Farkon Ganin Idona Book Compelet By Sajida Nijar.txt

Author :  Sajida Nijar Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   3 / 64

6K to 9K   out of 190.8K words

gaba tana tunanin shi kam yaya Abdul karim sai bin silsila kuturta da bin d'an aboki, bari dai ta je gida a mata kiran Mama ta ji yaushe zata sauko daga aiki, ita batama san aiki zata kwana jiya ba walahi ai da ta amshi yan kudade na bukatu.

Tana tafiya a hankali dan komawa gida, domin daga islamiyya ta fito ta ratso har shagon malan Ambu dan siyan cingan ta kuma jin muryar yaya Abdul karim ya ce" Inace mama bata da lafiya shine kika zo nan wajen?"

Turus ta yi ta juyo tana kallonsa, dan bata fahimci mamar da yake nufi ba, domin a gidan kaf ya'yan gidan basu san cewa Mama bata da lafiya ba ne ya sa bata kwana a gidan ba, da mahaifinsu ya fita jiya ya dawo da dare sosai rufewa ya yi ya yi kwonciyarsa, da safe kuwa babu wanda ya cewa ga inda take dan su din basu isa ya yi wata fira da su ba, mai aiki ce tace masu tana asibiti, suka dauka aiki ne ya sa ta kwanan domin mama likita ce ta mata wace takan kwana a asibiti idan ta kama yannayin aikinta

Da dan jin haushi kadan Abdul karim ya ce " Ina fata, ba du mazan garin nan suka kasa birgeki ba sai wancen mutumen da bai iya dauke kansa a kan ya'yan mutane ba ko *ANMY*!"

Wannan karron sai da ta ji yar kunya ta kamata, domin Abdul karim ya'yan kawarta ne, kuma a kaikaice ya jima da nuna cewar burinsa ita ce, sai dai bai riga ya zurma da yawa ba saboda yannayin gidansu, ama yana jiran dama dan kuwa da gaske yake, koda kuwa shi dinma yaron ne dan bai fara aiki Bama bale a yi tunanin wani baban abu ya shigo tsakani , ama yana da buri da soyaya mai karfi a zuciyarsa Tata, ta ture tunanin nan tana dan dubansa

A nutse ta ce" Wace mama ce ba lafiya yaya Abdul?"

Da dan mamaki ya dubeta ya ce" Ban gane ba, maman gidanku mana, Baba ne ya fadawa babanmu, shi kuwa ya fadawa Hajiata ta haka ne na ji!"

Ledar dake hannunta mai dauke da takalmanta silifas ne ta saki tana kallonsa sakamakon irin dokawar da kirjinta yayi kafin ta juya da gudu gudu sauri sauri gabanta na mugun dokawa tamkar zai balo ya fito daga kirjinta ta nufi gidansu ba ko dar din gannin magariba ta shigo, hakan na nufin kila mahaifinta ya shigo gida bata sani ba ta turo ta shigo ta nufi bangarensu da sauri tana kiran sunnan yayunta idannuwanta a rufe ta fada baban falon su murya na yi mata rawa ta ce"
07/12/2024, 14:40 - samiraharounayacouba: 🌺🌸🌺🌸🌺🌸🌺🌸🌺🌸🌺
*FARKON GANIN IDONA*
🌺🌸🌺🌸🌺🌸🌺🌸🌺🌸🌺


*LABARI DA RUBUTAWA*

*SAJIDA NIJAR*🇳🇪

*PAID BOOK*
*Y'AN NIJAR ZAKU TURO KATIN AIRTEL KO TA SAHELCOM TA DARI A WANNAN NUMBAR 93811618 SAI A SAKA KU A GRUP, YAN NAGERIA ZAKU YI TRENSFER NE NA 500 TA WANNAN ACCOUNT NUMBER 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank sai a bani shedar ta numbana kamar haka 93811618 , Sajida Nijar thank you 😍*

LITATTAFAN MARUBUCIYAR

DUK KARYAR KADA
Y'AR MAHAUKACIYA
NEMAN NA KAINA
BANI DA ZABI
DAGA TAFIYA ƊAUKAR SOJA
BAK'A CE
KUTKALE
DUK NISAN JIFA
MAGE
IDAN KA RAINA INDA KAKE
DUTSE
NI ZAN LADABI
ZAKIN SARAKAI
WATA KOKOWAR
DA CIWO A ZUCIYATA
AURE YAƘIN MATA
AZAL
WATA TAFIYAR
*Shafi na uku (3)*


*TALLAH, TALLAH, TALLAH*


*META FORCE*

*menene meta force*

business ne ingantacce business ne mekyau business ne daizaibaki kudi 💯
tunda ake duniyar network marketing ba’atabayin business din dayake bada kudi sosai kamar meta force ba kuma dollars ne sukebadawa sannan inkinason canja dalarki cikin mintuna qalilan zaki canja dollars dinki zuwa naira hankali kwance kinadaga gida dollars suna sauqamiki hankali kwance yawanci yan nigeria ko ince yan arewa bakuda lbrn wannan business din business ne daya karade duniya akwai qasashe da dama wanda sukafimuma cigaba sunacikin wannan business na meta force

*shidai meta force crypto currency* ne

kuma munsan cewa yanzu babu wani business dayake bada kudade a duniya yanzu irin crypto currency

akwai program dayawa acikin meta force wanda akayi lunching da wadanda ba’ayiba amma za’ayi nan bada jimawaba

yanzu bari mudau programs guda 1muyi dan taqaitaccen bayani akai

*TACTILE*

1 Tactile : matakin farko kenan dole idan zakshiga meta force saikafarayin registration a tactile sannan zakasamu damar shiga kayi joning sauran programs din
tactile yanada levels guda 12 1 to 12 kowani level da kudinshi level 1 5 dollars
level 2 10 dollars
level 3 20 dollars
level 4 40 dollars
level 5 80 dolllars

hakadai
kudin kowani level yake ninka na bayanshi saikzabi wanda zaka iya saikayi shi tactile ananne akasamun abunda muke qira

*Spillover*da*over flow*

wato kanazaune baka kawo kowaba zakaduba wallet kaga ansama mutum har dollars sun sauqama anbiyka kuma bakayi aikin komaiba a wadannan levels din dakasayadin ko wani levels dakasaya idan spillover yatashi fadoma to adadin kudin wannan levels dinne misali level 1 5 dollars to ynada dakuna 6 duk lokacin da kayiwa mutum register kokuma spillover yafadoma zakasamu 5 dollars ne akowani daki 1 amma banda dakuna 2 na farko da daki 1 na qarshe amma daki na 345 dukka sunafadowa biyanka za’ayi kaga 15 dollars kenan dakuna 3 sannan idan dakunan suncika za’aske sharemaka kasake zuba wasu mutane inma kaikanemosu inma spillover kasamu

to haka zakayita samun wannan dollars din a kowani levels dakasaya duk zagaye daya zakasamu adadin kudin daksayi levels dinnan sau 3 kagdai kudin dakasyi levels din sundawo harda riba kuma hak za’ayita sharema dakunan anasa wasu mutane koda mutanen sunkai millions 💃🏽💃🏽💃🏽💃🏽
Atakaice kenan sauran bayanin kubiyoni awannan number domin jinkarinbayani
👉0912 262 1080
*Sannan zaku iya zuwa kuyi browsing google youtube*

*zakusamu kowane irin bayani kukeso game da meta force
Aunty Hajja







LABARI



Murya na yi mata rawa ta ce" Aunty A'isha, aunty A'isha, kina ina?"

Da sauri Badawiya mai aiki ta fito ta ja hannunta suka nufi bangaren mahaifiyarta kasa kasa tana fadin" Babanku ya zo tun dazu, ya kawo mamanku, ki yi a hankali kar ya ji shigowar ki , daga ina kike Dije? bakya tsoron duka ko? Dije yanzu fa ke ba yarinya kankanuwa bace, ama saboda siyan alewa da cingan kina iya janyowa kanki duka da mahaifiyarki"

"BABA Badawiya wai mama bata da lafiya?"
Khadija ta katseta a lokacin da suka murda dakin suka shiga

Daga baya baya Baba Badawiya ta dakata, ita kuwa ta shiga tana kallon mama Fatima dake turara dakin mahaifiyarta da turaran wuta tana murmushi ta ce" Ga maman manya ta karaso, Anmi sannu da zuwa"

Da sauri ta karasa wajen da mahaifiyarta ke zaune , wato bakin gado, tana dan murmushi dan mayarwa gogonta amsar sannun da take yi mata ama hankalinta kacokam a kan mahaifiyarta har ta zauna tana sauke ajiyar zuciya kasa kasa idannuwanta na cikowa da hawaye ta ce" Na zata aiki kika hau tun jiya, ashe baki da lafiya? walahi ban sani ba mama , me yake damun ki? mama babanmu ne ya dake ki ko? me kika yi masa? mama me ....."

"ki ajiye numfashi, sannan ki tauna kalaman ki, menene wannan furucin da kike yi? dama ya taba dukana ne?" Hajia ta katseta a tausashe tana kallon fuskarta

Da dan mamaki ta dago ta zubawa fuskar mahaifiyarta ido, lokuta da dama takan rasa a bigirin da zata ajiye wannan lamari, irin yadda mahaifiyarta ke boye laifin mahaifinta bata san dalili ba, Duka? duka kam, iya duka , ba na wasan yara ba yake haɗawa da ita ya yi a zuwan ta tarewa ya'ya ya sauka kanta!, to ko shekaran jiya ai ya zabga mata bulalar dorina a gaban kowa, ama sai Mama ta ringa nuna ba'a yi haka ba?
A sanyaye sosai ta ce" Mama????"

Mamanta ta sake fuskantar ta da kyau, itama a sanyayen ta ce" Na'am Anmi?"
A hankali khadija ta duka ta ɗora kanta a kaffafuwan mahaifiyarta, muryarta na rawa sosai tace" Walahi sai na ji duniyar gaba daya ta tsaya cak, sai na ji tamkar numfashina zai bar gangar jikina, ban san baki da lafiya ba, da ban fita ba yau, mama idan wani abu ya same ki ban san ko zan rayu ba"

A hankali ta lumshe idannuwanta tana sake kallon hijabin Khadija da ya rufe gashinta, sai take gannin kamar har yanzu khadijarta bata wuce shekara uku ba, soyayar yarinyar yana da girma a zuciyarta kwarai da gaske ko dan ita kadai ta malaka, lokuta da dama takan ji a ranta idan fa ba dakinta ta kaita ba, to kuwa zata ci gaba da zama a gidan nan koda ana yankan naman jikinta ne

A hankali ta dago fuskar khadija tana kallo a tausashe ta ce" Ama kuma ke kin san Allah baya barin wani dan wani ya ji dadi ko?"

Khadija ta lumshe idannuwanta ta ce" Na sani, ama a kulun ina rokonsa ya cika min burina, ya ara min dama in cimma burina kafin ya raba"

Da dan mamaki mamanta ta ce" ke kuwa menene burinki haka?"

KHADIJA ta zubawa sansanya, ni'imtaciyar fuskar mahaifiyarta ido, sai kuma ta sada dubanta a hankali ta ce" Yaya jikin ki?" A zuciyarta kuwa fadi take yi' Burina na barwa zuciyata, ina da burin gannin na raba ki da gidan nan, ina da burin gannin na maki gini, na kilaceki, na saka ki a farin ciki, ina burin kaiki inda Aba ba zai kuma cin zarafin ki ba, shi yasa nake karatu dan bana so na dogara da aljihun kowa sai nawa, ina so in yi maki da kaina ba da kudin kowa ba, koda yake ba zan taba auren mai kudin Bama bale ya wulakantani saboda kudinsa!'

Murmushi Hajia ta yi, a tausashe ta ce" Alhamdulilah, na warke yanzun, maza tashi ki je ki yi wanka, ki yi sallah, ki dauki alkur'aninki ki je falon biyu ku yi tilawa" A ranta tana mamakin kaucewa maganar da ANMY ta yi.

Sake dago dubanta ta yi ta kuma kallon mahaifiyarta, ta juya a hankali ta kalli mama Fatima, sai kuma ta mike jiki ba karfi ta fice a dakin gaba daya

Ajiyar zuciya Hajia ta sauke ta mayar da bayanta jikin gadon tana lumshe idannuwanta

Fatima ta dan girgiza kai tana kallonta ta ce" Du tsatsauran halinsa da kike ikirari, du tunanin da kike kan ya fice a ranki kina son abinki, aunty yadda kike iya boye laifinsa a gaban y'arsa kina son abinki ne"

Sai da Mama ta sauke ajiyar zuciya kafin ta dubi Kanwarta Gogo Fatima a sanyaye ta ce" So? So? uhummmm, wannan Yaren ke kika san shi FATEEMA, kin san Ni me na sani? abinda na sani kokarin in kare martabarsa a idannuwan ya'yansa, abinda na sani in yi yaki duk rintsi kar su dogara da kalaman fatar bakinsu a kan mahaifinsu, a hakama yaya aka kare da kalaman bakin Anmy bale ta samu abin dogara?"

Ta dan nisa ta ce" Tunda na shigo wa'inda ban haifa ba suka kirayeni Mama na ji a raina zan so na gansu a aljanna, Fateema idan kina tune biyaya wa iyayensu sai sun yi tabas koda zasu samu rabauta, idan har suka shaku da abinda idannuwansu ke gani su din da kansu zasu maimaita sawun mahaifinsu ne wanda hakan ba karamin tabewa bane a duniyarsu daga matan har mazan, Fateema idan suka raina shi Ni na yi asara, idan suka masa duban abinda suke tunani da shi sunne zasu fada a halaka, kin san ina cikin matsanancin tsoron kar ya'yan nan mata idan an kai su dakin miji su yi rayuwa irin ta mahaifinsu? mace da aka sani da laushi da jan yaro a jiki idan suka ari rayuwar hantara, duka, zagi wa ƴaƴansu yaya kennan?.....ke dai ki yi soyaya ama Ni zan yi ta kula da ya'ya "
Daga nan ta yi shiru tana maida kwalar da ta cika mata ido
Ba kasafai zaka ga ta yi kuka ba sai idan tana magana da wanda yake na jinni kuma suke da shakuwa da shi, misali dai fateema, bayanta ko da wa zata yi magana zata yita kai tsaye ta kuma ture ta ci gaba da harkokinta,

Rayuwar auren malan bahaushe kennan, haka ake ciki ake damawa, Yawancin lokuta akan ce mata ita fa da sauki saboda bata rasa ci ko sha ba ko sutura, tsautsauran halin d'a namiji ne kawai ke bata wahala wanda kuwa malan bahaushe ke gannin ai dolema a yiwa mai nemo shinkafa uzuri a masa biyaya, haka Yaren mahaifiyarta yake wato Hajia Hadiza ta gidan Larabawa, tace da ita ta ture du wata damuwar yau da kullum da take fuskanta a wajen mijinta, kowa ma a ciki yake, tace da ita idan har ta ture zata yi rayuwarta normal ne, ta kwatanta mata ta bar maganar rayuwa kamar a Film wannan tatsuniya ce da ake zama a tsara a yi mata kwaliya dan a kayatar da mai kallo, tace da ita dole ne zata yi ibada irin ta aure, dama ai shi *Auren yaƙin mata ne*, shi yasa lokuta da dama idan ta tsinci kanta a cikin halin kaka naka yi na rayuwa ta gwammace ta tsaya a dakinta ta hau salaya ta yi ta kuka a gaban wanda ya haliceta, ko ta samu kanwarta ta yi mata kukan , sai dai yau da gobe tana samun damuwa mai girma dake neman kutso mata duniyarta har ya hannata wannan biyaya, ba komai bane sai tasowar y'ar nan jalin jal, Anya kuwa gaba gaba Anmi zata yarda idannuwanta na gannin abubuwan dake faruwa ta shanye ta kyale? irin abinda take ganni a idannuwan Talyat na sakata tunani da dama na yau da gobe, Allah dai ya sa mu dace

Gogo Fateema kasa cewa komai ta yi, ta juya ta ci gaba da idasa kimtsa dakin yayar Tata dan ba zata kwana ba gida zata je sai gobe kuma ta dawo, jikinta a mace, zuciyarta ba karfi, gaba daya hankalinta a tashe yake da lamarin nan, bata taba yarda da kalmar cewa da wani kudin gwara talaka ba sai a kan yayarta da gidanta, tabas yayarta na gannin jarabawar rayuwa, tana tayata da adu'ar Allah ya bata ikon cinyewa.

Sai da dare yayi Elhaji ya sa direba ya mayar da gogo Fateema gida sannan ya shigo ya kara nufa wajen da Hajia take, wato dakinta
Da ya shiga tana kwonce , tana jin motsinsa da kanshin turarensa dake fara yin salama kafin ya iso ta rufe idannuwanta tamkar wace barci ya dauketa, ya yi tsaye a kanta na yan mintuna kafin ya juya ya fice ya bi ta baya ya je bangarensa , bai ko bi ta kan yaran ba, dan kuwa ya san tana gidan, idan tana gidan bashi da darrrr, idan dai Hajia na gidan bashi da damuwa a kan maganar tarbiyyar ƴaƴansa, shi yasa yake mugun gaba da aikinta, Duda a yanzu ta yi ci gaban da bata kwana asibiti ama wani lokacin wani aikin na yin tsananin da sai ta kwana dole a asibitin, idan kwana ya kamata a asibiti balaki suke yi kamar zasu kashe junna, sai dai ya riga ya gane bafa zata ajiye aikinta saboda rainon ƴaƴansa ba, wannan karatun ta biya masa dala dala kuma ya dauka

Sai da ta tabbatar ya bar dakin sannan ta mike zaune ta zubawa waje daya ido tana tunani
Ita dai Allah bai bata aure da wuri ba kamar yadda ake yiwa ya'yan hausawa aure a shekaru sha bakwai in ta yi tsanani sha takwas zuwa sha tara, dan kuwa haka gidansu ake yi tun sha shida wasu an aurar da su, dan sai da kannenta suka yi aure kaf kafin Allah ya fitar mata da miji a cikin manema aurenta, ba kuma dan bata da maneman bane, a'a, kawai mai daukan ne sai a lokacin nan ya zo, wato a lokacin da ta kai shekara ashirin da daya
Bayan sun yi aure da shekara daya ta haifi y'ar nan mai sunnan mahaifiyarta wato Khadija , take kiranta da Anmi ko tace da ita TALYAT, tun daga lokacin dif haihuwar ta dauke, har zuwa yanzu da TALYAT ta kai shekara goma sha takwas a duniya ita kuwa take da shekara talatin da tara Allah ya bata wani rabon ashe ba mai jimawa bane ya fice shima.

Tabbas ta yi aure, kuma tana cikin jarabawar aure mai wuyar gaske, wanda lokuta da yawa takan gwamaci zawarci da wannan auren, kadararan aure mai zafin gaske, auren dake tafe da bugun numfashin ta da tashin hankalinta, sai dai idan ta dubi Anmi sai ta ji wani karfi a zuciyarta dake kashe dukkan yunkurin son fita daga gidan ubanta ta barta kamar yadda iyayen sauran ya'yan suka yi sakamakon tsaurin halinsa da kuma karshen zamansu da shi

*TALYAT* yarinya ce mai cike da ilimi, da sanyi, da nutsuwa uwa uba ita ta dauko kamanin kakarta ta gefen uba tamkar kaki ta yi ta tofar

Anmi nada nutsuwa kwarai matuka, sai dai tana da nata tarin rashin jin dake dagawa mahaifiyarta hankali idan ta dubeta
Tun Anmi na primary an sha kawo karar fadanta, dan tana yi mata nasiha yau da gobe ne aka samu ta rage sosai harma take yi idan ya zama wajibi ta yi domin ita ta sani a yanzu Anmy bata tsoron dukan mahaifinta dan dukan in an yi a kan laifi baya hannawa gobe ta maimaita laifin, gwarama a yi mata nasiha a kan abin
Mahaifin Anmi na yi mata wata irin soyaya boyayiya wace shi da kansa baya so kowa ya sani saboda yakan ce baya so son da yake yi mata ya hanna shi horata, shi yasa tsananin da ya saka a kanta ya so fin na yan uwanta, domin kusan kulun sai ya bibiyi makarantar ta ya ji me take ciki yaya karatunta da

3 / 64