Chapter 7 Reading ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt Arewa Novels

ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt

Author :  KARIMA TIJJANI MANSUR Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   7 / 40

18K to 21K   out of 119.4K words

kina nufi? "
"Calm down kasan yanayin ba da'ya ba, So I think my friend don't have interest about it"
"Hmm ok" Thank you"
"Kayi hak'uri fa"
No I know how to deal with her.
"Ok Gata to"
No ki rabu da ita.
"A,a dai"
"Ok"
Ta mik'a mata wayar.
"Hello,
"Hum, Hafsh me yasa kike min haka ne?
"Am sorry please I don't mean to hurt you my dear"
"Hmm, ok zamu yi waya to night."
"Bye"
Hafsah ta rungume "Basma thank you my friend"
"Me ya ce miki ne? kinsan wayar ba a hands-free take ba."
"No, ki share tunda yace komai ya wuce.
"Ok"
Hafsah dai wasai take jinta,sun shirya da Yusuf d'inta.
ina sonka Yusuf d'ina Allah ya tsaremin kai!!
Basma ta bita da kallo..
To da yamma bayan abba ya dawo daga wajen aiki gidan Hajiya ya wuce, bayan sun gaisa tasa aka kawo mishi abinci.
Yana gamawa akayi kiran sallar magariba yai al,wala,
"To Hajiyah daga can zan wuce."
A,a ka dawo dai"
"To Hajiyah.
Bayan ya dawo ya zauna a k'asa, yana fuskantarta, yasan da akwai maganar da zasuyi.
"Na dawo Hajiya"
"To madallah."
Dama cewa nayi shi wancan yaron da yake zuwa wajen Hafsah an daidaita ne?
Abba yaji abin banbarakwai,
"Wanne ake magana Hajiyah?
"Au to ,baku kirashi ba kenan."
"Wani yaro ne haka Mara k'iba. Shekaranjiya ya kirata a salularta (waya) ya zo ma nan sun gaisa."
Kan Abba ya kulle amma gudun kada Hajiya ta gane yace
" Oh to, eh saboda bata gama Makaranta, bane shi yasa"
"To yadai dace a tuntubeshi aji idan da gaske yazo."
"To za,ayi hakan Hajiya."
Yayi mamaki da Hajiya ta ambaci waya, amma don ya sake tabbatarwa sai yace.
"A wayarta kenan ya kira, sannan yazo Koh?
Hajiyah tace,
"Eh mana, kasan zamani cigaba yazo, da ya iso ma kiranta yayi ta fita."
"To Hajiyah ni zan koma."
"To ka gaida mutanen gidan."
"Allah ya kiyayeku Allah ya tsareku, daga mugun ji da mugun gani. Allah yai muku albarka."
"Amin Hajiya, Amin".
"Sai da safe"
"Allah ya tashe mu lafiya"
"Amin"
Abbah tuk'i yake amma gabadaya ranshi ab'ace yake, ya kasa yarda da abinda Hajiya ta fad'a mishi, yama za,ayi ayi haka? 'yarsa?..Hafsah?.. Ta mallaki waya bai sani ba? Ta dinga zance da saurayi wai duk bai sani ba?
Yasan tabbas da sanin mamanta.
Lallai zai nuna mata b'acin rai in dai haka ya tabbata..
Abin ya bashi madaukakin mamaki fa, inda badon hajiya ce ta fada ba zai taba yarda ba.
Wanne irin sakaci yayi har haka ke faruwa a gidansa??
Huci yake sosai da ya isa gidan. Mama na ganin yanayinshi tasha jinin jikinta...





.
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): β™₯β™₯β™₯β™₯
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
πŸ’”πŸ’”
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique In Your Love Heart Members.*




πŸ“„ *18*




Ahankali yayi sallama, mama ta amsa tana shirin mik'ewa ta karb'i jakar shi, taga ya nufi hanyar d'akin shi, tayi mamakin hakan.
Baya shiga d'akin shi daga dawowarshi, sai dai idan suna fushi da juna..
Ta Kalli yaran hankalinsu na kan kallo. Ta mik'e a sanyaye ta bishi.
Da sallama ta shiga, yana zaune akan gadonshi ya zubawa carpet d'in d'akin ido.
Ahankali ta nemi guri kusa da shi ta zauna.
"Sannu da zuwa"
Bai mata magana ba kuma bai d'ago ba.
Ta d'an sha jinin jikinta.
Ta d'an yi shiru, Mintuna kamar biyu sai tayi tunanin ta kawo masa ruwa.
Ta mik'e kenan ta fara tafiya taji ya kirata a hankali.
"Amina!!
Ta juyo ta dawo ta zauna wajen da take da.
"Me yasa kakai min haka?
Mamaki ne ya cika ta har yasa ta bud'a baki tace
"Menayi abban..
Ya tare ta cikin b'acin rai.
"Ok me kikayi kike tambayata koh? To
zaki fahimta idan na d'auki mummunan mataki akanku!!
😳
Subhaanallah ta fad'a a hankali.
Sannan ta kwantar da murya,
Haba Abban Hafsah, don Allah kayi hak'uri, Allah ya wuci zuciyarka."
"Hmm dole ki ce haka mana, amma fa kin bani mamaki wallahi.."
"Please kayi hak'uri don Allah, ka fad'amin Meyake faruwa?
"Hum"
Kawai yace.
Sai kuma yayi wani tunani.
'Ya lura ta kasa sanin meye laifinta, shi kuma ba shi da lokacin b'atawa wajen zaman fad'amata'
Don haka yace:
"Sai ki kirata tunda ai da sanin ki takeyin komai."
Ba zata ce bata fahimci da wa yake ba don tasan da 'Hafsah yake'
Ta mik'e cikin azama ta nufi d'akin Hafsah, abinda ya so firgita ta,
'waya ta ganta tana yi.
Ta Kai mata duka, ta sami wayar ta fad'i ak'asa.
Hafsah ta juyo a razane,
Maman ta watsa mata harara sannan tace,
"Sai ki taso abbanku na nemanki"
Hafsah ta razana da jin kiran.
Tuni ita maman ta fice.
Ko hijab bata sa ba itama ta nufi d'akin Abban.
Tayi sallama ta zauna.
Bata ga fuskar gaida shi ba.
"Ke waye ya baki waya??
Tambayar taso ta ruguza kanta kamar saukar aradu haka taji tambayar.
"Da ke nake"
Abban ya fad'a yana nuna ta da yatsanshi.
Hawaye ne ya fara biyo kankuncinta.
Shikenan yau ta kad'e. wacce k'addara ce ke neman afka mata Ayau.
"Zaki yi min magana ko kuwa sai nayi ball da ke a wajen nan."
Abban ya fad'a lokacin da yake kawo mata wani bahagon duka da hannunshi.
Mama tayi azamar tare hannun nashi. Abinda ya hana dukan sauka akan fuskar Hafsah kenan. Don la shakka daya sauka da babu abinda zai hana hak'oranta zubewa.πŸ˜³πŸ˜‚
Abba ya juyo a fusace, yana huci b'acin ranshi ya nunku, ya kalleta fuskarshi cike da b'acin rai..
πŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌ
*Am sorry kuyi haquri da wannan*
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): β™₯β™₯β™₯β™₯
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
πŸ’”πŸ’”


Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to :Unique In Your Love Heart Members.*
😘😘😘😘😘😘
*Kai jama,a, ni mai zance da masoya wannan novel ne??*πŸ€”πŸ€”
*Sai dai in gode muku kawai*πŸ‘ŒπŸ»
*INA GODIYA DA ALFAHARI DAKU INA MUKU FATAN ALKHAIRI.*
*KARIMA NAJI DAKUπŸ˜‡*
*ZAZZAFAN So NOVEL GROUP:*
🌹 ummu al,amen, Adam's Fudiyya, Maman affan, Ramcy, Hajara ayuba, Sarauniya Bilkisu.πŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌ
*UNIQUE IN YOUR LOVE HEART GROUP:*
🌹 Zeena Khalid, pure baby and the whole membersπŸ‘πŸΌ
*JIDDA TIJJANI NOVEL GROUP:*
🌹Deejah, Lawisa tanaskha, Binta musa salisu (Mamana), Maman Hanan, Nana Hauwa,u, juwaira lukman. And also Aysha Tukur (Maman Teemah and Ahmad)πŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌ
*RAYUWAR SUMAYYA NOVEL GROUP:*
🌹 ummu muhd, bintu muhd, Habiba abdul k'adir.
*SIRRIN MU:*
🌹 Ummu hibban 'yar baba, zaujatu muhibbuha, Mrs naseer.πŸ‘πŸΌ
*NOVEL ZAFAFA:*
🌹Mr Otu, sumyhala2017.πŸ‘πŸΌ
*MATAN AURE NOVELS:*
🌹SUA, Zeenah Khalid, pure baybee. πŸ‘πŸΌ
*NIDA K'AWATA FANS:*
🌹 Nadiya sadou, S ubanduma, maman umar, Aisha ya,u.πŸ‘πŸΌ
*KUNDIN NOVEL GROUP:*
🌹Zulaihart, Maman Hafsah, Khadeejah.πŸ‘πŸΌ
*TAURARUWAR MACE GROUP :*
🌹Sumayya hadi and Mami boy.πŸ‘πŸΌ
πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
*Am totally in love with you.. Kun gane ai*πŸ˜ŠπŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌ



πŸ“„ *19*



*Kafin* yayi magana ta riga shi,
"Haba, Abban Hafsah, don Allah d'auki al,amran nan da sauk'i."
Ya kalleta da kyau.
Ta karyar da kai.
"Don Allah"
Yayi shiru sannan ya dawo ya zauna.
Ya Kalli Maman.
Kinsan da zaman wayar?
"Nasani" a ta fad'a a tausashe.
Yaji zafin hakan sosai, don me zata dinga b'oye mishi, abinda ya shafi rayuwar 'yarshi. Yaso rufeta da fad'a sai ya tuna da 'yarsu a wajen..
Ya danne axuciyarshi. Sai fushin ya koma kan Hafsah da dama Itace mai alhakin laifin."
Afusace ya kalleta Yaushe ya baki wayar,? meya sa ma kika kaishi gidan Hajiya?...Wato ni ban isa ki kawo min shi ba koh? Hafsah har kin isa ki yi abu irin wannan bada izinina ba koh?
Hawaye suka biyo kuncinanta.
Meya sameta? tabbas tasan batayi wa kanta adalci ba.
"Abba Don Allah kuyi hak'uri wallahi bazan sake ba."
"Hum, hak'uri kike bani Hafsah?? Dama shi yasa kike sakaci da karatunki koh? Kika sa wasa a zuciyarki, saboda kina yin wani shirme can koh?..
'Tashi ki d'akkomin wayar stupid!!
Ya fad'a cikin wata tsawa.
Ta mik'e a hanzarce gudun kada ya daketa ta nufi d'aki ta dakko wayar.. Har yanzu hawaye bai daina zarya a kan fuskarta ba.
Ta durk'usa ta mik'a mishi da hannu biyu, ya karb'a ya ajye a gefenshi.
Mama dai tayi shiru, don babu damar yin magana.
"Kun dad'e dashi dama ban sani ba?
Abba ya jefo mata tambayar.
Hafsah ta girgiza kai.
"Magana zaki min,"
Ya fad'a cikin tsawa.
Cikin rawar murya tace, "A,a.
Abba ya kalleta sosai,
"Kice masa yazo ina son ganinshi"
Ba Hafsah ba har Mama sai da gabanta ya fad'i. Takai kallonta ga abban, yayin da shi kuma ya k'ara tamke fuska.
Sai ma ya kalli sashin da Hafsah take.
"Tashi ki bani guri"
Ta mik'e sum sum sum ta fita.
Shiru ya mamaye d'akin sai zuciyar kowa da ke sak'e-sak'e. Shi Abba jiran cewar Mama yake yayin da itama take jiran ya sauk'le fushin akanta. Sai kuma tunanin yau yasa taji kunya a gaban 'yarta, don basu tab'a haka ba agaban 'ya'yansu.
Can taji yayi ajiyar zuciya, had'e da juyo da kallonshi b'arin da take, itama lokacin ta kalloshi sai suka had'a ido.
Ya tsaya ya kalleta sosai, kallon daya k'ara raunana zuciyarta cike yake da tuhuma da kuma mamakin abinda tayi mishi, duk ta karanta wannan a idanunshi.
Ahankali tayi k'asa da idanunta, ta dafe kanta da hannu biyu.
Yace, Cikin k'aramin sauti,
"Amina!
Taji amma ta gaza amsawa.
Shikuma yayi shiru, tasan jiran amsawarta yake.
"Amina"
Ya fad'a a karo na biyu.
Muryarta a disashe tace. "Na,am"
Bai damu da rashin d'agowarta ba, ya fara magana.
"Kin san hali na, kuma kinsani idan nace 'eh' bana cewa 'a,a."
Ya d'an yi shiru sannan ya cigaba.
"Kinsan tsari na, kuma dake mukayi magana, ban fad'a miki kada ki bari hafsah ta kula wani yaro ba?? bance miki sai tayi candy ba?
Ahankali tace
"ka Fad'a"
To meyasa kika k'i bin abinda nace?.. Ko dan bake Allah zai tuhuma ba idan ta lalace koh??
Ta girgiza kai.
"Amina me kuke so wanda bazan yi muku shi ba?"
Ya d'anyi k'asa da murya.
"Idan kina son ta rik'e waya me yasa bazaki fad'amin ba.. Sai ki goyi bayan ta k'arbi abin hannun samari koh?
"To Allah ya gani dai ban hanaku komai ba!!..
Maganar daya fad'a ta k'arshe tayi wa mama zafi, sannan ta sa ta taji 'tabbas batayi dai dai ba..
Yau mijinta ne da kanshi yake fad'a mata wai ya fita hak'k'insu??
Kwallah ta cika idanunta.
Shiko bai k'ara kallonta ba ya mik'e ya shige toilet enshi ya murza key.
Bai sake mata magana ba tun da ya fito, kuma yak'i bata damar yi mishi magana ko hak'uri ne ta bashi.
Tana son ta fita ta duba 'ya'yanta tana tsoron kada ta fita ya kulle k'ofarshi, don tasa a ranta dole anan zata kwana.
Shine ma ya mik'e ya fita, dakunan yaran yasasu yin fitsari, sannan ya dawo falo yayi zamanshi.
Shiru Mama na zuba idon dawowarshi.
Sai can wajen d'aya 1:00am sannan ya tashi ya koma d'akin.
To Kwanan ranar dai haka sukayi shi babu d'adi dai...
B'angaren Hafsah kuwa kuka take yi gurshek`e..
Abubuwa ne da yawa suka had'ar mata, na farko nadamar zama silar samun sab'anin iyayenta, domin tasan da wayonta bata tab'a ganin hakan ba gabanta, sannan bataji dad'i Abba ya kamata da laifi irin wannan ba.
Na biyu kuma jimamin k'wace wayar ta da Abban yayi.
Sai kuma babban wato tunkarar yusuf da maganar abba.
Tunani dai shiya cinye rabin darenta.


β™₯β™₯β™₯β™₯ β™₯β™₯β™₯β™₯

Kwance yake akan gadonshi daga shi sai singlet da gajeren wando. Ya kwanta rub da ciki.
Wani tunanin shima yake yi daban.
Yana jin dad'in yadda yarinyar take sonshi sosai, shima kuma yasan yana sonta, amma matsalar yarinyar 'Local ce'
Yusuf kenan ke tariyo (tunanin) irin rayuwar da sukeyi shi da Hafsah. Abin na bashi mamaki wani lokacin kuma yana jin takaicin hakan.
Kamanninta ya shigo tunowa.
Kyakykyawa ce, shi dai ta mishi kyau! yana son komai nata, amma me yasa bata mishi soyayya irin wacce yake so?
Ta iya kalamai masu sanyaya zuciya (sweet words) ta iya kwalliya, ita d'in kalar manyan yara ce.
"Her smile kills me!
Ya fad'a a hankali.
Yusuf yana son ya samo musu mafita ne akan k'in yarda dashi da Hafsah keyi.
A ganinshi "zama cikin mutane d'aya masu yare d'aya, al,ada d'aya, addini d'aya shiya sa ta rashin wayewa. A ganin shi Hafsa nayin rayuwar _kifi acikin rijiya ne._
Matsalalolin ya kasa kashi-kashi da niyyar samo musu mafita.
Na farko shine 'Rashin yarda dashi da Hafsah keyi, wanda ya danganta shi da 'rashin wayewa'..
Yasani cewa fushinsa na rikitata, saboda haka ya d'auki aniyar nuna mata fushinshi a duk sanda tayi mishi hakan, tare da yi mata barazanar rabuwa da ita, har lokacin da zata bada kai...
Yayi murmushi samun nasara don yasan Hafsah bata da jarumtar jure fushinshi.
Na biyu kuma Rashin wayewarta da zama waje d'aya, mafitarsu a wajensa shine d'aukarta su dinga fita yawon shak'atawa lokaci zuwa lokaci.
Sai kuma sauran banbance banbance dake tsakaninsu wanda zai mayar da hankali wajen sace zuciyarta, hakan zai sakata zama daidai da ra,ayinshi.
*TSOKACI*
Sau da dama zama baya yiyuwa idan ra,ayi ko kuma hali bai zo d'aya ba, sai dai idan d'aya ya rinjayi d'ayan bisa ga bin ra,ayinshi.

Akwai banbance - banbance da yawa tsakanin yusuf da kuma Hafsah. Wanda silar su shine samun dace da iyayen kirki da kuma tarbiyya, sai kuma aka sami akasin haka daga b'angaren 'Yusuf'
Haka fahimtar da suka yiwa soyayya ma da akwai banbanci.
A wajen Hafsah ta d'auki soyaya ne irin ta saurayi da budurwa a matsayin : 'Musayar kalaman soyyaya a tsakanin masoya sai kuma kyautatawa da kuma sadaukarwa ga juna da kuma fatan zama a Inuwa d'aya wato 'Aure'
A wajen Yusuf kuwa yana ganin soyayya Itace farantawa juna da kuma zama d'aya babu banbanci.
'Duk da addini da al,ada sun nuna banbancin inda aka saka wani geji 'iyaka' tsanin Mace da Namiji a wajen mu,amala.'
To shi Yusuf bai ga wannan ba gurinshi ma idan dai 'True Love' ake yi babu zancen wani addini ko kuma al,ada kawai a zauna a bi ra,ayin zuciyoyi.
Domin a wajen shi 'Sacrifice' wato sadaukarwar da Hafsah ke ik'irarin tana masa ba ita bace, tunda ita ganin ta bashi 'Dukkan yarda' shine ta sadaukar mishi komai.
Shi kuma yana ganin idan gaske ne sadaukarwar tata ya dace ya gani a aikace ba ik'irarin da kalmomin baki ba. Shi yasa yake tantama bisa son da take mishi.
Rashin dacen Yusuf da iyayen kirki yasashi fad'awa cikin wannan hali da kuma gurb'ataccen tunani.
Wato tun yana yaro d'an kimamin shekara goma sha biyu, ya tashi cikin wata 'wahalalliyar rayuwa', wanda shi yasanta kuma zai kirata da wahala.
Wato iyayenshi kanyi wasu abubu
agabanshi wanda sun d'auke shi shi yaro ne. Ba ruwan su, kasancewarshi a kusa da su baya hanasu yin wani abu daya shafi mu,amalar aurensu.. Sannan yana zuwa gidan abokanshi 'Turawa' yana ganin yadda suke yi.
Tunanin shi ya kulle da son gano hakan menene? Amma saboda k'arancin shekaru ya kasa ganowa, sai lokacin daya kai munzalin wasu shekaru 15 -16, kuma akayi rashin dacen yana da yanayin buk'atar hakan sosai. Alokacin ne kuma ya bazama nema wa kanshi mafita.
Yusuf nada k'awaye mata a makaranta wanda suke mu,amala tare, kasancewarsu turawa sai ra,ayinsu ya dace da na juna.
Sukanyi mu,amalarsu kamar babu banbancin 'Jinsi' a tsakaninsu.
Yusuf a lokacin nada budurwa 'Jessica' wacce suke soyayyarsu ta yarinta.
Mummy shi ta b'ata bude Diary nashi wata rana.
Yayi rubutu a cikin abin gwanin takaici, wanda ita hakan ya burgeta.

*'My Love Jessica and I'*
Our first time kiss was at school garden..
Rubutu ne sosai yadda abin ya faru, tsaf mummynshi ta karanta, amma ta share abin tayi murmushi.
Wai d'anta ashe ya girma haka?? πŸ˜‘πŸ˜’
Da irin wad'annan abubuwa ne kuke ganin rayuwar Yusuf da Hafsah zata tafi a Inuwa d'aya bayan kuma gefe ga Abba na shirin kafawa ya tsare??πŸ€”
Anya ba ko dole wani daga cikin su yayi watsi da nashi ra,ayin ya bi na d'an uwanshi ba?
Idan hakane wa kuke ganin zai sauke nashi ra,ayin zuciyar YUSUF KO KUMA HAFSAH??πŸ€”πŸ€”
Muna Jiran ra,ayinku.
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): β™₯β™₯β™₯β™₯
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
πŸ’”πŸ’”

Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to :Unique In Your Love Heart Members.
*AUNTY KHADIJAH (MK MAKEOVERπŸ’„πŸ’‹)..GODIYA NKE,πŸ‘πŸΌ _KUMA MUNA BOOKING IDAN BIKIN HAFSAH DA YUSUFπŸ˜… YA ZO,_ KE ZAKI MATA KWALLIYA.*

Zamu hadu a page dinki na instagram #MK makeover.

*And also*
*D'AYA AUNTYN.*
*(AUNTY FATIMAH, MAMAN LITTLE MAMIE).. ALLAH Y A RAYA WANNAN BABY YA KUMA BATA GASHI IRIN NA FILLO KAMAR NAKI..*πŸ‘πŸ»πŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌ



πŸ“„ *20*



*Washe gari* da asuba, abban ne da kanshi ya shigo ya tashe ta, kamar babu abinda ya faru..
A al,adarshi 'knocking' dama yake mata sai kuma ya tabbatar ta tashi ta bud'e kofa, sannan zai wuce masallaci.
Gabanta ya fad'i lokacin da taji shi yana kiranta, amma kuma hankalinta ya kwanta da taji yanayin kiran, dama baya d'aga muryarshi da asuba..
"Yaya,..Yaya, ki tashi kiyi sallah."
Ahankali ta mik'e ta bud'e kofar.
Tun da yaga ta bud'e ya juya.
Tayi hamdala a zuciyarta bata son had'a ido da abban nata.
Akan darduma ta zauna bayan ta idar da sallah ta, tunano ta ina zata fara tun karar Yusuf da maganar abbah ta ke.
Gashi ya k'wace wayar bare ta kira shi. Ta mik'e ta bud'e wata jaka ta dakko zoben da Yusuf ya bata, ta dawo ta zauna.
'Tun ranar da aka koma makaranta ta karb'a a wajen Mama tace mata, zata mayarwa da Basma, shine ta boy'e shi.'
Ta kur'a wa zoben ido, tana tunano wanda ya mallaka mata shi, ahankali kwallah ta cika idanunta.
Allah ka taimakeni.. Allah kasa kada Abba ya rabani da farin ciki nah!!
'Idan na rabu da Yusuf na rasa komai.
Ta janyo Diary d'inta da yake akan 'Bed side drawer' (gefen Gado)
*'Together forever'*
_Our love is built up with scriface and devotion.._
_I will not let it be possible..!!_
_And.._
_I promise you to be
_with you forever no matter what difficult and challenges I'm_ _gonna face.._
" _I love you my_ _Yusuf!_

Ta rufe Diaryn ta ajye, sannan ta mik'e ta nufi kitchen wajen Mama, tasan ita ma babu dad'i ta kwana.
Maman tana kitchen d'in kuwa.
Tayi sallama tare da cewa,
"Mama,Gudmorning"Maman ta kalleta
"An tashi lpia"
"Lpia lau."
"Bari in fere miki dankalin."
"Ok kiyi sauri to, kinga kada ku makara a school."
"Ta k'ara kallonta.
Idan kin gama kije ki bawa abbanku hak'uri."
"To Mama"
Tana gamawa ta mik'e ta nufi d'akin Abban, gabanta na fad'uwa.
A tsaye ta tarar dashi a falon shi ya rataya jakarshi yana shirin fita.
Tayi saurin durk'usawa har k'asa.
"Abba barka da safiya"
Ta fad'a kanta sunkuye.
"Barka, dai kun tashi lafiya?
Ya fad'a babu yabo babu fallasa.
"Lpia lau.
"To madallah"
ya fad'a yana shirin cigaba da tafiya.
Ahankali tace "Abba, don Allah kayi hak'uri kaji"
Ya d'anyi murmushi.
"Hmm, yaya kenan kinyi laifi ne?.. Ba kina ganin abinda kika yi dai dai ba ne koh?
Cikin raunin murya tace.
"Wallahi Abba ba haka bane, don Allah kayi hak'uri."
Ya juyo, ahankali ya kalleta sosai, sannan ya dawo ya zauna.
"To Me yasa kikayi haka?
"Babu komai"
" Um, dama na nunawa mama fa wayar"
"Tambayar ki nayi me yasa kikayi haka?
"Um babu komai"
" To a ina kika sanshi?
Anan ta d'an fad'a mishi yadda suka had'u da Yusuf d'in.
Da yadda ya bata waya.
Amma bata fad'a mishi sun tab'a had'uwa a wani waje ba, sai ma ta nuna ranar da suka had'u gidan Hajiyah shine ganinta na biyu ita da shi.
Abban ya d'anyi shiru sannan, fara mata magana cikin nasiha, don ya fahimci ita take buk'ata.
"Hafsah ke har yanzu yarinya ce, baki san me duniya take ciki ba.
Ba wai ina hanaki yin wasu abubuwa bane da nufin k'untata miki..Kin manta ni mahaifinki ne?.. Ki daina tunanin zanyi wani abu da

7 / 40