Chapter 35 Reading ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt Arewa Novels

ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt

Author :  KARIMA TIJJANI MANSUR Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   35 / 40

102K to 105K   out of 119.4K words

sai me."?
Cewar Hajiya Halima kenan cikin fushi.

Zai tanka mata, matar shi ta tsaida shi. Sannan ta bige da rokon sa kan ya fito sun zo da mota. Don ita damuwar ta shine ya fito daga cikin gidan.

"Don Allah Alhaji kayi hakuri kajira mu a waje yanzu zamu fito da ita din."
Dakyar ya juya zai tafi yana hararar Hajiya Halima.

Itama hararar ta jefa masa kafin tace, "kasani baka daki banza ba don wallahi sai na dauki matakin sharia kan ci muni mutunci da kayi har gida.!!
Cikin kaushin murya shima ya maida mata martani.

Ki kaini kotun koli!! Kuma indai baki barta ta biyo ni ba kada ta kara kirana ubanta."
Fatima ce ta hau mishi magiya.
Don Allah Abba ka fito kayi hakuri.

Ya juya ya fita a dakin.
Ya bar Halima tana ihun sababi.

Hajiya Salma ta sunkuya tana wa Basma nasiha duk da har yanzu bata san abinda tayi ba.

Hajiya Halima ta janye ta tana magana cikin gadara. "Malama zoki bar gidan nan munafuka asirin da kikayi yayi saura ki jira nawa martanin.."
Hajiya Salma tayi murmurshi, "Hmm Halima kenan ke kika san asiri da kike ambatarsa amma kiyi wa kanki fada yarki macece.!!

Bata jira cewar ta ba itama ta juya saboda bata son tashin hankali. Tana cewa Basma, Kibi mahaifinki dai Basma don da uba ake ado sannan aure shine darajar mace.!!

Tanajiyo Halima tana zaginta amma sai tayi murmurshi kawai don bata da lokacin ta.


"Bayan fitar su Halima ta koma gun yarta tana rarrashi tare da kara hure mata kunne tana kara nuna mata ubanta ya tsane ta ne kawai don an rabasu da ita."


Basma taji nadamar abinda tayi amma tana tsoron bin mahaifinta. Don ta daku a wajen shi.


Amma dukan da yayi mata yayi tasiri matuka wajen shigar da ita hayyaci har ta fahimci tayi kuskure sannan kalaman shi sun tsorata ta.



Su hajiya Salma kuwa, sunje gida cike da hikima take shawo kan mijinta har ya dan sakko sannan ta nuna mishi illar zuwa gidan Halima sannan ta taushe shi kan ya dinga yiwa 'yartashi addua.

Sai daga baya ya sakko har ya sanar da ita a binda Halima ta aikata.
Hajiya Salma ta dade da mamakin abin daga karshe ta nuna mishi kada ya damu.


___________________________


Hajiya Rukayya ta zaunar da Nour sosai take tausar shi..ta karanta mishi abubuwan da take guje mishi akan auren macen da bata yi dashi da kuma illar auren mace mara tarbiyya da kuma yar mace. Ta bashi misalai da dalilai kala-kala sannan ta shiga nusar she shi abinda take gudu.

_Nour ni mahaifiyar ka ce, ko kana son ka auri mace n da zata rabani da kai.."? Ya kalleta ta jinjina kai. Tabbas bakasan son mace yana rufe idanu ba har a dinga hango laifin uwa imma ta hanyar kissa ko kuma ta asiri."? Mata da yawa sun rabamu maza da iyayen su. Ko kana son a dinga wulak'anta min kai ko yaushe ka zama baka da kwanciyar hankali."? Wallahi na tabbatar idan ka auri yarinyar nan sai kaji dama baka aure ta ba tunda har abin ya fara da haka._ "Ka tuna fa yadda babu kunyar ido na ko naka amma ta bude baki tace bata sonka haba nour ai so ba hauka bane.. nidai ina rokonka kuma ina baka hakuri don Allah ka cireta a zuciyarka badon bana sonta ba ko don na hana sunna, sai dai don a zauna lafiya kuma in sha Allah, zaka sami wacce ta fita kaji. Allah yayi maka albarka ya baka mace ta gari.

Amin mama inji Nour.

Don bata barshi ba sai da ya yaji ya cire kaso mafi yawa na son Basma daga zuciyar sa. Don yana matuk'ar son mahaifiyar shi idan ya tuno d'awainiyar da ta sha dashi yana k'arami. Don yasha jinya typhoid data sarke shi yana d'an shekara sha uku. Sai da yayi shekara daya yana fama. Babu wanda ya zaci zaiyi rai ma.
Ya saki jiki sosai kuma ya tabbatar wa da mahaifiyar tashi cewa ya bar abin.

Don haka lokacin Abban ya tuntubeshi da zancen yana fada mishi sunyi magana da mahaifin yarinyar yayi hakuri ya cigaba da shirye-shirye kada wannan abin ya dame shi.

Nour ya gyara zama yana zayyanowa mahaifin shi jawabi.

_"Abba dama bansa damuwa ba.. kuma abbah ni nama hak'ura na janye._ ya fada yana sosa kai.

Alhaji Mukhtar ya tareshi da fad'a. "Menene haka Nour."? Ita hajiya rukayyan ce tace maka ka yanje."?
Nour yayi saurin girgiza kai.
"A,a Abba kawai na hakura ne, zan nemi wata kawai."

Haba Noura so kake ka kunyata ni."?

Bayan munyi magana da mahaifin yarinyar nan ma kana so ka maidani karamin mutum kaima koh."?
Nour ya girgiza kai. A a Abba wallahi dama na hakura ne kawai bana so ayi mata dole."

Cikin fada Alhaji Mukhtar yace, "to a wanne dalilin zaka hakura da tunda kuke tare ka taba cewa baka so sai yanzu. To ma ai saika saka hankali a zancen. Ita yarinyar anya ba tilas ta ta akayi ko kuma zuga ba."? Don da bata ce bata so ba sai yanzu."?
Nour ya gyara zama ya zayyanowa mahaifin shi abinda ke faruwa tun asali kuma ya fada mishi cewa dama bata aminta dashi ba mahaifinta ne ya yanke mata hanzari yace ya turo amma dama bata son shi."


Alhaji Mukhtar ya yi jimm kafin ya samo abin cewa.
"Eh duk da haka dai kayi hakuri za'a san abinyi sannan ya dace kaje dai ku sasanta kai da ita don fasa aure fa ba karamin al'amari bane."

Nour yasan mahaifinshi don haka ya amince zai je. Kuma dama yana son yaje yaga Basma face-to-face don ya tabbatar mata shima dan halak ne.



Washe garin da yaje gidan su Basma yadda Abbanta ya tare shi yasa sai da yaji tausayin mutumin sannan Abban Basma da kanshi ya dinga bashi hakuri har Nour yaji kunya. Yana fad'in babu komai Abba.
A take Abban ya fad'a mishi cewa tana gidan mamanta.
Sannan ya roke shi. Don Allah kaje kaji Nour ka dinga hakuri da Basma.
Sannan yace ya jirashi.
Ya shiga ciki ya fito ya mik'a mishi wayoyin Basma gashi ka bata kaji. Amma da sharadi idan har ta yarda dakai kuma ta baka hakuri.
Nour ya karba da hannu biyu yana wa Abba bank wana. Abban sai albarka yake sa mishi yana ta kara bashi hakuri, tare da gode masa sosai. Nour ya nufi gidan cike da kwarin guiwa.

"Babu musu Basma ta fito da kace ana kiranta don bata zaci Nour bane tunaninta yafi bata Yusuf.

Sai da gabanta ya fadi da ta taganshi. Kuma yayi mata wani kwarjini na musamman.

Ta tsaya tana fuskantarshi. Ya k'are mata kallo duk zantukan mahaifiyar shi suka dawo mishi kunne, _babu abinda Basma zata nunawa sauran mata._
Zuciyar shi ta raya mishi wai ace wannan ce zata wulak'anta mishi mahaifiya, take yaji takaicinta ya kama shi.

Ita kuma wani tunani ne ya tsarga mata a zuciya.

_Tabbas Nour mai tsada ne kawai son xuciyarta da kuma yusuf yasa ta kasa fahimtar hakan, bayan haka ma gidan su da ta gani ta sha mamaki bata zaci sunkai haka ba._

A hankali ta fara lura da kallon kaskancin daya fara yi mata.

Ta bude baki zatayi mishi magana. Niyyar ta ta kira sunan shi. Amma ga mamakinta sai ya dakatar da ita.

Cike da izza yace.
Bana buk'atar magana Basma ina maman ku."?
Tayi mamakin maganar amma taji sanyi aranta zatonta wani abin ya kawo Nour.
Ta nuna mishi ciki.
Sannan ta mishi nuni da su shiga. Babu musu ya bita yana murmurshi.

Hajiya Halima bata gane Nour ba ita dai Idonta ya hango mata Basma da wani yaro wanda da alama yana cikin jin dadi kayan jikin shi sun bayyana haka, haka fatarshi.

Ya nemi kujera shima ya zauna. Amma hajiya Halima tayi mamakin yadda baiyi yunkurin gaida ta ba sam.

Basma kallon shi take sosai tana mamakin shi.

Hajiya Halima ta saki murmurshi ganin ya bude baki zaiyi magana, don tana mamakin yadda take mishi kallon sani. To kodai Yusuf ne.!!

Ya kalli Basma sannan ya kalli maman ya fara magana.

Am yadda kuka je gida kuma kuka sanar so nima nazo na sanar.
Ya kalli Basma ido cikin ido.
"Da ina sonki tabbas amma ni ma yanzu sam bana kaunar ki, don haka kamar yadda kikace idan na aureki xaayi Batacciya so bama zan aureki ba bare ayi haka.
Ina nufin na fasa aurenki but kudin na bar miki. Sannan ya ciro wayoyin a aljihun shi. Ya dire su ak'asa.

Wannan sakon abbanki ne yace na baki idan kin aminta da aure na amma ni babu buk'atar ki amince a gareni. Saboda haka gasunan."

Ya mik'e bai kara koda Kalma daya ba ya nemi hanyar fita.

Hajiya Halima ta kasa motsi.

Sai da ya iya fita sannan ta miko hannu kamar me neman abu. Bakinta kuma ya bude.
"Am dama wannan ne Nour din."

Basma bata iya bata amsa ba ta mike ta bishi cike da rashin sanin dalilinta ma na binshi, kawai dai taji ta babu nutsuwa. Bata taddashi ba sai ihu da kurar motar shi.


Kamar ta rusa ihu haka ta dawo gida. Hajiya Halima taji jugum babu bakin magana. Bata taba zaton yaron da gidan su sunkai haka ba. Bata jin Yusuf zai nuna mishi wani abu. Sai taji wani iri a jikinta itama amma sai ta nuna bata babu komai a ranta, tayi murmurshi ta kalli tace. "Hmm ya ga dama ya baki wayoyin kenan."

Basma ta tamke rai, ko kallon maman tata batayi ba ta debe wayoyin tayi _bedroom_ don idan ta kalli maman wani takaici mara iyaka takeji. Kuma ta rasa dalili.

Ta bude wayoyin babu chaji sosai amma duk da haka sai da ta lalubi number da take matuk'ar buqatar kira.
"Ai kuwa an d'aga."

Muryarshi kamar mai bacci taji shi yana "Hello, wanene."?

Abin ya bawa Basma takaici matuk'a, take ta bude murya sosai sannan tace. "Wanene"?
Yusuf ni kake tambaya wanene."?
"Do you mean that you delete my number."?
Cikin murya babu tashin hankali yace, "Please kada ki dameni fa.. ni nayi losing contact naki and please mind ur own business naga aure zakiyi so ki daina kirana."
Niba aure zanyi ba idan ma zanyi bazan daina kula ka ba bare kuma an fasa."
"Hmm, ya wartsake daga baccin.
Yayi wata siririyar dariya.
"Hah..tell the dull, but not me."
Cike da takaicinshi tace, look Yusuf wai zanyi maka k'aryane.
Nooo I know baki yin k'arya..but forgot kawai da wani yusuf don yanzu ba dashi kike magana ba bye.!!
Ya katse wayar.
Ta cije dan yatsanta ta kifa kai kuka takeso tayi amma ta kasa, yau dai ta tabbata _loser_ din data kira Hafsah. Babu Yusuf babu Nour.

Ta rasa masifar dake bibiyarta wato tun data ga Nour a gidansu take jin wani abu game dashi bare kuma yanzu data kara ganin shi a yau kuma ta mishi kallon tsaf. Gaskiya Idonta ya rufe. Gashi shi wanda take komai domin shi ya riga ya gama yayin ta, bata jin zai kara sauraronta aikuwa idan hakane bazai yuwu ta kyale Haala da Yusuf haka ba, kuma tabbas dole tayi da gaske wajen ganin batayi _biyu babu ba_ Dole ciki ta samu daya ko Yusuf ko Nour.!!🤔

Kwanakin da suka biyu gabadaya uwar ta kasa gane kanta duk ta daina walwala kuma ta daina hira da ita. Tana janta ajiki amma taki sakin jiki dole ta zuba mata ido. Tana kiran Yusuf kullum amma gabadaya ma ya daina daga kiranta.. daga baya ma ta daina samun shi da alama ya sakata a blacklist. Tana mamakin yadda Yusuf yai mata irin wannan watsarwar kuma tanajin ciwon hakan a ranta gefe ga damuwar Nour da take neman zamar mata jaraba. Don ba karamin mamakin hakan takeyi ba ita kanta.

Abinda bata sani ba shine; "Shi Yusuf sam baya son abinda zai kara hadashi da ita don yana ganinta yake tuno Hafsah haka kawai, kuma yana tuhumar kanshi da Basman kan Musgunawa Hafsah, ga mafarkanta da yake ta faman yi yanzu a kullum. Gashi sam bashi da wata kafa da zata hadasu kwata-kwata don taki accepting friend request dinshi a facebook.



Maman ta taje har gidan Alhaji Yunus ta debo mata kayanta. Taji dadin hakan amma bata nunawa maman a fuska ba. Amma kuma tana tunanin abbanta aranta tasan ta mishi laifi kuma har yanzu bai sakko ba amma batayi tunanin neman gafarar shi ba sam.





____________________
Yau da wayar shi ta karya, cike da jin dadi ta d'aga tanajin nauyin shi.
"Morning madam." Yace mata.
Itama tace morning..
Ya saki dan murmurshi tare da cewa can't u call me oga.!!?
Ta danyi yar dariya itama.
Hmm bazaki ce min ba koh, saboda ba oganki bane ni koh."?
Tayi shuru.. uhum."?
Ya kara ce da ita. Sai ta girgiza kai. Kamar ya gani. Yace "Hmm, cikin rage murya yace Hafsah."
Tayi shuru bata amsa ba.
Ashe dama kishi me dake haka."?
Taji nauyin shi sosai.
Sai tayi yar dariya.
"Ai kin hukunta ni da yawa kinga nima bana kuma ba koh don Allah."?
Ya fada da wani salo kamar yaro.
Dariya ta danyi.
"Kiyi magana please kina min rowar muryarki Hafsah.!!
A hankali itama kuma da niyyar jan hankalinshi tace, "A'a fah.!!
Aikuwa tayi nasara don Ukhashatu har gyara zama yayi.
"To yaya ne uhum."?
Babu komai fah ta fada.
Thank you Hafsah na please ki so ni kinji."?
Taji ya fad'a a maraice.
Tayi jimm tana nazari. _me zata mishi me ya fahimci ta fada tarkon shi._

Bata gama tunanin taji yace please, don annabi (saw) badon ni ba.
A hankali tace "Okey don mind."
Yaji kamar ta sauke mishi wani nauyi don haka ya sami sukuni wajen kara tambaya.
"Please say you love me.!!
Ta sauke numfashi a hankali wanda har cikin kunnen shi zuwa zuciyar shi.
Please durling.!!
ya kara rok'a.
Cikin siririyar murya ta ce, "Okey I love you."!!
Yaji dadi sosai har da gyara zama sannan yace, please "say it again."!!
Tana so ta tabbatar mishi da son da take mishi don haka babu jira ta kara fad'a. "I love you.!!
Dadin kalmar yakeji akunnen shi kamar me don haka ya kara nema.
Once again dear.!!
Cikin shagwaba tace "Nooo sau it to me."
Babu musu shima ya fada da taushin murya nashi ma har da salon tabbatarwa. "I love only you.!!

Ta sauke siririyar ajiyan zuciya. Hadi da cewa thank you dear.!!

Yaji dadin godiyar.
Don haka yace _you deserve more dear.!!_ taji dadi sosai sai dai kuma wannan kalma yana daga cikin kalaman da Yusuf ke fada mata.
Amma ji tayi kamar yau ne aka fara fada mata.

Zaki fita aiki koh."?
Ya tambaye ta.
"Eh."
Okey kada nasaki kiyi late koh."?
Tayi shuru sai agogo data kallah.
Okey ki shirya my dear sai kin dawo please ki kulamin da kanki."
"Okey u too tace mishi."
Thnk you Queen bye."
Sukayi sallama ya katse wayar yana murmurshi itama haka.

_______________________
Abban shi ya kirashi sannan ya nemi karin bayani akan zancen daga karshe ya bayyana mishi komai. Abban ya nuna jin dadin shi kafin ya zarce da kalu-balentar shi.
Yanzu idan auren nan tazo cikin gaggawa ina zaka zauna Ukhashatu."? Tun da saboda haka nake nuna maka kayi gininka amma kaki.
"Afwan Abba bansan abubuwan zasu zo min haka bane."

Babu komai ai haka al'amarin Allah yake sai ku zauna a gidajen nan na estate ko baka so."?
Ukhashatu cikin ladabi yace inaso Abba an gode Allah ya kara girma."

Amin ya Allah
inji khady.



Duk wani shiri anyi shi angama su Abba suka tsaida ranar zuwa.
A ranar Hafsah babu aiki amma sai ta wuce gidan auncle abdullah don suna dasawa da matar shi sosai tana da kirki. Hafsah bata san dalili ba amma taga mama ta nuna tana son taje can din yau, duk da ta zaci ko wani sakon mama zata bata amma bata bata komai ba banda sakon gaisuwa.

Su kansu su Zainab sunyi mamaki da suka ji wai neman auren yayarsu za,a zo.

To dai anyi komai cike da mutunta juna, su Abban Ukhashatu sunzo don har da Abban Ukhashan saboda matuk'ar son da yake Ukhashatu.

Basu tafi ba sai da suka cake kudin aure kimanin naira d'ubu d'ari.

Basu tsaida rana ba dai amma a yadda suka tattauna abin bazai wuce wata uku zuwa hudu ba saboda kada Abbah ya shiga harkar zabe.

Yau farin ciki na dabanne wajen Ukhashatu, abbanshi, hajiyarshi da kowa na gidansu, haka abban Hafsah da duk yan gidan banda Hafsah da bata san abinda akeyi ba.

Bayan shigowar abbah cikin gidan shida yan uwanshi su biyu; sunyi suka gabatar da kudin ga hajiya Amina _maman su Hafsah._
Tasa albarka sannan tayi addua. Bayan tafiyar yan uwan Abba, Abba ya gargadi su Amira kan kada su shaidawa Hafsah halin da ake ciki a waya su ta dawo shi da kanshi zai sanar mata.

Abban Ukhashatu sun tafi suna yabon karamci irin na su Alhaji Habeeb, adduar alkhairi kawai akewa juna.

Zuwa dare duk wanda bai san da zancen neman auren Ukhashatu ba a wanda da ya dace su sani to duk sunji labari sai fatan alkhairi ake kawai.


Ukhashatu jinshi yake kamar ango a ranar yayi godiya ga Allah babu adadi sannan yaji kwarin guiwar aiwatar da wasu abubuwa game da Hafsah wadanda ya dade yanaso ya aiwatar toh dama dama yake jira saboda kada aga ya zak'e ko ya wuce _makad'i da rawa._


Washe gari dai yayi niyyar fara bujuro mata da kudurin.


Ita kuwa bataji komai ba sai dai yawan faduwar gaba da ta dinga ji tana gidan auncle abdullah. Auncle yasan da zancen amma daya dawo baiyi wasu alamu da zasu nunawa Hafsah wani abu ya faru ba sai dai ya nemi data kwana tunda dare yayi mata kuma ta amince sannan ya shaidawa abbah cewa zata kwana.
Mamakinta a ranar sunyi waya da Ukhashatu har ta dinga mamakin yadda yake farin ciki sannan Kuma ya kirata da wani suna wai, _Amaryata!_

Bata kawo komai ba sai dai ta fuskanci cikin nishadi yake matuk'a kuma ranar motsi kadan taji yace, "Allah ya kai mu ranar aurenmu amaryata.!!
Ranar dai tasha ruwan kalamai da tarairaya.

Amma wani abin mamaki sai Washe gari daya kirata inda yayi mata wata magana da tasa ta fusata don aganinta bashi da hurumi akai..

Da safe ne misalin karfe 11:30pm.



Sun gama break ita da yan matar auncle da dansu guda daya Hamid ana ce mishi daddy sai yar da take goyo ita kuma sunan hajiya ne da ita wato kakar su Hafsah.


Tana kashinkid'e tana tunaninshi a lokacin. Abubuwa da dama take tunowa game dashi.

35 / 40