcin da nake yi.
Na tashi na fara murkususu. Tun ina yi akan gado, har na fado kasan carpet. Gabadaya ciwon ya gigitani, ban taba jin azababben ciwo irin wannan ba.

Da kyar na iya lalubo wayata na kira Yaya, yana dauka ya fara tambayar lafiya? Saboda yasan ban cika kiranshi idan ya tafi wajen aiki ba, musamman ma ranar da ba girkina ba. Ban iya mishi magana ba, sai gurnanin ciwo kawai daya dinga fita daga bakina. Nan da nan ya rikice, yace gashi nan zuwa.

Ina jin lema tana fita daga jikina, amma bani da kuzarin daga kai in ga ko menene. Ban ma san lokacin da Yaya ya dawo ba saboda hankalina ya gushe daga jikina.

Lokacin dana dawo cikin hayyacina, tuni cikin jikina ya zube.

Lokacin da wata likita daga cikin likitocin asibitinmu ta isar min da wannan sako, dauka nayi mafarki nake yi.
Sai da naga Yaya ya shigo, jiki babu kuzari, fuska very defeated, kawai na saki kuka ina jan Innalillahi...

Dr. Anita ta matso ta dafa kafadata tana lallashina har na dan nutsu nayi shiru, nasiha ta dinga yi min mai shiga cikin jiki da nuna min hakan ikon Allah ne, shi ya bamu shi dama tun farko, tunda kuma ya dauke kayanshi ba sai muyi hakuri ba. Sai da taga na daina kukan, sannan ta juya wajen Yaya shima ta mishi jaje, sannan ta barmu ni dashi.

Muna hada ido da Yaya, na sake barkewa da wani kukan. Ja na yayi cikin jikinshi kawai yayi yana shafa gadon bayana har sai da nayi mai isata, sannan ya dago kaina. Shi kanshi idanunshi sun kada sunyi jawur kamar wanda zai fashe da kukan. Nasan karfin hali kawai da jarumta irin ta namiji ce yake yi.

Ya taimaka min na tashi zaune saboda jikina babu karfi, likita tace ya bani abu mai ruwa in sha, a bani magani, amma sam na kasa cin komi. Sai da yayi kamar zai min kuka sannan na samu na dan kurbi yoghurt din daya kawo min. Ya bani maganin na sha.
Komawa nayi na kwanta, shi kuma ya zauna a gefena ya kamo hannuwana cikin nashi ya damke, wasu zafafan hawaye suke ta zirya akan kumatuna. Ya sanya hannu yana dauke min hawayen, cikin sanyin da muryarshi tayi, yake bani hakuri, yana kara yi min tuni akan yarda da kaddara.

Da alama maganin da aka bani har da na barci. Saboda ba'a jima ba barci mai nauyi ya daukeni.

Ban tashi ba sai washegari da safe. Ina bude ido, naga Janan zaune a gefena. Ban san lokacin da tazo ba, nan na sake bude wani shafin kukan tana aikin lallashi. Daga karshe nayi shiru, ta taimaka min na shiga bandaki nayi wanka. Na fito ta bani abinci na karya, na sha magunguna.
Tace Yaya ya zo da safe, yace zai kirani a waya saboda ana nemanshi a office ne, kai kawai na iya gyada mata.

Wajen karfe goma kuwa ya kira ni, na dauka muka gaisa. Dole na ware muryata sosai saboda kada ya karanci damuwar dake nake ciki. Nasan na kwallafa raina akan cikin jikina, amma Yaya ya fi ni. Tafiyar da yayi zuwa Niamey, haka ya dawo da kayan wasan yara kala-kala. Daki guda ya ware, yanzu ya kusa cika da kayan wasan yara dana sanyawa.
Ya tambayeni saukin jikina, nace mishi naji sauki. Nan muka dan sha hira dashi kafin muka kashe wayoyin da alkawarin zai sake kirana idan aka jima.

Yinin ranar cikin amsar waya da mutane yan dubiya muke, har yanzu na kasa yarda da cewa babu cikin jikina, amma idan na tuno hakan yana daga cikin kaddarar Allah, sai in kwantar da hankalina.
Matan Yaya ma sun leko zuwa rana, da dai-daya ma suka zo. Sai da Ameerah tazo ta tafi sannan Raheemah ta zo.

Zuwa can yamma, na dan warware daga jiki har zuci. Likitar data duba ni jiya, ta shigo ta sake duba jikina. Bayan yan tambayoyi data min na amsa, ta tabbatar min da cewa zuwa nan da kwana biyu ma zasu iya sallamata. Nace mata nagode.

Tace "amma barinki ya bani mamaki Nailah (haka yawancin mutanen asibitin suke furta sunana saboda basu iyawa), last time da kika zo muka duba ki, komi lafiya lau daga ke har dan cikinki, ba kwa fuskantar wata barazana. Kin tabbatar baki ci, ko sha wani abu da zai fitar da cikinki ta karfi ba? Saboda daga yanayin abin kamar da karfi cikin ya fita".

Na girgiza mata kai a hankali, nace "kawai dai kaddara ce Allah ya aiko".

Ta girgiza kai cikin nuna fahimta, "haka ne, Allah ya mayar miki da mafi alkhairi. Ki kwantar da hankalinki fa kinji? Kada ki sanyawa kanki damuwa".
Na sake mata godiya, ta mana sallama ta fita.

Tana fita Janan tayo kaina da tambayoyi, nace "ni fa bana son wani tada rigima da maganganu. Idan ma wani abin ne, Janan ina da shaida ne? Koma menene, mutum ai kanshi ya yiwa. Don Allah kada ki bari ma Yaya yaji wannan maganar, Allah kadai yasan abinda zai yi akai. Ni na barwa Allah komi, na kuma yarda babu abinda yake faruwa face cikin yarda da izininsa. Don haka ki manta da maganar kawai".

Ta rausayar da kanta gefe guda, "to shikenan ai tunda haka kika ce. Zaki ci abinci?".
Ta watso min tambayar tana nufar kulolin dake ajiye a wajen wadanda yawanci abokan aikina ne na nan suka kawo min su, nasan duk don ta dauke hankalina daga kan zancen ne. Murmushi kawai nayi na gyada mata kai.




[Hello there! 😽].









*☆⋆45⋆☆*





Kwana na biyu ina hutawa a gadon asibiti. Bayan an tabbatar da lafiyata da komi, aka sallamomu muka koma gida. A ranar Janan ta koma Kaduna ina ta mata godiya.
Sai dana kara kwanaki uku ina kara hutawa, sannan na koma bakin aikina na kuma karbi girki. Rayuwa ta koma normal, mun maida komai bayanmu mun fuskanci gabanmu.

Zaune muke gabadayanmu a falon Yaya da misalin karfe tara na dare. Yanzu har Raheemah ta kan fito ayi hira da ita, kafin dare yayi kowa ya nemi makwancinsa kuma.
Na fahimci Yaya a mutum mai son karfafa zumunci da son kusanci ga iyalinshi, hakan yana kara min girmanshi da kimarshi da nake gani a cikin idanuna. Duk da cewa ta fanninsu, ba hakan suke so ba.

Na tashi na shiga kicin, fruit salad din dana hada yayi sanyi karara, na dauko forks guda hudu, na koma falon. A tsakiyarmu na ajiyeshi tare da ajiye cokulan masu yatsu, muka fara shan fruits din aka kuma cigaba da hira. Sai dai hirar kamar kowacce tata kawai take yi, idan Yaya yana hira da daya, baka ji biyun sun sanya baki sai dai su kalli TV ko kuma suyi shiru da bakinsu. Duk yadda yaso ya saka mu cikin hirar gabadaya abin gagara yayi, idan ma ya sanya bakin wata a cikin hirar ta danyi magana, sai ita dayar kuma tayi kim da baki, sai ta jira sun gama hirar sannan ta sako wata. Abin gwanin ban dariya, na dai yi ta kokarin makale tawa a ciki.

Duk da cewa a hakan ma ba karamin kokari yayi ba, tun da yanzu har mu kan zauna mu duka a waje daya ba tare da kaji kananan maganganu suna tashi ba. A ganina hakan kamar an fara daukar matakin farko kenan wajen hade kai.
Sai dai, tunda na dawo daga asibiti, wani shiru da matan suka yi su duka, yanzu babu bataccen girki idan nayi, Ameerah ta daina shiga dakin Yaya tunda safe, haka ita kanta Raheemah ta daina wannan yawan mitar tata. Jikina kawai yana bani ba daidai ba. Sai inji kamar shirun nan nasu, 'silence before the storm' ne.
Ko kuwa sun fara shiryuwa ne??.

Kadan-kadan Ameerah ta fara yatsina fuska, tun ana yi babu wanda ya kula har Yaya ya lura, ya kalleta cike da alamar tambaya, "lafiya, baki jin dadi ne?".
Duk sai muka juya hankulanmu kansu.

Ta girgiza kai a hankali, "cikina nake ji yana juyawa... Kamar zanyi amai...".
Tana rufe baki, ta tashi a sukwane tayi dakin Yaya, mu duka ukun muka tsaya muna kallon-kallo, kafin muka tashi da sauri muka bi bayanta.
Tana cikin bandaki tana ta kakarin amai, Yaya ya matsa da sauri ya tattagota suka dawo dakin, daga shi har mu sannu muke jera mata wanda take amsawa cikin jan numfashi. Muka rankaya muka koma falo muka zauna.

Muna zama ta fara wani kakarin da yatsina fuska, Yaya yace "wai wani abu yana damunki ne?".
Tana daga baki, sai cewa tayi, "ai ita warin kankana ne yake tada mata hankali".

Na daga girata sama cikin tsananin mamaki, Raheemah kam sai ta kama baki. Yaya yace in dauke farantin in maida kicin tunda mun gama shan fruits din. Ban ce komi ba na dauke kayan, a raina ina nanata ikon Allah kenan mai rike zariyar wando.

Na koma muka cigaba da hirarmu, har lokacin kwanciya barci yayi duk muka tashi. Na koma dakina nayi shirin barci, na koma dakin Yaya.

Cikin dare kawai sai karan waya muka ji, Ameerah ce wai cikinta ya dameta da ciwo. Nan muka nufi dakinta muka sameta tana ta birgima akan gado. Yaya yace min "ko kina da maganin ciwon ciki ne ki bata ta sha?".

Nan na koma daki na lalubo maganin boskafone na koma dakin bayan na biya ta kicin na dauko ruwa mara sanyi.
Nan na sameta kwance shame-shame a jikin Yaya. Ban ce musu komi ba, na mika mishi maganin, ya tallafo kanta zai bata maganin, nan tayi fir tace ba zata sha ba.
Yaya ya fara aikin lallashi, amma ta kafe.
Cikin nuna alamun gajiya da halinta yace "kinsan ba neman magani kike yi ba, zaki tado ni da tsakiyar wannan daren, idan ba zaki sha maganin ba zan tafi in kyaleki yanzu wallahi".
Sannan fa ta karba ta sha. Har wajen karfe hudu na dare muna kanta. Ni naki tafiya daki duk da sai da Yaya yace in tafi, ban san ko ciwon gaske take yi ko na karya ba. Sai da aka fara kiran assalatu sannan barci ya dauketa. Sai lokacin muka koma daki.

Bayan kwana biyu da yin haka, sai gata wai taje likita ya aunata ance tana da ciki. Nan suka hau murnarsu ita da Yaya, na bisu da addu'ar Allah ya raba lafiya. Wani abin mamakin shine, yanayinta sam bai yi kama dana masu ciki ba. Yadda take da, haka take yanzu, babu canjin komi a tattare da ita. Hakan yasa na fara tunanin anya ba cikin karya bane ba kuwa? Sai dai a yadda Yaya yake ta doki da rawar jiki akan cikin wannan, nasan ko giyar wake na sha ba zan fito in ce mishi ga abinda ake ciki ba. Don haka na kawo idanu na zuba musu, koma dai menene, nasan it's only a matter of time, zamu ga ciki dai ya bayyana ai ko?.

Ranar nan ina jinsu ita da Raheemah suna gabzawa, ranar Adi tazo gidan ta wuni, a cewarsu itama ta samu wani house of rep dake zaune anan

43 / 52