Chapter 39 Reading AUREN SIRRI Book 2 Complete by Aisha Bagudu.txt Arewa Novels

AUREN SIRRI Book 2 Complete by Aisha Bagudu.txt

Author :  Aisha Bagudu Category :  Old Hausa Novels

Chapter   39 / 123

114K to 117K   out of 366.6K words

lov sannan yace mun tashi lafiya .

,tana murmushi tace lafiya lau dana , yakata shi kaima ?

,ya shagwabe fuska kmr wani karamin yaro yace lafiya Amman ba lau ba .

Ummi ta zaro idanu tunaninta ko wani abu ne yana shi yin bacci .
,meyasa Meka ya kai dana ummi ta fadi hakan tana mai nazarinsa " Ahankali ya shagwabe fuska byn tunaninki ne ya saka gaba ya hanani yin bacci ummi ta sake zaro idanu tare da sakin murmushi irin na manya.

Aiko " tunanina bai kyauta min ba wlh .
" Har daya hanawa tilon dana samun natsuwa"

Deeni yasake narke fuska yana duban umminsa , Allah first lov ki nemo shi tunanin ki hukunta shi da kanki .

ta sake yin murmushi kusan koda yaushe agaban mahaifiyasa haka yake zama tamkar wani jinjiri , ummi numfasa sannanAuntyna tace maza tashi kaje nasan yanzu haka ko breakfast bakiyi ba kike shirin fita ?

A sukwane ya Mike tsaye yana duban ummi .
"mkr kinsani wlh amman daga wajen yin break zan wuce office , ganin yana tsaye bashi da alamun tafiya ne yasa tasan abinda yake Jira ,dan haka tashiga yimasa addu'a tare da sake nuna masa mahimmanci Zeenat a gurinsa .
sannan ya fice daga dakin hade yi mata sallama ..


Koda ya bar part din first lov part din zeenat yashiga kwance ya tadda ita Tayi zurfi cikin duniyar tunani sannan idanunta na kallon celling dakin da dukkannin alamun ma bata samu runtsawa ba .


'Ahankali Yasa hannunshi ya ja yatsun kafarta dashi ' a sanyaye ta kallosa da idanunta tana may sauke naunauyen ajiye zuciya sannan ta zuba masa kwayar idanunta cikin nasa hk shima yake kallon tare da dan matsowa kusa da ita sosai yana son sake karantar yanayin da take ciki .

haka kawai wani lokacin yake tsintar kanshi da tausayawa mata ,sbd yadda take maseefar sonshi da kishinsa.

daidai kunneta yakai bakinsa, kana yayi kasa kasa da muryarsa yace meke damunki haka Zeenat .......? 'Ahankali ta girgiza masa kanta ,alamun bbu komai, ya furzar da iska mai zafi daga bakinsa .
saannan yace ok..to meyya hanaki bacci?

Ahankali ta juyo ta zuba masa kananun idanunta tana kallonsa dasu sosai take jin yadda kaunarsa ke sake taso mata tamkar zata huda mata zuciya , tare da mamaye mata dukkan sansanr jiki .
Sai data kalleshi son ranta sannan ta sauke numfashi 'ahankali muryata a shagwaba tace kai ne da tunaninka ya hanani runtsawa.

ya runtse Idanunshi sannan Ya bude su Dan sake dubanta suka hada Ido dashi ta lumshe masa idanunta tana sake tabbatar masa da iya gskyrta ta fada .

yes .... tunaninka ke damuwana yayinda kewarka ke hanani ke hanani sukuni ballanantana na samu sararin ishashen bacci .

, ajiye zuciya ya sauke tare da zama gefen bed side dinta ,yakamo tafin hannuta cikinsa yana murzawa ahankali 'ahankali .
tsareta yayi da rikitattun idanunshi yana kallon cikin kwayar idanunta .
' itama shi take kallo still take ta dinga jin wani iri iri ajikinta . gabadaya tsigar jikinta suka Mike tsaye yrrrrrrrrrrrrr......

Bazato ba tsammani taji sautin muryarsa meyasa kike son halaka kanki da tunani na Zeenat ?

cike da damuwa yake magana , alhalin duk maseefar da tasameki kece silar jefa kanki ciki.

kau da kanta tayi gefe window ta zubawa wajen idanu kuri batare da tasan abinda yakama tace ba .
" ganin da yayi hawaye ne keson zubo mata , yasa hannusa Yana juyo da fuskarta garesa suna sake fuskarta juna.

yace karki soma barin hawayen nan su zubo daga idanunki sbd bana bukatar ganinsu km basu na tmyeki ba .
D karfin tsiya ta ciza lip's dinta tasoma kokarin mai da kukanta.

inason kin manta komai dangane da abinda ya faru baya kicanza new life banason ganinki cikin wannan moon din "ko kinason first lov ta fuskanci wani abu na damunki byn damuwar rashin haihuwa da tasan itace matsalar mu , ta girgiza kai yace kiyi fatan samun wasu ya'ya masu albarka .
maganar dayayi mata kadai Ya taba tsantsar jikinta tare kwantar mata da hankali.
Hannuwata dake cikin nashi tasa ta matse tafin hannushi cikin tare da danne hawayenta , muryata a sarke tace Ina sonka dayawa my heart..... ,meyasa kaima bazaka soni tamkar yadda nake maka ba Ina son kasancewa tare da kai bana son yin nisa daika .

Uhmmmm Zeenat kennan Ina sonki man abinda kika aikata gareni ne yasa soyayyarki takasa yin tasiri a zuciyarta sannan kece kika hana wannan soyayya samu gurbi may mahimmanci,Amman dai... Sai km yayi shr tare da mikar da ita tsaye ya mannata da gafen jikinsa yana shafa bayanta 'ahankali , .
dan yasan duk randa basu kwana tare ba "bata samun ishashin bacci ga tarin tunanin rashin haihuwa da take kwana yi wanda duk ita tajefa kanta cikin .


Ahankali Ya juyo daita suna facing juna tare dadago habarta ya zubawa fuskarta eyes dinshi sannan ya kai bakinsa kan nata ya tsotsan lip's dinta yace I still care about you.

murmushin tasakar masa Wanda ta jima batayi irinsa ba ,cikin jin dadi ta kamo tafin hannushi muje kayi breakfast .

am orready late Zeenat anajirana a office nebazan iya tsayawa cikin komai ba . uhmmmm nidai please muje kaban ko 5 minutes na hada maka ko tea ne kaji.
ya karyar da kai kawai yana dubanta , atare suka jiro hannunsu sarkafe da juna har darning wanda daman komai a kammale yake ta zaunar da shi cikin sauri sauri ta hada mishi tea kurba uku yayi ya Mike tsaye , tasan yanzu tana sake yin wani complain .
sunanta sorry a gurinsa Dan wannan kulawar dataga daga gareshi tasan darajar addu'ar data kwana tana yi ne da km ummi dake tsaye a tsakaninsu har Bakin kofar main falon din su takai shi ta Mika masa briefcase dinsa Dan bayarda da hakan sannan ta koma dakinta ...

Direban sa wanda shima soldier ne yataso da sauri yakarbi briefcase din hannunsa hade da Sara masa sannan ya bude masa murfin kofar.
,tun kafin karosowarsa Bakin get din gidan securities ke Sara masa har aka bude get suka bar gidan ..

Tunda ta tashi tayi sallar asuba take kwance takasa fita ko nan dacan tana jiran kira daga masu gidan Amman shr ga yuwa tasoma kmr me .
Mikewa tayi jiki a sabule tashiga bayi wanka tazo ta canza kaya tare da zubawa sarautar Allah Ido can taji ana nouking dakin ahankali ta Mike ta bude kofar ummi tagani tsaye ta dan matsa taba hanya tashigo dakin sannan ta gasheta cikin sakin fuska ummi ta amsa tace nablah ya kwanan bakunta ?

Ta Dan yi murmushi tare da cewa alhmd ummi tace Masha Allah yanzu dai muje kiyi breakfast daga nan sai mamana ta nuna miki aikin da zaki rinkayi ummi nagama fadar haka ta juya itama nablah tabi bayanta ...

Falo uku sama uku kasa uku banda dakuna wanda sunkusan goma acikin gidan , madam kmr yadda taji laraba nakiranta da shi ita ke nuna mata komai.

A yatsine tace ki dauki gyaran sama kibarwa laraba kasa nablah tace mata to dan batada zabi sai abinda tace ..
har falon magidan da dakin sa komai dai ataikaice sai da aka nunamata Kuma tun a rana tasoma aikita hade da tattaro kayanta tadawo sama kmr yadda ummi tabata umarni .

Misalin karfe takwas dai dai na dare nablah ta kammala da komai na aikin gidan har part din abinci wanda tare da madam muzeenat sukayi komai wai tana son ta kware fannin abinci mai gida dan haka gabadaya agajiye take likis.

Tana shiga dakinta kwanciya tayi bata dade ba bacci yayi gaba daita.



MMN SUDAIS CE
[7/12, 7:07 AM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗




AYSHA A BAGUDO


Page 62



" kyakkyawar yarinyar ce dai ta sake zuwan masa. deeni kuwa dake kwance warwars akan makeken royal bed dinshi ya zuba mata Idanunshi kawai , tundaga kan kwantaccen sumar gashinta kanta yake binta da wani irin mayataccen kallo mai cike da tsantsar sha,awa yayinda zuciyarsa ke wani irin harbawa da sauri da sauri ..ganin yarinyar ta miko masa zara zaran yatsun hannuta masu matukar kyau da daukar hankali ne yasa shi azamar fizgota jikinsa batare da wani bata lokaci ba ya rungumeta tsam tsam ajikinsa tare da cusa kanshi cikin sumar kanta yana shakar dadeden kamshin jikinta "take yarinyar itama ta narke masa ajiki tana taba wasu part na jikinsa cikin wani irin salo a haukace tamkar wani zaki DEENI yasoma romancing din every part of her "cikin zafi zafi ya hade bakinsu waje daya yasoma tsotsa tare da lumshe rikitattun idanu.. ........ sosai yake juya yarinyar yadda ya so batare da wani abu yamasa shamaki ba.
daidai komai yagama faruwa atsakaninsu ne ya farka afrigice zaune kmr jiya yana sauke numfashi sama sama..
tare da karanto addu'ar da duk tazo bakinsa na neman tsari daga sharin shedan ,ganinsa mafarkinsa nasaba da sharin shedan dan gabadaya yarasa dalilin dayasa yatsinci kanshi cikin irin wannan yanayin mai cike daban tsoro da alajabi .. hakika shi bazai ce Ga abinda ke damunsa acikin yan kwanakin nan dayasa yake tsintar kanshi cikin irin wannan birkitaccen yanayin ba .

Tsawon lokaci ya dauka yana zaune Yayi shr kawai yana tunani.
" yayi yayi ya gane abinda ke damun rayuwarsa Amman Sam yakasa domin duk ta inda ya duba bai gano takamaiman abinda yasa yake irin wannan mafarkin ba ..... 'ahankali yasa hannushi yajanwo hanky agefen bed dinsa ya goge gumin daya rufeshi . dan duk da AC dake aiki acikin dakin bai hana Gumi tsatsafo masa ta koina ajikinsa ba .. .. sannu ahankali yakai idanunshi kan agogon bangon dake manne a dakin.
karfe biyu yagani daidai ajiyar zuciya ya sauke tare da koma yayi kwanta lamo.... yana juyi kawai batare yasan abin yi ba dan kwata kwata idanunshi ya kyan kyashe bbu alamun bacci acikinsu tunani kawai yake yana juyi. ...


Washegari

da safe byn ta idar sallar asuba bata koma bacci ba saboda tasan yanayinta domin tana komawa bacci me nauyi ne zai dauke ta.
" kowa Kuma yasan yadda baccin safe yake dan haka kishigida kawai Tayi kan pray mate .



karfe bakwai daidai ta fito daga dakin da'aka sauke ciki. shr koina babu motsen kowa ballanantana mutun ya saka ran ko akwai wani bil,adama acikin gidan kasancewar week end ce.


tafiya take 'ahankali cikin tsanyi jiki , har ta iso part din ummi takutsa kai ta shiga da sallmarta ...

nan ma shr ba motsin kowa ciki "can taji " alamun motsen ruwa a bathroom dan Haka tabbatar da ummi tana.

" bata wani tsaya batawa kanta lokaci ba ta soma yin abinda yakaita, daidai nablah tagama gyara koina ummi tafito daga bathroom..

tana ganin nablah ta saki fuskarta sosai tare da yin murmushi . nablah ta gaishe da ummi cike da girmamawa .

Ummi ta amsa tana mai Bin nablah din da wani irin kallo mai hade da mutuntaka .

Jikinta nablah a sanyaye takarasa toilet din ummi tawanke koina tasss ... sai da tabbatar data gyara duk inda aka nunamata tasss ..

Amman banda part din mai gida Dan so take sai ta gama da koina acikin gidan sannan tashiga part dinsa saboda tsaro ..

Tsaye take a bakin kofar da zata shigar daita cikin part din mai gida.. hannuta rike da handle din kofar .
"takasa murdawa tashiga a dalilin zuciyarta da tasoma wani irin harbawa da sauri .
ta dinga jin wani irin ajikinta wani irin yanayi ne na daban ta tsinci kanta ciki .
,yayinda wani part na zuciyarta ke bata umarni tashiga kawai batare da wani tsoro ko fargaban ba , a tunaninta may be ma yafita ,duk dai tasan week end ce bai zama lallai yazanmato yana ciki ba.
Amman kwata kwata fargaba datake ciki ta hanata yunkurin kusawa cikin dakin ..
,sai da ta runtse idanunta tare da tattaro jaruntar ta sanyawa gangar jikinta , sannan ta iya murda handle din a natse tashiga dakin ,da idanun take bin dakin da kallo Sha,awa.
koina tsab tsab tamkar an gyara bbu wata alamun da zai nuna mutun na rayuwa a cikin dakin , ahankali ta kamo gefen lip's din bakinta ta Dan ciza kadan kana ta soma abinda ya kaita .

Daki daya ya rage a cikin part din da bata gyara ba Dan haka ta kutsa ciki ta soma da wanke toilet ta zo kan royar bed dinshi, ahankali tasa hannuta kan blanket din dake rufe da gado da niyyar cirewa ta nike Dan kwata kwata batayi tunanin zata samu bil ,adama kwance cikinsa ba" a tsorace Tayi sauri sakin blanket din
' tana zare idanu waje tare da furta wayyo Allah nah a kasan ranta , take jikinta ya dauki kirma ta gigice tama rasa hanyar fita dan neman tsira daga cikin dakin.

tsabar rikecewa batasan sanda ta kama handle din kofar bathroom ba ta afka ciki ... Ai ko tana ganin ba kofar fita bace ta sake juyo da sauri ,bbu inda baya rawa ajikinta tare da tattara kayan moupystick dinta tabar dakin da saurin bala'i tana haki sama sama tare da fidda numfashi .

A can bakin corridor din dake tsakanin part din deeni da ummi taja ta tsaya ta sake fidda numfashi tare da addu'ar Allah yasota.. ..

shi kuwa deeni dake kwance ya sake lumshe rikitattun idanunshi kawai dan tun shigowarta dakin idanunshi ke bude ganin itace yasa shi sake lafewa jikin pillow , dan shi ko yaya akayi motse zai farka.
yadda yaga ta gigice ne ya fi tsaya masa arai .
Dan Haka a tsanake ya tmbyi kansa to me hakan yake nufi da wannan gigicewar dayaga tayi ?

tabe bakinsa yayi tare da jan tsaki sannan yacigaba da baccinsa .

Sai kusan azahar sannan yatashi ,yashiga bathroom yayi wanka hade da alwala yana fitowa ya goge jikinsa ya shafa lotion ya zira jallabiya long sleeve tare da fashe ilahirin jikinsa da turaruka masu mugun kamshi da daukar hankali....
ahankali yake saukowa daga step hannushi rike da gefen jallabiyarsa har ya iso babban falon gidan inda ya tarar da duk ahalin gidan zaune .

ya gaida ummi yayinda zeenat ta gaidashi .

nablah da tun
saukowarsa taji tana kiciniya da numfashinta dake namen barin gangar jikinta ta gaisheshi muryarta aciki.

Yana jinta Yayi banza daita tamkar bai jita ba Sai ma hankalinsa daya dauka kacokan yamayar kan ummi dake kallo, muryarsa a dake yace first lov ni zani masallaci ta juyo tana dubansa tare da ce wa To sai kadawo yarona , sa kai ya fice .

takasan idannu take kallon every step of him dab ..dab... kmr wani jinin sarauta yayinda duk takunsa daya ke daidai da bugun zuciyarta har ya bace wa ganinta idanunta nakansa km Sai lokacin tasamu natsuwar zuciyarta, dan gabadaya ilahirin jikinta bbu inda bayi sake ba .

Muryata Ummi ce tasa ta sake dawowa cikin natsuwarta . nablah ki dawo kan kujera man ki zauna kin wani je can kin rakube akasa... maza taso kidawo nan kusa dani kinji "ki saki jikinki damu nan ma tamkar gida ne , a sanyaye nablah ta Mike tayi kmr yadda ummi ta umarceta .

Ummi tacigaba da magana . kishirya zuwa anjima akwai doctor da zata zo ta miki test kinji nablah cikin sanyin muryarta tace to.....

Ummi tasa hannu ta dauki remut tana canza channel zuwa zeeword .

, zeenat ta dan juyo a wulakance tana kallon inda nablah ke zaune tare da watsa mata wata uwar harara .. bakinta ta tabe kawai cigaba da aikawa nablah da harara iri batare da tabari ummi taganta ba ita dai haka kawai take jin tsanar yarinyar har cikin ranta .

39 / 123