Chapter 47 Reading AUREN SIRRI Book 2 Complete by Aisha Bagudu.txt Arewa Novels

AUREN SIRRI Book 2 Complete by Aisha Bagudu.txt

Author :  Aisha Bagudu Category :  Old Hausa Novels

Chapter   47 / 123

138K to 141K   out of 366.6K words

salisu din ya zama wakilin nablah .


Sule yaji mamakin wannan auren daka daura abu kmr a al,mara to daman ogansa aure zaiyi batare da sanin kowa , to wannan wani irin aure ne Haka .

Byn angama daurin auren deeni ya mikowa mlm salisu jakar kudin amman mlm salisu yaki kabar sai ma cewa da yayi nasuru ka rike kudinka domin bbu abinda zanyi dashi .

duk da bansaka km bansan daga inda kazo neman auren diyata ba Haka kawai naji Na amince nabaka auren nablah Ni kawai abinda nake bukata daga gareka shine ,idan Allah Yasa kadawo daga tafiyar dazakayi lfy kasadani Ga danginka amman bazan karbi kudinka ba .

Wani irin kunyar dattijon ne yakama DEENI yaji tamkar kasa ta bude ya netsina ciki dan kwata kwata baiyin tunanin dattijon zaiki amsar irin wannan kudin ba .a wannan zamanin da ake ciki, na kaka nakayin.
da wuya kasamu irin dattijon duk da alamun bbu dayake hangowa atattar dashi muhalinsa kadai yaisa ya tabbatar wa mutun yadda yake gudanar da rayuwarsa.

Haka kawai deeni yasamu kanshi da kiran dattijon da baba ... dan Allah karkayi min Haka kar kace baza karba kudin nan ba

Da farko nayi tunanin bazaka amincemin da aurenta bane 'cikin wannan lokacin danafi bukata shiyasa kaji na daura sharadi akai .

Amman yanzu dattakonka gareni yafi karfin wannan kudin .
dan Haka har ga Allah Na baka wannan kudin idan ma kana bukatar wasu zan karaka maka ..

mlm salisu yace Sam bazai karba sai wani abokin mlm salisu din yasa baki sannan yasa hannu ya amshi jakar kudin Tare da sanyawa deeni albarka .

daman km yana da bukatarsu. Sukayi sallama da zumar Sai Allah Ya dawo dashi ..


Mlm salisu Yashiga gidansa cike da murna yana duban Salmah da nurat Sai mahafiyarsu dake zaune suna tattaunawa akan batun nablah din .

Yakarasa shigowa yana murmushi Tare da ajiye musu jakar kudi a gabansu ya zuge.

Kudin suka bayayyana bbu Wanda Bai ji tsoron ganin kudin ba sbd tsabar yawansu .

Mlm salisu yace
Ku duba kuga ikon Allah sanadin diyata nabla Yar albarka Na samesu suka shiga dubansa da alamun tmby a saman fuskokinsu .

, yacigaba yanzu nan Na daurawa nablah aure da wani mutumin kirki dayazo neman aurenta km shiya bani wannan kudaden da kuke Gani .

mahaiyarsu saratu wacce suke Kira mama tace wacce nabeela kake mgnr ka daurawa aure .

,Ina da wata nabeela ne byn diyata ,ita din aka daurawa aure yanzu.
gama sadakinta nan ya fidda wasu kudin .

Mama tace ,cewa zakayi kasiyar min da yarinya kawai bawai ka daura mata aure ba amman abinda zai sa hankalina ya kwanta sanin inda nablah take a halin yanzu .
Dan haka duk ma Wanda kabawa aurenta kabashi gaibu . Ka dai daura aure dashi ne Amman bashida mata .


Mlm salisu ya hade rai Ke dai kika sani Yar Bakin ciki kawai Ai ba tun yau nasan bakya son cigaba Na . Yau dai tawa ce to Na aurar daita Ga Wanda nake so km kina zaune za'a yi bikin nablah ta wuce gidan aurenta .

Duk magangun da mlm salisu ke yi mama Tayi shr batare da ta sake cewa komai ba sbd alamun da Salmah Tayi mata Na kar tayi mgn .

Ke km Salmah mlm salisu ya kanta wlh wlh kinji ransuwar muslimi kwana biyu kacal nabaki ke dawo min yarinyata may kan sa'a da kan arziki kafin nasoma cin uwarki ,dan wulakanci ke kina zaune a gidan mijinki lfy Sai tawa Yar ce ta iya zuwa neman abin duniya ke kar ma Na sake ganin kafarki a gidan nan muddin ba da nabeela bane shasha banza dabatasan ciwon kanta ba yaja tsaki yana kokarin shegewa ciki kuryar da jakar kudinsa . Gabadayansu da idanu suka bishi da shi hankalinsu ,a tashe.



Kirrrrrrrrrr... kirrrrrr ......kirrrrrrrr... karar bell ya cika koina a gidan.
nablah dake tahowa daga kan step ta hanzarta saukowa da sauri ta nufi Bakin kofa ta bude .

Kabiru may wankinsu Zeenat ta Gani tsaye a 'bakin kofa yana sakar mata murmushi itama murmushi Tayi masa tare da gaidashi.

Daidai lokacin da motar deeni tasanyo kai 'cikin estate din idanunshi suka sauka akan nablah fuskar nablah dake sakarwa kabiru murmushi .
take annurin dake fuskarsa ya dauke gabansa ya daki uku uku ya fadi yayinda zuciyarsa tashiga aikinta data saba wato dokawa da sauri har sanda sule yayi parking motar idanunshi nakansu yakasa daukewa.

mlm nablah kennan ya gida da aiki inji cewar kabiru .
Nablah tace duk lfy wlh ya naka aikin Shima ya amsa mata da lfy suka shiga hirarsu sama sama dashi sbd sun dan saba .

Kusan minti goma deeni yayi , zaune a mota ya kasa fitowa sakamakon dokawar da zuciyar takeyi da sauri ya dinga jin tamkar ana masa wanka ne da tafashashen ruwan zafi ne ajikinsa yayinda natsuwarsa ke kokarin barin gangar jikinsa take gumi ya rufe shi takoina ajikinsa .
ahankali ya ciro hanky daga aljihun gaban rigarsa ya goge gumin dake tsaftsafo masa batare da ya sauke idanunshi daga kallonsu ba har zuwa sanda yaga kbr ya Miko mata kaya a wata jaka ya juya yana sake yiwa nabla murmushi .
Wanda sauran kadan zuciyar deeni ta tarwatse tsabar frigici .
Ahankali yasoma kokarin fitowa daga mota byn sule ya bude masa .


'Tana shiga gidan taje ta, ajiye kayan a inda tasaba ganin ana ajiyewa sannan ta nufi kitchen tasoma aikin girki hade da wanke kayan da akayi amfani dasu, kasancewa yau Sunday ce.
Laraba tana church ummi kuma sun fita tare da aunty zeenat da safeena ba yadda ummi da safeena basu daita akan tazo su fita tare tace A'a saboda ita bata damu da yawan fita ba ko agidansu.

cikin sanyi jiki take aikinta da zeenat ta gama koya mata kalar abinci da mai gidan yafi son cin ne yau aka bata practices dan aga yadda kwarewarta tayi.

kamshin turaren mat Hamilton 27 datashaka ne ya haddasa mata faduwar gaba Wanda tun safe take jinta Haka .

DEENI tsaye abakin Kofa kitchen din yana aiko mata da kallon tsana byn yaje yayi freshe up .

'Cikin tsananin tsoro da fargaban abinda zata Gani ta juyo karaf idanunsu suka sarke cikin juna take zuciyoyiinsu ya bagu... gabansu Yashiga faduwa .
da sauri tayi kasa da kanta ta dinga karanto duk wata addu'a datasani na neman tsari .

Ahankali ya tabe bakinsa yakaraso cikin kitchen din Sosai .
"cikin muryasa may matukar dadi da sauraro yace ke..uban me kike Jira da har yanzu baki gama abinci ba .

wani irin shock...ne yajata ,jikinta yasoma sheking takasa furta komai ya daka mata wata irin razananniyar tsawa ke ..
Ba magana nake miki ba yakarasa maganar cikin kunar rai .

"muryarta na rawa tace dan Allah kayi hakuri wlh nakusan gamawa yace you are very stupid dake da gamawarki kina tunanin an daukeki aiki ne dan kidinga yiwa mutane iskanci da aikin ba'a kan lokacin ba.

mamaki hade da tsoro sukayi nasarar lullubeta ko kwakwarar motse gagararta yayi .

yayinda haushinta ya sake turnuke wuyan DEENI a harzuke ya fizgo hannuta yace ke me kike takama dashi ke waye ma ubanki duk fadin Africa da har zandinga miki magana kiyi banza dani tayi kokarin fizge hannuta sai dai kashi ...ta kasa abunku ga soja.
gata yarinya karfin su ba daya ba , ko namiji DEENI yarike da wuya ya iya kwatar kansa.

ranta ya baci matukar dan haka itama fusace tace dan Allah malam ka sakar min hannu .

kallon baki isa ba ya watsa mata sannan ya sake matse mata hannu Sosai yana kallonta cikin tsigar wulakancin hade da sake damke laulausar fatar hannuta.

yace ki kwace hannu mana idan kin isa , tasoma girgiza kai dan wani irin radadin azaba da takeji acikin kashin hannuta .
tayi kasa da kanta 'tana zubda hawaye tausayin kanta domin ita takawo kanta cikin wannan maseefar datake ciki.

ashe rabon wahala ne yakawota gidan batasani ba .

sai da yaga ji dan kansa sannan ya wurgar da hannuta nata da karfe ya juya cikin tafiyarsa ta kasaita da jan hankalin duk wanda ya kalleshi.

minti goma kacal na baki kigama sannan yakarasa barin kitchen.
ta durkusa kasa tare da fashewa da wani matsanancin kuka tasoma datasanin zuwanta aiki uguwar lekki ,da kyar ta iya mike.

tacigaba da aikin girkin hawaye nabin kuncinta sai da ta kammala da komai ta shirya akan dening area sannan tazo ta wuce ta gabansa yana kwance a kan three sites hannunsa dafe da kirjinsa har tayi step daya zuwa uku tajiyo shigowarsu ummi ta dawo ahankali hade dayi musu sannu da zuwa .

ummi da safeena suka bita da kallo byn ta amsa sannan ummi tace ya naganki haka wani afrigice afrigice nablah ta kirkiro murmushin dole tace bbu komai ummi .

Amman naga idanuki kmr kinyi kuka cikin sanyi murya tace uhm ....dazo ne danake aiki wani abu ya fadamin a ido .

ummi tace ok sannan ta juya gun zeenat dake zaune kusa da DEENI tana tambayarsa ko yaci abinci .
a harzuke ya bude idanunshi tare da watsa mata harara sannan ya juya mata baya please i don't won't any distoping ... now.


Zeenat bata daddaraba Ta sake tmbyesa kowani abu Nadamunsa ne . Zeenat.... yakira sunanta why are you distracting my hrt ... tace sorry Tare da mikewa tsam tayi dakinta gudun kada ya wuce akanta duk da batasan sanadin fushin nashi ba.

nablah dake tsaye kusa ummi dan oready safeena ta bar gurin tace bari nima na bace daga nan .

dan abinda nablah tayi noticing daga deeni hatta matar aurensa ba raga mata yake ba.
,Ina Ga ita bazanr bazara dan Haka ta zame ta gudu dakinta tabarshi da ummi .


Ummi ta zauna gefensa tana tofeshi da addu'oi tarasa wani irin zafi rai ne haka ke damun dan nata abin fushi dama wanda bana fushi ba duk yi yake.
tsawon lokacin yana kwance har sanda yaji kiransa daga masallaci dake 'cikin gidan ya mike a sukwane ya dan kalli ummi kmr zaiyi mata murmushi sai kuma ya fasa ta kira sunansa ya dago batare da ya amsa ba Kaci abinci ?

ya yasina fuska har dimple dinsa na lotsawa dan haka tagane bai ci ba .

da hannuta ta nuna masa alamun yakoma ya zauna .
da kanta taje dinning ta bude kulolin abinci taji kamshin ya bugi hancinta ta zubo masa abinci takawo masa har gabansa.
Tace oya ci abinci ahankali yasoma motsi bakinsa first love nifa bazan ci wannan jagwalgwalon yarinyar nan ba ummi ta koma ta zauna inda ta tashi ta hade fuska tamau takiyin magana sai idanu data zuba masa 'tana kallonsa .
dan haka yake wani lokacin idan yana cikin fushi dayaga ta hade rai sai kaga yasoma shiga taitayinsa dan HK ya dan sake fuska kadan yasoma cin abinci yana kai lomar farko yaji kunnenshi ya dan sheking yasa hannunsa yana tsosa gun wasa wasa dai sai da oga DEENI ya tashi da Rabin plate sannan ummi ta sakin ranta tana masa dariya tace har ka koshi kennan da dai kakarasa cin jagwalgwalon mana shegen salo da iyayi kawai .
ya yasina fuska yana kallon umminsa yace uhmm byn manage kawai nayi wajen tura abinci ummi ta sake yin dariya tooo ..nagode dakayi manage Kaci yagane sarai tsokanarsa ummi take dan hakabya mike yana ce mata shi ya wuce masallaci .

Ita kuwa nablah tana shiga dakinta karamin Fridge din dake dakin ta bude Tasha ruwan.
gashi tana jin wani irin maseefaffen bacci Amman batason tayi bacci byn la'asar sai yanzu tasoma kwadayin rike waya a hannuta dan ko ba komai zata rinka rage mata kewargida. tajawa kanta tsaki tace kai nablah kin cika yawa wlh karfe biyar daidai ta sauko parlour kasa tasamu lokacin duk suna kallo .
ko kallon inda ummi da deeni su ke zaune batayi ba wajen zeenat tayi tana tmbyrta ko akwai aikin da zatayi duk da tasan ta kammala da komai kuma laraba ma ta dan jima da dawo wa


Zeenat ta girgiza kai kawai batare datace komai ba Shima ganin ummi dake zaune.
dan yanzu takanyi shakkan yi mata wani abu a gaban ummi.

Nablah ta juya takoma dakinta ta zuge handbag dinta ta dauko currency affairs 'tana dubawa ahankali har aka Kira sallah magariba.




MMN SUDAIS CE
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO


*Waannan shafin sadaukarwa ne gareku masoyan arziki tare da yi muku fatan alkhari a duk inda kuke kaunar dake tsakaninmu daga Allah ne ,Ina rokon Allah s.w.a ya barmu taren Tare har abada sannan ya hada fuskokinmu a jannatul firdaus Ameen*

*Mrs splendid*
*Maryam tijjani Adam*
*Safeena mukhtar getso*
*Maryam kalgo*
*Adaweeyyah*
*MMN hafeez*
*Murja*
*Fateema abuje bagudo*
*Aina,u gadan kaya*
*MMN Aliyu*
*MMN illima*
*Faiza bsbs*
*MMN sadik*


*Ina Mika godiyata gareku all auren sirri fans sakonninku yana isowa gareni kai tsaye Ina jin dadi yadda kuke Nuna min kauna Ina addu'ar Allah Yasa kar soyayyarsa nan ta tsaya iya social media kawai tazarce har illa Masha Alla kyawun tare inshallahu*






Page 70




Mikewa Tayi 'cikin sanyi jiki taje tayo alwala tasoma gabatar da sallar magriba , baita ta Mike daga kan praymat dinta ba har sai da Tayi sallar isha'i.


Kwance take lamo akan gadonta ita daya Tayi shr hannuta rike da karamin litattafin garkuwar muslinci, hisnul muslim. 'tana dubawa ahankali Amadadin abin da take karantawa ya dinga shiga kwalkwaluwarta sai ma wani tunani ne yazo mata .
Sosai ta afka 'cikin damuwa yayinda tunanin duniya ya taru yayi mata yawa .



Tunanin gida da mamanta da mahaifinta har ma da ah'linta, duk shi yafi damun xuciyarta ,ko a wani yanayi en gidansu suke cigaba da rayuwarsu ?


Ko wani hali mahaifinta yashiga lokacin daya dawo gida ya iske bata nan ?

Allah shine masani ...ta fadi hakan 'cikin zuciyarta 'tana may langwabar da kanta gefe .
" take nadamar rashin bin umarnin mahaifnta yashigeta, gashi takawo kanta cikin tsaka may inda ba,asan darajarta da mutuncinta ba" to meyye amfanin zuwanta neman kudin shiga Jami,a alhalin mahaifinta Bai yarda da hakan ba.

Anya kuwa batayi kuskure a rayuwarta ba ?
Anya kuwa ko kudin tasamu zasu mata albarka datake son cigaba da karatunta dashi ?


Ta Dade kwance 'tana tunanin rayuwarta ganin bbu sarki sai Allah Yasa tabawa zuciyarta hakuri ......Tare da Mike ahankali tayiwa kofar dakinta key sannan tashige bathroom with that thinking tayi wanka
shape shape Tare da dauro alwala gabadaya.

tafito 'tana goge jikinta da dan karamin towel din dake daure ajikinta Wanda Bai Ida gama rufe mata jikinta ba sosai. Dan kana kallon wasu surorin jikinta a bayyane .
,sai data gama gogge koina a jikinta sannan daga karshe taje ta maida towel din jikin kofar bayi.
Ta dawo gaban mirrow ta tsaya 'tasoma kokarin tufke yalwantaccen sumar kanta gefe" Wanda tsabar yawansa yasa da kyar take iya tattarosu ,Tare da tufkesu gefe daya domin tasamu damar yin bacci Sosai dan wani lokacin idan ta tufke gashin a tsakiyar kanta bata tasamun natsuwar yin bacci Sosai.



A Ranar DEENI Bai samu damar sanar da umminsa komai a game da aurensa da aka daura da nablah ba.
sbd haushin yarinyar da yake tawainiyya da zuciyarsa km hakan yasamu nasaba ne da ganin da yayi mata Tare da kabir mai wankinsu .

Ko yanzu da yake zaune a dakinsa bbu komai ajikinsa facce dan karamin wando short niker iya cinyarsa .
"koina ka kalla ajikinshi gashi ne kwance sai sheki da daukar hankali suke Tare da birgerwa tsabar kyawun halitta da Allah (s.w.a) yayi masa , kwantaccen gashin jikinsa suna kwance luf.luf..ta koina abin Sha,awa yayinda kan nipply dinsa dake manne Dass da kirjinshi zagaye da gargasan gashi , sai yazamo tamkar wani ado ne akawa nipply din .

DEENI ba baya wajen kyau da tsarin jiki shi din cikakken nmj ne guda har da rabi ,wato first class saannan unique man abin so da bukatar kowace macce gashi da mugun shiga rai .
"kallo daya zaka yi masa kaji yatafi da hankalinka . document ne da file files zube agurin yana kokarin sa hannu acikin takardun dake gabansa , ganin da yayiwa yarinyar dazu da rana ne ya sake fado masa, take yaji gabansa yayi wani irin mummunar faduwa yayinda zuciyarsa tasoma bugawa da sauri da sauri .... hankalinsa a tashe yake mamakin da al,ajabin abinda yasashi jin haushin ganinta da kB dazu .

to meyyesa .... meyesa zanji haushin Dan kawai naganta tare da kB?
tmbyr daya jihowa kansa kennan wanda bashida may bashi amsar tmbyrsa ahalin yanzu .

Ya Dade zaune a dakinsa hade da zubawa takardun dake zube gabansa idanun kawai so yake ya gano takamaiman dalilin da Yasa yake tunanin yarinyar da yake ikirarin Bai son aurenta asalima ya tsani ya bude idanunshi ya ganta near him . rasa gano dalilin daya sa yaji haushin

47 / 123