Author : KARIMA TIJJANI MANSUR Category : Romantic Hausa Novels
zaki fad'amin ba"..
Jikinta ya hau rawa, wallahi babu ko ina..
K'arya zaki min, zan tattaka ki anan wajen, ki bud'e baki ki min magana, shashashar banza"..
Ya fad'a yana shirin mik'ewa ya d'akko bulala.
Cikin hawaye ta fara magana, Don Allah Abba, kayi hak'uri wallahi, bansan fita zamuyi ba, shine ya ja motar,..
Ina kika je na tambayeki,"
"Park". Me kikayi acan?? Wallahi babu komai,"
Wato saboda baki da kamun kai koh, ? To yayi miki kyau, ban tab'a yi miki dukan da kika suma, bane shiyasa. Ya nuna ta da yatsa, wallahi wallahi Hafsah ki shiga hankalinki akan abubuwan da kika k'irk'irowa kanki, idan ba haka ba, zakiyi mamakin abinda zanyi miki, shashasha kawai." kuma daga yau kada na k'ara ganin kinfita ko da k'ofar gidane, ko makaranta ma kin daina zuwa!!"
Ta d'ago a razane ta kalli, abban, wanda uwar hararar daya galla mata, yasa tayi saurin mayar da kanta k'asa.
"Innalillahi, shikenan ta, kad'e ta jawo wa kanta, Abba ya hanata zuwa school, babu batun, karatunta kenan? saura fa sati d'aya su fara 'WAEC' , yanzu ya zatayi kenan, babu zancen fita? Wane irin k'unci zata shiga.??
'Zufa ta wanke mata fuska, babu shakka zata iya cewa k'addara ce tasa Yusuf, ya fita da ita, banda haka, me sukaje yi wannan waje?.. Su basu sai komai ba, hasalima, a gurin Yusuf, baiyi yunk'urin tab'a ta ba, bare tace alhakin hakan ne' Kawai Tsautsayi dai.!!
"Tayi shiru, tana nazarin rayuwar da zatayi babu fita.
Wallahi idan baki sauya tunani ba, zaki matuk'ar shan wahala a wajena."
Tashi ki fitarmin "ana!
Kalaman Abba, kenan da suka katse tunaninta.
"Cikin kuka tace Don Allah kayi hak'uri wallahi bazan.."
Ya kuma daka mata wata uwar tsawar "Fita nace",
Ta mik'e jiki babu kuzari ta fita.
Tana fita parlour, mama ta ga yanayinta, sai ta mik'e sai d'akin Abban,..
Ta nemi kujera ta zauna.. Fuskarta fal da takaici.
Abba ya karanceta tsaf, kafin tayi magana ya riga ta.
"Amina kin bani, mamaki, wato bazatayi laifi a hukuntata ba koh,.. kin fiso abarta tayi tayin abinda taga dama babu kwab'a.. Bakya fargabar abinda zai je ya zo Kennan."
"Ni ba cewa nayi kada a hukuntata ba, amma ai dukan da kayi mata yayi yawa, macece fa"
Abba yai murmushi mai sauti, kina nufin kin fini sonta ne, ko kuma me?
Tayi shiru azuciyarta tace "Ai hakanne" _lol_
'Jin tayi shiru ya cigaba da magana cikin son fahimtar da ita, don ya fahimci itama cikin fushin take, ba zata tab'a fahimtarshi ba idan shima ya nuna mata fushinshi.'
"Amina, kullum fata na shine in sauk'e nauyin hak'k'inku dake kaina, Hafsah fa 'yata ce, bazan yi abinda zai cutar da ita ba, komai ina yin shi ne don ta sami kyakykyawar tarbiyya, ina roko'nki idan bazaki tayani ba, to ki daina adawa da duk hukuncin danayi mata."..
Ta d'ago da niyyar tayi magana amma ya hana ta, ta hanyar daga Mata hannu"
"Dakata, wallahi kema na tabbatar jiya bakiyi baccin kirkiba, saboda tunanin meyafitar da ita, ita da wani?.. Ki bar yi mata shaidar tana da hankali ko kamun kai, ni bana zarginta da komai amma, wallahi _ba,a shaidar yaran yanzu..._ kuma kema nasan daga yanzu hankalinki bazai k'ara kwanciya ba matuk'ar tafita daga cikin gidannan har sai ta dawo."
Mama tayi shiru tabbas kalamashi gaskiya ne'.
Kuma sunyi nasarar sauke fushinta akanshi, don haka ta shiga bashi hak'uri,
"Kayi hak'uri to, na fahimceka, insha Allah bazaka k'ara jin bakina, akan lamarinta ba"
Ya girgiza mata kai, "A,a ai 'yarki ce, kema kina da hak'k'i akanta,.. kiyi ha'kuri kema, ki dinga yi mata addu,a kawai."
Ta d'aga mishi kai, "To in sha Allah",.. Ni dama kawai dukan da ka mata ne, ya tsoratani kuma kasan fa duka baya gyara"
Yayi murmushi harda jijjiga k'afa "Nasani"
Cikin nutsuwa ya kuma ce mata,
"Na hanata fita, koda zuwa makaranta ne, don haka kisa mata ido, sosai.
"Tom, shikenan"
Bata da musu akan matakin daya d'auka..
Kuma ta fahimceshi sosai, saboda haka ta bar wannan zancen, ya miqe zan fita wajen daurin aure Adawo lpia Allah y tsare,
ta miqe don rakiyar shi. Kmr ban ita ke fushi da shi ba..
Hafsah ta, dawo rayuwa kamar mujiya acikin gidan, kullum tana d'akinta, babu dai wanda yake k'yararta acikin gidan amma duk ta tsargi kanta, kuma babu wanda ya damu, da hakan.
Akan idonta su bashir suke shiryawa su tafi makaranta itako ko oho, sai bashir dake Cemata "Yaya 'yan ajinku suna ta tambayata nace musu baki da lafiya ne.
'Hakan shi yafi damunta, gashi tun ranar nan, Abba, yayi watsi da ita gaisuwar ta kawai yake amsawa. Gefe kuma kewar Yusuf da tunaninshi sun addabeta, hakan yasa tayin wata 'yar rama, tayi bak'i.'
Haka har sati ya zagayo ranar lahdi, kuma washe gari zasu fara exam, kuma Abba yasan da hakan, Amma, har ya dawo babu wata magana daya yi mata...
*Kuyi haquri da wannan*ππΌππΌ
*Hajiyar ku ce*ππ»
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): β₯β₯β₯β₯
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
ππ
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique In Your Love Heart Members.*
π *25*
*Sai* da safen mama tashigo tace mata, 'ta shirya zuwa makaranta. K'arfe 9:00am ne, exam d'in, don haka, da 'Nura' yazo, Abba cewa yayi ya kaisu bashir, ita idan lokacin yayi ya dawo ya kaita.
'Tunda ta jita a mota taji wani farinciki ya ziyarceta, tana son tajita cikin k'awayenta, sannan tana son ganin Basma.'
Sanda taje ana daf da shiga, saboda haka bata sami ganin Basma, ba. Kuma cikin rashin sa,a ajin da suke exam daban ne.
Suna fitowa daga 'Papper', Aysha D'ahir ta nufo ta.
Suka cafe hannu.
"H Hamid ya jiki..? Wallahi har kin rame!"
"Hafsah dai tace Da sauk'i kawai"
Ke wallahi mutuminki ya dameni, kullum sai yacemin in had'aku
a waya idan nazo school,..So na fad'a mishi baki da lafiya, ne but ya damu fa sosai"
Hafsah taji dad'in hakan har da lumshe ido,
"Oh Allah sarki My Yusuf, nima nayi missing nashi wallahi"..
"Please ki had'amu"
"Am sorry to say "Na baro wayar a gida because naga exam za,a fara, kada ayimin seizing, but don't worry in sha Allah tomorrow zan Had'aku".
Hafsah ta rungume ta "Thank you my friend!!"
Muryar Nura (Drivern su) taji, yana cewa, "Hafsah, kiyi sauri don Allah"
Ta rik'e hannun Aysha, "See you tomorrow bye"
sai taji zuciyarta ta d'an k'untata 'Ashefa yanzu ba da bane'.. (Wato abba ya bawa Nura umarnin idan tana da paper biyu, matuk'ar bazata wuce awa 4 biyar a exam ba, Nura ya jira ta tagama sanan ya dak'k'ota, wannan doka ce akanta, idan kuma ta haura lokacin gama exam yace mishi laifinshi ne'
'Haka tanaji, ta shiga mota bata sami ganin Basma, ba.'
Wasa-wasa har sunyi rabin exam d'in, amma bata sami had'uwa da Basma, sun zauna ba. Suna had'uwa a duk lokacin da ta zo su gaisa. Watarana suna d'an fara hira, ake shiga 'Exam'..
Sanan hirace irin ta group, bata samun keb'ewa da Basman, kuma mafi yawanci tana riga su basma fitowa, kuma, da Nura ya k'yalla ido, ya ganta zai ce suyi gida..'
Haka Aysha ta bata hak'urin, rashin had'ata da Yusuf, saboda ta daina zuwa da waya. Agabanta, aka k'wace ta wata... Hafsa amma kiyi ha'kuri in sha Allah gobe ki shigo da wuri zan had'aku."
Haka kuwa, akayi dama exam d'in ta karfe tara ce, kuma Abba ma yana da copy na timetable d'in, tun daga dare take shirya irin k'aryar da zatayi, abarta yau ta bi su bashir'.
Taje ta sami Abba, afalo. Saboda ita yanzu da wuya ki ganta a falo, ko yasa yaushe tana 'Bed room'.
"Abba"
"Na,am,
Ta d'an yi shiru..
"Ya akayi".
Inji Abban'
"Um, dama ance gobe mu shiga da wuri saboda, jibi, zamuyi 'Catering' ne, to wai akwai abinda malamar zata koya mana.
Ta k'arashe maganar tana kallon Abban don taga ya k'aryar tata ta karbu'?..
Abba ya kalleta sosai, ya nazarci yanayinta, sannan yace ,
"To ki shirya ku tafi da su bashir".
Tayi murmushi "Nagode, Abbah"
Har takai bakin k'ofar d'akinta yace mata,
"ki dinga yin addu,ar neman nasarar Exam d'in dai."
"To Abba"
'Ta shige d'aki'
'Cike take da farinciki, da tunanin gobe ya zata kasance da Yusuf, d'inta a waya.' Hakan ya bata damar yin ishashshen bacci mai cike da ni'imar mafarkin Yusuf, d'inta a cikinsa.'
Washe garin ranar, ta zame mata mai sa,a, wato Basma, tazo sannan ga Hafsah, cikin zumud'i ta nufi Basma ta rungume ta. "Basma Yunus!!
Basma ta d'anyi murmushi H Hamid kin b'uya,"
Wallahi, bari naje wajen Aysha Taheer, na dawo.
"Ok, Basma ta fad'a tana bin bayanta da rakiyar wani kallo'..
*"Kuyi Hak'uri please wallahi bacci nke ji"*
*Hajeeyah Kareemerh*
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): β₯β₯β₯β₯
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
ππ
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to: Unique In Love Heart Members*
π *26*
*Tana* isa wajen Aysha suka tafa, taja hannun Aysha sukayi cikin class. Baifi mutum uku suka gani ciki ba, kasancewar, yawanci basu zo ba.
'Suka nemi wuri can baya suka zauna.
Aysha ta na danna waya take cewa,
"H. Hamid, wallahi guy enki na sonki fa, ya damu yaji muryarki, you're lucky wallahi"
'Suka tafa.'
Ta mik'a wa Hafsah wayar, "yawwa ya d'aga"
'Hafsah ta mik'e ta koma wani desk en.
'Hello'
"I miss you my baby!..
'Da kalmar daya tareta kennan.
Hafsah, taji ta cikin wata duniya mai cike da farinciki.
"Me too dear nah!"
"Baki nemana ai hafsah"
Taji dad'in kiran sunan nata da yayi har cikin zuciyarta.
Ta jingina jikin 'abin jingina' dake jikin desk d'in, babu abinda take sai murmushi.
"Am sorry dear, it's not my fault wallahi, Abbanmu ne ya hanani"..
"Hmm"
Tacigaba,
Please ka daure ka zo wajen Abba, shine zai bamu damar kasancewa tare, please I beg you" 'Ta k'arashe maganar cikin murya mai rauni.'
"Hum" Yai ajiyar zuciya. "Okey" in sha Allah but ki bari kiyi candy koh, since 10days, remained.
"OK thank youu, dear'
"Hmm, dear friend enki asked me to attend her birthday nd graduation party,..and she asked me to come with you"..
"Hum, Hafsah tayi ajiyar zuciya.' Lokaci d'aya taji ba'kin ciki da kishi sun rufe ta, wai wanne irin rainin hankali basma ke mata ne"? "What did she mean?
"Baby, kinyi shiru"
"Hmm, dear please wai mene ya sa kamin haka?
"What do I did?
"Hmm, me yasa kake yin waya da Basma, ban sani ba"?
'Ya kwantar da murya " Am sorry mai baby, I told you I just respect her.. Please zaki je party en koh"
"Noo bazani ba"
'Ta fad'a da fad'a.'
"Hmm, yai murmushi, yayi k'asa da murya "Am sorry, please kije zanzo muje dake, don Allah kinga basma is our friend"..
Ta maimaita cikin murya mai bayyana mamaki'
"Our friends,?' Hmm, let me tell you, basma is no longer my friend ehe"
"Hahh, your friend is my friend so, please calm down stop feeling jealousy, she's just a friend"
'Yayi maganar cikin dariyar da ta d'anso tafiya da ita, 'tana son dariyarshi.'
'Ta d'an share kawai ta binne kishin a k'asan zuciyarta, bata son ta b'arar musu d'an farincikin da suke ciki bayan sun dad'e cikin kewar juna'.
'Cikin shagwabar daya saba, yace, "Baby what about yours ina za,ayi namu party en"
Ta d'an hadi'ye takaicinta, da dane ai Abba abinda zai mata yana da yawa, amma yanzu bata tunanin za,ayi mata wani abu"..
"Kinyi shiru"
Yace da ita,
"Nothing, bana son party"
"Oh my baby, why?.. Mene yasa ke komai baki so?
"Hmm, babu komai, ka share kawai."
Yai ajiyar zuciya "Ok, but I will prepare something special for you"
Tayi saurin cewa thank you, but please ka barshi kawai"
"Baaby,?
"Uhum"
"Kina fushi da nine koh?
"No, ni bana fushi da kai Allah" tayi saurin fad'ar hakan'
"So meyasa kike rejecting abinda nake so"..? "Babu komai wallahi dear", ni bana son party ne "
"Ok, ya wuce'
"Yanzu yaushe zanzo ganinki?
'Tab'.. Ta fad'a a zuciyarta.
Shi ana ga-yak'i yana ga-k'ura'!!π
π
"Hmm, sai bayan kazo kaga Abba."
"Hm okey", yace mata kawai, don ta rufe mishi baki'
"I love you" ya fad'a mata babu tsammani, taji dad'i sosai,
Me too dear"!
"Ok, sai anjima, koh, take care of yourself "
'Sai taji babu dad'i fiye da koyaushe idan suna waya yai mata sallama, da k'yar tace mishi,
"Bye bye,"
'Yai mata kiss, a wayar'
'Ta gaza cire wayar
daga kunnenta, har wata k'walla ce ta cika mata ido, sai yaushe abba zai yarda da Yusuf?
Tayi zumbur ta mik'e da ta tuna aika aikatar da Basma, tayi mata, ta mik'awa Aysha wayar, tare da cewa "Thank you sister," ta fita da sauri, tana huci, kishin Basma ya rufe ta...
'Tana zaune tana cin cake, Hafsah ta zauna gefenta tana d'an huci,
"Am Basma ina son magana dake".
Basma na ganin yanayinta itama ta d'an daure fuska, "Uhum go ahead"
'Ta fad'a batare da ta bawa zancen Hafsan muhimmanci ba.
"Me yasa kike kiran yusuf a waya? Sannan mene zaki wani gayyaceshi partynki"
Basma ta d'an gyara zama, "Am H. Hamid dama shine kike wani huci?"
"So maida wuk'ar" ta fad'a tana kaucewa hafsan hanci. Hafsah ta m
do ke hannunta,
"Kinga ki fad'a min dalili".
'Basma tayi dariya, "Nothing fa I just take him as my brother, so kuma nasan idan na gayyaceki partyn bazaki je ba, shine na fad'amishi, becouse partynma na dare ne"
"Hmm, waye ya ce miki bazani ba, kuma da kika fad'amishi shi zai sani naje,?..kinga please, kada ki k'ara kiranshi, kiyi ma delete contact enshi, Bana son irin haka ni"
Basma ta d'anji ta kaici, amma sai ta share, saboda har yanzu, ba,a zo inda take so azoba."
"Haha H. Hamid' kenan"
"Yanzu dai please kuzo partynnan ke da shi"
"Bazan zo ba" shi tunda kin gayyaceshi sai yazo ai"
"Hmm, H. Hamid, kenan, ai nasan yusuf zai zo"
"Mts, Hafsah taja tsaki sannan ta bar mata gurin.'
Basma tayi murmushi "Hmm yarinya ai dama baso nake ki zo ba yarinya"
'Yau Hafsah cikin nishad'i ta yini a gida, har da taya mama aiki. Mama taji, dad'in hakan har tana mata nasiha'..
"_Hafsah dama babu, wanda ya sauya miki a cikin gidannan amma duk kinbi kin damu kanki kin daina shiga cikin 'yan uwanki,.. ??_ _Mufa iyayenki ne, idan bamu miki fad'a ba wane zai miki, Don Allah ki gyara rayuwarki, ki daina abinda kike yi kinji"._
Ta gyad'a kai, "In sha Allah mama na daina".
"Yauwa, Allah yai miki albarka"
"Amin"
Abba ma yau yaga d'an chanji a tattare da ita, ('Yaga tana walwala'.) ya ji d'adin hakan, yau har hira sukayi da ita..
Dama ba a son ranshi yake d'aure mata fuska ba, kawai dai yana son 'horontata' ne.
'Yanzu har sun gama exam, kuma, ayau ne sukayi papper ta k'arshe yau kuwa yawanci duk sunzo da waya, bayan anfito daga exam akasha hotuna, da ('exchanging numbers,) ana farinciki ana kuma tunanin kewar juna.. _'Rayuwar makaranta kenan'_
'Gobe ne kuma za,ayi graduation party na makaranta, an gayyaci iyayen yara, sannan kuma kowanne dalibi an bashi damar gayyatar mutum uku banda iyayenshi.
Sai kid'e kid'e da raye-raye ake a ajujuwan, uniform yasha zane, da rubuce rubuce, musamman d'an k'aramin farin hijabinsu' ita dai Hafsah batayi ba'
Aysha ta tawo da gudu tana ihu 'Yeee H. Hamid you're lucky gaskiya'.. Ajin yayi shiru ana son jin me zatace,.. 'Aisha ta cigaba da magana'
"She's the first person that received 'A Congrats Text' from her hubby" class ya rud'e, "heyy.. Can wata ma ta d'aga "Am the second'!!!
Suka rud'e da ihu..
Basma tanajin, abinda akace kan Hafsah, ta cije lebenta, azuciyarta tace, "Hmm, yana son yarinyar anya kuwa.. Zanyi nasara?.. Wata zuciyar tace mata "You have everything he needs, and you can give him. So that _u are the winner"!!_
Tayi wani ihu da yasa kowa ya juyo da kallonshi zuwa gareta'
"Heeyy,.. Celebration of new life"!! Ta buga hannunta akan desk wata ma ta d'ora nata, haka sukayi ta tawowa da gudu, suna d'orawa, sannan suka d'aga hannenyen suka watsar... Happy candyy!!
Azatonsu murnar candy Basma takeyi'
'Hafsah ta ja hannun Aysha suka bar cikin hayaniyar nan, suka zauna kan 'baranda'
'Kinga text en fa har uku Aysha ta fad'a tana mik'a mata wayar.
'Ta karb'a cikin zumud'i tafara karantawa'
_'Am very happy to witness this remarkable day, am wishing you happy graduation.._
_Wishing you best result, babynah.._
_"Hmm,.. My dear struggle has now ended,.._
_'Congratulations to myself bcoz, now, I know_ _I will get more Caring from you.. Happy_
_graduation baybee nah'_
'Hafsah tayi murmushi taji d'adin hakan sosai.. Sai ta hau 'typing' reply:
'Thank you my dear'
"You made me feel special.. Much of love to you."
Bata dad'e da turowa ba sai ga text na transfer 2000 credit, ya turo..
Can kuma text ya kuma shigowa, ('For aysha thank you')
Aysha har da tsalle, "Wow Hafsah kimin godiya naji dad'i wallahi..
Hafsah tayi murmushi kawai, tana son ta fad'awa yusuf taron da za,ayi gobe, tana kuma tsoron kada su had'u da Abba, don tasan Yusuf baizai tab'a yin yadda baza,a gane ba.
'Washe garin makaranta ta cik'a sosai, da mutane hall d'in taron yasha decoration, dalibai sunyi kyau cikin rigar graduation mai kalar dark blue da ratsin ja' suna kan kujerun da aka tanadar musu..
'Abba da Mama sun sami damar halarta.. Can idanun Hafsah suka hango mata wani kamar Yusuf, gabanta ya fad'i.. Tsoro da kishi suka had'ar mata. Kada Abba ya ganeshi ta shiga matsala, sai kuma kishin cewa basma ce ta gayyaceshi.. Haka dai tayi shiru cikin fargaba.
'Anyi jawabai masu muhimmanci da kuma nasiha ga d'alibai, daga k'arshe aka fara raba kyautuka, ga d'alibai masu hazak'a.
'Daga ajin maza aka fara, sannan bangaren mata, a B'angaren 'Art class' Hafsah ce ta farko a mata, wacce aka fara bawa kyautar d'aliba mafi hazak'a (Best student), sai monitor ta ajinsu, sai wata d'aliba sai Basma, d'alibai da yawa sun sami kyautukan.'
Ak'alla hafsah ta k'arbi kyautuka guda uku, sunyi hotuna da malamansu sannan aka nemi a fito waje domin iyaye su sami damar yin photona da 'ya'yansu.
' Hafsah tayi saurin zillewa, tayi bayan wasu ajujuwa, tace wa Aysha ta kira mata Yusuf don Allah, saboda ta nuna mata shi tun cikin 'Hall' don hafsah kusa da Aysha ta zauna.
Yana ta waige waige Aysha ta mishi magana "Am kaganta can". Ya biyota sukayi bayan class d'in.'
' Tun daga nesa yake mata murmushi, ita ma haka, yana k'arasowa tace your welcome dear"
Ya akayi kazo yayi murmushi, nasan za,ayi ne fa"
"Thank you alot.. I hope ba basma ce ta gayyaceka ba"
Yai 'yar dariya, no ba ita bane"
"Sure?
"Yes, I swear i just come for your sake.."
"No baby I trust you, basai ma ka rantse ba, thank you"
Ta mik'a mishi gift d'in ya karb'a yana cewa
"Wow how lucky iam,? to have a Gifted and also the school over roller.. As my girlfriend"!..
Tayi 'yar dariya kana tsokanana ko?
Sai ta lura ashe Aysha video take musu, ta nuna ta da yatsa kin ganki koh,"
"Perfect match" inji Aysha, "Yusuf yace thank you"
'Aysha ta musu, photona sosai kuma sunyi kyau, Hafsah, ta tuno ta baro su Abba, gabanta ya fad'i, ta kalleshi