Chapter 26 Reading ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt Arewa Novels

ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt

Author :  KARIMA TIJJANI MANSUR Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   26 / 40

75K to 78K   out of 119.4K words

yanzu ta kama wani layi daban na rayuwar ta, _kowa tasa ta fishsheshi._
bata da wani abin buk'ata daga garesu ( _Yusuf da b
Basma_ ) dukansu...
__________________
"Hello.!!
Hello, Barkanka da yamma
Barka dai
" I hope you're fine naji kwana biyu baka picking call."
Ya d'anyi ajiyar zuciya, wato ita dai bata tab'a watsar dashi, duk da yanzu ta k'arfi da yaji ya canja mata ra,ayi akanshi, amma har yanzu sabon nan nata na kiranshi yana nan har yanzu.
"Hmm, Bahijja kenan, bana jin dad'i ne kwana biyu."
"Subhanallah meya sameka.?
"Ciwon kai nake fama dashi amma naji sauk'i sosai ma."
Ta d'anyi ajiyar zuciya ahankali,
"Allah ya k'ara lafiya sannu fa."
"Yawwa thank you."
Suka d'anyi shiru, can tace, "ko inzo dubiya ne."?
"No naji sauki fa nagode ba sai kin zo ba."
"Hmm, kai dai kawai baka son nazo ne."
"No ba haka bane."
"Hmm, tayi murmushi kawai."
"Okey shikenan Allah ya k'ara sauk'i."
"Amiin k'anwata."
Ita abin ma dariya ya bata duk da gefe guda tana tausayawa kanta, amma sai taji tayi dariya kawai, ya ta iya da kaddara."?
Shima dariyar ta danji yayi,
"Sai anjimanka."
"Okey thank you."
Kiran nashi da tayi, ya k'ara sashi jin kewar Hafsah, sosai, ya kalli agogo, yanzu ne daidai lokacin da takeyin program d'innan a television, ya mik'e a hankali ya nufi falon Hajiya, cikin d'an mamaki Hajiya ta kalleshi, ya nemi guri ya zauna, sai dai abin taikaici ba tashar suke kallo ba, ya dai daure ya zauna, har zaman ya gundure shi, ya tashi kawai zai fita sai kuma yaga Hajiyar ta dauki remote ta canja tashar zuwa can d'in.
Sai kawai ya dawo ya zauna, nan ma Hajiya ta bishi da kallo kawai.
"Ya jikin naka?"
"Da sauk'i."
Kasha maganin yau."?
Idon shi kan TV yace "Eh Hajiya."
Allah ya k'ara sauki."
"Amiin."
Ba,a fi minti 15 ba, aka gama shirin, yaji dad'in kallon aranshi sai yaji an sauke mishi wani nauyi daga kanshi.
Ya dan zauna kad'an, sannan ya mik'e ya wuce d'akinshi.
'Sai dare sannan yayi tunanin kiranta.'
Tana falo ita da kowa na gidan kiran nashi ya shigo, mufida ce ta miko mata wayar, ta kalli sunan daya bayyana, sai taji sanyi aranta, gefe kuma ya haddasa mata fad'uwar gaba, ko meye dalili oho.
Tana jin kunyar a kirata ta mike tabar su a parlour ta wuce d'aki, ciki kuwa ga abbansu da Mama, amma tasan ita da kanta tafi samun nutsuwa, idan ta keb'e tana waya, ko da wanene takeyin wayar kuwa.
Ganin wayar zata tsinke ne, yasa ta d'aga tare da mik'ewa tayi hanyar bed room d'inta.


📝
*HAJEEYAH*
*KHAREEMERH.*


♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so*
*(Guba ne)*
💔💔
*By:*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh )*
*Dedicated to Unique in your love heart group members.*



📄 *50*







*"Hello"*
Taji yace.
"Hello"
Ta mayar mishi.
Ta taka da sauri tashige bedroom din ta zauna gefen gado.
"Kina lpia."?
Lpia lau,
Kwana biyu kinjini shiru koh.."?
Bata san amsar da zata bashi ba don haka tayi shiru.
"Uhum."?
Yace da ita.
"Um."
Tace dashi.
"Hhum"
Yayi ajiyar zuciya, ya kwantar da murya.
"Hafsah."
Taji kiran ya ratsata, amma sai bata amsa ba.
Shima badon ta amsa din ya kirata ba don haka yacigaba da magana bayan d'an shiru da yayi, cikin nutsuwar murya yace,
"Baki nemeni ba kuma koh."?
Sai taji 'yar kunya, har ta fara k'ok'arin kama kanta da laifi.
"Um um."
Tace mishi,
"Hmm yayi murmushi mai sauti,
"Um um kikace."?
Sai tayi saurin kama kanta, kada fa yaga zak'ewarta.
Ya cigaba da cewa, "Bani da lafiya ne!"
Sai taji gabanta ya fad'i.
Takuma jiyo shi yana maimaita,
"Rashin lafiya nayi Hafsah, wajen _5days_ ina ciwonkai."
"Ya salam." Taji bakinta ya furta ahankali.
"Sannu"
Cikin murmushi yace, "Yawwa naji sauk'i alhamdulillah."
"Allah ya k'ara sauki."
"Amiin"
Yace cike da jindad'in yadda ta nuna kulawa.'
Ya danyi shiru sannan yace,
"Ai na ganki kina program d'inki a TV."
Murmushi kawai tayi.'
"Bani da lafiya amma sai da na fito na kalla."
Ta k'ara yin murmushin daya ji dad'inshi sosai cikin kunnuwanshi, har ya furta babu shiri.
"I Miss you!
Jin kalmar tayi bazato, ahankali ta sauke ajiyar zuciya, tare da zamewa ta kwanta.
"Kinji,"?
Yace da ita.
"Uhum"?
Tace, cike da jin nauyin shi.
"Hmm, cewa nayi "I miss you, I miss ur voice.!!
Lumshe idanunta tayi, sannan ahankali ta bud'e, daidai lokacin da yakecewa,
"Kinji me nace yanzu."
"Um."
Tace,
"Okey thank you."
yace.'
Ta rasa dalilin godiyar amma taji d'ad'inshi da zata ce mishi, ~_"For what."?_~
Sai kuma tayi shiru.'
"Ina son inzo wajenki, idan zan samu."
Sai taji gabanta ya fad'i.
Na sami sauk'i, naji kawai inason zuwa inganki, kinga da na mutu a rashin lafiyar nan shikenan koh.?
Shiru taji kawai, ta daiji jikinta ya d'anyi sanyi.
"Idan zaki bani dama _Friday_ nazo."?
Tayi shiru tana tuno yaushene ma _Friday_ d'in.
"Uhum"? "ko baki shirya ganina ba."?
Tayi shiru.
Okey ki bani lokaci, duk sanda kika shirya kinji."
"Okey tace mishi."
"Kada na dameki koh."?
"Goodnight!!
"Bye bye."
Tace.
"Okey..
Ya kashe wayar yayin da itama ta janye wayar daga kunne.
Bata motsa daga inda take ba har zuwa mintuna, tana mamakin yadda take jinta kamar bata tab'a waya da namiji ba, idan tana waya dashi, meyasa haka oho."?
Mamakin yanayin da take shiga take, da kuma yadda take, amsa wayarshi da irin biye mishin da takeyi..





*'WANI B'ANGAREN'*
_________________________
'Tana kwance, shiru ita kad'ai tayi tagumi fuskarta cike da damuwa fal sam bata son ta ina zata fara ba, amma dole ne ta samarwa kanta mafita tunda bata da ishashshen lokaci.'
'Ta janyo wayarta, ta danno number shi, ta samu da
kyar ta shiga.
'Wayar tayi ta ringing amma ba,a d'aga ba, har ta gaji ta hak'ura, sai kuma ta tuna cewa lokaci yana k'ure mata.'
'Don haka ta shiga Email ta fara tura mishi sak'o..'
"I called you but u didn't picked my call.. WHY??
Please ka kirani sai muyi magana."
'Bayan ta aika ne bbu jimawa kuma yai mata reply da "Okey" kawai.
'Tayi ta jiran kiran nashi amma babu kiran.'
'Abinda bata sani ba shine, shi yanzu gaba-d'aya ba ta ita yake ba sam, don shi ya gama yayinta.'
'Sai can dare kiran nashi ya shigo, da sauri ta d'aga.
"Hello
"Hi
"How are you
"Am fine, um naga kin kin min Email mene ya faru ne."
'Hum tayi ajiyar zuciya.' sannan ta marairaice ta fara magana.'
"Akwai damuwa ne fah. Yesterday, Dad ya kira ni, yace min in fito da wanda nake so amana aure.. If not kuma yace akwai wanda ya mishi magana so zai bashi dama kawai."
"Tunda ta fara yake sauraronta har tazo nan sannan yace,
"To yanzu what's solution."?
Cikin takaici tace,
"Hmm you already knew that ba zan iya auren wani ba idan ba kaiba koh.."?
"What.. what are you saying..??
'Wutar kanta ta d'auke ta tsaya cak, au tambayarta yake me take fad'a ma."?
Sai kuma taga asarar ta k'yaleshi don haka tayi k'arfin halin cewa, "Yusuf nasan kaji me nake fad'a maka, amma kake nunamin baka ji ba koh."?
"Hmm.. Yai wani murmushin rainin hankali.. "naji mana... kuma aini murna ma zan miki zakiyi aure koh."?
"Hum, Okey haka kace koh."?
"Hmm, so ya kike so nace en mata."?
"Hmm, thanks
thank you very much."
'Ta fad'a cike da rashin sanin matakin d'auka.'
"Okay, yace kawai sannan ya katse wayar.'
"Ta saki wayar ta fad'i k'asa, ta dafe kanta da hannu biyu, bata da wani abinyi sam..
'Kogin tunani ta fad'a akan yadda rayuwarsu ta baya ta kasance..'
'Idan ta k'irga zata ga a daddafe tayi shekara d'aya da rabi rabon da taga Yusuf ido da ido.'
'Ta sani, asanda ta mallaki Yusuf ta mallakeshi sosai har tsahon shekaru kusan uku ta shimfida mulki a rayuwarshi tayi sa,ar rabashi da wasu abubuwa muhimmai cikin rayuwarshi misali "HAFSAH."



Tun a wancan lokacin ta tabbatar wa da kanta cewa, "Lallai soyayyar da Yusuf ke yiwa Hafsah, ta gaskiya ce, domin sunsha fad'a akan ambaton Hafsah da Yusuf ke yawanyi tare da zargin kansa akan _'Ya ci Amanarta'_
Yusuf ya kashe mata kud'ad'e da ita kanta bata isa ta kirga su ba, sun shimfida rayuwa mara dad'in bada tarihi.. Don tun tana abubuwan ta ab'oye har takai mamanta ta sani, lokacin hankalin maman ya tashi, amma ta gaza iya yin komai don ta bari sai da abin yafi k'arfinta.'
'Alokacin ta yanke shawarar maida Basman wajen mahaifinta, wanda mamakin hakan ya sashi shakkar karb'arta.
'Da kyar ya yarda ta koma gidan nashi, ya kuma saka ido sosai akanta, ahankali ya fara gano cewa tabbas tarbiyyar 'yartashi ta dade da rugujewa.'
Sanda Allah ya dubeshi sai akayi sa,ar barin Yusuf K'asar gaba-d'aya ya sami aiki.'
Lokacin neh Abban Basma yaga tab'ara kala-kala, wato Basma ta sha auna tserewa daga gida a nufinta na sai tabi Yusuf duk inda zai tafi, akan wani alk'awarin k'arya da Yusuf d'in yayi mata wato zai aure ta acan k'asar da zai koma.'
Lokacin tana level 200, a makaranta
Bayan tafiyar Yusuf d'inne, lokacin Basma ta fara ganin sauyi daga gareshi, sannan ta fara fahimtar cewa lallai sahun giwa ne ya fara take na rakumi, _wato yaje can ya had'u da dai-dai shi.'_
Lokacin kuma ta fara fuskantar rashin kulawa daga gareshi har takai sai su shafe sati bai waiwayeta ba.'
'Ayanzun ma da ta nemeshin, sun shafe fiye da wata d'aya, basuyi magana ba koda a waya kuwa.'
'Ta sani bata da wani tsayayye, wanda zata iya kawo mishi zancen ya aureta, duk tarin samarin nata irin kalar Yusuf d'inne wadanda suka maye mata gurbin shi bayan tafiyarshi.'
'Nour' shine Abba ke son had'ata dashi, duk da bai kamata ta kira hakan amatsayin 'Auren had'i' ba, domin Abba ba d'akko shi yayi yace zai bashi ba, ganinshi yayi a wajenta kuma dake ya gaji da irin take- taken ta sai yai mishi izinin ya turo iyayenshi kawai, kuma akayi dacen shima hakan ne manufarshi.'
'Bashi da wata makusa, d'an manyan mutanene, shekarunshi ba zasu wuce 30, ba, bai wani girmi Basma sosai ba, amma yana da nutsuwa sosai.'
'Basma ta ja tsaki, sanda ta tuno shi, wai ita ake shirin yiwa aure ba tare da son ranta ba.'
'Ta rarumi wayarta ta danna kiran wata k'awarta.'
"Hello Basma."
"Teemah, babu lafiya fa."
"Meya faru kuma."
"Kinga na kira Yusuf yaki ma ya saurareni yadda ya dace bare muyi magana."
"Kinsan me zan fad'a miki k'awata."?
"Ina jinki."
"Wallahi mu,amalarku tayi k'arko keda Yusuf."
"Bangane me kike nufi ba."
"Hmm, ina nufin yadda kuka dad'e tare keda shi, kema kin sani samarin yanzu ba amana ce dasu ba, bare shi da yanzu ma bakwa kusa keda shi."
"Hmm, Teemah, ahakan kike fad'ar haka."?..kin san rabona da Yusuf kusan 2years kenan."?
Koma yayane nidai ina fad'a miki kun dad'e keda Yusuf, kuma ni yanzu shawaran da zan baki shine kawai ki yarda kiyi aurenki don banajin Yusuf zai aureki.!!
"Ke Teemah, bana son wulak'anci, ai ke auren kikayi da kike cewa inyi aure kuma a rainin hankalinki zaki ce in auri wani ba Yusuf ba."??
"Hmm, ni dai gaskiya na fad'a miki, kuma ni ko ayanzu na sami wanda yazo yacemin yana sona da aure, wallahi auren shi zanyi kindai san babu yadda za,ayi kuyi irin rayuwar da kuke da Yusuf sannan kuma yace zai aureki.!!
"Kada ki fad'a min maganar banza, har ni zaki zaga, kice muna rayuwar banza, kema ba irin ta kikeyi ba."?
"Hmm, Basma ni ba cemiki nayi ba ita nakeyi ba, amma kinsan ni bankaiki ba don, ban watsar da mutunci na atiti ba, _kefa dakanki kika fad'amin kin bawa Yusuf komai saboda haka kisan da sani Yusuf ba zai aureki ba zaki ce na fad'a miki.."_
"Ta katse wayar, tabar, Basma na zage-zage tana fad'in k'aryane bazai yiwu ba."
Daga bisani ta mik'e ta nufi, d'akin abbanta, fuskarta babu annuri don amsa kiran da yayi mata.
Tayi sallama a ciki-ciki sannan ta shige ciki.
Yana zaune, akan kujera, yana kallon TV, ta nemi guri ta zauna.


Cikin nutsuwa ya juyo ya kalleta, ta k'ara tamke fuska.
"Basma, ya muke ciki a maganar mu."?
Ta keb'e fuska kamar zatayi kuka, batace komai ba sai kallonshi da takeyi.
"Tambayarki nake don kada na yanke hukunci ki ga anyi miki ba daidai ba."
Bataga alamun wasa a tattare dashi ba don haka ta shiga hankalin ta kada ta tsaya wasa tayi wa kanta.
Ta bude baki ta fara magana, cikin shagwab'a.
"Abba fa munyi magana da Yusuf d`in yace zai zo k'asar nan nan da wata d'aya.
"Wata d'aya."?
"Eh Daddy"
"Hmm Basma ki shiga hankalinki dani, ba maganar wasa nake miki ba, kuma bazan tab'a zaman jira sai wata d'aya yayi zan yanke hukunci ba."
Ta d'ago da sauri ta kalleshi, cikin damuwa, "Allah abba da gaske zai zo."
Cikin fad'a ya fara mata magana,
"Wai ma waye Yusuf d'innan da kike ta fad'arsa, kullum daga anyi magana sai ki kawo zancen wanda baya nan, waye ubansa, ki fad'amin ni naje na same shi."



Gabanta yayi wata muguwar Fad'uwa,
"Ta d'ago ta kalleshi.
"Eh, na gaji da wasa da hankalin da kike min, idan ma k'arya kike babu wani Yusuf ai zan sani ne."
Kawai yaro, yazo da magana amma kina sani ina ta magana biyu, to baki isa ba, kuma kada na sake ganin kin fita daga gidan nan bada sani na ba."
Na baki sati daya idan banga Yusuf a gidannan ba, to dole ki karbi, zabina, shashashar banza kinfi gane kiyi ta gantali ko."?
Hankalinta tashe ta nufi d'akinta, sam ta rasa sanin abinyi, gashi wai har wata dokar hana fita aka sa mata wanda tabbas tasan ba zai yiwu ba.
Kamar an tsikareta ta fizgo wayarta babu shiri, ta danna kiran mamanta, tana d'agawa Basma ta fara kuka, cikin tashin hankali take tambayarta "Lafiya meya faru."?
"Ba kece kika kama kin dawo dani gidannan sai wulak'anta suke gashi sun zuga abba wai aure zaiyi min.!!
Duk da tasan za,a runa, amma maganar ta shigeta da taji cewa, ba zab'in 'yar tata za,a bata ba.'
"Aure, kuma..??
Tab to wa zai aura miki."?
Wani ne daga yazo gurina ya ganshi shine yace ya turo iyayenshi."
"Okay ki kwantar da hankalinki zamuyi maganar da shi bazata yiwu ba."
Ta danji sanyi aranta don haka tace "To Mama."
Maman ta d'ora da cewa, "Wato hajiya Salman ce ke zuga shi ko."? Shikenan dani take zancen, dama ke kika jawo wa kanki ai, badon haka ba me zai kaiki gidannan da zama, I hope bata takura miki ita da samarin 'ya'yan nan nata."?
Basma tasan Indai gaskiya zata bi hajiya Salma a 'ya ta d'auketa, yayyenta maza su uku ne biyu, sunyi aure sai kuma mace guda d'aya "Aunty Meenat."
Sai Basman wacce uwarta ita kad'ai mamanta ta haifa sannan ta fita, sai na'imah sai autar hajiya Salma wato Nuratu.'
"A,a ni bana ma shiga harkarsu, yaya Abdul ne yake samin ido komai nayi sai yayi magana."
"Tab bazai yiwu ba, dole zan mishi magana babu wanda ya isa ya takura miki gida, gidan ubanki ne kema."
"Thank you mum."
Kuma ki maida hankali akan karatun ki, yawon nan da kike yi idan ma baki daina ba gaki ga Dad din naki nan ai."



________________
Yau ne rana ta farko da ya fara yi mata magana a chat. Ya mata sallama da wata number, ta amsar sallamar tare da cewa "wa yake mgna."?
"Hmm yace, tare da tura mata murmushi.
"Okey you don't chat with strangers ko?
"Hmm" tace mishi kawai."
Ta duba user name dinshi _UK_ kawai taga an rubuta.
"Kina magana da ukhasha "
Rasa reaction d'in da zatayi tayi, bata da wannan number d`in, shi kuma yaga ta gani kuma yana jiran amsarta.
"Ok you're welcome!
Tayi saurin lalubo abin cewa.
"Thank you yace mata."
"Ya kike ya gida"?
"Lpia lau"
"Ya ayyuka naki ya fans"?
Sai ya dan bata dariya tayi murmushi.
"Hmm suna lpia."
"Masha Allah.
"Hafsah.!
"Yes."
"Please ina son inzo wajenki Allah.!
"Taji gabanta ya fad'i."
"Hmm tace don ta rasa abin ce mishi."
Plz nasn kina da uzuri.. Amma ki taimaka min da Friday."
"Friday?
Ta tambaya
"Yes plz."
"Ina son had'uwar mu dake"
Hmm Okey diz coming Friday?
Eh ina da lkc sosai ranar kene dai bansaniba ko kina dashi.
"Okay zan duba."
"Oh my God yaushe?
"Soon!
"Plz help mee!!
"Hah, tace.
"Hmm da gske ina son ganinki.
"Koo ?
"Allah.
Okay Gud."
"Plz wallahi n damu dake fiye da tunani."
Okay thank u.
"Kin yanke shawarar."?
"No, Ina duba free time ne."
"Hafsah manya a taimaka dai."
Okay
"Sai dai sat day.
"Oh!
"What?
"Nthng en mata, nagode zan katse uzuri na domin ke!
"Hmm..
"Yes kin isa ai"Ngode hakan ma.
"Amma plz ki brni nazo da yamma kinji"?
Yamma.."?
"Eh plz.
Why.."?
Shine nke da time kuma inason ki ganni sosai.
"Hmm!
"Am sorry plz!!
"For..?
"Da nace _ki ganni,_ bansaniba ko bkya buk'atar hkan."
"Hmm,
"Yes but ni ina so."
"Kna so me?
"Inganki mana Hafsah en mata."
Ya dan b'ata kunyar kalmar.
"Hmm"
okey bye.
"Kin gaji ne ko?
"Bacci znyi.
"Ok ki huta have nice sleep!
"Thank u!
"My Dear Hafsah!
Gud Night!!
'Ta kashe Data ta tayi shirin bacci da tunanin hirarsu ko ba komai ya d'ebe mata kewa, ta rufe idanunta tana tunanin ya had'uwar tasu zata kasance."?



📝
*HAJEEYA*
*KHAREEMERH*


♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so*
*(Guba ne)*
💔💔

*By:*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh )*
*Dedicated to Unique in your love heart group members.*





📄 *51*




*Tana* kwance take tuno abubuwan da suke faruwa.
Wato tun bayan wayar da sukayi da mamanta har take ce mata zata yiwa Abban nata magana. To maman ta sameshi amma kuma had'uwar tasu ba tayi dad'i ba.

Gashi saura kwana kad'an lokacin da daddynta ya d'ibar mata su cika..


Wato da daddare maman tata, tazo gidan, dake ba wani gaisuwar arziki suke yi da matar gidan ba, sai ta wuce d'akin 'yar tata kai tsaye ta zauna.

Basman na kwance tana danna wayar ta maman ta shigo, ta mike tare da rungume ta cikin farin ciki. sukayi murmushi, mama you're welcome,
Basma tace, cikin jin murna, sannan ta sake ta.

"Yawwa baby na ya kike."? Ta fada yayin da ta nemi guri ta zauna. Sannan ta fara kallon ko ina na dak'in, an tsara d'akin sosai yadda har ta gama kallon k'urillah d'in ta bata gano abin yin k'orafi ba.

Basma ce tayi mata magana.
Mama menene"?
Tayi murmushi babu komai, ya ake ciki."?

Basma ta shagwab'e murya kamar zatayi kuka.
mama, wallahi Daddy yace bazai chanja ra,ayinshi ba, yace min wai one week ya bani.
Sai ta k'arashen zancen da kuka.

Maman tata ta rungumo ta tana rarrashi.
"Sorry my Baby kiyi hak'uri na fad'a miki ki daina damuwa kinji babu wanda zai miki abinda bakya so."

Mama baki ga yadda Abba yake ba wallahi bana tunanin zai chanja.

Basma, ki k'yale komai a hannuna nace ki daina damuwa kinji, tashi ma kije ki fad'a mishi nazo."


Ta mike ta fita, bata jin zuwan maman nata zai yi amfani, yadda Abban nata ya kafe akan lamarin.

"Abba Mama tazo."
Afusace yace, "Tana ina."?
"Tana room d'ina."
"Okey ina jiranta."
Ya mayar da hankalinshi kan abinda yake.


Cikin takun k'asaita ta iso cikin falon nashi, ta nemi wajen da yai mata ta zauna.

"Ina yini."?
Tace dashi fuska babu walwala sai shan kamshi take.


Ya zuba mata ido, har yanzu, tana burgeshi sai dai bazai iya sake zama da ita ba, saboda halayenta, sam bata son zaman lafiya, shi kam bashi da burin raba matanshi.

"Lafiya lau"
"Ya amsa."


Ta shak'i iska sannan ta fara magana.

"Basma ce tazo min da wani bahagon zancen da nake tunanin k'aryarta ce ta shirya."

"Ya d'an tsare gida sannan yace, wanne zance fa."?


"Am naji tace wai kace ta fito da

26 / 40