Chapter 12 Reading ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt Arewa Novels

ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt

Author :  KARIMA TIJJANI MANSUR Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   12 / 40

33K to 36K   out of 119.4K words

zuciyarta mai kama da kishi..
'Kafin k'wak'warta ta dawo dai dai, tafin daya karad'e cikin Hall d'in ya fargar da ita, ta mayar da hankalinta kan Yusuf dake, mik'o mata kwalin wayar 'iPhone' ta zaro ido sosai babu shiri ta amsa cike da tsakanin farinciki, wanda kafin Yusuf ya farga ta rungume shi cikin nuna jin dad'inta.. Nan kallo ya koma kansu, kowa a wajen da abinda ya ke sak'awa, wasu na ganin ta burgesu, inda wasu ke ganin abin 'ban-barakwai', 'tunda wai shi d'in ba sunan saurayin basman yake amsawa ba, (Saurayin k'awarta ne') tambayar anan shine wane irin k'awance suke??...
'Tunda jikin su ya had'u, kowannensu tunane tunane suka had'arwa zuciyarsa..
'Ita Basma jinta tayi cikin wata duniya, da har ta manta gaban jama,ah suke.. Sanan tanajin aranta ta kusa samun Yusuf koda kuwa ta wannan hanyar ce!
'Shiko Yusuf abinda zuciyarshi take karanta mishi shine, 'wannan abin ne kawai ya rasa a wajen Hafsah, amma gashi a karon banza wata dake amsa sunan k'awarta tayi mishi, wai kawai don nuna jin d'adin kyautar daya mata, kuma a gaban jama,ah babu tsoron komai..? Kawai sai zuciyarshi ta shiga kokonton anya ma kuwa Hafsah na sonshi'..
'Sai ya fara kushe tarban da ta mishi ranar 'Graduation' d'inta. Domin tun ranar ya zaci samun haka daga gareta, idan ya mata kyautar bajinta, wacce ke cikin ledar daya bata.
'Niko nace, 'Yusuf ba sai idan hafsan, tama San meke ciki ba!'..🤔
'Tafin ya tsagaita yayin da Basma ta sakeshi a hankali, anan ne kuma aka saka musu Wak'ar da zasu cashe shi da ita, sunyi rawa sosai irin wadda ransu keso, kuma yanayin wayewarsu ta yarda da ita..
'Daga k'arshe dai, taro yayi wa kowa dad'i aka tashi ana nishadi kamar kada a tashi, wajen k'arfe tara na dare, sanan aka watse, sai 'yan tsirarun k'awayen Basma sai Yusuf da wad'anda baza,a rasa ba. An tattara komai na gift d'in driver daya kawo basma ya tafi dasu zuwa gida.. Yusuf ya d'an ya fitota suka d'an keb'e, ya fara bata hak'urin rashin halarta hafsah, har yana mata k'aryar cewa Mamanta ce babu lafiya. Basma ta d'an rage fara,arta da taji zancen Hafsah, abinda bai sani ba shine ita ai dama haka take so,' ta d'an daure tace mishi "Ok no problem'.. Ya d'aga mata kai sannan yace "shi zai tafi,"
ta kur'a mishi ido, 'Wanda shi kuma yayi mamakin kallon, har mamakin ya bayyana akan fuskanshi, sai ta kama kanta..
'Babu kunya tace mishi to su wuce mana, ya sauke su ita da k'awayenta tunda drivernta ya tafi yace mata..
"No problem"
'Suna tafiya cikin sassanyar motar tashi wanda sanyin AC ya sanyaya ga daddad'an k'amshi. Yanayin yana wa basma dad'i sosai, ji take bata tab'a yin irin wannan farin cikin ba tun da take a duniya.. Komai yanda ta so yakasance a birthday d'in haka ya kasance, 'dama cikas d'in shine zuwan Hafsah , kuma cikin sa,a bata zo ba.'
'Ita ce agaban motar sai kuma k'awayenta uku a baya, guda d'aya ce 'yar makarantar su wato 'Aysha daheer' wacce gulma ta sa ita ma ta tsaya har aka tashi, don so take ta kaiwa Hafsah cikakken bayani tun daga farko har k'arshe.. Shiyasa tana ganin su basma sun shiga motar Yusuf itama ta biyosu ta danna kai ciki, tace itama a sauke ta, tunda duka hanya ne'. Da yanayin Basma aysha, ta gane bataji dad'in hakan ba, amma ta share domin ganinta ba zai hana ta cika manufarta ba ayau.' Hakan basma ta sa aranta.
'Slow music ne ke tashi, sai hira jefi jefi da k'awayen basma na kusa da Aysha keyi wanda ko kallon juna basu yi ba, kasancewar babu sanayya a tsakaninsu sannan kuma kowa naji da kanta.. Aysha ta d'akko wayarta tana dannawa, amma ta kasa kunnenta sosai don jiyo abinda basma ke fad'a wa Yusuf.'
'Shi dai tuk'inshi kawai yake domin sauri ma yake ya je gida ya fara shirin zuwa club, domin zuwanshi gurin partyn nan da kuma abinda basman tai mishi ya saka mishi son halartar club d'in, ko ya samu wacce zasu jone, a daren.
'Cikin kashe murya Basma ta fara mishi magana, idonta na kan hannunshi dake tuk'i... Gaskiya na gode sosai fa' hankalinshi na kan titi ya bata amsa, "Kada ki damu aike, k'awan Hafsah ce"
Sai ta ji d`acin maganar aranta wato shi komai sai ya sako Hafsah aciki?.. Sai ta chanja hirar da cewa, "Gaskiya ka iya driving sosai. Yai murmushi sannan ya ce "Thank You"
Tayi wani fari wanda shi baima lura ba, sannan tace "Hmm, am yanzu ne kam dai dai time en da daddy na yace nima zan koyi driving"
Yace "Is good" ba tare da koda ya kalleta ban, domin shi baya buk'atar surutu a lokacin.. Don idan yana tuk'i baya son a mishi magana..
Ita dai Aysha idonta na kansu, yadda zata fi fad'awa Hafsah komai dai dai..
'Tayi mamakinshi shi da basman. Hira basman ta dinga d'an janshi da ita wanda ya k'ara bayyana mishi tabbas ita ce tsarin rayuwarsu yazo d'aya, wato hirar club da sauransu.
A'haka aka iso inda Aysha zata sauka ta musu godiya ta wuce cike da mamakin abubuwan.


'Sai da suka sauke kowa sannan yusuf ya kai basman gidan mamanta, wai sai ta buk'aci ya shigo su gaisa, da yaki' ya nuna mata yana sauri ne, amma ko me ya tuna oho sai ya wuce suka shiga'
'Wata hamshakiyar mace ya gani taci ado sosai ta hakimce akan kujerar falon, suna shiga Basma ta fad'a jikin ta, "Mummy wallahi duk na gaji fa!"
'Matar tayi murmushi "oh sorry baby ai kece kun ja abin da yawa. Ta maido da kallonta kan yusuf dake zaune shima yana kallonsu yana murmushi, "mum good evening" how are you? "Am Fine, how's family" they're fine. Gud'
Ahaka sukayi gaisuwar tasu, sannan ya mik'e tare da cewa "Gud night"
'Ta sakar mishi fuska sosai tana cewa "Ok bye bye ka gaida Mum"..
'Ita dai fa sun gaisa ne kawai, amma bata san alak'ar su da Basma ba, amma taji aranta yayi mata, kuma duk da bata barin 'yarta kula samari to tabbas zata iya barinta dashi domin daga ganinshi d'an manya ne'..
'Basma ta mik'e ta bishi sukayi sallama, wannan karon har da rik'e hannunshi su gaisa, ya tsaya shiru hannunshi cikin nata yana nazarinta sosai, tuni wani abu ya tsarga mishi cikin zuciya, ya zare hannunshi tare da yi mata murmushi, ya d'aga mata hannu alamar bye-bye ta tsaya har ya shiga mota tana kallonshi, ta saki ajiyar zuciya a hankali tana fatan Allah yasa sak'onnin data aika mishi ayau sun isa, kuma zasuyi tasiri yadda take so...
😇Muje zuwa dai..👍🏻👍🏻
*Hajeeyah Kareemerh*🍒
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔



Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to: Unique In Love Heart Members*






📄 *29*


*Lokacin* da Yusuf ya bar Hafsah kuwa tunda ta shiga gida jikin ta yayi sanyi, kawai sai taji tana buk'atar kad'aici.
'So take kawai ta keb'e tayi kuka, amma tana shiga gida bayan ta bawa mama sak'on ta juya da nufin wucewa d'aki, Maman ta kirawota, hakan yasa tayi saurin saita yanayinta ta dawo ta zauna, Maman ta kalleta cikin ido, sannan tace, "Ki je ki d'ora mana abinci kinji." Babu yadda ta iya haka ta mik'e ta nufi kitchen d'in, gabanta sai fad'uwa yake haka kawai takejin zafin Yusuf, saboda kafewa da yayi sai yaje Birthday d'in.. Sai wajen ana kiran magriba ta kammala, sannan tayi sallah, lokacin kuma Abba ya dawo, hakan ya tilasta mata fitowa falo ta zauna don ta lura baya son ganinta cikin d'aki idan ba lokacin bacci ba.'
'A dining sukayi dinner d'in, sannan 'Abba yace ayi musu tatsuniya, yana murmushi yace "Mama ce yau zata fara yi musu."
_('Abbansu Hafsah yana da wani ra,ayi: 'Wato ba koyaushe yake barin su kalli TV ba')_

Maman tayi dariya, sannan fara yi musu, ta tsuniyar "Na goma" duk sun nutsu suna sauraronta, har da Hafsan itama, sai da ta gama, Abba yace Hafsah tayi musu, tayi d'an murmushin kan leb'e, sannan tace, "Abba bashir yayi mana, ni sai na tuno wacce zanyi"
'Dukansu suka hau yi mata dariya, suna tsokanarta wai ta kasa.'
'Ita kuwa d'adi taji don sam batajin yin magana mai tsawo ko sauraron wani dogon zance a lokacin, sai da suka gama lokacin kuma baifi k'arfe takwas ba sannan Abba ya kunna musu 'Solar' kasancewar babu wuta, sannan suka saka wani tsohon film d'in ',(Home alone') suna kalla cikin nishad'i, hakan yasa hafsah taji d'adi sosai ta mik'e, 'Abba ya bita da kallo, sai ta kawo mishi uzurin cewa bacci take ji'
'Ya jinjina kai, sannan yace "Shikenan, kiyi addu,a," ya Kalli mama, ita ma ta kalleshi, itama ta karanta mishi nata mamakin', Na baccin da hafsah tace tanaji, a irin lokacin k'arfe takwas baifi da rabi ba'.. 'Abinda yaran sai k'arfe tara da rabi ko goma suke bacci, shima sai Abban ya kora su, saboda makaranta.'
'Hafsa ta kwanta shiru, ta takurawa zuciyarta kan dole sai ta gano, abin da ke tsakanin Yusuf da Basma.. Da har ya sashi kafewa kan zuwa birthday d'in don kada ran Basma ya b'aci.' Yadda zuciyarta ta karanta mata kenan..'
'Abubuwa da yawa zuciyarta tayi ta karanto mata wanda ita kuma gefe guda tayi ta k'okarin sai ta k'aryata hakan, don kada ta jawo wa kanta tarwatsewar farin ciki babu shiri'
'Da farko kawai ta sa wa ranta, Basma tace wa Yusuf 'Tana Sonshi ne..
'Sai kuma ta tuna a irin class na basma tana fad'ar cewa ita babu namijin daya isa tace tana sonshi'.. Sai ta sauya tunanin da cewa ' kodai kawai son kula maza ne da iyayi irin na basma yake jan hankalin Yusuf d'in zuwa ga kulata, ??
'Kishi ya baibayeta Wani b'angaren kuma na zuciyarta ya shiga rarrashinta, da nuna mata sam fa wannan tunanin ba haka bane, 'Idan ta lura da irin kallon da yusuf yayi wa basma ranar da suka fara had'uwa, sai kuma d'inbin soyyayyarta (ita Hafsan) da ke dank'are cikin zuciyarshi, wacce bata da kokontonta, idan ba lokacin da ta shiga rudu, irin wannan ba'..
'Da taga dai, ta rasa abin kamawa, sai kawai ta bari kalmomin Yusuf sukayi tasiri, itama zuciyar ta ta ta,allak'a abin da, 'Ganin kirkin basma da Yusuf d'in keyi, kamar yadda ya fad'a mata, wanda kuma hakan sanadinta ne ita Hafsan.'..
'Ta saki nannauyar ajiyar zuciya, sai lokacin taji dama-dama, sai kuma ta shiga nemawa zuciyarta hujjar da zata k'ara yarda da hakan.' sai tunaninta yakai kan ranar da yusuf d'in ya turowa Aysha katin 2000' wanda shima fa kawai albarkacinta taci don kawai, suna waya da wayarta.'
'Ahankali taji zuciyarta na hak'ura da lamarin har taji tausayin Yusuf d'in bisa mummunar fahimtar datayi mishi, take taji zuciyarta ta k'ara kamuwa da sonshi, taji kawai babu abinda take son ji sai muryarshi. Amma ina babu dama, hakan yasa ta tsunduma tunanin yadda suka rabu d'azu tana k'ara halarto irin kyan da ga yayi yau d'in...
'Ahakan har tayi bacci'
'Washe garin ranar Yusuf na kwance a d'akinshi da daddare, yaji kira ciki wayarshi, ya duba yaga basma ce, ya d'aga kiran tare da kai wayar kunnanshi. "Hello"
Takai k'arshe wajen kashe muryarta wacce ta yi tasiri sosai a kunnuwanshi tace, "Hi, ya kake"? Am fine" "Ok gud, ya gajiyar birthday yai dariya, "Hah babu gajiya kuke cewa koh"?
'Itama tayi dariya "Oh Na manta fa you're Californian.!" suka k'ara yin dariya, sannan ta mayar da muryarta kalar ta tausayi, kamar mai yin kuka tace, "Yusuf,..
"Na,am." shima ya amsa cikin taushin murya'
'Sai kawai ta saki kuka, hankalinshi ya tashi, ya rud'e ya hau rarrashinta, bai san ma me yake fad'a mata ba.'
"Am sorry baby, kiyi ha'kuri please calm down, ki fad'a
min make faruwa waya tab'a ki ko Hafsah wani abu ya faru"?
Sai da tayi kukan sosai sannan ta saita muryarta cikin shashshek'a ta fara magana, wanda shi yanayin muryar ya d'auki hankalin shi'
"Am na rasa wa zan fad'a wa, damuwata sai kai,.. Cikin nutsuwa yace "Mata ina jinki" tayi ajiyar zuciya sanan ta cigaba,"
'Saurayina ne kawai don kazo birthday kuma yaga yadda kayi treating ena shine yace wai ya rabu dani!! Ta k'arashe maganar cikin kuka"..
Yusuf yayi shiru, yama rasa me zaice, tausayin basma ya rufe shi, cikin in, ina ya faro magana, " Um, d.. Do youu mean kun rabu kenan"??
"Of course".. Ta fad'a tare da k'ara rushewa da kuka..' "Oh my God"!
Yusuf ya fad'a, to Meyasa? A wanne dalilin, wato kishi yake da shi kenan,?? Yama rasa me zaice, sai kawai ya b'ige da rarrashinta "please kiyi ha'kuri, kada ki damu, I know it will hurt, but kiyi ha'kuri in sha Allah zaku sasanta kinji..'
'Zuciyarta ta dugun zuma, ita ba haka tasoji ba, amma sai ta kanne kawai, tace mishi, " I told you mun rabu kuma bana jin zamu k'ara yin wata soyayya ni da shi, so just pray for me 'Allah ya bani wanda ya fishi'
'Ya sauke ajiyar zuciya tare da cewa, "Amin."
Sai kuma ya shiga yi mata 'yar hira, yana kod'a kyan datayi a ranar birthday d'in
Duk a k'okarinshi,
na ganin ya kwantar mata da hankali, domin ji yake, shine sanadin tarwatsewar farincikin ta, ita kuma abin nema ne yasamu, taji dad'in hakan sosai.'
'Da k'yar sukayi sallama.'
'Wai ko anya zancen Basma gaskiya t
ne??
'A gaskiyar zancen dai, shine, basma bata gayyaci manyan samarinta, wad'anda tasan zasu ji haushin ganinta da yusuf ba,..Amma da gaske ne tayi fad'a da wani saurayinta amma shima d'in kawai na rage zafi ne, baza,a kirashi da saurayinta na sosai ba, shine ta fa ke da hakan ta d'ora kukan makircinta akai, buk'atar ta kawai Yusuf ya tausaya mata, tana son tausayinshi yayi tasiri akanta, wanda shine zai zama mabud'in cimma dukkan manufarta, kuma gashi cikin sa,a ta sami hakan.'
'Domin ita tayarda da cewa, tausayi shike jawo soyayya..'!
'Basma ta kwanta har da burgima don murna, tabbas ta juyo k'amshin nasara.'
'Ana cikin haka kira ya shigo cikin wayarta tana dubawa tayi tsaki sanan ta d'aga.
"Hello basma iam Aysha d'aheer"
"Ok, so ya kike"?
"Lafiya lau"
'Suka d'anyi shiru sannan Aysha tace,
"Basma Yunus Manyan gari,"
"Hmm, basman tace cikin rashin kulawa, domin tun ranar birthday d'inta taji ta tsani Ayshan, saboda gani take kamar munafurci ne ya kawota.. Hafsah
ce ta turo ta donta kaimata munafurcin abinda ya faru kawai.'
'Amma dake ance bariki iyawa ne sai, ayshan ta chanja salonta, ta gyara muryarta tace,
'Gaskiya Basma, kin burgeni ranar nan fa, sai ranar na tabbatar H.Hamid jaka ce'
Basma ta shek'e da dariya,
'Aysha ta cigaba, wato in banda hauka irin nata, ko yaushe zaki bari number Saurayinki a wayar k'awayenki?? 'Sannan kuma Kalli yadda don k'auyanci ta ki zuwa birthday d'in ta barshi shi kad'ai yazo, Basma tace "Hmm.'' So take ta gano inda Aysha ta nufa, Don tana tsoron kada dai bugar cikinta takeyi.'.. Amma hankalinta ya kwanta da taji Ayshan tace, "Ni wallahi ma sam gayen bai wani dace da ita ba, bafa type enshi bace."
'Sukayi dariya sosai ita da Basman, har Basman ta samu damar cewa, "Kema dai kya fad'a Aysha'.. "Hmm ai wallahi sam babu colour, yarinyar da babu inda take zuwa!!"
'Anan basma ta saki jiki sukayi hira, sosai da zata fad'awa Ayshan wayar da sukayi da Yusuf d'azu, amma sai ta fasa, suka kashe waya, Basma na farin ciki ta samu wata mai bata shawara akan al,amarin...

🤥 *Sabon salo*


.
*Khareemerh tijjani Mansur (Hajeeyah Kareemerh*
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔

Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to: Unique In Love Heart Members*




📄 *30*






*Kimamin* sati d'aya kenan dayin birthday d'in, Basma, kullum Hafash zuba idon ganin Yusuf take yi, amma shiru.'
'Duk da tasan ita take hana shi zuwa, amma sai zuciyarta ta fara raya mata 'kodai ya manta da ita ne'? ('Zuciya kenan')
'Ita a yadda tayi kewarshi batak'i yazo d'in ba, idan yaso sai, tace wa Abba, 'Zuwa yayi ya amsa kiran da yayi mishi'...😅😅
'B'angaren su Basma kuwa, abu yayi nisa ita da Yusuf, kullum sai sunyi waya, kuma Basman ce ke kiranshi, shi kuma baya k'in d'aga wa
'Yau da sukayi waya ne, take tambayar shi, 'Wai shin yau zaije club ne? Yace mata bashi da niyya, amma idan zataje shima zaije, taji dad'in hakan da yace, 'wato idan hakane tana iya samun alfarma kenan a wajenshi?..
'To kwa tabbas zata gwada sa,arta.'
'Aranar da suka had'u a club d'in bayan sunsha rawa sosai, basma ta nemi dasu k'ebe tana so su tattauna, ya rik'o hannunta, ('Wanda zuwa lokacin k'aramin abune a wajen su su rik'e hannun juna') suka fito daga cikin hayaniyar zuwa harabar wajen inda aka ajye kujeru domin zama.'
'Kafin ta fara magana ya riga ta, don shima d'in yana da abin cewar da yake ganin bazai iya hak'uri har ta fad'i nata ba.'
"Please basma help me" ta kalleshi da mamaki, "With what?
'Ya marairaice please ki daure kije gidansu Hafsah, ki bata wayanki ina so muyi magana ne please"!
'Take yanayinta ya chanja wanda shima sai da yaga hakan, har ya karanta mata alamun tambaya a fuskarshi, sai tayi saurin wayancewa ta k'irkiro murmushin dole ta d'ora akan fuskarta.'
'Hmm, banyi maka promise ba, but zanje cikin satin nan. 'Yai ajiyar zuciya tare da ce mata "please basma help me, kinji,' na kuma bata waya ne, so i think Abbansu ya kuma k'wace wa.'" ta d'an cije lebe sannan ta daure tace mishi, "Ok don't worry"
Yai murmushi sannan yace, "Thank you"
'Ya kuma tattaro hankalinshi gurinta, sannan yace, "What about yours?
'Tayi wani murmushi sannan ta gyara zamanta tace cikin wata marainiyar murya,
"Nawa yana da wahala, bana jin zaka yarda."
'Ya girgiza mata kai had'i da cewa, "No, please tell me, zanyi miki kinji"
'Sai lokacin ta sami k'warin guiwar fad'amishi abinda ke ranta.'
"Um, tun lokacin da muka rabu da ex ena, yake min abubuwan da banjin d'ad'i, yana min maganganu a status, sannan yace wai ban isa na sami saurayi wanda ya kaishi ba, so ina son in nuna mishi k'arya yakeyi..' Tayi shiru data zo nan a zancen, yayin da shikuma ya bata duk hankalinshi, da yaji tayi shiru, yai mata alamar, 'Yana sauraronta ta, ta cigaba.'
"So please ina so ne ka dinga acting like you're my boyfriend.."
"What? Ya fad'a yana girgiza mata kai,
"No, I can't, am not like that, please am sorry to say 'bazan iya ba!"
'Basma ta d'ora mishi ido ta kasa d'aukewa, daman tasan

12 / 40