Farkon Ganin Idona Book Compelet By Sajida Nijar.txt

Author :  Sajida Nijar Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   20 / 64

57K to 60K   out of 190.8K words

SHIGO META FORCE DOMIN CIKAN BURIN KI DA KIKA DADE KINA SON KI CIKA TA GEFEN KUDI HAJIYATA IDAN KINA META FORCE KI KASHE KUDI BAKOMAI BANE A WURIN KI DAN HK KADA KIBARI KIYI WASA DA WANNAN DAMAR YIMAZA KISHIGO KEMA KI FARA SAMUN KUDI IN DOLLARS WATO MAZAJEN KUDI*πŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌπŸ’ƒπŸΌ
πŸ‘‰0912 262 1080





LABARI



A GIDAN HAJIAR LARABAWA
Hajia bata saka mama a gaba da nasiha ko fada ba, hasalima gyara mata shinfida ta yi tace da ita ta kwonta ta yi barci

Ita dai Mama ta kwonta din, ama idannuwanta a kan yan matanta dake zaune sun kunna tv din Hajia sunna kallo sunna fira da dariya abinsu dan tunda ta daina kukan suka sake suke shagulgulansu

gannin har yama na kokarin yi ba'a yi maganar girki ba ya sa baba salamatu zuwa wajen ta larabawa ta duka dan amsar bayanin cefane saboda girki, domin ta tabbata yau an dora tukunya ko dan bataliyar nan ta Hajia da take tafe da ita

A nutse Hajia ta dubi Mama ta ce" Usaina, tashi ki bata kudin cefane ta yi ta je ta gani ko ta samo nama? warhaka anya an sami nama?"

Baba salamatu ta ce" Au nama za'a saka Hajia?"

Hajiar Larabawa ta gyada kai ta ce" Nama za'a saka na kirki kuwa ko zabi, kin ga yaran nan ai basu saba da cin girki lami ba, tashi mana Usaina ""

Mama ta mike tana kallon Hajia da mamaki ta ce" Hajia kudin cefane kuma? Ni fa ko sisi ban zo da ita gidan nan ba, kudin taxi dinma ban san wa ya biya ba"

Hajia ta kafeta da ita, a tausashe dan gudun kar yaran su jiyo ta ce" To ama kin san ai ya'yan nan ba zan iya ciyar da su ba ko Usaina?, dole zaki ringa bada cefanensu, ga ya'ya kun saba musu dadi basu san miya babu zaki ba, zan ringa bada shinkafar ama cefanen sai kin ringa yi ai Usaina, ko baba? da ace bakinki ne ke kadai sai in yi dolena tunda Ni na haifa ama wadinan y'ayanki ne ai Usaina "

Baba salamatu ta sada kai tana boye dariyar yannayin da Usaina ta yi a zaune kamar an maujeta dan tsananin mamakin Hajia

Zata yi magana Khadija ta fado dakin, a fujajan take, hijabinta da takalmin ta du ba a jikinta ba, ihu take yi ta zube a gabansu tana burgima

Mama ta zauna da kyau tana janye kafarta da ta diro mata ta zuba mata ido, Hajiar Larabawa ta talabota tana fadin" Subahanallah, subahanallah subahanallah takwara , waye ya dake ki? subahanallah takwara lafiya? ina hijab din da takalman?"

Khadija ta langwabar da kai tana hawaye ta ce" Ni na sani takwarraty ana son kashe maki Ni?, Ni da kaina ban san inda suke ba"

Sidik ya dafe haba yana kallon iya shege ya ce" Ki ji tsoron Allah Anmy a zaure fa kika cire kika yar!"

Khadija ta murguda baki tana sakin harara ta ce" Ka ga ba ruwanka, takwarraty kin ji abinda zai min? wai auren dole, wani mataki zaki dauka?"

Hajiar Larabawa ta dafe haba tana furta" Bari in fara rangada buda burina zai cika zan kai ki dakin mijinki kafin in mutu, kaikaikaikai Allah ya yiwa babanki albarka y'ar nan, aure dai aure?"

Khadija ta bata rai taba kallonta ta ce" Baki san bana so ba? a kan me za'a min auren dole? na tabbata kuma mai kudi ne zai aura min, Ni fa na tsani mai kudi, ba zan taba auren mai kudi ba saboda na tabbata wulakantani zai yi, kuma kin san idan har ya min auren nan sai na saka shi uku, guduwa zan yi zuciyarsa ta buga dala yanzu haka yana cen kamar zai suma na fito na taho, gwara dai kai Babanmu ya kyale , in ya tafi kowama ya huta ina dalili....................."

wartota mama ta yi ido waje ta direta gabanta
bata bata damar gane komai ba ta shiga jibgarta

Lubna ta dora hannu a kai ta saka ihu, Maman ta janyota itama ta haΙ—a da ita ta ringa jibgarsu sai babba salamatu ta iya kwatarsu dan Hajia da ta ja ta gaza sai ta kwalawa baba salamatu kira

Mama na haki ta ce" Dan baku da kunya Ni zaku saka a gaba kuna yiwa badakalar harshe? , ke Lubna zaki ce ku rufe ubanku , ke kuwa har ki ce zaki bijirewa ubanki gwarama ya mutu ku huta? an gaya muku in ya mutu hutawa zaku yi? uku zaku shiga, ku ji kowa ya barku da halinku a duniya, danginku sai sun guje ku saboda wanda ya haΙ—a ya tafi ya barku, Ni zaku rainawa wayo ku ringa neman raina ubanku a gabana? ku tashi ku bani waje yan rainin hankali ku tafi maza ku kama aikace aikacen gidan!"
Ta karashe da karfi, ai kuwa suka mike suka fita har sunna gware, Khadija kuwa nan ta zuba da kudin da ta amso a wajen babansu suka yi waje da gudu su duka

Hajiar Larabawa ta sauke ajiyar zuciya tana kallon baba salamatu ta ce" kin ga mai y'a ta daki abinta a gabana"

Mama ta sada kai tana huci

Hajia ta sake cewa" to in ba rashin kunya ba, ai ke kika yi suka gani, su ai sun zata abin kirki ne tunda yanzu kika maimaita min in bai bar maganar yiwa takwara aure ba human right zaki kai shi, kin ga kuwa dan d'ansa ya rufe shi ko dan takwara ta gudu saboda za'a yi mata aure ai ke lafiya lau ne haka kike so ko?"

Mama ta dago tana kallon Hajia, zai kawai ta sakawa Hajia kuka, murya na rawa ta ce" Yanzu Hajia abinda zaki ce kennan? Hajia ina hakuri da mutumen nan ama sai da ya kai Ni bango, kina kallo Hajia babu abinda bana gani da shi, shine zai ringa wulakantani?, Ni fa ba hanna shi yiwa yarinya aure zan yi ba, hasalima nice na kai masa shawarar ya aurar da ya'yan nan saboda abinda na fara gani ba zan so ace an mike da shi a gidansa ba, ya fatatakeni ya cika baki da alfahari karshe na kawo ido na zuba masa dan doguwar magana da shi ta zama fitina ba kowa zai iya ba, ama ta yiwu ace shi sai nemana da rigima? daidai nake da shi Hajia babu inda zan je ina nan"

Hajia ta gyada kai ta ce" Hakane kuma, kar ki yarda, yi zamanki kawai ku bijire abinku ya fi...., yanzu kawo kudin cefanen"

Mama ta sake duban Hajia, jiyan nan fa ta turo mata kudin ta na wata kudin da ita da kanta ta yi kiranta tace sun yi yawa bayan ga su shinkafa, macaroni, cuscus, garin masara da su doya da dankali komai an jibge cefane kawai suke yi na kayan miyar da ba yawa , ama Maman tace ta rike idanma sun kare a gobe ta sanar mata za'a kawo wasu, shine yanzu kuma take fadin haka ko? dan kawai dai a gigitatata a sa ta koma gidan ko? to kuwa ba zata koma ba, in ana so kar a basu abinci a gidan, sai kawai ta yi kwonciyarta tana nadewa hadi da sake fashewa da wani kukan

Hajia ta tabe baki tana kallon kudin dake kusa da katifar ta dauka tana fadin " Kin ga salamatu kamani in tashi mu je cen inuwar a min shinfida in sha hantsi, Ni kam wannan y'a ta manta hawan jinni ne da Ni sai ta sa ya tashi ta sakani a gaba da kuka, bari a ranta maki kudin cefanen a siyo zabi mu yi dabge dan kuwa ba zan ciyar masa yara da miya lami ba, kudadenmu mu du mun saka su a hanyoyin da suka dace sai dai ana iya ranta maki kya biya...."

Baba salamatu ta kamata suka fito fili ta sa aka yiwa Hajiar shinfida mai kyau ta je ta ringesa a innuwa , Khadija ta zo ta kwonta a jikinta a hankali tana fadin" In baki hanna aka min auren dole ba duniyar zan bar maki ki shiga uku takwarraty , ki azalzala y'arki ta bijire masa kin ji?"

Hajia ta yi murmushi tana fadin" Kin zubar da kudi, na waye kudin nan masu yawa?"

Sai a lokacin khadija ta tuna, ta ce" Aba ne ya bani da nace ya ban kudin taxi in zo nan din nima, bawan Allah bashi da lafiya fa, baki ji muryarsa ba har abin tausayi, kamar ba Abanmu ba horor "

Hajia ta girgiza kai kawai tana dane dariyarta, wato ya'yan Elhaji da matarsa kaf shakiyai ne na bugawa a jarida, Allah ya shirye su ya shiryi babansu


Kusan karfe biyar na yama amarya ta karasa gidan Baba Hamza

Tunda take bata taΙ“a shiga cikin gidan ba sai yau, sau biyu dai sunna zuwa gaishe shi sukan gaisar da shi a nan wajen Elhaji ne su juya, sai hau da Allah ya sa ta yi zuwan nan na yama akace ta shiga ta karasa baya wajen shukoki yana cen


Tun daga nesa ya ajiye sandar da suke buga ball shi da kurma ya nufota yana tafe a hankali da yannayin girman jiki na shekaru da ya dauka har ya karaso inda take tsaye tana mamakin girman fillin ball din, kuma ball din irin yar karamar nan ce da ake bugawa da sanda ta je ta fada ramin nan, irin ball din nan ta masu kuΙ—i, ashe har haka mutumen nan keda dukiya? ikon Allah

Dukawa ta yi har kasa ta sake gaisar da shi

Cike da girmamawa da dantijantaka baba ya ce" Ke ce ke tafe? bismillah mu je ciki wajen iyayen naki mana"

Du irin yadda take son shiga cikin a cikin zuciyarta ko dan ta idasa kasshe kwarkwatar idannuwanta sai ta kasa , saboda abinda ya kawota, a tausashe kai a kasa ta ce" A'a baba, dama zuwa na yi in sanar maka baban yara na asibiti, ama da sauki dan dai a sanar maka ne duba da sun yi fada da baba ado"

Sai da ya ji gabansa ya fadi, Allah ke hada jinni , Allah ya haΙ—a nasa da na bawan Allahn nan, ko dan yana yi masa yannayi da nasa cilon d'an da uwar gidansa? lalle bawan Allahn nan yana da mahinmanci sosai a duniyarsa

A hankali ya ce" Subahanallah, me ya same shi? dazu fa lafiya na baro shi...., koda yake baya bata da kadan, a wani asibiti yake ne?, tashi tashi bari in taho nima, ki sanarwa direbobi sunnan asibitin da dakin da yake"

Ya karasa fada yana nuna mata hanyar da direbobin suke sannan ya juya da dan gagawa ya nufi inda kurma take yana yi mata alamun zai je ya dawo

Da hannu ta masa alamun a dawo lafiya sannan ta ci gaba da game dinta


Bangaren AL'WALID ya nufa yana ayana' Yanzu haka baban kurma yana cen yana fama da karafunan nan'

Samunsa ya yi tsaye da kayan sport a jikinsa, farare irin wa'inda yake sakawa idan zai yi wasan wuka, kansa da abin kare kai, sunna yi shi da bakonsa

Dakatawa yayi har suka dasa aya saboda ba'a daukan lokaci sannan ya juyo yana cire casque din kan nasa ya ajiye saman wani dogon table ya nufo inda baba yake tsaye da kula , sannan a tausashen da yake yi masa magana ya ce" Fita zaka yi?"

Baba Hamza ya ce" Eh, ina so in je asibiti ne kakan kurma aka kwontar"

Dubansa yayi da kyau, ya dan dage girarsa Ζ™adan dan maganar da ya so yi, sai kuma ya dauke dubansa a tausashe ya ce" Ba zaka bari in je maka ba?"

Baba ya girgiza kai ya ce" A'a gaskiya, zan je yanzu yanzu in dawo in sha Allah"

Ajiyar zuciya ya dan sauke a nutse ya ce" A dawo lafiya"

Har baba ya fita ya dawo , ai kuwa ya ganshi a tsaye yana kallonsa

Murmushi yayi a lokacin da ya dago hannunsa zai taba wajen goshinsa, ya ga wai yanzu AL'WALID ya kere tsayinsa, yau da gobe, shi abin tsufa ya sa ya rankwafa AL'WALID din kuwa da yake yanzu yake cikin shekarunsa sai tsayinsa ya bayyana sosai ga budewar da shi bashi da ita a da, dan a zamanin tasa kuruciyar bashi da kakarfan jiki irin wannan ko kadan

Wajen goshinsa ya taba inda ya mana abinda zai boye ciwon da ya ji

A tausashe ya ce" Wai me ya ji maka a nan?"

Hannun nasa da ya taba shi da shi ya riko ya sauke hannun nasa a tausashe ya furta" Dan bigewa ne"

Baba ya dan kure fuskarsa da kallo sai kuma ya juya ya tafi

Yana tafiya AL'WALID ya taba wajen shima....., sai ya samu kansa da fitar da karamin murmushi ya girgiza kansa ya je wajen kujerun da kayansa ke ajiye kama daga kan waya da abin sha

Zama yayi ya dauki wayarsa ya bude, saboda tun dazu yana hangen hasken da take badowa tana daukewa,

Tarin msg din dake wayar da misss call ya saka shi lumshe idannuwansa

Ba tare da ya bi ta kan kiraye kirayen nata ba ya rubuta mata msg kamar haka" Yau zan gan ki"

Daga haka ya ajiye wayar ya shiga dan juyar da kansa a hankali a hankali yana jin jijiyoyin wuyansa na saki sosai

A hankali ya bude idannuwansa daidai aple wash din dake daure a hannunsa ya sauke ido.....a hankali ya furta " *FARKON GANIN IDONA DA ITA....TA FASA MUN GOSHI* "

Ya samu kansa da yin wani murmushin a hankali ya furta" Allah ya sa a daina maganar nan........dan ba zan juri fashewar kai ba, ga dukan alamu kuma yan gidansu du yan dambe ne"

Tunda suka dawo daga gidan Aba a jiya yakan samu kansa da yin murmushi har ya furta wasu kalamai wa'inda suke nuni da ya dan samu nishadin da ya jima bai samu ba

A kusa kusan nan, zai iya cewa ya jima rabonsa da ya yi fira da sakewa da mutun , mace ko namiji irin haka......ya dauki lamarin komai serius ya sakawa rayuwarsa da motsinsa, hakan ya sa abin ya tsaye masa a rai yake saka shi murmushi

Mikewa yayi da tawul yana goge zufar dake karra tsatsafo masa ya tarda abokin nasa dan ya masa salama domin yana son shiga yayi wani abin kafin a jima


Baba Hamza da direba basu zame ko'ina ba sai clinik din da Aba ke kwonce

Bai wani sha wahala ba aka gwada masa dakin da Aba ke kwonce, dan haka ya karasa cikin tafiyarsa ta tsofi ya shiga neman izinin shiga

Aba dake zaune ya rafka tagumi abin duniya ya ishe shi, tun ba'a je ko'ina ba damuwa na son fin karfinsa, ya gaza yarda da abinda idannuwansa suka gani, ya gaza yarda, uwa uba wace zai iya yin maganar da ita kansa tsaye ta yi tafiyarta, wai ace amarya a gefensa a zaune da nufin ita ke jinyarsa ama tana fama da waya a hannu? shi tun dazu da ta fita Baima san inda ta nufa ba, yarinyar nan ita da kanta yanzu tsoronta yake ji, dan kuwa lamarin y'arsa Karima na son gigitashi har ya sa ya kasa yarda da kowa


Da kyar ya iya bada damar a shigo yana dago dubansa ya sauke a kan baba Hamza da ya shigo a hankali yana tafe irin tafiyar tsofafi da kula sosai da kuma kiyayewa


Baba Hamza na dubansa ya ce" Subahanallah, kace dai jikin tabuwa yayi da gaske tunda gashi har an baka gado? "

Tarin tambayoyi ne a zuciyar Aba, yana duban baba dake neman wajen zama ya ce" Alhamdulilah, da sauki, gidan ba ka koma?"

Baba ya girgiza kai yana zaunawa ya ce" A'a, amarya ta sanar da Ni "

Aba bai san lokacin da ya furta" Innalilahi, mai hankalin ta tafi ta barni da mahaukaciya, me tace maka?"

Baba ya dube shi a tsanake, kanna kallonsa zaka fahimci cikin tashin hankali yake

Baba Hamza bai kula furucinsa ba sai tambaya da ya jefo masa wace ta sa yayi shiru yana sauke ajiyar zuciya, wato wace ta tafi ina? Duda ya san amsar tambayarsa ba zai.wuce yace Hajia ta tafi gida ta bar amarya ta yi jinyarsa? shi kam Yana girmama soyayar da Elhaji ke yiwa matarsa,

Aba ya dago yana dubansa a hankali ya ce" Gidan Hajiar Larabawa ta tafi tunda safe"

Baba ya dube shi a dan zabure ya ce" Sakinta ka yi itama?"

"A'a, ban saketa ba, wai me yasa za'a ringa min wannan mugun alkaba'in? ban saketa ba, fushi ta yi ita da yaran suka tafi gidan Hajiar Larabawa tare"

Baba Hamza ya zuba masa ido, yana auna maganar da ya fada yana yiwa kowace fashin baki har ya gama fahimta sannan ya ce" Subahanallah, me ka yi mata da zafi haka? kana nufin ita ta tafi gidansu, sauran ya'yan kuwa duk sun je ina?"

Aba ya fitar da huci ya ce" Ni babu abinda na yi mata, Ni ta wanke sumul sanan ta yi tafiyarta da yaran"

Baba ya dan buda ido abin mamaki, sannan ya sake kure Aba da kallo a tausashe ya ce" Ka fada min abinda yake faruwa mana, me ya faru?"

Aba ya rasa inda zai kama, gaba daya sai ya dora laifi a kan amarya da ta je ta fadawa baba Hamza bashi da lafiya tsabar bata da hankali, yanzu idan ya ji wata fitinar ce ai shi da kansa zai iya cewa an fasa auren nan a masa bakin ciki a hadasa masa hawan jinnin da zai kai shi kiyama

Gannin ya ki yin magana ya sa baba fadin" Shikenan bari in je inda take na san ita ta fada min abinda yake faruwa, Allah ya kyauta maka, kai ace baka da gwani a rayuwa? in kana rigima ka cireta a gefe, yarinyar nan kana ganninta ka san Allah ne ya wanke ya baka, ama sai ka kure hakurinta?"

Aba ya ce" Ka zauna ka ji, babu abinda na yi mata fa, duk abinda yake faruwa laifinka ne fa ba na kowa ba"

Baba ya kalle shi shekeke jin abinda yake fada

Aba ya dora da fadin" Ka ga ita matsalarta boko, banzar bokon nan du ta cushe tunanin gimbiya, kana jin wani abu , a lamarin nan na ga abinda ya fi karfina sosai, sun nuna min sunne mata

20 / 64