Author : KARIMA TIJJANI MANSUR Category : Romantic Hausa Novels
suka had'a ido, duk sai suka kasa d'auke idanuwasu kusan minti guda, Aysha kuwa na gefe tana faman musu video, sun burgeta sosai'
Atare suka saki murmushi,.. Ahankali tace baby na baro su Abba, so let me go to them, "
Yai mata murmushi "Okey' ahankali ya zaro wata leda ya mik'a mata.
"Ta girgiza kai" shima ya girgiza mata nashi kan'
Aysha ta mata alamar ta karb'a ta amsa ta mishi godiya'.
"Thank you dear".
"You deserve it"
Ta mik'awa aysha, ta rad'a mata
"Ki "ajyemin, ko yaushe ne zan karb'a.
"Ok"
Suka taho taga alamun Yusuf ma biyo su zaiyi, ta juyo tace mishi, "Please dear, act like you were aysha's bros"
"Okay"
'Ya fad'a yana murmushi.
'Hafsah ta d'aga mishi hannu, ta k'ara sauri ta wuce ta barshi shida Aysha'
Tana isa ta saki fara,a Mama wai Ashe chanjen gift aka min shine teacher d'inmu yace nazo achanja min"
'Ta k'arashe maganar tana mik'awa abba kyautar" ya karb'a yana murmushi Allah ya sanya albarka"
'Sunyi hotuna sosai, ita dasu Abba da bashir, da wasu k'awayen nata, Aysha ma wajen nata family ta tafi, akabar Yusuf gefe yana kallon su Hafsah yana murmushi, can ya hango basma ya tafi wajenta'
'Sunyi pictures shida ita, tacewa mamanta yayan k'awarta ne.
Sai da aysha ta gama ta hango shi wajen basma aiko taje ta yafito hafsah, suka zo akayi pic en dasu, duk da Hafsah bata ji dad'in ganin shi, wajen basman ba, kuma dake basman 'yar duniya ce, sai ta dinga jan hafsan da hira, suna gamawa, suka wuce wajen su abba, aysha ta gaida mama da Abba, sannan yusuf ma ya gaidasu, gaban hafsah sai fad'uwa yake, mamakinta abba har hannu ya mik'a mishi, suka gaisa, Hafsah tace wa mama Mama wannan k'awata ce aysha" "Ok, Aysha angama school Koh "? Tace "Eh mama,"
"To Allah ya bada result mai kyau." "amin"
Aysha ta mik'awa Yusuf Wayarta, "Please yaya yi mana pics,
Ya karb'a yana murmushi, yai musu ita da su mama,
Sanan sukayi selfie a wayarshi shida Aysha da Hafsah"
'Shi dai Bashir baki ya saka don ya gane yusuf' lol
Abba yai wa Yusuf sallama to mu zamu wuce Allah ya sanya alkhairi.
"Amin dady"
Abba da Mama sun jera sunyi gaba yayin da ita da Aysha suna baya yusuf na tsakiyarsu ', cikin rad'a rad'a yake mata magana,
Please baby kizo partyn nan gobene"
No, bazan je ba?
"Why?
"Kawai.
"Ya Kalli Aysha "Please friend ki rok'e ta taje"
Aysha ta Kalli "Hafsah waike meye haka?
"Hmm, Aysha baki ji, me basma tamin bane, nan ta d'an rad'a mata"
Aysha ta jinjina kai "Ok, kinsan basma, kiyi ahankali dai" "Ok"
"Nima ta gayyaceni fa"
"Hafsah ta tab'e baki kawai"
Dai dai lokacin sunzo bakin gate, dake, a waje su Abba sukayi parking, har sun fita daga cikin makarantar su'
Yusuf ya d'aga mata hannu bye dear, naji dad'i yau sosai, kuma, zanzo gobe muje party"
"Please kada kazo dear kasan da akwai matsala... And please kada kaje party nan"
Yai murmushi,
"No baby dole ne wani yaje, because basma bazataji dad'i ba ke bakiyi attending ba nima haka"
"Hmm, ni dai bance kaje ba"
Sunzo daf da fita, saboda haka, ya d'aga mata hannu,
Itama ta d'aga mishi "Bye bye dear "
Thank you aysha"..
Aysha ma ta mata bye bye"
'Ta tarar da su mama har sun shiga mota, itama ta shiga, tana fargarbar, 'Kada fa Yusuf yaje wannan partyn gashi babu, damar su tsaya suyi magana, sosai..'
Ta hango shi yana d'aga mata hannu, sanda motarsu ta hau kan kwalta'...
*HAJEEYAH KHAREEMERH*
*CE*ππ»
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): β₯β₯β₯β₯
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
ππ
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to:* *Unique In Love*
*Heart Members*
π *27*
*Sun* isa gida cikin farin ciki, suna shigowa Mufida ta taso ta rungume Hafsah "Happy graduation yaya". 'Hafsah taji dad'i itama ta rungume ta "Thank you sisi na!"
'Mama ta shiga hidimar zuba musu abinci.. Yau girki na 'musamman' (special) akayi. 'Dama tayi shi tun kafin su tafi makarantar.'
'Bayan sun kammala ne, suka yi sallah, sannan kowa ya shiga yin tashi hidimar.
'Hafsah dai wanka ta shiga, bayan ta fito tayi kwalliya cikin sabuwar Atamfar 'Super Holland' tayi kyau sosai ko powder bata shafa ba.
Ta fito falo ta zauna shiru, shima d'in don kada Abba ya ganta babu walwala ne a cikin rana mai muhimmanci a wajenta irin wannan ya zargi wani abu.'
'Amma a b'adinin zuciyarta ('in side of her mind') abubuwane dank'are wad'anda suka sabbaba mata yin shiru.
'Na farko shine; Fargabar alak'ar dake tsakanin, basma da Yusuf, 'wacce irin mu,amalar girmama wa ce a tsakaninsu bayan, ta kasancewar basma k'awarta.. Da har zata sa Yusuf kasa k'in amsa gayyatar basma, bayan ita da take sanadin had'uwarsu tace bazata ba?
'Na biyu shine kewar 'yan ajinsu da kuma bak'in cikin rashin samun hanyar yin waya da Yusuf. '
Sai na uku tunanin makomarta a wajen Abba.. 'Yanzu dai tayi candy, tana zuba idon ganin ''Shin zai bata 'yancin rik'e waya da kuma na tsayawa da saurayi''?
'Cikin wannan dogon tunanin ne taji kiran Abba d'aga d'akinshi.. Tayi saurin mik'ewa ta nufi d'akin.
'Da sallama ta shiga , yana zaune akan carpet ta tarar da shi, ta durk'usa sannan tace "Abba gani" ya sakar mata fuska, 'Fiye da koyaushe a kwanakinnan.' "Yauwa yaya, yanzu anyi candy koh? An zama yaya sosai" tayi murmushi ya mik'e ya nufi, k'ofar bed room d'in cikin d'akin, mintuna kad'an ya dawo da leda ahannu, ya zauna a wajen da ya tashi, sannan ya mik'a mata ledar yana fad'in, "To ga gift d'in Abba shima" ta mik'a hannu biyu ta karb'a tana godiya, Abba an gode Allah ya saka da alkhairi"..
Ya amsa da "Amin yaya" sannan cikin nutsuwa yayi mata 'yar takaitacciyar nasiha.
("Hafsah yanzu kin girma fa, yanzu keya dace ki dinga tashin k'anne'nki su tafi makaranta ba ni ba ko mamanku." "Kuma kada ki ga kinyi candy ki sa wasa a ranki, yanzu lokacin da zaki fara karatu da kuma sanin rayuwa, saboda haka ki maida hankali don Allah, ki dinga addu,a kinji")
'Ta gyad'a kai "To Abba"
"Yawwa Allah ya miki albarka ya bada result mekyau"
"Amin Abba"
'Ya d'an nisa sannan yace,
"Ki bar batun party sai bayan exam ta fito za,a had'a miki babban party, kin ga sannan kin san matsayin jarrabawarki koh"?
'Ta gyad'a kai kawai'
Cikin nutsuwa ya sake ce mata,
"Yaya ayau naso in baki waya, amma na fasa, saboda dalilin da kema kin sanshi, amma zan duba na gani zuwa wani lokacin.
Bataji dad'in hakan ba, amma yanzu, sai taji tabbas cewa laifinta ne'.
'Ta kasa koda gyad'a mishi kai ne'.
Ya kira sunanta "Hafsah!"
Sai da ta amsa sannan yace yana nuna ta da yatsa'
"kada ki d'auka gama makarantar da kikayi ya baki damar yin magana da wani saurayi..ban baki wannan damar ba,.. Kada ki sake ki saurari wani, har sai kin turo shi ya ganni na mishi izini".. Kinji koh?
'Ta jinjina kai Eh" yauwa, to tashi kije'
'Sai taji duk jikinta ya d'anyi sanyi.
'Tana fita babban falo taji kiran mama,ta sameta a d'akinta, "Mama gani,"
Itama wani abu ta mik'a mata acikin wani d'an box akwati mai kyau, "Gashinan na happy graduation ne" taji dad'i sosai,
" Nagode mama" ta fad'a tana murmushi.
'Bed room d'in ta nufa, ta zauna kan gado, ta ajye kyaututan agefe, jinta take wata mai sa,ar iyaye, tabbas ta k'ara tabbatarwa kanta iyayenta na k'aunarta. Ta d'auki ledar Abba tana shirin bud'ewa, 'Mufida ta shigo da gudun, cikin wata 'Red gown' tayi kyau sosai,
"Yaya ki fito falo,"
Hafsah ta zaro ido Menene?
Tayi murmushi tana d'an rawa da k'afarta alamar a k'age take, ('She eager')
"Surprise ne"
Hafsah ta mik'e.
Yaya ki chanja dressing, ta fad'a tana shigowa cikin d'akin sosai, ta bud'e drawer ta dakko wa Hafsah, wata T. Shirts purple sai wani wando light pink Hafsa tasa da sauri, tana son taje taga Menene'?
Tayi sauri tayi d'auri me kama da turban, akanta da wani purple d'in d'ankwali, ta nufi wajen dressing mirror ta fesa turare, sannan suka fito.
Bashir, duk k'annenta ta gani, sai abokin bashir na'eem, sai wata k'awar Zainab dake a mak'otansu Nusaiba',
Tsaye suke sun kewaye table d'in dinning, sun d'ora cake akai.. Suna ganinta suka hau ihu happy graduation' suna tafi, ta shiga tsakiyarsu ta tsaya, suka yi photuna da wayar Mama, sannan aka fara irge "5..4..3..2..1.." Ita da Mufida suka rik'e wukar sannan suka yanka, sannan akashiga ci, ana b'ata fuska da cream, sai da suka gama sannan suka yi wasu photunan a wayar Abba, sai lokacin daf da magariba sannan suka gama, domin wak'a suka kunna a speaker na falo sukayi ta rawa isu-isu'
Hafsah yau farin cikinta babu misali, har ta manta da wani tunanin yusuf gaba-d'aya bayan sunyi sallah aka dora da kallo, ko bed room, d'inta bata shiga ba, sai wajen 11:00pm, kowa ya mik'e don yin bacci.
Hafsah ta shiga toilet tayi wanka, ta saka rigar bacci sannan ta kwanta. A gajiye take sosai don haka ko takan gift en abba da Mama batabi,ba bare kuma wani tunanin Yusuf, bacci yai gaba da ita'.
Da safe ta tashi fresh babu wani tension sai bayan, sun karya ne, sannan ta dakko kyautukan nata.
'Na Abba ta fara bud'ewa, 'wani agogone mai kyau na mata, sai takalmi akwalinshi goalding color ya had'u, sai wani tsadadden turare.'
Taji d'adin kyautar sosai, tana murmushi ta bud'e box d'in Mama, wani zob'e ta gani mai kyau d'an k'arami.
"Thank you my parents!!
Ta furta a fili.
'Da yamma tayi wanka cikin b'akar after dress da d'an mayafi, mama tace zata aikata wani gida cikin layinsu ta karb'o mata turaren wuta da Matar take siyarwa, ta fito ta nufi gate, aiko tana bud'ewa tayi gamo da Yusuf tsaye jikin motar shi, yayi kyau fiye da duk ranakun data tab'a ganinshi, ta dafe k'irjinta sanadiyyar bugawar da yake, shi kuma sai wani murmushi yake yi na farincikin ganinta cikin sauk'i.
Cikin tsoro ta k'araso babu ko sallama bare sannu da zuwa ta fara mishi magana cikin tsoro, " Haba dear kafa san abba ya hana, yanzu ni aikena akayi".
Ta fara tafiya, gudun kada Tsautsayi yasa Abba ya gansu.
'Shima binta ya fara yi abaya, ta tsaya, sannan ta d'an juyo ta kalleshi, shi kuma ya hard'e hannayenshi a k'irji,
"Please ka daina bina kaji, ka tafi"
"No, bazan tab'a tafi ba, zan raka ki ne"
Tayi shiru, sai kuma ta cigaba da tafiya, shi kuma ya cigaba da binta har zuwa gidan da zata.
Ta ca ke a k'ofar gidan, shima ya tsaya yana fuskartata, ahankali ta fara magana.
"Dear please Meyasa kazo?
"Hmm, baby ko welcoming nawa biki yi ba kin namin abu kamar baki son ganina koh"?
Tayi shiru, sai taga rashin kyautawarta'
Atak'aice tace "Am sorry you're welcome dear, please ka daina cewa bana farinciki da ganinka,.. Kawai ina tsoron Abba ne, yanzu ma Allah ne ya sa mama ta aikeni, da aikawa zakayi kirani koh? Ya jingina kanshi yana murmushi "Of course"
Ta sauke ajiyar zuciya, Ok"
Suka d'anyi shiru sannan yace am baby nazo ne muje party kinga nan da one hour ne za,a fara."
Ta d'ago ido ta kalleshi suka had'a ido ya kashe mata ido da'ya.
Ta girgiza kai baby nace maka bazan je ba fa".. Kuma nace kada kaje kaima please,"
"Hmm, Meyasa?
Kawai bana son kaje, ta fad'a tana d'an had'e rai"
Yai dariya, "Haha ke dai kada kije, amma, ni zanje"
Sai taji maganar ta b'ata mata rai'
Ta jinjina kai,
"Ok thank you"
Ta shige cikin gidan ta barshi tsaye'
_'Ni ko nace Hafsah dama Yusuf na yin laifi'_π€π
'Tayi sallama sanan ta shiga cikin falon gidan, bayan sun gaisa da matar, ta bata sak'on sannan ta fito.. Yana tsaye har lokacin, yana ganinta ya nufota "please baby, kizo muje."
Ta yi mishi wani kallon tuhuma "No bazan je ba, ka wuce kawai"
Yai ajiyar zuciya "Hmm, ok,"
Ta fara tafiya, shikuma ya biyota don dakko motarshi dake k'ofar gidan su'
Ta juyo ta d'an tsaya ta kalleshi, sai b'acin ranta ya k'aru, taga ya mata kyau sosai, to meye na dole sai yaje wannan party?
Cikin b'acin rai tace mishi, tunda kace sai kaje, to kaje d'in, kuma kada ka min magana a hanya'.. Sannan na gode da abinda kayi min."
Ta na kaiwa nan tayi saurin wucewa ta barshi.
"Hafsah..baby.."!!
Yai ta kiranta amma taki koda juyowa, bashi da zab'i illa ya bita a baya.
'Tafiyar kurame sukayi har zuwa gidan su Hafsa. Ya tare mata hanyar shiga ita kuma ta tsaya cikin fushi da kuma tsoro tana kallonshi, cikin nutsuwa yace,
"Am sorry baby, kiyi ha'kuri don Allah".. Basma is important to us, ki bari naje please"
Takaici ya rufeta, ta d'aga mishi kai, kawai, wanne irin hali ne dashi, tana nuna mishi bata son abu amma shi kuma ya dage yana wani nuna mata important'
Ya d'an matsa mata ta rab'a cikin gate d'in, ya kirata a hankali "baby"
Ta kalleshi da ido kawai, ahankali yace "Bye Bye"
"I love you" sannan mata sassanyan murmushi wanda ya tsaya mata a rai har taji ya sakko mata da k'wallar kewa da kuma kishi'.
Ta d'aga mishi hannu kawai duk da tana jin zafin shi shima ya d'aga mata suka d'an b'ata lokacin kallon juna, sannan tunanin kada Abba ya zo ya ganta, ya fargar da ita ta wuce ciki babu shiri.
Shi kuma ya shige cikin motarshi cike da nishadi'..
*Hajeeyah Kareemerh ce*
ππΌππΌππΌ
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): β₯β₯β₯β₯
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
ππ
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to: Unique In Love Heart Members*
*Much of love to you:*πππππ
*"My Namecy ina yinki irin sosai d'innan fa,(KARIMA TIJJANI ADAM")* *Kina k'aunar wannan novel.. Allah ya kawo mj na gari musha biki..* ππΌππΌππΌππΌ
π *28*
*Ba* wajen partyn Ya nufa Kai tsaye ba. Don sai k'arfe 7:00pm za,a fara. 'Dama yazo ne da niyyar idan yazo su d'an fita shak'atawa daga nan sai su wuce wajen partyn.'
'Sai daya gama yawonshi, sannan ya nufi wajen partyn, gefe guda kuma da kewar Hafsah zuciyarshi. 'Yana jin dama da ita zasu je.'
'Hall (D'akin taro) ne mai d'an girma, wanda yasha decoration, an sanya kujeru da table aciki. Ya tsaru kuma yayi kyau sosai.
'Yawancin wad'anda suka halarci taron, matasa ne, maza da 'yan mata.. Anyi shigar peach colour da blue, sunyi kyau sosai.
'Anata surutu, ga kuma kid'a da yake tashi na slow music. 'Har zuwa lokacin da ita uwar gayyar ta iso, ita da wata k'awarta 'Jalilah'..
'Daf da zasu shigo cikin hall d'in ne, aka tsaya da kid'a, sannan 'MC' ya sanar da isowarta.
'she's coming, she's approaching, she's around the corner.. The big girl all over this hall.. 'Akayi tafi.. Sanan ya d'ora..
"I mean the one whose today is her day.. whose every one attended this party in honour of her... "Basma Yunus is coming...
'Akad'auki ihu da tafi.
'Ta had'u sosai doguwar wasu riga da (gown) wanda aka yi mata wata katuwar tsaga har zuwa guiwa, tayi kitson attach, tasha kwalliya sosai tasa dogon takalmi, suna rik'e da hannun juna ita da k'awartata da tasha wani makeken bak'in glass a fuskarta..
'Takowa suke cikin yauk'i da k'warewa, lokacin kuma, DJ ya saka musu Wak'ar 'Romantic' ta ('Korede Bello') har suka isa wurin da aka tanada domin zamansu..
'Daga nan ne kuma aka fara, gabatar da komai, ancashe sosai, inda Yusuf ma ba,abarshi a baya ba. Ansha rawa sosai.. Sannan aka nemi da ayanka cake, Mc ya fara sanarwa cewa, 'Hafsah itace zata taya Basma yanka cake'. Sunanta yasha kira a wajen, a matsayin best friend d'in Basma' (wannan tsarin Basma ne)
Shiru babu Hafsah.'
'Mc ya bud'e murya yana cewa, 'muna bada hak'uri bisa ita wadda ake magana, bata k'araso ba..
'Yusuf ya mik'e cikin takunshi na kwarewa, ya nufi wajen Mc, ya mishi rad'a a kunne. Sannan Mc ya maida speaker abaki ya fara magana cikin k'arad'i.
"Am tabbas naji
dad'i kuma wannan shi ake kira da 'True Love'.. 'Don Allah atafa mishi, nan aka hau tafi akan abinda basu san ma me akayi ba.' ('Duk cikin turanci ake magana')
'Bayan tafin ya lafa ne, Mc ya fara yi wa yusuf tambaya, kamar haka' (ya kara mishi loud speaker')
'What's your name'?
My name is Yusuf 'Bashir Imam'..
You're...??
Hafsah's
Boy friend.. Yusuf d'in ya amsa,
Nan guri ya cakud'e da tafi.. Da ihu.. Mc ya cigaba, " you came to.. ??"Represent my girlfriend who's the Basma's best friend."
Yusuf ya kuma bada amsa, nan aka hau tafi..
'Mc yace ' wato dai uzuri ya tare wannan k'awa ta basma saboda haka ta turo jaruminta, domin ya wakilceta, "kaii don Allah atafa mata.. Aka d'auki tafi babu k'ak'kautawa, fiye da minti biyu sannan akayi tsit kuma. A lokacin aka kuma gayyato wasu k'awayen basma su biyu, d'aya gefen Yusuf d'aya kuma gefen da Basma take.. Basma ce ta rik'e wuk'ar sai tattausan hannun Yusuf akan nata wanda hakan ya k'ara mata jin nishad'in taron. Sai kuma hannayen sauran k'awayen nata..
'Aka fara k'irge 1,..2,..3,..4,..5, sanan aka yanka cake enπ wanda aka rubuta 'HAPPY BIRTHDAY BASMA'
'Suna gamawa aka kuma rud'ewa da ihu da tafi, inda DJ ya saki Wak'ar 'Happy birthday to you..' Yusuf ya yanki' wani madaidaicin cake ya saka mata abaki.. 'Aka hau yi musu tafi.. Daga nan nan aka cigaba da shagali, aka cashe sosai. Yayin da Yusuf ya fita domin d'akko gift d'in da zai bayar daga motar shi.
'Bayan an tsagaita da rawar, ne aka fara gabatar da gift ga Basma.
'Ta samu kyautaka da yawa tun daga kan greeting cards, zobuna, agogoba, da sauransu, bayan kowa ya gabatar da nashi ne, aka nemi Yusuf daya gabatar da nashi. Gurin yayi tsit ana zuba idon me zai bayar...
'Suna tsaye shida ita suna fuskantar juna, yayin da idanuwan kowa ke kansu sai mai camera dake aikin d'aukarsu, sai kuma wasu daga cikin mutane dake faman d'auka a wayoyin su.'
'Mc ya juya ga Yusuf ya kara mishi abin magana, sannan yace, "Your words to Basma"..
'Cikin muryarshi mai d'adin sauraro da turancin shi, 'wanda ya kasance irin na 'yan asalin yaren, 'yace:
"Happy birthday,.. Wish you long life and prosperity'.. Happy birthday once again our friend...
'Taf Taf, aka d'auki tafi..'
'Sannan ya mik'a mata wani greeting cards da aka rubuta,
_'On your birthday I wish you much pleasure and joy;_
_I hope all of your wishes come true.._
_May each hour and minute be filled with delight,.._
_And your birthday be perfect for you'!_
_'Happy birthday to you'.._
'Basma ta sa hannu biyu ta amsa, tana murmushi, sannan..ya ciro wani akwatun zobe sai walk'iya yake, daga aljihunshi ya mik'a mata, shima ta amsa, akayi musu tafi, ahankali yace mata 'This is from Hafsa' .. Sai Basma taji wani abu ya tsarga mata a