Chapter 32 Reading ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt Arewa Novels

ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt

Author :  KARIMA TIJJANI MANSUR Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   32 / 40

93K to 96K   out of 119.4K words

mufeeda koh."?

Shidai Bashir shuru yayi, Jamila kuma ta zuba musu ido bata son tasa musu baki.

Please Yaya ki zo dai jiranki ake."

Yana gama fad'ar haka ya fice.

Yana fita Jamila tayi magana.
"Ki tashi Hafsah, kinga may be ya dad'e yana jiranki, kinga _no wonder_ ma tun d'azun nan ma shi ya kiraki so kada yace kina mishi wulak'anci don ya biyo ki har gida."

Jamila ta mik'e ta d`auki Jakarta ta bud'e, ta zaro wani pink jambaki da powder nan ta d'azu.
Ta mik'awa Hafsah, Ki shafa wannan lipstick, zai miki kyau, wannan powder shima kuma ki rik'e yana da kyau.

Hafsah ta tsaya saroro tana mamakin Jamila.
Jamila tayi murmushi, ki amsa mana."
Ta ajyewa Hafsah a gefenta.
Nagode Jamila.
Hafsah ta fada, sannan ta d`auki jan bakin ta mik'e ta, Kalli mudubi.

Ta dinga murmushi ganin yacce tayi kyau matuk'a.

Ta dan goga Jan bakin tana murmushi azuciyarta tana godewa Jamila, don yau tana da burin ta yanki ukhasha da yawa.

Wow Jamila thank you fah, dama kefa kin iya kwalliya, amma wanna daurin like irin makeup artist ce
ke.!!

Ta bude drawer zata dakko mayafi.

Jamila tayi murmushi.

Hmm, H hameeed, da gaske d`in ita ce.
Hafsah ta juyo da mamaki.

Jamila ta jinjina kai, Hmm, H. Hammed sana,ar da ake zaton inayi ba ita nake ba yanzu, Allah ne shaida ta, shiyasa nace miki zanzo zuwa na musamman ina so ki bani shawara, inaso na inganta rayuwata nima."

Jikin Hafsah yayi sanyi ta matso a hankali ta kamo, hannun Jamila.
Sam Jamila batayi irin raunin da Hafsah tayi ba, Hafsah har kwalla ce ta cika mata ido.

Jamila ta lura, sai tayi murmushi kawai, ta yarda cewa a duniya bata da kamar Hafsah H hameeed.

"Ki saka kwalli mana."
Jamila ta share zancen da fad'ar haka.
Hafsah ta juya ta d'auka.

Jamila ta sa hannu ta d'akko turaren data gani cikin drawer, sannan ta rufe drawer da murfinta.

Aka kuma turo d'akin, wannan karon mama ce.
Fuska babu annuri sosai ta leko d'akin ta k'are musu kallo, Hafsah nasa kwalli Jamila tsaye.
Jamila tayi saurin cewa, "Sannu mama."
Lokacin ta bude baki zata fara magana.
Maimakon ta amsa ta sai kawai ta fara maganar ta.


"Ke Yaya ba cewa akayi kinyi bako ba."?

Kafin Hafsah ta amsa mata. Ta kalli Jamila "Yawwa."
Hafsah ta juyo.
Mama gani nan fah.
"Zo ki wuce toh."
Sannan ta kalli Jamila. Ki jirata kinji."
Aa mama nima ina sauri ne bari mu fita tare."

Mama bataji dadin hakan ba, kawai sai ta juya tabar musu d'akin.

Jamila ta fesawa Hafsah turare itama ta fesa.

Hafsah ta dakko takalmi a hannu suka fito.


Jamila ta durkusa da suka iso palour, "Mama, sai anjima.!
"To ki gaida gida."
Zasuyi gaba, mama ta kira Hafsah.

Suka fara tafiya sun fita kofar palourn har sun nufi hanyar waje, mama ta kira Hafsah.

Hafsah ta dawo tana mamakin kiran.

"Zauna kiji."
Hafsah ta zauna.
Mama tayi shuru, ta shiga wata sabgar ma.




















Kusan minti biyu, suna shurun.
Awaje kuma Jamila na tsaye.


Hafsah ta rasa dalilin kiranta da mama tayi, gashi bata mata magana ba kuma.

"Tashi kije ma kawai .!!
Mama ta fad'a mata.

Da sauri Hafsah ta mik'e ta fita.


Jamila ta tsargu da kiran da akayiwa Hafsah. Amma da Hafsan ta fito bata nuna mata komai ba. suka had'u a harabar gidan.



Ukhasha tun sanda Jamila tazo ta tsaya ya lura da ita, dake suna daga gefe shida Basheer.

Don ya hana Basheer tafiya sai janshi yake da hira.

Acikin hirar ne ya gane cewa Basheer k'anin Hafsah ne, kuma ya ji cewa Basheer ba anan yake karatu ba, kuma shima engineering yake karantawa.



Sannan daga baya yaga Hafsah ta fito, Basheer na ganin fitowarta ya mik'e yayi waje Ukhashatu sallama,
"Agaida gida yaya nah.!"
Ukhashatu ya tsaya yana kallon shi, "Haba aboki ya zaka tafi kuma."?
"Dama zani wani waje ne."
Ukhashatu ya mik'a mishi hannu sukayi musabiha.
"Okey thanks alot, zan kiraka in sha Allah tunda kayi swapping layin."

"Okey nagode ka gaida gida." Inji Bashir.



Hafsah niyya tayi da ta wuce shi, ta raka Jamila in yaso idan ta dawo taje wajenshi. Amma sai ta kasa samun nutsuwa da hakan.
Tana ji ajinkinta kallontan da yake. Kawai sai ta nufi wajen shi. Ganin haka Jamila ma ta bita amma sai ta tsaya daga can gefe.

Wani shudadden murmushi suka dinga yiwa juna, ukhashatu yaji zuciyar shi fes, kamar an wanke mishi, ganinta yake kamar wata sabuwa, yau tayi mishi wani kyau ne na musamman daya tafi da tunaninshi..

Assalamu alaykum.
Cikin sakin murmushinya amsa mata yana k'ara kallon cikin idanunta.
Hafsah ta kawar da kai tana murmushi.

Tana tsaye har yanzu. Ahankali taji yace "Queen!!
Ta amsa mishi da idanu.
Yayi mata nuni da kujera. Sai ta girgiza kai.
Ya kalleta cikin kwayar ido, cikin marairaice fuska yana neman dalili.

Tayi mishi nuni da Jamila.

"Kawata ne mun dad'e bamu haduba for years yau tazo min so zan dan taka mata ne."

Hafsah ta manta da ukhasha take magana, sannan kafe ta da ido da yayi yaja tayi saurin furta wad'annan kalaman babu shiri.

Ukhashatu ya lumshe ido a hankali, sannan ya zuba su can Wajen da jamila take. Hakika farkon tahowarsu tafi mishi kama da k'anwar babar Hafsah, amma da suka doso shi, xubinta da Yanayin shiga yasa yaji ya kori wancan tunanin kuma yaji yana bukatar jin wacece ita."?


Murmushin ya saki, sannan yace "Okey, kuma ba zaki kawota mu gaisa ba."?
Ya fad'a da zolaya.
Hafsah tayi murmushi sannan ta matsa ta kira Jamila.

Cikin yauk'i tazo amma yin tozali da idon ukhasha sai da yasa ta gyara tsayuwarta. Shikuma ya sami dama yayi mata cikakken kallon na seconni a lokacin.

"Sannu Barka da yamma."
Cikin sakin fuska yace "Barka dai."
Hafsah koh sai murmushi ta ke.

Daga nan Jamila ta nemi zata tafi, ta hanyar kallon Hafsah sannan batayi magana ba ta fara tafiya.



Hafsah ta d'agawa ukhasha hannu alamun yayi hakuri tana zuwa. Ta bi bayan Jamila tana murmushi.

A hankali ya sauke ajiyar zuciya. sannan a zuciyarshi ya furta k'awarta."?

Hakika dole yayi nazarin akan al,amran. Kada dai ace Hafsah nayi mishi rufa-rufa ne. Banda haka kawayenta biyu kenan wad`anda kana kallon su zaka d'ora zuciyarka _a layin shakku game da su._ Amma me yasa take ce mishi ta dad'e rabon da ta had'u dasu."?
Me take nufi."?
Anya bata zo da rainin hankali ba.?
Ita kanta tasan basuyi kama da qawayen kirki ba sam shiyasa bata son a ganta dasu, shine dalilin kenan daya sa take yunk'urin kare kanta, ko nisanta kanta dasu idan ya ganta dasu.!!
Ahankali ya furta, _dole na nemi sanin dalili._

Baya mata mummunan zato, amma baya jin zai iya zuba ido tana mu,amala da k'awaye irin wad'annan.
Amma koma menene to dole yasan dalilin daya sa take mishi k'arya.
_Na dad`e ban ganta ba for long ko for years!!_



Shafshaf Hafsah tayi sallama da Jamila hankalin ta duk yayi wajen ukhasha, suka tsayar da Matsaya cewa Jamila zata dawo idan ta dawo daga Dubai.




Yanayinshi ya d'an nuna sanyi. D fara,a ta nufo shi sai yaji sanyi cikin zuciyarshi, tabbas Allah ne yayi mishi gam da katar d`in samunta.. Hakika komai nata yayi mishi. Komai cikin nutsuwa da hankali..

Ahankali cike da kulawa yace mata "Sannu fah."
Muryar tayi tasiri wajen sata saurin amsawa tare da sakin murmushi.
"Yawwa ya kake ya hanya."?
Alhamdulillah hope ban katse muku hira ba.

Hafsah ta girgiza kai.

Noo, dama gaisawa ta biyo mukayi."

Okey, ya fada sannan ya kauda zancen da cewa kamar rad'a. Kinyi min kyau matuk'a, kina da kyau masha Allah."

Hafsah ta saki murmushin jin dadi.
Sannan taji ya kuma cewa, "Ai da gaske you're beautiful shi yasa kika burkita min lissafi.!!

Hafsah ta saki murmushi, tana dan sunkuiyar da kai.

Bayan dan shuru sannan yace, ya mum ya family."?

Suna lafiya lau.
OK so ya kike kema."?
Ya fad'a cike da kulawa wacce zaka karanta kai tsaye cikin idanunshi.

Ahankali tace "lafiya lau.!!

Alhamdulillah, Kinsan dole nayi taking care, na mai sunan Hajiyata.


Hafsah tayi murmushi, sannan ta gyara daidaitonta a kujerar.
"Sunan hajiyarka kenan.?
Yes my queen Hajiyata sunan ta kenan kuma tana so na."!!
Ya k'arashe zancen yana mata murmushi.

"Allah ya kara lafiya.
Ta fad'a a hankali shikuwa yaji ta tarr.

Cikin nuna jin dad`in adduar yace, "Amiin Queen."

Suka d'anyi shuru kafin Hafsah ta dan daga mishi hannu, please "Ina zuwa.!!
Ya girgiza kai yana kallon ta. Ta mishi alamun tambaya da ido.

"Please kada ki tashi.!
"Tayi murmushi, i'm sorry yanzu zan dawo.!!

Yaji dad`in kalmar _i'm sorry_ d`in data ce. Ya saki tattausan murmushi.
"To kije.!
Sannan ya cukune fuska kamar yaron da aka kwacewa alawa.πŸ˜€

Ta mik'e tana kunshe dariyarta.

Tana juya baya ya zuba mata ido yana k'arewa tafiyar ta kallo, _cikin nutsuwa take._ yana jin dad`in hakan har ta shige kofar cikin gidan.

Ita da mufida suka dawo, ta rakota da try d`in lemo, ita kuma ta taho da snacks da dambun nama..

Suka mishi sallama dukkan su, ya amsa, suka ajye a kan table d`in, sai faman bin hafsah da ido yake.

Mufida ta gaida shi.
Ya amsa cikin sakin fuska sosai.
Hafsah taja kujera ta zauna, ta d'anyi kafin ta dago da niyyar mishi magana.
Karaf idanunsu suka had'u dama shi kallonta yake.
Ta dan kalleshi na seconni itama, shi ko ko kiftawa baiyi ba, hakan ya bata tsoro tayi saurin k'asa da ido ta fasa maganar.

"Itama k'anwarki ce."?
Ta d'aga gira kawai.
Yayi murmushi.
Sannan yace, Hafsah.!!
Ta tsayar da duk tunaninta kanshi amma bata ko motsa ba bare ta amsa.

Ya dace kisan ko ni waye koh."?
Ta saki murmushin jin dad`in zancen.
Ya d'ora "Tun kafin ki gaji dani."
Ta sake yin murmushin dai.

Ya jinjina kai yes, amma kafin in fad'a miki sai kin amsa min wata tambaya.

Ta kalle shi cikin ido tana sauraren shi.

Cikin nutsuwar daya tattaro ya had'a da rage sauti kai tsaye ya tambaye ta.

Zaki aure ni"?... Ya d'an tsaya sannan ya k'arasa, don Allah ki fad`amin.
Ya saki hannayen shi ya ware su, "nayi miki kalar wanda zaki iya rayuwa dashi."?

Hafsah tayi saurin kawar da kai gefe, bata son wannan titsiyan nashi, yau wato bama a waya ba a fili yake mata wannan zancen."?


Sukayi shuru, sai iskar Yammar dake kad'a su.


"Please ki fad'amin. Don Allah.!
Hafsah ta yi ajiyar zuciya a hankali kafin tace, "Please ka bari mu bar wannan magana kashe lemon ka ga snacks nan."

Yayi mata murmushi, "Nagode da hidima. Sannan ya kalli abincin ya k'ara kallon ta, Babu abinda zaki bani nak'i ci, amma bani da nutsuwa idan banjin amsar tambayata ba please."

I will tell you ai." so take subar zancen a yanzu don haka ta fad'i haka.
"Okay you promised koh."?
Tana murmushi ta girgiza kai.
Hmm, Allah sai kin fad`amin. Ya fad'a sannan babu jira ya shiga zuba lemon a cups. Yau ma guda biyu ya zuba nata da nashi, ya mik'a shi gabanta sannan ya d`auki nashi ya fara sha haka, kafin ya fara had'awa da cake."

Kallonshi Hafsah kawai take yi da wani shauk'i. Kadan yaci ya koma ga dambun naman, ya fara ci yana mata hira.

"Mama na tana son abin nan, gaskiya yayi dad'i thank you my queen."

Ya d'ago ya kalle ta, "Kisha mana."
Ta girgiza mishi kai.
Why."?
Naka ne ai.!!
Nawa ne to ai nina baki."
Hmm, nima ai nina baka."

Baisan sanda ya sa dariya ba. _Dama tana magana haka kamar shi."?_



A fili yace, "Hmm kina da wayo... Kin fi ukhasha wayo.

Tayi murmushi itama.

Ya d`auki toilet paper ya goge hannunshi.
Bayan ya motsa bakin shi azuci yayi hamdala sannan ya zubo mata idanu.

Nagode Hafsah na, na gode da hidima, duk da ke bakya min karar na baki abu kici.!!
Tayi murmushi ta kawar da kai.
"Ai baka ci da yawa ba."

"Ya isheni, nagode, ganinki yana k'ara min koshi.!!

Suka yiwa juna dariya.

Kafin ya tattaro nutsuwa yace, "Hafsah.!!
Itama ta bada hankalinta kanshi.

Zan fad'a miki gaskiya tsakani ga Allah ina sonki, kuma ina son in aure ki...


Yayi shuru yana karantar yanayinta.

Kinyi min a matsayin mata komai da komai.

"Ni ba wani bane, haka mahaifi na, sunan mahaifina Khady Abubakar, yana aiki da ma,aikatar shari,a. Hafsah banyi zurfi a boko ba masters kawai gareni..Sannan ina aiki a wani company, civil engineering shi na karanta.!!

Ya tsahirta anan yana kallonta sosai, Hafsah tayi shuru ita dai, bata da dogon buri akan auren hamshakin mai kud'i, amma tana da burin samun miji wanda yasan darajar ta, wanda zai kula da ita.
A ganinta ukhasha zai iya hawa wannan matsayin.. Tabbas bataji makusa a tattare dashi ba sam.



"Ban miki ba ko Nayi miki."?
Ya kalleta da wani salo yana tambayar ta.

Murmushi tayi.
Indai banji amsa ta ba nan da gobe, to banyi miki ba. Ya fad'a yanayinshi na bayyanar da gaskiyar abinda yake cikin zuciyarshi.


Hafsah ta yi Jim, sai ta kau da zancen da cewa, "K'annenka nawa toh."
Ta bashi dariya ma, sai ya kalleta da murmushi, ke naki guda nawa ne.
Kai tsaye tace "Four.
Ya jinjina kai, "Tab ni kam tsoho ne.

Ta zuba mishi ido.
"Ni ina da ya ma."
Ya fad'a.
Hafsah ta tsare shi da idanu.

So take ta gane ko da wasa yake.

Sai taga ya nuno mata photon a wayarshi, sun d'auka shida wata akan kujera, 'yar wacce bazata wuce shekaru biyu da rabi ba, ta zagayo ta bayansu ta dafa shi.
Hafsah ta zaro ilahirin idanunta.

Sunyi kyau matuk'a, amma sai kishin macen kusa dashi ya hanata ganin haka.


Ta d`auke kanta, ukhashatu ya lura da yanayinta da ya sanya shi cikin wani nishad`i mara misaltuwa. _Ashe ana kishi nah."!_
Ya fad'a a zuciyarshi a fili kuma ya kuma hasko mata photon.
"Kinga mamanta."
"Bata kalla ba tare Allah ya raya.!!
"Amin Nagode.
Yace mata.

Sukayi shuru babu magana tsahon muntuna.


Sannan ta ji shi yana cewa, k'annena suna da yawa nine na uku a gidan mu.

Hmm, tace mishi kawai.

Kin zaci nine dan fari koh."?
Yace da ita, azahiri haka ne amma saboda takaicin shi take yasa tace, "Noo, ni bana raya kai na nawa ne a gidanku, kamar yadda banyi hasashen kana da aure ba.!!

Ba k'aramar jarumta ukhasha yayi wajen hana kanshi tintsurewa dadariya ba.
Kiyi hakuri, mantawa nayi ban lissafo miki da shi ba.
Takaici ya hana ta tanka mishi.


Suka k'ara yin shuru, sannan yace, kin gama service d`in koh.
"Um."
Amma naga kamar still kina aiki a wajen.

"Sun d'auke ni ne.!!
Ta fad'a mishi kai tsaye.
"Okay Masha Allah Allah ya sanya alkhairi."
"Amin."
Ta fad'a fuska babu annuri, tunda ta d`auke shi tun d'azu bai dawo ba.

My queen, ukhasha ya fad'a yana yar dariyar da ya rik'e.

Sai taji ya bata haushi ma.

Sun dad'e cikin shuru kafin yace a hankali, _ina sonki wallahi."_

Taji ya k'ara bata mata rai, Azuciyar tace, _k'arya ne.!!_
_Agurin Hafsah gani take Soyayyar mutum biyu bata had'uwa azuciya lokaci d'aya._

"Please ki fad`amin." Ya katse mata tunani da cewa haka.

A dakile tace mishi what."?
"You loves me, ba kin fad'a min ba rannan inaso ne na tabbatar."

Da k'yar Hafsah ta mayar da k'wallar da ta cika mata idanu.

Ukhashatu ya fuskanci raunin da tayi sosai don haka ya tausasa murya.

"Please inason naji don Allah please I love you my queen."

Maimakon ta ba amsa sai ta sunkuyar da kanta tana dan cije leb'e.

Ukhashatu ya shagala da kallonta a haka.

Kyakykyawar farar mace, komai nata madaidaici, ga yangar halitta komai cikin nutsuwa, sai raunin da yayi zuciyarta yawa, ga _k`i fad'i_

A hankali taji shi yana wata Siririyar dariya me jan hankali.

Ta d'ago a hankali.
"Kiyi hakuri na daina.!! Ya fad'a yana daga mata hannu alamun rok'o.

Bata fahimci me yake ce mata ya daina ba amma zafinshi da takeji bazai barta ta iya mishi magana ba.


Suka sake yin shuru dai, ya dakko wayar shi yana dannawa.


"Ki tura min photonanki please koda ta Whatsapp ne inason na dinga ganin ki Hafsah na.!!

Taji yace haka.

Bata tanka mishi ba.

"Ya share babin ya k'ara cewa, Ki fad'a min abubuwan da kike so da wanda bakya so."

Ya fad'a a k'ok'arinshi na kawar da wannan Yanayin da ta shiga, wanda a bad'inin zuciyarshi ba k'aramin kona mishi zuciya shurun nata yake yi ba, dauriya kawai yake, don yana son jarraba ta sosai.


"Bana son k'arya!!
Yaji ta fad'a kai tsaye baiyi zaton zatayi magana ba sam, sai gashi tayi cikin d'aure fuska.

Ya saki tattausan murmushi, yana girgiza mata kai, don yasan dalilin ta na fad'ar haka.

Nima haka Hafsah, bana son karya kuma in sha Allah ba zaki same ni maiyi miki itaba..

Ya tsura mishi ido, Shikuma ya d'aga mata gira, cikin k'asa da sauti yace, _"sai dai ina da zolaya.!!_

Ba tayi dogon tunani kan abinda ya fad'a mata ba, banda haka da ta d'ora wasu zantukan nashi a ma,aunin zolayar dayake yana dashi.
_Misali auren daya ce mata yana da.._


Hmm, tace mishi kawai. Sai ya kalleta itama ta zuba mishi ido sai ya b'ige da yi mata wasu dogayen zantukanshi masu sanyaya mata jiki.

Kiyi hak'uri idan a zuwan nan da nayi nayi wani abu daya bata miki rai, babu zuciyar da zan so in sata farin ciki kamar taki, sai dai idan ina tare da ke bana iya control d`in kaina, ina iya yin komai ne domin na burge ki, sai dai a samu akasin ke a wajenki ba abin burgewa bane, tunda ban kware wajen karantarki ba tukuna.


Nagode, da irin hidimarki gareni, amma ina son inji amsata ko da a waya ne, don Allah idan banyi miki kalar wanda zaki aura ba ki sanar dani.!!

Ta bi shi da kallo, shima ya k'ura mata ido.

Bari na barki kada na cika ki da surutu, Nagode Allah ya huci zuciyarki..

Lokaci guda ya mik'e itama sai ta mik'e d'in. Ji tayi zuciyarta na tafasa, sam bata tsammaci tafiyar shi yanzu ba,
Ji tayi kamar, hasken wajen ne zai d`auke idan ya tafi..


Bata ankara ba taji yana ce mata kiyi hakuri ki karb'i wannan, ta dawo da kallonta gunshi, kud'i ne sababbin 'yan dariya biyu, _wrapper_

Ta tsaya sororo tana kallon shi, kafin tayi yunkurin yin magana ya rigata.

Bance don kina da buk'atar su ba ko wani abin, sai dai inason na dinga kyautata miki nima da iya abinda nake da iko, kamar yadda kike min.

Ya ajjye su akan table d`in sannan ya daga mata hannu yana murmushi mai tsaya mata a rai.
"Bye bye.!!

Ya juya ya nemi hanyar shi ta fita ya barta daskare a wajen ta zubawa kud'in idanu....




πŸ“
*HAJEEEYAH KHAREEMERH*
[17/03, 2:54 p.m.] UMAIMA BASHEER: β™₯️β™₯️β™₯️β™₯️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so (Guba ne)*
πŸ’”πŸ’”

*By*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Khareemerh)*
*Dedicated to unique in your love heart*



*IN SHA ALLAH ZAN TAKAITA BOOK D`IN CIKIN 3PAGES. DALILI SHINE MUN KOMA MAKARANTA KUMA KARATU YA KANKAMA..*
_SAI AYI HAKURI DA YADDA LABARIN ZAI ZO ATAKAICE._πŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌ




πŸ“„ *59*



Ukhashatu na fita motar Abban su Hafsah na sako kai, don haka ya dakata aka bud'e mishi ya shigo, lokacin ita kuma Hafsah lokacin ta gaji da tsaiwar ta wuce ciki cikin sanyin jiki..



Abba yaga ukhashatu kuma ya yayi mamakin ganinshi tunda yasan ba abokin Basheer bane.

Sai da yayi parking ya fito, ukhashatu dake rakabe a gefe ya

32 / 40