Author : Aisha Bagudu Category : Old Hausa Novels
dayaga hango zeenat zaune ya zubawa motar ido har sanda ta fito ahankali suka jiro suna hira Amman banda zeenat dataji gabanta ya yanke ya fadi dan tun lokacin da aka mata rana ,rabonta dashi dai dai sun kusan geftashi yakira sunnanta zeenat..... tacigaba da tafiyarta dan batason abinda zai km hada ta dashi cikin sassarfa ya biyo bayanta yasha gabanta cak taja ta tsaya suna kallon junansu,yayinda su Maryam suka cigaba da tafiyarsu suna tsaye batare da dukkansu suyi yunkurin yin magana ba kamil ya gyara tsayuwa ya tura hannuwansa duka cikin aljihun wandonsa ya kafeta da idanunshi ta sunkuyar da kanta kasa sannan tace lfy yaya ka tsayar dani muryasa a dashi yace lfyr ce takowa haka yanzu zeenat kin kyauta kennan ki zabi wani kibarni byn duk lokacin dana dauka Ina fama da soyayyarki ,a she kinsa bakya sona kibarni inata faman hauka akanki tace Allah yaya ba haka bane Amman kayi hakuri dan Allah, ya sake gyara tsayursa , yayinda idanunshi ke kanta har yanzu yace iya hakuri ne kawai zai wadatar da zuciyar da tayi sama shekara biyu tana mata da miki so.... yace Shikenan bbu komai Nagode Kwarai da abinda kika saka min tace ka dauka haka Allah yaso ni din ba matar ka bace yayi murmushin karfin hali sannan yace haka ne fa al'amarin ubgj Amman agaskiya DEENi ya cuceni ,tace kabar cewa ,tayi ta dago suna kallon juna fuskarta dauke da murmushi ta bude baki kennan Sai ga motar DEENI ta kuno kai cikin compound din km shi suke facin Ai take maganar ta ta tsaya sakamakon DEENi data Gani zaune a mota yana kallonsu duk kasancewar akwai dan duhun magariba hakan ba zai sa takasa gane bscin ransa ba , gabanta ya yanke ya fadi , ,shima kamil din shr yayi bai sake yin magana va kusan minti goma yayi yana kallonsu koda bata ga fuskasa sosai ba tasan a daure take ,har sanda DEENi ya fito yayi matarsa key idanunshi na kansu ,cikin tsoro da frigice zeenat tace ni zanshiga ciki ,kamil yace Shikenan Allah yabaki zaman lfy ta gefensu yazo yazo ya gifta hade da jan tsaki sannan ya wuce . a filli ta furta wayo Allahna nashi uku kamil ya sake yin murmushi dole sannan yace da'aka me,da kika shiga uku, nifa Banga abinda ya birgeki a DEENi ba,har da kika iya zabarsa , kalli fa yadda jikinki ke rawa saboda Allah tamkar kinga wani malaika tsaki taja hade da zabga masa harara dan Allah kabarni naji da damuwa Ai duk kai kaja min matsala Ina zaman zamana da yanzu Ina cikin gida💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 21-22
Wani irin kallon mamaki fk yake masa , ,gabadaya ya zamo tamkar mutun mutumi ,a zaune a gurin ,
Yarasa meke damun brain din DEENi , mutun Sai girman kan tsiya da nuna isa ,fk ya dinga masa kallon bahagon mutun wanda
Shi sam bbu ruwan shi da fadar duk magana da tazo bakinsa .
In a low voice fk yace yanzu duk wahalar danayi akan yarinyar nan yatashi a banza kennan?
DEENi ya tabe bakinsa hade da cewa A'a bakayi a banza ba tunda gashi "zan aureta gaskiya ce dai na gaya maka,dan kasan ita din ba ra'ayina bace .
Amman narasa dalilin da yasa zuciyata ke muradin kasancewa tare daita "alhalin bata sonta nake yi ba .
fk ya sake dubanshi sannan yace dan rainin wayo kawai "kar ka mai dani tamkar wanda bai san komai ba mana .
,tunda har ita zuciyartaka ta iya amincewa daita, har kaji zaka iya aurenta definitely kana sonta" ko yaya ne" ,. Amman maganar kace baka sonta,wannan ma ba gaskiya bane .
deeni yaja tsaki hade da furzar da iska ta bakinsa" sannan yace matsalata dakai kennan rashin saurin fahimta .
fk yace ta yaya kake so na fahimta ?
Alhalin ga zahirin gaskiya nan" idan son da kake mata ne ,na fahimta wannan.
,Amman kace wai kai baka sonta km kake kokarin aurenta , wannan ne fa bazan taba fahimta ba.sai dai kayi hakuri ,
DEENI ya sake furzar da huci may zafi ranshi yasoma baci muryasa a sarke" yace da alamun kana son mu samu matsala dakai fa" muddin baka daina cewa Ina son yarinyar nan ba .
Idan km kafin son haka ya daga kafadarsa alamun Shikenan ,.
parlour ya dauki shr na wani "dan lokaci, yayinda deeni ya jingina bayansa da kujera da yake zaune, hade da soma jijiga kafarsa daya a tile's dakin " runtse idanunshi Yayi dan jin daci abinda fk din yace"
'ta yaya ma " zai nace akan lallai yana son yarinyar byn shi yasan auren kawai yake da bukatar yi" bawata ,aba soyayya ba ...
maganar fk ce ta daki dodon kunnenshi" to yanzu meyye solution akan maganar, tunda yarinya ta rigada ta amince ?
Ahankali ya bude rikitattun idanunshi ya sauke su ,akan fuskar fk sannan yayi magana cikin sanyi tamkar wanda aka takura masa dole. Yace karkadamu zan samu yaya mahamud ,Ai kagama may wuyar " tare da maida idanunshi ya sake lumshe su tamkar dai yadda yayi dazu .
girgiza kai kawai fk yayi. uhmm shi wannan bazai taba canzawa ba .
halinsa, na nan kmr dai yadda yasan shi" haka km yataso da murdanden raayi " shi komai baya so matsawar ba ra'ayin sa bane"fk yayi magana ne akasan ransa,,.
Ganin da yayi DEENi ya bawa banza ajiyarsa yasa shima ya mike yayi masa sallama yayi ficewarsa .
Daga gurin DEENi kai tsaye fk part dinsu shemah yayi ,ba bata lokaci yasamu yaro ya tura ayi masa kiranta dan ya kudirtawa ransa ,yau ce, ranar da zai isar da sakon zuciyarsa gareta domin yagaji da cutar da kansa .
tafito sanye cikin doguwar rigar material puppy colour mai shegen kyau hade da yane kanta da karamin mayafe baki,
ahankali take isowa gareshi duk step daya datayi Sai kirjinta ya motsa sakamakon dukiyar fulani dake gareta.
tun fitowarta ya zubawa kirjinta idanunshi kyam ko kyafta ido bai yi yana kallon yadda albarkatun kirjinta ke motsawa, lumshe idanunsa shi yayi na wani lokacin ,sannan ya sake budesu ahankali. mutuwar tsaye yayi a gurin " har takaraso inda yake tayi sallama.
bai dauke idanunshi "akanta ba .Sai ma cigaba da yayi" da binta da wani irin mayataccen kallo wanda yasa shemah tasha jinin jikinta.
Ganin irin duban da take masa ne yayi saurin ,sauke idanunshi,tare da sakin ajiyar zuciya, ta gaisheshi ya amsa cikin sakin fuska, yana sake bin koina na jikinta da kallo dan tayi masa kyau matuka ,rigar jikinta irin mai flay akasa ce Sai dai taka mata a sama sosai. cikin sanyi murya tace yaya faruk Gani , Yace Ai naganki .
,yayi shr yana tunanin ta inda zai soma ,itama shr tayi Sai dai,haka kawai ta tsinci kanta da jin ,faduwar gaba. haka nan kallon da yaya faruk din kema ,yasa taji wani iri ajikinta ,dan haka ,ta sunkuyar da kanta kasa tana Jira daga gareshi.
,can numfasa,hade da jin kwarin gwiwa yazo masa ,ya danyi gyaran murya" yace daman nazo ne na fayace miki abinda na dade Ina boyewa akanki , taji gabanta yashiga faduwa ,ta dan dago kadan ,taga ita yake kallo , ahankali tace na mefa? Sannan ta km maida kanta kasa tana jin yadda gabanta ke lugude faduwa.
Yayi murmushi yana cigaba da kallonta, cikin natsuwa da jarumta.
yasanar mata koma .
tun da yasoma magana tayi shr kawai hade da sake sunkuyar da kanta kasa, sosai badan tana jin dadin sauraron abinda yake kokarin fahimtar din bane ,taji hankalinta ya yayi matukar tashi dan haka , ahankali ta dago kanta , ta zuba masa idanunta , Sai data tabbatar daya gama fadar abinda yakawoshi a dan frigice tace ,dan Allah yaya kayi hakuri wlh akwai wanda zuciyata ta dade da kamuwa da soyayyarsa , Amman kayi hakuri idan maganata ta bata maka rai ,yace Ina fa za bata min rai Ai iya gaskiyar ki kika fada Sai dai ki sani zuciyata bazata iya wannan hakura dake bani ba Sai d zan baki lokaci kiyi tunani akai , tace tunanin me km zanyi? nifa bawani tunanin dazanyi ka dai yi hakuri kawai ka nemi wata ,ta juya ta wuce tabar sa nan tsaye .
,da mamaki yabi bayanta da kallo ya dauki lokacin tsaye a gurin batare da yasan abinda zaiyi ba , Ganin tsayuwa nasa bata da wani amfani yasa yasoma kokarin daga kafafunsa da suka masa nauyi, ahankali yake daga kafafunsa yana saka da warwara" da tunanin makomasarsa a gurinta .
,a fusace shemah tashiga part dinsu tana zuba tsaki da zage zage har mmnta ta tambayeta abinda yasameta tace mata bakomai.
Byn kwana biyu
Da misalin karfe takwas na dare fk ya km samu shemah da zance ,shi fa bai ji zai iya wani hakura daita ka " kawai tayi hakuri ta amincewa da aurensa , domin shi yana matukar sonta ,tace ni dai dan Allah yaya kayi hakuri wlh da bbu wanda nake so ne ,zan iya aurenka dan kaima baka rasa komai da zankika ba . kadai yi hakuri kawai .
al'amarin dayayi matukar dagawa fk hankali kennan ,yayi shr kawai yana kallon yanayinta tare da nazarin kalamanta masu kokarin tarwatsa masa zuciyar rasa " yatasa yadda zaiyi daita, can dabara tazo masa, dan haka ya tsareta da idanunshi Yace ke banso iskanci da rainin hankali fa" ni zaki cewa kina da wanda zaki kike so byn Banga uban da kike saurara ba.
,lafazinsa yayi, matukar bata haushi da mugun bata mata rai" dan haka ranta a bace tace to dole ne Sai na aurenka kaje Kanemi wata mana ko ana soyayya dole ? ta juya a fusace zata bar guri ,ba zato ba tsammani taji ya fizgo hannuta , gabadayanta ta fado jikinsa , idanunta "zaro a tsorace, ,take taji wani irin faduwar gaba fiyye da wanda taji dazu , .
Hannuwansa dukka yasa ,ya rungumeta tsam ajikinsa yana sauke ajiyar zuciya "daidai kunneta ya kai bakinsa Yace uhmmm maimaita abinda kikace Ina jinki?
cikin tsiwa tace wannan wani irin iskanci ne dazaka wani rungume mutun ?
Ok nine ma nake miki iskanci ?
Uhmmmm fa shemah karkibari muyi haka dake ,tace muyima mana ,dan Allah ni malam kasake ni ,yayi murmushin karfin hali sannan yace zaki amince ta girma da arziki ne.
ko km na" jawo soyayyartawa " ta karfin tsiya ,.batare da na wahalar da kaina ba. muryarta na rawa ta sake cewa anki a amince da soyayyarka .
ko ana so dole ne ?
, dan Allah ni kasake ni , tun ban saka maka ihu ba ,ya zuba mata manyan idanunshi kawai yana kallonta. ahankali ,yasoma yawo da hannushi a sansar jikinta " gabadaya jikinta ya dauki kirma " abinda bai taba faruwa daita ba kennan" tunda take arayuwarta ,wai namiji ya rabi jikinta har takaita ga runguma ,dan takaici ma batasan sanda ta saki kara ba , kwalla ce cicciko a idanunta . Ya dan sausauta
Rungumar da , yayi mata ya zubawa fuskarta ido hawaye yaga yana silalowa daga idanunta ahankali ya sauke ajiyar zuciya,yasa yatsansa ya dangwalo hawayen dake bin fuskarta yana kallo Yace duk wannan kukan akan nace Ina sonki ne kike zubda hawayen ki?
,tayi shr taki cewa komai dan haushi , ji tayi kmr ta daura hannuta akanta ta sake , kurma ihu , ahankali ya sake maida ita jikinsa ya rungumeta yana shinshina wuyanta Yace please kidaina zubda hawayenki, Akan nace Ina sonki wlh duk ma wanda kike tunanin zaki aura nafi shi sonki , yasoma shafa bayanta da hannushi daya , daidai nan Sai ga big dady dake dawo daga masallaci take yaja birki , a tsorace yake binsu da kallo cike da mamaki da alajabi abinda yagani , meke shirin faruwa km yau acikin zuri'arsu ,fk yacigaba shafa bayanta tare da sake manneta da jikinsa yana rarrashita tayi hakuri ta amincewa aurensa .
dagowar nan da zai yi da niyar rabata da jikinsa karaf idanunsa suka sauka cikin na big dady dake tsaye ,gurin da Yar sandarsa yana kallonsu. "duk da duhu ne hakan bai hana ganeshi ba gabansa yaji yayi muguwar faduwa"take jikinsa ya dauki kirma duk da ya tsorata ,hakan bai sa ya saketa ba Sai dai yaji dadi Ganin da big dady din yayi musu .
yasan hakan zai sa a aura masa shemah batare da wani bata lokaci ba "tsabar frigice da yake ciki Ne yasa yakasa rabata da jikinsa gabadaya jikinsu rawa yake shemah da batasan wainar da'ake tuyawa ba .
sake lafewa tayi ajikinsa saboda irin rungumar dayayi mata ba wacce zata iya kwacewa bace" har big sanda big dady ya wuce su a gurin shemah batasa big dady yagansu ba , ahankali fk yasoma rabata daga jikinsa " har zuwa yanzu " hawaye bai daina bin fuskarta ba. Bai tsaya Ganin yanayin datake ciki ba hannuta ya damko yasoma tafiya.
ita kum tana biye dashi a baya , bbu wanda ya iya cewa dan'uwansa komai ,har yakawo part dinsu yaja ya tsaya , sannan ahankali Yace please... shemah kiyi hakuri dan girman Allah kibar kuka nan haka ba nufi na ta kuraki ba .
Ina matukar kaunarki" Ina miki son da ko ni kaina bansan lokacin dana fara ba Amman zan baki lokacin ki sake yi tunani ,zan dawo zuwa jibi yana gama fadar haka ya juya ,da kyar yake iya daga kafafunsa tsabar frigice da nauyin da suka masa zuciyarsa tamkar zata buga , dan fargaba haduwarsu da big dady "shi yasan ba makawa" tunda har big dady yagansu" aure kmr anyi an gama Amman kunya fa? Tana nan har abada .
,har ya iso part dinsu wanda kusan nan samari suke zaune wayanda basuyi aure gumi ke tsatsafo masa,
Itama shemah da kuka ta shiga part dinsu , mamanta dake zaune a parlour tace ke lafiyarki kike kuka ?
ko juyo batayi ba daki ta wuce ,ta fada kan gado ta cigaba da risgar kuka to yaya faruk yake nufi da yana sonta alhalin ita DEENi take mutuwar so ..... Dan haka tace wlh bazata taba aurensa ba ,tunawa datayi ba'a musu auren dole a family dinsu sai sun amince da juna yasa taji hankalinta ya kwanta Amman gabadaya jikinta yayi bala'in yi sanyi, haka ta kwanta da tunanin abinda fk yayi mata Ta dinga jinsa ajikinta tsagar jikinta suka mike ga kamshi turarensa daya fureera ,ko ta juya kamshinsa da hannushi ke yawo a koina na jikinta,.
Washegari ma kin fitowa tayi daga daki ,gabadaya
Yinin ranar a kwance tayi shi batare data fita ko parlour ba .
,fk bai dawo gurinta ba kmr yadda Yace mata kusan sati kennan tsakani ,shiyasa hankalinta ya kwanta Sosai tayi tunanin ko ya janye ne Tare da yiwa kansa fada ya hakura daita ,dan haka ta sake abinta.
kwatsam Sai gashi a wani daren lahadi byn ta gaisheshi, a dage ,yayi murmushi yace shifa yazo ne akan maganar su ,a fusace tace wata magana kennan?
i tough mun gama da wannan zance tunda nace ban sonka , Yace haka kika ce ,tace eh ko dole sai anyi soyyaya dakai?
,Yace ba dole kiyi soyayya dani ba ,Amman Ina son in tabbatar miki da aurena yazame miki dole ,yakamo hannuta ya sumbaci tafin hannuta sannan wuce ya yabar nan tare da damuwa ,
DEENi yasamu yaya mahamud yayi masa bayanin shi kuma ya samu big dady da zance tsohon yaji dadi Sosai jin sun hada kansu yace Shikenan bbu damuwa zai tuntubi yarinyan tukun yaji kafin yaasan abinyi .
Bayan wata daya
A wata lahadi da takasance ta karshen wata wanda sukeyi taronsu na family.
Holl din cike da yaya da jikoki tare da iyaye kowa kagani cike yake da tsantsar murna sabanin shemah da jikinta ke a tsanyaye sakamakon jin rade radin datayi na DEENi ne zai aure zeenat km Sai lokacin tasan dalilin dayasa zeenat ta mata wulakanci kwanaki
Byn wani lokacin gaishe gaishe ne yasoma biyu baya.
Takan shemah big dady yasoma, bai tsaya jin tabakinta ba yace akwai wanda taKe so ne ? Tace A'a yace shikennan yabawa faruk aurenta Take hawaye wanke mata fuska baita ba ko fk dake kokarin kiran DEENi wanda shi kadai bai iso ba , duk da hukunci big dady yayi masa dadi hakan bai hana jin gabansa faduwa ba daidai lokacin DEENI ya dau waya yaakayi ne mlm zaka dameni da kira fk yace angama dani fa sauran kai DEENI yace mezanzo yi km ? Fk yace kai fa dan rainin hankali ne zaka ce bakasan abinda akayi ba yau , uhmmmm tare da katse kiran Yama kashe wayar gabadaya dan bai son damuwa ,.
Kuka sosai shemah takeyi ta dinga datasanin cewa bata kowa gashi an kasaba mata auren fk nan Aka kira zeenat itama big dady yayi mata Mata tmbyrta ta Amince Sai sanda akazo neman su fk aka nemi DEENI akarasa kiran duniya akayiwa wayarsa taki shiga ,daga karshe big dady yace tunda yaji raayin zeenat din Ai