Author : Aisha Bagudu Category : Old Hausa Novels
,ayi maganar zuwa asibiti ,tace ga zance ga magana .
Su samiha da sukake shigowa suka gaishe da ya deeni ya amsa yana kokarin mikewa.
Tare da cewa To madam ni zan dan fita say na dawo .
Zeenat dake kwance kan cinyar Ummi tace ok Yaya ni dai say zuwa jibi zan dawo.
uhm kiyi zamanki ,inkin iya ma karki dawo.
,Ummi ta harareshi tace wani irin magana ce haka ?
, first lov baki ji abinda tace min bane tsabar ta rainani.
,to yi hakuri sarkin zuciya jeka say kadawo Allah ya tsare .
ita dai zeenat tsit tayi da bakin ganin yadda ya dau zafi , kyacci yayi tare da jan tsaki sannan Yasa kai ya fice abinsa .
Hirar yaushe gamo ta barke tsakaninsu.
,Ummi ta dubi zeenat me zaki ci a dafa miki ta dan langwabar da kanta tana tunanin abinda zatace Amin soyayyiyar doya ,Ummi ta sake kallonta da kyau dan sanin data mata bata cin doya ,shr kawai tayi ta nufi kitchen .
Har dare suna tare dasu shemah sunki tafiya .
,to oga da kanta ce yau tazo gida, dan zeenat ce lidarsau gabadaya komai za'a yi sai tabada Command sannan za'a yi .
" dan haka gabadayasu suka taro anan part din Ummi suna ta hira har sanda Ummi tagama soya doyar tace Maryam tazo ta daukar musu.
tare suka ci suka sha ,sai zeena bata wani ci may yawa ba .
say faman murna take ganinta cikin yan'uwanta .
ta gefe daya km ga Ummi murna tamkar ta kasheta dan dadi .
,har mantawa tayi da wani deeni ,dama wayarta gabadaya.
, deeni yayita kiranta a waya yaji shr taba dauka ba.
,har say data kaishi ga kiran Ummi ta miko mata wayar .
ta karba tare da bmyr Ummi da hannuta waye ,mijinki abinda Ummi ta fada kennan.
Ai da sauri Ta manne wayar a kunneta tare da sallama ,ko amsa sallamar bai yi ba .
Yana jin muryarta yace ke.... dan iskan Ina kika shiga kika bar wayarki ,tun daxo Ina faman kira?
,mikewa tayi tsam tayi ciki dakin Ummi tare da marairaice murya wayyo dan Allah Yaya kayi hakuri wlh abinci nake ci .
km wayar tana cikin hand bag dina.
Cin abinci ne har tsawon awa hudu ?
Kifa kiyaye zeenat .
naga kmr kanki na rawa rawa fa.
Say hakuri take faman bashi ,shi km yana sake botsarewa ,ki cigaba zan gyara miki ,zama ne bar ganin kina kusa da Ummi ,km kishirya ganin nan zuwa ,mu wuce ,gida .
Batasan sanda ta sakar masa kuka ba.
tana sake bashi hakuri ok kuka ma zaki yi wa mutane tsabar kin raina min hankali ko .
, , ita dai batace masa komai ba say ma hakuri data tacigaba bashi .
, dan Allah Yaya kar kamin haka kabarni zuwa byn suna na koma .
,gobe ne sunan fa.
,anki abar ki' idan ma kika sa wasa ,sunan ma ba zakizo ba gabadaya naga abinda zai faru.
,kawai ya kashe wayarsa batare da tsaya jin abinda zatace ba .
Sosai take kuka har takaraso ta mikawa Ummi wayar duk da ta dan goge hawayen fuskarta hakan bai hana Ummi ganewa ba .
,ta tambayeta tace bbu komai ,haka dai zakice bbu komai kiyi ta zama da abu acikin har yazo yamiki illa.
,ta zauna tare dayin shr sure Maryam ma sudan ga sauyi a tare daita Amman bbu wanda ya damu da tmbyrta ,suka cigaba da hirar su sama sama .
Shr kawai tayi zaune a gurin yayinda ta dinga jin wani abu nataso mata a kahon zuciya, tasa hannu ta dafe kirjinta tare da runtse idanunta gam cigaba abin yayi da taso mata .
gabadaya cikinta ya aushine ,bakinta yacika da miya ,wani irin amai taji yana taso mata ,da gudu tayi bathroom din dake manne a main parlour .
Ako ta dinga Kwara amai ba kaukautawa tare da rike cikinta .
Aman ta dinga kwarawa tamkar zata amayo da kayan cikinta . gabadayansu suka gigice sukayo kanta sunata mata sannu.
Maryam ce tayi dakin Ummi dan ta sanar mata.
Wani yunkurin amai ta sake yi ,dai dai lokacin da deeni ya sawo kanshi cikin gidan
,da sauri ya karasa shigowa duk da bai san takamaiman wakeyin amain ba.
,suna ganinsa suka dare gabadaya ,ga mamakinsa zeenat ya hangota durkushe Sai amai take Kwara gabadaya ta galaibaita jikinta yayi week ,atare suka yo kanta shi da Ummi kusan ma yariga Ummi karasowa bakin kofar bayin yana kallonta har lokacin amai take
say dai ga , dukkanin ,alamun bbu wani wadataccen abinci acikinta .
Ahankali ya durkusa a gabanta ya dafa kafadarta yana mata sannu.
,zaman dirshan tayi a bakin kofar tana mayar da numfashi .
Ta fashe da kuka da ,tare da jingina jikin bangon .ruwa ya dibo ya wanke mata bakinta da fuskarta .
ganin haka yasa Ummi juyawa takoma dakinta tare yin addu'ar Allah ya inganta musu , daman ita tun wancen zuwan nata datayi gidan nasu ,take ma zeenat din kallon may ciki.
Zeenat duk tarasa inda zatasa kanta taji dadi.
km har lokacin su samiha na sunki tafiya , ahankali deeni ya juyo inda suke tsaye cirko cirko suna kallon shi da zeenat din .
,muryarsa zafafe Yace tsayuwar uban me kukewa mutane ,yan iskan banza kawai yarinya tana mai anrasa wanda zai taimaka mata ,duk kunzo kun rufeta kuna kokarin kasheta.
,Ai tunin suka gigice suka soma tattara inasu Ina su ,subar gidan .
Yaja tsaki ya km maida kansa kan matarsa .
Juye juye kaiwa take tana kuka tare da kiran sunan Ummi .
ya fizgota tare da daka mata tsawa kina hauka ne ?
ko kallonsa batayi batayi ahankali tasoma rarrafawa tafito daga bathroom din ta zauna kan kujera ta jingina kanta tacigaba da kuka tana mayar da numfashi.
ya Mike ya dawo kusa daita yana kallonta yasa hannushi zai dafata ta Mike da sauri Ta km shige bathroom ta durkusa tashiga kwara wani amai ,jikinta har wani rawa yake.
lokaci daya jikinta ya dauki zafi ya riketa yana mata sannu ta langwabe masa tasoma kokarin mikewa ya rikota.
Yace Ina zaki? gurin Ummi zani .
,say km ta fada kansa wayyo kwanciya zanyi na gaji yaya ..
Ya dagota ya wanke mata baki da jikinta ,ya dauke cak yayi dakin Ummi ,daita.
Ummi ,ta dinga jero mata sannu .....
, mikowa Ummi hannuta take alamun tazo gareta.
,Ummi takarasa ta zauna kusa daita ta kamo hannuta cikin nata.
,sannu zeenat .ya jiki
Ahankali zeenat ta lumshe idanunta ,cikin sanyi murya yadda deeni bazai ji abinda zata fadawa ummin ba.
Tace ,ummin dan Allah karki bari Yaya deeni ya tafi dani gida ,take gaban Ummi yashiga dukan uku uku.
,itama ummi cikin muryata kasa kasa tace wani abun yake miki agidan ta girgiza kai.
wlh baya min komai sbd sunan shemah ne.
,say lokacin gaban Ummi yabar faduwa dayake .
tace shikennan ta Mike tabar dakin ,shi km deeni ya dawo inda Ummi ta tashi.
,daukarta yayi ya zaunar daita akan cinyarsa ,ya hada fuskarshi da tata waje daya ido cikin ido suke kallon juna , zeenat ....yakira sunan da wata irin murya ta wacce tayi nasarar kashe mata jiki ,ta amsa da Na'...am ....my hrt.
sunan data kirashi dashi yayi mishi dadi Sosai har yasa shi yi murmushi wanda har dimple dinsa ya lotsa .
Idanunsa ya zuba mata yana sake kallon kwayar idanunta .
Yace Me kika sanarwa first lov wanda ni kika kasa sanar min after ol ma
meke damunki kika dinga kwara irin wannan amai ?
Ta girgiza masa kai kawai alamun bbu komai .
Yace yanzu yakike jin jikin naki.
da kyar ta iya bude bakinta tace daidai nake jina.
say abunda ba'a rasa ba .
,yace kinci abinci ma kuwa?
,tayi murmushin karfin hali ,tareda cewa naci doya dazu itace ma ta dinga tasomin .
Amman Tunda na amayar daita naji ,daidai.
, Yace ok ki shirya mu wuce gidanmu ko ..
ba mutsu tace masa to tasoma kokarin mikewa yace bi ahankali fa .
Tsab ta shirya abunta kmr bbu abinda ta shuka .
, parlour'n kasa , Suka tadda Ummi a zaune tana kallon labarai a CNN.
'ahankali Ummi ta dago tana kallonsu ,Ina zuwa haka km .
,sukayi suru suru dukkansu suna duban Ummi dake zaune.
say ma deeni ne yayi karfin hali cewa gida zamu .
gidan lfy zaku byn kana kallon yarinta badata da lfy shine ,zaka wani ce gida.
Ba gida ba tukun runbu zaku dan Allah ni kyalle min yarinta takara samun natsuwa .
,Yaya da naci haka idan zaka iya kadawo jibi ka tafi daita.
DEENI yaji tamkar kasa ta tsage yashige cikin Dan tsabar kunya da takaici abinda Ummi tamasa ,.
Take 'ya Gane setup , ne kawai aka masa dan kar zeenat din tabishi .
dan haka ya dinga kallon zeenat din tare da hararar ta .
Da sauri tace Allah Yaya ni bbu ruwa acikin ,mu wuce kawai abunmu .
da hannushi ya katseta ,karki dama kiyi zamanki kawai basai kin bini ba ya juya.
,tabi bayansa da hanzari zata bishi.
Ummi takira sunnanta ke zeenat dawo nan ahankali tasoma girgizawa Ummi kai tamkar wata kadangaruwa.
Wai ,bada ke nake ba inji cewar Ummi ,jikinta a sabule ta dawo kusa da Ummi .
ta zauna ,duk jikinta yayi mata sanyi .
Ummi tace kima saki jikinki ki manta dashi ,ki daina wani dar dar .
,ke wai har yanzu baki bar jin tsoransa ? Zeenat Ta zubawa Ummi ido kawai tana kallonta ,Ummi tace kin tsareni da idanu .
, zeenat tace Ai kece Ummi da wani abu.
Aa ba haka yakama kiyi masa ba.
.ni dana so ki lallabaminshi ya Amince da kanshi Shi kika tunzarashi .
Ummi ta saki baki Aa ba tunzarashi nayi ba kashe shi nayi .
,wawiya kawai kicigaba da jin tsoronsa say ya kwashe miki hanjin ciki tare da manna miki hauka .
Dan haka Zeenat din tayi shr ,dan gsky bataji dadin abinda tayi masa ba .
ahankali ummi ta dinga janta da hira har dai zeenat din ta saki jikinta sosai suka shiga hirarsu .
Har shadayan dare , zeenat tasoma gyangyadi Ummi tace suje su kwanta .
Kwance take akan gadon Ummi .hankalinta kwance take sharar bacci ba matsi ba takurar oga deeni ,yau daya taji salama , har taso ta makara tashin asuba sai da Ummi tayi da gaske tukun ta mkie .
Washegari ranar suna yaro yaci sunan mahaifin deeni ,wato aliyu .
Deeni yaji dadin sosai da karar da faruk yayi masa .dan haka takardar gida sukutun deeni yabawa bby kusan shi yayi komai na suna har raguna sunan yaron da kaya akwati goma sha biyu , ,hatta Holl din da,akayi taron suna shi yakama Amman ita kwata kwata batasani ba dan ko kiranta baiyi ba .
Har Washegari suna deeni bai nemeta ba irin shariyar dayayi mata , ya dameta, yaushe rabon ,daya shareta irin haka .datasani tasoma yi gashi angama suna mijinta na fushi daita.
Tayi zugun har Ummi taso ta harbo jirginta .
Dan sai data tmbyrta alahan tunanin wannan mijin naki kike ? zeenat tayi murmushi tare da wauancewa haba dai Ummi,tunani km .
Tap jikina ne kwata na
ke jin yana min nauyi .
Ummi tace ya day kamata kuga likita .
Daren ranar sam takasa runtsawa zeenat tayi abin mamaki gabadaya ,kewar mijinta ce ta addabi ruhi da gangar jikinta .
ta dinga jin alamun hannushi yana yawo aka dukiyar fulaninta , hatta kashim turarensa tana jinshi tsam ajikinta .
,takoina ta juya ,mijinta take Gani ,idan ta runtse idanunta km shi take Gani yana make love daita .
A zubara ta Mike zaune ,tana kankame da jikinta .
tamkar may jin rawar sanyi.
Ummi data ji motsenta yaki karewa ,ta dan juya tana dubanta tare da cewa tace lfyrki kuwa .
,a sanyaye zeenat Yace lfy lau Ummi ? Ummi tace to me ya hanaki bacci?
Tace mafarki nayi ummi ,.
Ummi ta tabe baki to kiyi addu'a ki komai.
tace to tayi addu'ar kmr yadda Ummi tace ahalin ita tasan ba wani marfarki tayi ba.
,tsabar jarabar DEENI ya saba mata daita kedamunta .
haka ta koma ta kwanta ta dinga juyi da mutsmutsun , Amman bacci sam ya gagara daukarta har asuba bata samu ta runsa ba.
km bata daina jin hannushi na kai kawo. jikinta ba .
,
[5/7, 4:05 PM] +234 818 621 2985: 💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗
AYSHA A BAGUDO
Page 41
Da kyar zeenat tasamu ta tashi tayi sallah takoma ta kwanta cike da kewar mijinta.
ta kudindine jikinta cikin bargo sakamakon sanyi sanyi data keji .
kamkame jikinta tayi waje daya,tana jin dama sukasance tare ,wani irin feeling dinsa take jin yana tasoma mata.
' har wani rawa rawa jikinta yake .
Ummi dake zaune akan pray mat tana lazimi tana hankalce da duk wani motsinta Amman tashareta .
Fargaba cike tsoro suka cika zuciyar zeenat.
kardai fushi Yaya deeni yayi daita ,wanda yasa yakasa zuwa gareta .
dako duniya tayi mata warbar kunu.
kwanki biyu din dabasa tare jinsu tamkar shekara biyu ne .
hawaye masu dumi taji suna silalo mata a kuncinta tasa tafin hannuta tana dauke su ahankali.
tana jin zafi da radadin abinda Ummi tayi mashi dan tasan , haushin haka yasa ya hanashi zuwa gidan gabadaya .
Ahankali Ummi ta Mike tana nade abin sallarta byn tayi addu'a.
Ahankali takaraso inda zeenat din ke kwance lomo tamkar may baccin gaske.
, ta zuba mata ido kawai duk cikin bargo take hakan bai hanawa ummi na nazarinta ba .
Ta dan dade tsaye akanta kafin daga baya takira sunanta Cikin sanyi murya mamana 2 shr ....... Kina jina fa dan nasan idonki biyu .
Say lokacin zeenat ta yaye bargon da dake luluba ajikinta tasoma murmurza idannuta tamkar wace ta dade tana sharar bacci .
Make damunki mamana ko gidanki kike da bukatar komawa inji Ummi?
,da sauri zeenat ta girgizawa ummi kanta .alamun A'a
Tace To naga duk kinki sakin jikinki kinyi wani laushi dake ko wani abu ke damunki na lura jiya bawani bacci kikayi ba?
da kyar zeenat din ta Mike zaune tare da bude bakinta tace bbu komai, to mezaki ci yanzu ? Ummi ta sake tmbyrta .
muryata a sanyaye tare da yatsuna fuskarta tace komai mayye .
ta fadi hakan ne darasa abinda kema dadi .....
Ummi ta juya ta fice daga dakin , tabar zeenat da juyayin rashin jin duriyar mijinta .
Some minti back
Ummi ta dawo dakin hannuta rike plate da jug ta jawo karami stood dake gefen gado ta daura plate din indomi data dafo mata akai .
,sannan tace ki tashi ga indomi nan na dafa miki .
, zeenat ta sake komawa ta kwanta ta Mike ahankali ta ziro kafafuwanta kasa.
kmr kar Ummi ta ambaci sunan indomi .
shikennan taji kirjinta ya rike gam ,aiko ummi na bude plate din take taji kanta yasoma jujjuyawa zuciyarta ta ausine a guje tayi hanyar bathroom din dake dakin Ummi ta dinga kwara amai ba kaukautawa .
Da sauri Ummi takaraso gareta tana yima mata sannu , sai kakarin amai take amman bbu abinda yacigaba da fitowa sbd rashin abincin da bbu acikinta.
ta galabaita matuka gurin yin Aman .
Ummi ta dinga ji tsautsayi na ratsata tana girgiza hakan ya dinga tunowa ummi da yar,uwarta farida .
hakika laulayin farida kika dauko zeenat , Allah ya day inganta ya bada masu albarka .
ummi na tsaye har say dataga tadaina yunkurin amai sannan tashiga cikin bathroom din sosai ta dibo ruwa ta wanke mata baki da fuskarta sannan tace tayi wanka .
Koda tafito ma kwanciya ta sake koma .wunin ranar xurrrrrr akwance zeenat tayi shi .
Amman duk da wannan halin datake ciki hakan bai sa ta daina jin mijinta agangar ajikinta .
Jin shr shr ba deeni ba kiransa a waya yasa hankalin Ummi tashi danhaka ta yanke shawarar ta name shi a waya .
Byn ya dauki waya ,tun kafin yace wani abu Ummi ta rufeshi da fada rashin zuwansa ta inda take shiga bata nan take fita ba .
, tace ga matakar nan kwance bbu lfy amman dan tsabar wulakanci yau kwananka biyu rabonka da gidan nan .
Shr yayi sai daya bari umminsa ta sauka. sannan yasoma bata hakuri.
Dan girman Allah first lov kiyi hakuri wlh nima yarinyar nan tana cikin raina wasu abubuwa ne suka sha kaina shiyasa kwata-kwata baki ganni Amman inshallahu da zarar na dawo aiki zanzo . Karma kazoTayi hanging din wayar .
Misalin karfe takwas na dare daidai deeni yashigo gidan .
sanye yake cikin wasu hadaddun kanan kaya blueblack din wandon jeans da black top anyi rubutu white MM sport a gaba da baya rigar.
, kamshi turaren Hamilton ke tashi ajikinsa , ahankali cikin wata irin murya may ciki da kwarjini da haiba yayi sallama tare da murda handle din kofar umminsa ya sanyo kanshi cikin dakin ido suka hada da umminsa ya sakar mata murmushi.
ita km ta watsa masa hararar wasa . Kamshi turarensa ya sake baibaiye dakin ummi .
tun bai kai ga karasa shigowa ba.
Ita kanta zeenat lefe tamkar bacci gaske . Batashirya kallon kofar ba amman kamshin turaremsa ya hankaltar da ita mamallakin zuciyarta ne yaiso.
Dan haka ahankali ta ta da saci kallonsa sannan ta maida idanunta ta runtse tsabar murna may gwaraye farinciki dan