Author : KARIMA TIJJANI MANSUR Category : Romantic Hausa Novels
makamancin haka sai ranki yayi mummunan b'aci, shashasha, kuma yanzu ma zan iya fadawa abbanki matuqar na qara ganin abin me kama da wannan. Kuma wayar na kwace bazaki qara ganinta ba. Kuma duk ranar da kika sake naji labarin kin k'ara kula yaron nan to ki tabbatar kamar abbanku ya sani ne."
"Bazan qara ba mama kiyi hak'uri."
Binta mama tayi da kallo kawai, sannan ta fice cike da mamaki.
Ta boye wayar sannan ta saita nutsuwar ta kada Abban Hafsah ya gane, sam bata son tada mishi hankali da irin wannan zancen ba.
Da alhinin k'wace wayar Hafsah ta kwana har ta kasa yin isashshen bacci. Allah Allah take safiya tayi taje makaranta ta sanar da Basma.
"Na shiga uku Basma, mama ta kwace wayar nan fah."
"Basma ta d`aka mata duka ke garin yaya, banza."
Tsautsayi Basma, waya nake tazo ta tadda ni, Allah ya rufamin asiri ba Abba bane ya ganni da na shiga uku.!!"
"Hmm, gaskiya ke doluwa ce, idan nice wallah bazan bayar da wayar ba."
Hafsah ta zaro ido. Kaii Basma tafa riga ta gani.
"Hmm, kedai tunda kinyi sakaci ai shikenan.
Please Basma, help me Mama tace kada ta sake ganin yazo na fita, wallah ina sonshi Basma, ya zanyi in dinga ganinshi gashi babu waya."?
"Please help me.!!
Dariya Basma tayi me isarta sannan ta kamo Hafsah tayi mata rad'a a kunne.
_"Ke dallah can appointment zaki dinga hada muku."_
Hafsah ta zaro ido, kamar a ina kenan nifa bana fita kinsani.
"Nonsense ki zo gidanmu mana."
"Kaii Chab Mama bazata barni ba."
"Hmm, kina da abin haushi H Hamid."
"Ba kina zuwa islamiyya ba."?
Eh ina zuwa."
"Why not kuna had'uwa idan kin fita.
Hafsah tayi shuru tana tunani, can kuma ta tuna tabbas babu mafita idan ba hakan ba don haka ta rungume Basma tana godiya.
Sanin da Hafsah tayi basma na zuwa da waya yasa tace,
"Please ki bani wayarki, na tura test Allah yaso n riqe number d`in.
"Hmm, ungo badon halinki ba. Ta ciro wayar daga aljihun uniform ta ba ta.
"Dear it's Hafsah, Mama na ta kwacen waya, ina son mu hadu, yau a bayan layin mu by 2:00pm plz kada kazo Gidan mu.
Minti kad'an ya kira, ta d'aga.
Baby me kike fad`amin, mamanki ta kwace waya.
Eh okay, mun had`u na baki wani.
"Noo dear thank you."
Aa zan taho miki dashi..
Ta katse wayar saboda tsoron kada a kama su da waya.
murna take sosai babu sauran damuwa.
Hakan ne ya faru kuwa, bayan Hafsah ta koma gida tayi ta nuk'u nuk'u har qannenta suka gaji da jiranta, mama tace suyi tafiyar su.
Dama haka take so don haka Basma ta tsara mata.
katon hijab ne har qwauri sai doguwar riga, sune uniform d`in. Ta sab'a Jakarta ta cewa mama ta tafi.
Yana ta kai kawo a layin, tun qarfe 1:30pm yake wajen har ya fidda ran ganinta.
Ya saki ajiyar zuciya sanda ya hango ta, ya nufi motar shi da nufin ya kunna su shiga ciki amma ta mishi alamar daya bari.
Ta gabanshi tazo ta wuce, sannan ta mishi inkiya (signer) da ya biyo ta.
Ahankali suke tafiya, har zuwa _lokon su Jamila, dake lokon_ babu Mutane sosai, kuma dama suna bin hanya biyu ko su bi tanan ko subi titi street.
A Wani dakali suka yada zango.
Ya kura mata ido yana murmushi, ya mata kyau sosai, taji ta a wata sabuwar duniya, _Lallai babu abinda ya kai soyayya sanya nishad`i._
"Baby I miss you."
Ya fad'a a hankali.
murmushi tayi itama.
Really"?
Yes ya fad'a yana jinjina kai.
"Me too my dear.
Itama ta fad`a.
Ya sakar mata murmushin daya sa ta shagala da kallon shi.
Bata ankara ba taji ya kamo hannunta, dole ta farga, tana kokarin kwacewa ta tuno basma.
_"Saura kuma ki nuna mishi qauyanci!._
Bata fahimce ta ba a lokacin amma Idan hakane dole tayi kyauyanci kuwa, yaushe zata bari haka na faruwa.
Ta zame hannunta a Hankali ta sannan ta miqe tana rungume, hannu a qirji, amma kirjinta sai bugawa yake da sauri da sauri don tsoro.
"Dear lemme go kada nayi late."
Ya kura mata ido, baiyi magana ba dai.
Ya miqa mata qaramar wayar hannun shi.
Okay take this."
"Noo dear."
Please ki karba mana, da me zanna contacting dinki."
Mama zata bani wayata.
Ta fara tafiya don ta fara tsorata da makarar da tayi.
Ya bita suka jera.
"Plz mana baby."
"Am sorry dear, zan amso nawa nace maka."
Ya karanci tsoro a idonta don haka ya kyaleta.
"OK ki dinga kirani a wayan friend dinki.
"Okay."
Sai da ya kusa rakata makaranta sannan suka rabu, ya miqa mata wata Leda dake hannunshi.
Da zata k'i amsa, ya
had'e ranshi sosai.
Dole ta karb'a saboda bata son su tsaya ja'inja, taqara bata lokaci, sannan tana tsoro kada idon-sani ya ganta."
"Thank you dear."
"I love you." Yace mata.
"Me too dear."
"Bye see you later."
Ya fad'a yana kallo ta.
Suna ta waiwayen juna, cike da farin ciki Hafsah take, gaskiya ya had'u bata tab'a zaton samun saurayi kamar wannan ba.
Gefe guda, tana fargabar riqe hannunta da yayi, Allah yasa dai ba haka yake ba.
sai kuma fargabar makarar data tafka, don ma ansan bata makara...
.[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): β₯β₯β₯β₯
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
ππ
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique In Your Love Heart Members.*
π *12*
*Ko* da Hafsah taje islamiyya acan ta rabar da abinda yusuf ya kawo mata..
Ice cream ne sai tarkacen kayan ciye -ciye..
Bayan ta dawo gida ne tana d'akinta mama ta kira ta ta dawo falo.
Tun daga rannan mama bata barin ta ta keb'e ita d'aya a d'aki idan ba lokacin bacci ne yayi ba..
Da safe suna isa makaranta layinsu Basma ta nufa, sai dai cikin rashin sa,a ranar gaba d'aya Basman bata zo makaranta ba.
Haka hafsah tayi zaman makarantar babu wata walwala.
Fatima ce ke fad'amata "Hafsah wallahi kwana biyu kin chanja, ko son zaman cikin class bakya yi.."
"Hmm, ruk'ayya wani abu ne ke damuna wallahi..
"Kuma kike rasa dawa zakiyi shawara sai Basma Yunus koh?"
Hafsah ta d'an sha jinin jikinta sai kawai ta kawo mata wani zance.
"Fatima ba wani abu bane kinsan k'awata jamila da nake fad'a miki?
"Eh"
Nan hafsah ta shiga labarta mata abinda ya sami Jamilar..
"To yanzu neman yadda zaku nemota kuke ko me??"
Hafasah bata da amsar bata don haka tace bazaki gane ba Fatima"
"To Allah ya taimka"
"Amin" inji Hafsah.
A ganin Fatima Basma ba k'awar da za,a zauna shawara da ita bace.. Ina ma taga hankalin da zata hango abinda Hafsah bata gano ba,?.. Ita damuwarta ma wai me suke tattaunawa ne??
Don bata yarda da abinda Hafsan ta fad'a mata ba.
A saninta Basma ba wata k'awar hafsah bace, hasalima abokiyar takararta ce don idan hafsah tayi sakaci wani lokacin Basma ke k'wace mata 1st position d'inta.
Basma akwai shishshigi da bani na iya.. Tana son shiga al,amran da babu ruwanta..
Tatasone agaban mahaifiyarta don tun tana shekara 5 suka rabu da mahaifinta. Sanadin haka yasa yake sakarwa maman tata kud'i har 'albashi' yake biyanta wai ladan d'awainiyar da take da 'yarshi duk wata dubu d'ari..
Mahaifiyar Basma business takeyi, kuma tana yawan yin tafiye tafiye sai tayi fiye da sati bata gari ko kuma ma k'asar gaba d'aya.
Don haka koyaushe basma na gidan k'awayen mamanta (Can take kaita idan tayi tafiya).
Don bata da kowa a kano duk danginta na kaduna, amma tunda tayi aure take zaune a kano, ita kad'ai sai 'yan aiki sai abokan hul'arta mazaa da mata da kullum suke zarya a gidan..
Idon Basma a bud'e yake sosai, domin idan mama tayi tafiya, haka manya- manyan samari ('ya'yan k'awayen mama) suke d'aukarta zuwa yawo, sune club, sune park, sune party.
Duk da haka mamanta na sata tayi karatu dole. (kuma don ma tana da kwakwalwar karatun ne.)
"Kiyi karatu basma ki dogara da kanki, kinfi k'arfin raini..
"ki daina la,akari da babanki yana da kud'i.."
Ahakan kuma take hanata kula samari, amma duk da haka bata hanata zuwa wajen wani party ko wani taro idan ya kama...
To,Hafsah bata samu damar tattaunawa da basma ba sai washe gari lokacin, malaminsu na lissafi zai shigo ajin suna hango shi suka fice, Basma na cewa "Mts yanzu zai damemu da wani revision."
SS 1a suka shige suka nemi guri suka zauna acan baya..
"ya kukayi H Hamid?
"Um,Basma yazo na fad'a mishi. Amma ba shine matsalar ba."
Ta fad'a cikin damuwa.
"To Mene matsalar?
Tayi k'asa da murya sannan tace
" Yusuf yana son rayuwar turawa, yana k'aunar ya tab'ani.. Wai haka yace min na mishi kiss"π³
"Mtsss"
Basma ta ja wani dogon tsaki.
"To sai me? Ke da irin local soyyaya zaki nuna mishi, wallahi kin bada ni"
Ni duk kinsa ma raina ya b'aci."
Hafsah dai tayi shiru ita yaushe zata fara wannan watsewar??
tab' Allah ya tsareta.
Amma dake kamar tana tsoron basma ne sai tace
"Basma yanzu an fasa kiran nashi kenan?
"Hmm ai kece, ta mik'a mata wayar tana cewa ungo saka number d'in..
(Al,adar Basma ce zuwa da waya makaranta.)
Ringing biyu aka d'aga.
"Hello" yace
Hafsah ta kalli Basma, bata san me zata ce ba.
Basma ta harareta.
Sai ta dawo kan doka da oda.
"Am, dear iam Hafsat"
"Oh my gosh!
Ya fad'a cikin wata k'ara my baby I miss u alot"
Ta daure tace "Me too"
"ya kake?
"Fine but thinking of you, wai when ur mama zata baki wayarki ne?
"Um very soon in sha Allah."
"Um um ni dai ban yarda ba kawai mu had'u anjima na baki wani"
"No, ka barshi yau zan karbi wayar"
"OK thank you my baby, yaushe ne zanzo my eyes want to see u kinji.?
Dam gabanta ya fad'i ashefa bata fad'a mishi an hanata kula shi ba..
"Um, am.. Ka bari mama ta bani wayar,
"Nooo ni dai I can't wait, pls baby nah"!
OK ina school kaga yanzu ka bari zamuyi waya, but pls kada kazo sai mun kuma yin waya."
"OK, bye bye i love u" π
"Thank you"
Gama wayarsu kenan, Geography teacher ya danno ajin, kuma shine form master d'in su Hafsah (shine ma ya gansu ran nan)
Suna ganinshi suka mik'e ya kallesu kawai..
"Again?
Ya fad'a yana rik'e haba..
"Yunus and Hamid What are you doing here??
"Am.. im Nothing sir"
"Ok, very good".
Ya fad'a yana kad'a kai.
Suna fita Basma ta Shek'e da wata shashashar dariya..
Tana wani abu da fuskarta kamar ta ga wani abin tsoro, look at your reaction H. Hamid, when Teacher catched us,...π±π¨π€₯ uhum kamar kinga zaki" hahh ππ
A gida kuma mama tunani takeyi akan, Kodai ta bawa Hafsah wayarta ne, a tunaninta, hafsah 'ya macece wacce Yanzu shekarunta sun kai 17, bai dace a matsa mata ba, don takai munzalin tsayawa da saurayi. Don ma abin ya zo da zamani da dane ai da tuni tana d'akin mijinta..
"Ai kuma ya dace ki nuna mata kuskurenta"
Wata zuciyar ta fad'a mata...
'Zan bari zuwa suyi hutu'
Haka mama ta kudurce a ranta..
To kusan kullum a makaranta sai Hafsah sunyi waya da Yusuf, kuma kullum zancen shi d'aya yaushe zai zo?
"Ka bari dear, ka bani two weeks"
Haka ta fad'a mishi wata rana, lokacin sun fara jarabawa.
"What? Mene kina cewa??
"Ok bakya sona ne I realized, ok I will leave you kawai"
Ya fad'a, kawai ya kashe wayar.
"Na shiga uku Basma kinji wani abu kuma"??
"To ya zan miki an baki shawara kink'i karb'a, ba saiki bari ya kub'ce miki ba."
Ta fad'a cikin rashin nuna damuwa da zancen.
"To aini basma tsoro nakeji..
"To ai shikenan"
Ta kuma kiran number ba,a d'aga ba.
"Oh my God! dama haka yake da fushi?.
So bata kuma samu sunyi waya ba sai ana gobe hutu (Bayan malaminsu ya kirata ya mata fad'a akan karatu )
Da k'yer ta samu ya hak'ura, amma yace mata dole ne su had'u cikin wani satin.
Aranar da aka musu hutu, ranar ne kuma bayan ta dawo, mama ta kira ta suka zauna a falon maman..
"Hafsah kinga kin girma, ki nutsu kisan abinda kike yi, zan baki wayarki..
Ta d'ago cike da murmushi,
"Nagode, Mama.
Ba wannan ba, kada ki bari abbanku ya ga wayar nan, sannan kiyi taka tsan -tsan da samari, bance ki kula kowa ba, tunda abbanki baya so,.. Kuma kada ki k'ara karb'ar abu makamancin wannan a hannun wani."
"Nagode Mama, in sha Allah zan kiyaye."
Ta mik'a mata wayar,
"ungo ki b'oye, k'awayenki kawai na yarda ki kira"
Cikin zumud'i ta karb'a..
Baki 'nunamin result d'in naki ba."
Tsoro ya cikata, babu yadda zatayi haka ta dakko ta bata.
"Kaii, ya akayi haka Hafsah??
Bari abbannaki ya dawo, wato don an hanaki kula samari shine zaki k'i maida hankali kan karatunki koh?
(A tunanin Mama kenan)
"Kiyi ha'kuri Mama wallahi ba haka bane."
"Yayi kyau"
Tashi kije kya had'u dashi ai"
Tana zuwa daki'n ta tura mishi text zuciyarta cike da farin ciki.
"My phone is with me.. But don't call me now, let's have phone by night..
I love you!!
*To shine fa wayar da tayi yau, bayan ta dawo daga wajen abban ya mata fad'an karatu, shine kuma wayar da mama ta kamata tanayi a darenna..(Page 1 to 3 )*ππΌππΌ
*Muje zuwa muji wannan soyyaya ya zata kaya..*π
*Hajeeyah Kareemerh ce dai*ππΌ
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): β₯β₯β₯β₯
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
ππ
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique In Your Love Heart Members.*
πππππ»ππ»ππ»
*Jinjina gareku ZAZZAFAN SO NOVEL GROUP*
π *Farida (Farisam*)
π *Gimbiya Bilkisu*
π *Basma A adam*
*ΩΨ§ Ψ·Ω
*
π *Ummi M shehu*
π *Amina Yusha,u*
π *Umman Aryan*
π *Maman husna*
π *Mufy expensive*
π *Mummy khali*
ππΌ *Ina yinku π― kamar yadda kuke yin novel d'ina*π
π *13*
*Nunkuwar* shak'uwarsu da yusuf, nunkuwar soyayyarshi azuciyarta..don a kullum soyayyar yusuf k'aruwa take a zuciyar Hafsah.
Ahakan kuma waya, kawai suke shima ab'oye, amma kullum cikin lallab'ashi take akan lokaci ya kusa da zai zo wajanta..
Wata hira da sukayi, wata rana da daddare suna waya. Ya saisaita murya, dai dai yadda yafi jawo hankalinta gareshi.
"Baby"
Tace "Na,am dear"
"Ina son yi miki wani question ne"
"Ina jinka"
"Wai kina sona kuwa?
Ta d'anyi shiru sannan tace
"Haba dear me yasa kamin wannan tambayar?
Yai k'asa da murya "Am sorry bana nufin b'ata miki rai, ina tunanin, ni kad'ai ke wahalar son ki ne"
Ta marairaice.
"To Ba haka bane wallahi, u know my friend Basma koh, har cewa take wai
'Me yasa nake sonka da yawa ne?
Ya gyara kwanciyar shi, "To wane answer kika bata? "
Haka nace mata, "kanada abubuwan da nake so ne,..an then ka iya soyayya"!!
sai taji yayi dariya ahankali.
"Hahh da gaske ina da abubuwan da kike so kuma na iya soyayya??
Ta gyad'a kai kamar a gabanshi.
"Exactly yadda nake son mijina ya kasance, to haka kake."
Yai ajiyar xuciya "Thank you my hafsat!
Ya fad'a da wata kasalalliyar murya.
"Meya faru?" Ta tambayeshi.
Ya kuma ajiyar xuciya sannan yace "Am bacci nakeji, and abinda kika fad'a yasa naji wani 'Laziness' ya saukar min.
'Kasala kuma'??
Ta tambaya da mamaki.
"Oh, no kada ki damu, ki gaidamin da k'awar taki.. Gud night"Ya kashe wayar.
Sai kawai ta yi kissing d'in wayar, abinda bata tab'a yi ba a tarihin soyayyar su..
Wata ranar juma,a hafsah ta shirya cikin wata doguwar rigar atamfa fiffted. Tayi kyau sosai ta yafa d'an k'aramin mayafi. Batayi kwalliya ba sosai.
Ta fito falo, tace wa mama "Mama zan tafi, "
Maman har da bata kud'in mota.
"don Allah Hafsah kada ki dad'e har abbanku ya dawo"
"In sha Allah"
"Ki duba ta.
"Tom"
Ta rayata jakarta ta fito."
Cewa maman nata tayi wai ' Mamansu basma ce bata da Lpia zataje dubota, wai har asibiti ta kwanta.. 'Wannan shawarar basma ce, da Hafsah ta dame ta ya zatayi da yusuf?'
Tana zuwa unguwar ta kira basman a waya. Don bata san gidan nasu ba, layin ta kwatanta mata, da number gidan. Tana zuwa ta tarar Basman ce kad'ai a gidan sai 'yan aikinsu, maman tata bata nan.
Gidan nasu ya tsaru babu laifi..
Basma ta ruk'unk'ume ta,
" H, Hamid a gidanmu lallai ina da Manyan bak'i.
A falo suka zauna wanda ya had'u da gujeru da adon fulawoyi..
Basma ta sa aka kawo mata kayan ciye ciye..
Kad'an taci. Ta Kalli agogon dake falon.
"Kinga bai Kira ni ba har yanzu, gashi mama tace kada na dad'e."
"Hum, kema ai baki shirya ba"?
Hafsah ta kalleta cikin rashin fahimta.
"Kinga ni tashi muje ki shirya dallah, ahaka zai ganki"?
Taja hannunta, babu musu ta bita.
Wani dak'i suka shiga daya tsaru sosai basma ta nuna mata toilet.
"Ki shiga ki wanke fuskanki"
Ta shiga tayi yadda tace d'in.
Tana fitowa taga rashin ajye mata wasu riga da wando (pencil) iyakacinshi guiwa rigar kuma T. Shirt ce amma bata da hannu.
Ta nuna mata kayan "kisa wannan"
No, basma sunyi k'anana gaskiya"
Ta d'an b'ata fuska
"Kinjiki ai"
Ta mik'a mata wata powder shafa wannan"
Ta karb'a, Hodar ta amsheta sosai.
Ta mik'o mata sauran kayan kwalliyar
"Gasunan bari nayi wanka."
Ta shige toilet.
Hafsah ta yi kyau sosai.
Tana gamawa Basma ta fito d'aure da towel ajikinta da kuma wani d'an k'arami hannunta tana goge jikinta dashi.
"Wow kinyi kyau"
Yanzu dai ga wani humra ki shafa saiki sa kayan."
Ta dakko mata wani towel a drawer ki d'aura wannan sai ki cire gown d'in.
"Hafsah ta kalleta Nifa gaskiya Basma bazan iya fita gurinshi da wannan kayanba"
"So wai meyasa?
Kawai,ki barni da wannan gown d'in yayi ai"
"Nooo, bazaki fara zuwa wurinshi da dressing na wani atamfa ba gaskiya, dole ne ki chanja malama."
"To gaskiya sai dai a chanja wani."
"OK ai ga drawer d'innan duba wanda ya miki.'
Ta fad'a tana nuna mata wardrobe d'inta.
Suna cikin haka wayar Hafsah tayi k'ara, da d'auka da sauri.
"Hello"
Am baby nazo unguwar wane link ne?
"Om..
Ta mik'awa basma ta kwatanta mishi.
"Sai kiyi sauri ki nema wanda zaki sa."
Ta fad'a tana mik'a mata wayar.
* * * * *
* * * * *
Wani kyakywan had'ad'd'en saurayi (First Class) Basma ta yi tozali da shi..
A zatonta da yadda Hafsah ke kwarzanta mata yusuf bata ta'ba zaton yakai Kwatar hakan ba.
(Colour of my dream)
Ta fad'a a zuciyarta.
murmushi kawai yake sakarwa Hafsah, tare da wani irin kallo wanda ya so rikitata.
suka isa wajenshi..
Hafsah ta nemi gefenshi shi ta tsaya.
Ahankali tace mishi
"You're welcome my dear"
Ya zuba mata idanu "Thank you my baby"
"Am mu k'arasa ciki Koh?
Basma ta fad'a.
Sai lokacin ya kalleta. yace
"Sannunki fa"
Tayi wani murmushi cike da gogewa
"Am yawwa..
Basma na gaba suna bayanta..
Wani d'aki ta bud'e musu dake farfajiyar gidan, sanyin AC ga kuma wani daddad'an k'amshi dake tashi..
A wata kujera ya zauna three seater,
Hafsah ta zauna a 'me kallonshi' suna fuskantar juna.
"Am ina zuwa.."
Basma ta fad'a, sannan ta fita, sai wani rangwad'a take.
Falon ya d'anyi shiru, kusan mintuna biyu, sai kawai kallonta da yusuf yake..
"Can taji yace " you look so cute my baby".. Kinyi min kyau."
"Thank you"
Kazo lpia?
"Lpia lau, but full of kewanki amma."
Ya fad'a yana wani d'age gira.
Tayi 'yar dariya.
"Gani nan kam yanzu Koh??
"Ya mamanku"
"She's fine"
Ya d'an gyara zama sannan yace
"Baby baki son ganina koh,? duk na rame, kin hana in ganki..
"Am sorry ba haka bane, na fad'a maka abbanmu ba zai barni fitowa ba, sai nayi candy."
"Hum long distance, u