Chapter 23 Reading ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt Arewa Novels

ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt

Author :  KARIMA TIJJANI MANSUR Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   23 / 40

66K to 69K   out of 119.4K words

wajenta.

Ya kalli kanshi sosai a madubin, sannan yasa hannu ya gyara zaman hularshi yayi kyau matuk'a cikin _Brown shadda_ da sukayi ankonta, bai da kiba sam, sannan ba dogo ne irin sosai ba, yana layin tsakiya dai, fatar shi ba fara bace tas, amma tana da haske sosai, yana da saje a fuskar shi, haka dukkan jikinshi akwai gashi, amma basu cika cika ko tsayi sosai ba.
Akwai shi da kwarjini idan ka kalleshi, bashi da yawan magana barkatai musamman inda bai da sanayya ko sabo da mutanen gurin, amma yana
da hira harda zolaya indai ka mishi farin sani. Bai bata lokaci sosai wajen tsayawa kallon kanshi ba, ya fesa turaruka masu sanyin k'amshi, sannan ya fito, daga d'akin kawai.

Lokacin suma k'annen nashi sun gama shiryawa, sunyi kyau sosai, cikin shigar _blue black lace_, mayafansu mayalwata, baza,a ce sun fito da tsaraici ba. Sai kuma suka b'ige da zaman d'aukar photo.

_Wani abu game da Khady Abubakar shine, baya hana 'ya'yanshi mata zuwa biki, ko wani taro, indai har ya yarda da tsaftar mutanen, sai dai dole zasuyi shiga ta mutunci, wacce dama kullum cikinta suke, sannan ba,za,a barsu su tafi su kad'ai ba, sai dole ke da 'yar uwarki ko yayanki ko k'aninki. Sannan basa sakewa su haura k'arfe takwas na dare.

_Aganishi ka hana yarinya mace zuwa taron biki, kamar shiga hak'k'i ne da kuma bada k'ofar shigowar b'araka, don a yadda yaran yanzu suke muhimmanta biki, to idan ka hanasu dole su nemi hanya ko da bada saninka ba, har gwara ma a fita da saninka, kuma matuk'ar ka tarbiyyantar dasu yadda ya dace, babu abinda zasu yi na zubar da mutunci ko makamancin haka._

Yanzu haka ma sai da ukhasha ya nemi izini a wajenshi, sannan da k'yar ya yarda.

"Ku idan zakuyi biki kuyi iya ku mazaa, mana, amma kun hada har da mata."?

Ya sosa k'eya, "Akaramakallahu, ai na matan ne, gayytar mu sukayi.

"Ku bar angon ya je shi d'aya mana, tunda abin na mata ne."
Bashi da bakin magana sai yayi jim, kafin ya tuno abin fad'a, don baya son yawan tsawaita magana irin haka da Abban nasu, don ba,a nasara akanshi, sai dai idan yayi niyyar abu kawai zaiyi.

"Shiyasa zan kaisu tunda an gayyace su."
" Zaka kai ku dai, ai har da kai kaima zaka ce zaka kaisu, kawai kun bata abu ne yanzu, mata na biki kuce sai kunje.. Shi ango ai da walima aka sanshi ita yake had'awa shi."
"Tuba muke, ranka ya dad'e."
"Yaushe ne kace."?
"Yaune da yamma.
"To Allah ya kaimu amma ba,za,a kai dare ba koh."?
"In sha Allah."
Ukhasha ya fad'a. Don yasan ba tambaya bace a wajen abba umarni ne kawai, yana nufin kada akai dare, don yasan partyn da aka fita, dayin magriba ai dole akai dare.
Cewar shi ta 👇
( _amma ba za,a kai dare ba koh."?_ ) Girma ne da kuma iya magana yasa yake umarni da sigar tambaya, Don babu mamaki idan sunyi daren kaji yana tuhumar su, ~_"Bance kada akai dare ba."_?~

K'ofar d'akin da suke ya nufa. Ya tsaya a bakin k'ofa "Kuyi sauri fah, ni na fito." Da sauri suka fito, suna zolayar shi, "Yaya anyi kyau fah.!!

_______________
Suna zaune a kan kujeru, a wani wajen shak'atawa, Bashir Hafsah Zainab Ameera da Mufida.

Idon Hafsah ne ya hango mata wata kamar idon sani a wajenta, ita da wani suke tahowa, cikin takun k'asaita, kayan jikinta kamar sa b'arke saboda kama tan da sukayi, babu ko mayafi a jikinta. Suna k'ara nufo su tana k'ara wayewa da wacece, nan ta hau tab'a Basheer tana nuna masa ita da yatsa, "Basheer, ka ga wata, wallahi Jamila ce, ba bari dama na dad'e ina nementa."

Tayi zumbur zata mik'e Bashir ya rik'ota, "Haba sister ki bari mana, ki daina nuna su, me zaki mata idan kinje."?
"Ka barni Bashir, baka san na dad`e ban ganta ba, nayi shekara biyu rabon da na ganta."
Zata kuma mik'ewa ya kara rik'eta
"Plz ki bari yanzu ba fa kamar da bane, ki kyaleta kawai, babu lallai ma ta kulaki."
Nan ta hau mishi magana fad'a-fad'a kamar zatayi kuka, "Don't you know for how long nake nemanta amma kuma zaka hanani, kasan me nake ji araina.. I hate Wannan rayuwar da Jamila take, bazan iya dinga zuba ido ina gani ba..

Yasan halinta da saurin kuka, don haka, ya shiga rarrashinta, "I'm sorry aunty ba hanaki zuwa zanyi ba, amma ki jira ita tazo kinga da alama ma ta ganki, kuma tunanin da kike akanta yana da wuyar yuwuwa yanzu fa, ba,a iya chanja mutum lokaci d'aya. Bata ce mishi komai ba ta mik'e ~_"Ai idan da alkawari ba zata ga Jamila ta share ba, ko a wanne hali take ciki kuwa._~
Shima dole ya tashi, yawa sauran k'annen nashi alamar su biyo su kawai, ya musu nuni da su dakkowa Hafsah jakarta.

Jamila na hango, Hafsah, ta rabu da wanda take tare dashi tazo da gudu ta rungume ta, sun nuna jin dad`in ganin juna kafin, Jamila tace, Ai ina ganinki sometimes street haka ko wani waje, akwai distance tsakanin mu that's why bana miki magana.

Hafsah dai bata iya cewa komai ba, sai murmushi, kallon Jamila kawai, take, gaba-d`aya ta chanja, idan baka mata kyakykyawan sani ba ba zaka gane ta ba.

Jamila ta miko mata waya, lokacin su Ameera sun k'araso inda suke, ta daga musu hannu, ga mamakinsu duk sai da ta ambaci sunan su, "Ameera Zainab, Mufida, sannunku."

Ta kalli Bashir daya tsaya can gefe, bata mishi magana ba, shima kallon nata kawai yayi, ta mik'awa Hafsah wayarta samin phone dinki anan, munyi magana naga kina sauri nima ina sauri.
Hafsah tasa mata, ai kafin tau
k'ara kalma d'aya Jamila tabar wajen tana d'aga mata hannu.

Hafsah tayi ajiyar zuciya, zainab tace, "Yaya is she your friend Jamila."
Hafsah ta jinjina kai, ba zata iya magana ba.
"Chab." Ameera tace.

Mota suka shiga Basheer, yaja bai yiwa Hafsah maganar Jamila ba sam, Hafsah kam gaba d'aya yanayinta ya sauya ya koma damuwa, tsoron Allah ya k'ara shigarta, wai Jamila ce haka, babu ko mayafi, wacce a da bata iya yawo Inba da hijabi ba."? Kishin hakan ya cika zuciyarta, bai dace ta zuba ido tabar Jamila haka ba, ko ba komai ada ta amsa sunan k'awarta, ita gashi ta zama wani abu, amma Jamila fa, sam abinda take babu mai alfahri da ita.
Take ta sawa ranta zata yi iya kokarin ta wajen dawo da Jamila kan hanya, ita kanta tasan abin yana da matuk'ar wuya aiki ne ja, amma kamar jahadi ne, to kuma babban k'alubalen shine rashin sanin ta ina zata fara."?

Su Bashir nata hira ita kuwa tsit kake jinta, yana kallonta ta madubi, sai yaji ta bata mishi rai ma. _Duk wannan sauyawar da damuwar akan mutum d'aya, da babu alak'ar kusa ko ta nesa yanzu Tsakaninsu, matar da take yin abu bisa saninta, kuma da hankalin ta da ilimin ta."? Mene zaisa ta damu kanta, tunda ita maiyi d`in tana ganin daidai ne._

_________________
UKhasha tuk'i yake sosai, yayi watsi da tsokanar da su fadwa ke mishi, shakiyan ci ne kala kala, _Wai gaskiya yaya tunda Yaya Jabeer yayi aure kaima ya dace, kayi tunda dama ku biyu kuka rage._ Yayi burus dasu baice musu komai ba. Yanaji fadwa na bawa maryam labarin, _Bahijja_ da ke sune a baya. Sukayi shewa harda tafawa, ya juyo rai a had'e.
"Bana son shashanci, Allah zaku fita daga motar nan kuna min ihu a mota."

Haha.. Dariya suka mishi, ya juya kawai ya cigaba da tuk'inshi..

Wani Uturn suka zo daidai, lokacin Basheer shima ya taho dake mik'ewa zasuyi street su, shi kuma ya riga ya taho, Allah, ya kiyaye aka d'an bigi bayan motar tasu kawai. Dukkansu parking sukayi, kafin Bashir ya k'araso shi har yazo inda suke, _"Yi hakuri mai gida._ Abinda Basheer ya fara fad'a masa kenan, ya daga mishi hannu, _"Bakomai bakomai, muyi hakuri duka._ motar taku batayi komai ba."?

"Eh.. Inji Basheer "Hope kuma haka." "Babu koma, ka dinga kula kawai k'anina"!!

Karaf idanunsu suka had'u dana Hafsah. Yaji wani shock, Tabbas Itace.
Itama fad'uwar gaba taji, _kamar ta sanshi fa._

Bashir na shirin juyawa zai koma mota, _Dan Allah k'anina kaji mana._

Basheer ya dawo da mamaki.
"Me kace."?
"Um.. K'annen nan naka ka taimaka min da d'aya."
Bashir ya kalleshi da mamaki.
Me yake nufi kenan.?
Yayi k'asa da murya don yasan tambaya yake shirin yi mishi.
Kaga bamu da lokaci kana sauri ina sauri, taimaka min da number.

Bashir yayi jim, kafin yace okay.
Ya sa mishi number, yayi saving.
Ya mik'a wa Bashir hannu sukayi musabiha, "Nagode sosai abokina."
Bashir ya shiga mota, shi kuma ya k'arasa inda yayi parking, ya buda motar, gaba-d'aya yanayinshi ya sauya zuwa sanyi, akan idonshi suka wuce, da alama su ba wajen bikin zasu ba.

Yayi amanna Allah ne, ya dube shi ya k'ara had'a su. Su Fadwa sunyi mamakin sauyawar shi lokaci d'aya.

Basheer kuwa ya tafi yana mamaki, mutumin nada kyan mu,amala, shifa aka bugawa amma shine ya fito...

Mufeeda ta ji bazata iya shuru ba tace, Yaya naga kamar kunyi exchange numbers da wancan."
"Eh.."
Kawai yace mata, don bai son fad'ar dalili don baisan wa ya gani cikinsu ba, aranshi yaji yana fatan _Allah yasa Hafsah ce._

Da suka zo wucewa ma sai da ya d'aga wa Basheer hannu, sannan yaja tashi motar...

_Addu,a Kawai yake axuciyarshi Allah ya taimake shi akanta ta yarda dashi..._

📝
*HAJEEYA KHAREEMERH*

♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(masoyin k'warai )
*Cigaban littafin Zazzafan so*
*(Guba ne)*
💔💔
*By:*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh)*
*Dedicated to Unique in your love heart group members.*



📄 *46*



*Allah-Allah* yake ya dawo gida, ya kira number da ya karb'a, number da ko sunan mai ita bai tambaya ba.
Biki yayi dad'i sosai. Ango da amarya kowa na cikin farin ciki, anci an sha, sannan an sha rawa, gobe shine kai amarya.
Ko a wajen bikin ma kiran bahijja wajen uku, amma bai ji bama saboda k'arar kida bare ya d'aga.
Sanda suka dawo gida kuma, wajeny misalin tara na dare, shi kanshi shakkar shiga gidan yake saboda Abba bare kuma k'annen nashi. Babu yadda ya iya biki ne na aminin shi, ya kamashi ne sosai abin, banda haka shima ba son hayaniyar biki yake ba, kuma muddin baiga k'annen shi gurin bikin ba bazaiji dad'i ba, shiyasa yaje da su na yau.
Yana parking suka fito, shima ya fito, bai wuce ko ina ba sai d'akin abban dake gefe.
Da sallama ya shiga, amma ba,a amsa ba, sai akayi gyaran murya alamar ya shigo.
Ya sami guri ya zauna, yana jiran abban ya gama jan charbin da yake. Carbin k'ato ne irin mai dubun nan, Allah ya so ya kusa gamawa, yana kammalawa ya kalleshi.
Ai kafin Abban yayi magana Ukhasha yayi. "Afwan akaramakallah, bamu dawo da wuri ba, abinne ba,a fara da wuri ba.."
Ya d'aga mishi hannu kawai.
"Mun gode, Allah ya k'ara girma." Zai mik`e Abban ya dakatar dashi da hannu. Ya dawo ya zauna.
Yayi gyaran murya kafin yace, "Kaje kiran da Baffan yayi maka koh."?
"Wata fad'uwar gaba ta ziyarce shi, _Abba yasan da maganar kenan, indai haka ne toh dole ya k'ara k'aimi don idan har Abba ya fara sa baki a maganar abin bazai mishi kyau ba._
"Eh naje Abba."
"To madallah, sai ayi k'ok'ari tunda ansan aje na wasu.
Ukhasha ya sunkuyar da kanshi kawai, a zuciyarshi yana cewa, _Ai ni na riga na samu.!!_
"Za,a iya tafiya, Allah ya bamu alkhairi."
"Amin, Abba sai da safe."
Ya fita, shima kanshi sauri yake yaje ya gwada number nan.
Yana ta k'okarin kira amma kiran Bahijja dake ta shigowa ya hana sau biyu yana _rejecting_ ya gaji ya d'aga rai a b'ace yace, "Wai ke meye hakane, ki kyale ni da-Allah, haba.!!
Ya katse kiran, sannan ya hau kiran number, _is switched off ake ta ce mishi_ amma ya k'i yarda sai kira yake yana kumawa,
har ya gaji ya daina, gaba-d`aya yaji ranshi babu dad'i to ko dai alhakin yarinyar can ne da yayi wa tsawa, tunda yasan irin son da take mishi bai dace ya mata haka ba. Nan take ya yanke shawarar ya kirata ya bata hak'uri ko shima Allah zai taimake shi, don ya tabbatar indai bai samu number ba ayau to tabbas ba zai iya barci ba, yarinyar ta rikita shi lokaci d'aya, musamman yau daya k'ara ganinta, ai ji yayi jininshi na tafasa, gaskiya ba k'aramin al amari ne ya same shi ba.

Ya lalubi, number Bahijja, ya kira, ringin kad'an tayi ta d'aga tare da sakin ajiyar zuciya. Shuru yayi itama tayi shuru, shi har ga Allah tausayinta ke tsarga mishi a zuciya. "Me yasa bakiyi bacci ba.?
Kawai ya fara da haka. Cikin shashshek'ar kuka ta fara magana, ba kaine kace kada na k'ara kiraka ba."?
"Ya isa toh, kiyi hak'uri kece kika batamin rai, ina gaban abbana kina ta kira.
Murna ta cika zuciyarta, yau ita ce, ukhasha ke bata hak'uri."? Wacce irin rana ce yau data zo mata da sa,a haka."?
Yana ji a kunnenshi tana sauke ajiyar zuciya, ta ma rasa me zata ce.. "I'm sorry.." Yaji tace, kana jin muryarta kasan tana cikin farin-ciki, shi kuma zuwa yanzu ya k'agu ya kashe wayar.
"Ok, kiyi bacci kinji."
Yace mata haka, amma ita sam bata son su katse wayar, yadda take jin farinciki yau, sai ta b'ige da mishi shagwab'a. _Um..um._
"Kinga koh, meyasa haka toh ina miki magana sai ki k'iji, ni inason nayi bacci ne toh."
Sai kuma ta shiga hankalinta. OKey Dear ka hak'ura da abinda mamana ta maka."?
Cikin k'osawa yace mata yes."
"Thank you."
"Okay gud night."
Yace mata, tare da kashe wayar.
Ita kuwa farincikin daya sa mata Allah ne kad'ai yasan yawanshi. Tayi wani juyi akan gado cike da murna. Sai murmushi take, _Yau Itace ya nuna damuwa da ita haka.. Duk da ba yau kad'ai yake cewa ta daina kiranshi ba, amma tasan duk ranar da yayi mata irin haka, baya k'ara saurarar ta. amma yau shine har da biyo kiranta..? Gaskiya taji dad`i da alamun nasara sosai a tattare da ita.


Mamanta ce ta shigo, ta tsaya akanta, bayan ta k'are mata kallo, ta lura da wayar dake hannun ta tace, waya kike da wannan mara mutuncin yaron koh."?
Ta ke ta had'e rai, "mama please ki bari, stop abusing him, ni banga me ya miki ba fah!!
Uwar Tayi kwafa, "Hmm, idan an zage shi sai me, banzar yarinya kawai, idan bakiyi wasa ba, sai na k'wace wayar taki ma.
Yar ta juya mata baya tana k'un-k'u ni.
_Bahijja, yarinya ce wacce bazata wuce shekaru 19, ba, asalin yaren mahaifiyar ta Ibra ce, mahaifinta kuma, bahaushe ne, mahaifiyar ta basa tare da mahaifinta, sun rabu tun tana yarinya, kuma ta hana shi ita. yarinyar na da kirki sab'anin mahaifiyarta, bata dad'e da kammala karatun ta na secondary ba.

A tsarin Ukhasha da ra,ayinshi, sam babu irin yarinyar a rayuwarshi, yanayinta, shekarunta, yanayin tarbiyyar gidansu duk baimishi ba sam, abinda yasa ma mu,amular su tayi tsaho haka, saboda yana tausayin yarinyar, gashi shekarunta sunyi k'ank'anta ace tana fuskantar abu irin haka, ban da wannan da tuni ya yanke mu,amalarsu ko ta Yaya ne..
Kawai shi ya yarda kaddara ce ta had'a su.

_Wato wata rana ne, garin anyi ruwa irin na asubahin_ _nan, shi kanshi badon dole ba, da bazai fito ba a lokacin, amma haka ya fito aiki. Kuma ranar sai ya chanja hanya akan hanyar da yake bi, saboda yayi sauri yaje inda zashi don ya so ya makara. Akan hanyar ne ya gamu da yarinyar cikin uniform, tana tsaye bakin titi, ta rasa mota. Da kanta ta tsaida shi, ganinta da uniform yasa ya tsaya._
_Sai da ta shiga, sannan tayi mishi magana "Ina kwana.."? Don Allah can gaba zaka ajye ni, na rasa mota ne."_
"Okay, yace, mata bayan ya amsa gaisuwarta.
Hankalinshi nakan tuk'i, ya manta wayar shi akan kujerar da zata zauna ya bari, sai dai ya lura kamar ta d`auke wani abu sanda zata zauna.
Lokacin da aka k'araso makarantar su, tace masa ya tsaya anan zata sauka.
Ta mik'a mishi wayar, kawai yasa hannu ya karb'a.

Tana ta godiya.
Shine ma ya tambayeta sunanta,
"Babu komai, ya sunanki ne, tace _Bahijja_ "kaifa.? Yace "Ukhashatu."
Tayi murmushi ta juya tafi.



To tun a washegarin ranar, shi dai bai san ya akayi ba, kira yake ta shigowa wayar shi, da wata number, tun bai d'agawa har ya d'aga take ce mishi, Bahijja ce."
Tambayar farko daya mata shine, "Ina kika samu number ta."?
Tayi dariya kawai, tak`i bashi amsa, sai cewa tayi, "Godiya na kira nayi maka."
"Kada ki damu."
Yace mata.
"Zamu iya dinga gaisawa a waya."?
Shi kuma ganin ta yarinya, kawai sai yace, "Eh k'anwata amma sai kin fad'amin inda kika samo number.
A wayarka na gani.
"Hmm.."ki daina d'aukar wa mutum waya."
Tace "Toh.
"Kayi saving number."
Zanyi, sa anjimanki."
Tun daga ranar take kiranshi, watarana ya d'aga watarana ya share, shi bai kawo komai a ranshi ba, ganinshi yarinta ce , kawai. Bai ankara ba har sun shafe wata uku.
Lokacin tace mishi ta gama makaranta.
Yayi mata murna. Sannan tace, "Ko zai zo partynta."?
"Bana zuwa party.!!
Yace mata.
Tayi shuru bata yi magana ba. Sai bayan da ya manta, kawai sai gata a gidansu, abinda ya tada mishi hankali kenan, ya akayi tasan gidansu. Ta kirashi a waya, ka ganni k'ofar gidanku za,a barni na shigo."?
Yayi dariya sannan ya gimtse, "Idan kika ce wajena kika zo za,a barki mana.
Shi duk cikin wasa yake maganar.
Minti kad'an ya jiyo ta window d`in d'akinshi suna magana da Fadwa a harabar gidan.
Tambayar ta take, "Don Allah ina zata ga ukhasha."
Ita kuwa Fadwa cikin mamaki take ta jero mata tambayoyi, wanne ukhasha."? Anan gidan, ke wacece, bama gurin Zainab kika zo ba."? Dake taga ba zata wuce sa,ar zainab d`in ba.
Babu shiri yana jin muryarta yayi sauri ya fito, lallai yarinyar bata da hankali da gaske take kenan.
Ya rasa da fuskar da zai tare ta, sai kawai ya had'e rai, "Ke dama da gaske kike."? Ita kuwa murmushi take na jindad'in ganinshi.
_"Eh, ai nasan gidan ku dama."_
Bashi da lokacin b'atawa wajen tambayarta ~_"Tayaya.?_~

Kawai sai yayiwa Fadwa nuni alamar _taje inda zata._
yana gani tana kunshe baki alamar dariya take mishi.
Yayi kwafa azuci,
"To kije gida, kada mamanki ta nemi ki, kuma ki daina fitowa irin haka, mata basa zuwa wajen maza."
Ya fad'a yana kakkauda kai.
_"To gashi_ ta mik'a mishi, ledar hannunta. Bai karb'a ba ya tsaya yana mata kallon mamaki.
"Kayan party d'inne."
Nagode yace mata, rai a had'e zai juya ya barta

23 / 40