Author : KARIMA TIJJANI MANSUR Category : Romantic Hausa Novels
hakan Yusuf ya mik'e a zafafe ya wanke fuskar ta da mari.' tayi saurin rik'e kuncin, tana masa kallon k'askanci, shikuma sai huci yake yi.'
'Sai lokacin bakin Hafsa ya bud'e daga kullewar da yayi, ta mik'e cikin zafin nama tayi kan Yusuf.'
'Taci kwalar shi cikin rashin hayyaci, ta fara magana cikin kuka, da huci,
"k'arya kake Yusuf, yaushe ka zama munafikin mata..? Yaushe ka kware a yaudara..? Yaushe ka zama d'an iska??.. Yusuf ka cuceni.."
"Yanzu koh zaka aikata haka,.. karasa dawa zakuci amanata sai Basma..??
"Wayyo Allah, Yusuf ka cuceni wallahi, bazan yafe maka ba..'
'Tana k'arasa fad'in haka, ta sakeshi tare da hankad'ashi da duk k'arfinta.'
'Tun da tayi masa rik'on ya gaza aiwatar da komai banda kallonta da yake, sai tunani da dama cikin zuciyarshi.'
'Yasan dai bai kyauta mata ba, amma to ya zaiyi da rayuwarshi.'?
'Tana hankad'a shin yai saurin zama a kujera domin ya kusa fad'uwa, ya dafe kai cikin rashin sanin mafita.'
'Kamin yayi wani yunkuri yaji saukar wani bahagon mari a kuncinsa, asukwane ya d'ago don ganin wanne mai tsautsayin ne ya mare shi.'
'Aysha ya gani tsaye akansa tana huci, azuciye yakai hannu da nufin yi mata wani wawan duka, amma sai yaji an rik'e hannunshi, ya juyo rai a b'ace don ganin waye ya katse mishi hanzarin sa.'?
'Hafsah ya gani ta dakatar da shi cikin rawar murya mai rauni tace tana hawaye, "Yusuf dukanta zakayi, don ta rama abinda ka mata."
"Yusuf ka koya min darasi kuma na koya..' me nayi maka da ka saka min da wannan mummunar sakayyar.? Yusuf ka yiwa rayuwata illah, sai da na gama yarda da kai sannan kaci amanata..'
'Ta durkushe a gurin tana kuka mai tsuma rai.'
Shima a sanyaye ya durk'usa gabanta.'
"Hafsah believe me, banci amanarki ba, bakya tausayina koh, kiss and even hug baki rab'a yimin ba as my girlfriend, amma, Basma fa ita ta..''
"Ya isa! Ya isheka!! Ta fad'a cikin wani fad'a da wata murya mai k'ara gami da kuka, da haka basma ta fini a gurinka koh Yusuf, ta fad'a tana nuno, Basma data sab'a jakarta a kafad'a, tana gyara mayafi don shirin rantawa a na kare kafin hankalin Hafsa ya dawo ta juyo kanta.'
Nibance ta fiki wajena ba, idan ta bani abinda kika hanani kinga kowa matsayinshi daban',..
"Kai wanne iri ne Yusuf mai yasa baka ji ne, ehe, Meyasa ba zaka d'auka hakan laifi bane ko a addini.."
'Maganganun datake yi mishi kenan.'..
"Ta juya ga Basma, kin bani mamaki,kin ci amanata in sha Allah Allah sai saka min.."
'Ta finciko Aysha suka fita, inda Yusuf da Basma suka tsaya kallon kallo a junansu.'..
*Yours*
*Khareemerh T Mansur*ππΌ
[1/12, 1:56 PM] Hajeeyah Karimah (Writer): β₯οΈβ₯οΈβ₯οΈβ₯οΈ
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken heart story*
ππ
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to: Unique In Your Love Heart Members*
π *33-35*
*Basma* ta saki ajiyar zuciya tana wa yusuf kallon tuhuma, shikuma ya had'e hannayenshi biyu alamar Afwan sannan ya fice da hanzari, yafi su Hafsah.'
"Hafsah, hafsah baby.. Please ki tsaya mana".
'Kiranta yake amma Aysha sai faman janta take, tana d'aga mata kafada, alamar kada ta tsaya.'
'Abin mamaki sai ganin Hafsah, tayi ta fizge hannunta, ta d'an yi baya, ta tsaya cak.'
'Ya saki ajiyar zuciya, sannan ya k'araso cikin sassarfa.'
Am sorry Baby, wllhi banci amanarki ba, kuma, ki believing me, bazan tab'a rabuwa da ke ba, even if i got everything from Basma.."
"Ya isa,!! Ta fad'a cikin tsawa.'
Kana nufin hakan ba cin amana ne ba koh?"
'Ya dafa kai, ke kika janyo koma menene, i have tell you for multiple times, idan baki yarda dani ba, komai ya faru kada ki zargeni."
"And I swear to God, ko yanzu kika daina guduna, zan rabu da Basma."
"Ki yarda ban miki cin amanar rabuwa da ke ba'!
'Ji tayi hankalin ta na neman barin jikinta.
'Wanne irin soyayya kenan sukeyi, Zai rabu da basma idan ta aminta da buk'atar sa,.. Idan kuma ba haka ba zata zauna da kishiyarta kenan wato Basma??
"A hankalce ma abin babu tsari. 'Ta rasa wanne martani zata mayar mishi, iya bak'in ciki dai ta shak'a acikin kalamanshi, har wani abu ne ya tare, mata mak'oshi.'
'Ta girgiza kai cike da k'uncin rai tace cikin sanyin murya.'
'Yusuf na gode da sakayyar da kayi min.'
Kuma nagode, da matsayina da ka nuna min.' ta nuna kanta, "Yusuf wai ni kayi wa haka koh? "Na gode, wasu hawaye masu zafi, suka sakko zuwa, kan kuncinta.'
'Cikin gudu gudu, tayi saurin bar mishi wajen.'
'Kiranta yake amma ina tuni Aysha ta janye ta sukayi gaba.'
'Mai gadi ya yana musu a sauka lafiya,Hajiya.'
'Cikin sa,a suka sami Napep, cikin layin duk da GRA ne,
'Tunda suka shiga Hafsa keta faman aikin kuka, Aisha na faman rarrashinta, amma ina, abu yaci- tura, babu abinda take fad'a sai "Aysha yusuf yaci amanata, ya cuceni."
'Ita dai Aysha hak'uri kawai take bata.'
Sun kusa isa gidansu Hafsah, aka kira Aisha a waya, ta d'aga.'
"Hello mama,.. Ok, tom ina hanya yanxu zan dawo.'
'Ta Kalli Hafsah.' Kinga mama ce ke kirana, idan aka sauke ki sai ya wuce dani da nayi niyyar in raka ki gida.'
'Hafsah ta gyad'a kai kawai.'
"Amma don Allah Hafsah ki saita kanki kada mama ta gane, halin da ake ciki."
'Hafsah ta gyad'a mata kai.' ta d'akko 'Handkerchief' daga cikin Jakarta, ta mik'a mata.'
"Please ki goge hawayenki."
'Ta karb'a tana gogewa wani na k'ara fitowa.'
'Har k'ofar gida, aka kaisu.' Kuma, tun sanda suka shigo layin, ta cikin madubi, Hafsah ta lura da motar Abbansu dake bayansu.'
"Don Allah ki cire damuwa ki mai da komai kamar bai faru ba, please H. HAMID."
cewar Aysha kenan sanda akayi parking a k'ofar gidansu Hafsah.'
'Dak'yar Hafsah iya cewa, "Nagode, sosai Aysha ki gaida mamanku."
Tana fitowa daga cikin Napep, d'in motar Abba na sako kai, kuma ta tabbatar ya ganta.'
'Tayi saurin tura gate ta shige ciki tana k'ara goge fuskarta.'
'Tun daga yanayin data ga mama tasan da akwai matsala, gashi kuma maman ta k'ura mata ido tun amsa sallamar ta.'
'Tasha jinin jikinta sosai, sai lokacin ta tuna cewa 'rufe gidan tayi ta fita.'
'Tayi hanyar d'aki kenan mama tace, "Ke, zonan."
Cikin rawar jiki ta juyo ahankali take takawa takowa.'
"Daga ina kike"?
'Cikin tsawa maman ta tambayeta.'
'Nan ta hau kame- kame,..
"Um..wai ni..? in.. dama Aysha ce.."
'Mama ta daka mata tsawar data sata razana.'
"Zaki fad'amin min ko sai ranki ya b'aci."??
'Dai dai lokacin Abba ya shigo falon, jin mama na yin fad'a yasa yace, "Menene wai yake faruwa, lafiya."?
'Hmm inji mama, tare da yin kwafa 'k'
ta nuna Hafsah, da yatsa, gatanan sai ta fad'a maka tunda kazo kai.'
'Cikin rashin fahimta Abba yace,
"Me yake faruwa ne ki fad'a min me ta yi kuma."??
'Mama ta nuna ta, ka ganta, wai na fita na bar mata jiran gida, shine ta fice ta kulle gidan ta fice yawonta.."
'Abba yayi dogon numfashi, ya zauna kan kujerar bayanshi, ya kalli, hafsah data durk'usa a k'asa. cikin kaushin yace Ke, ina kika je. ehe"?
'Cikin rud'ewar murya tace "Abba dama Aysha ce tazo na rakata asibiti.."
"Shine kuma fuskar ki ta kumbura koh"?
'Ya katse hanzarin ta da tambayar.'
'Ta kai hannunta ta shafa fuskar, sai yanzu itama Mama ta lura da jan da idon Hafsah yayi.'
'Hafsah tayi kus, ta kasa bud'a baki tayi magana, sai hawaye ma da suka cika idanunta, na k'uncin da zuciyarta ke ciki.'
'Duka, da Abba da Maman ido suka zobo mata ta lura sosai da kallon tuhumar da dukkansu, suke mata.'
'Kwakwalwar ta chakud'e, gefe na k'okarin tariyo mata abinda ya faru da gidan su Yusuf, gefe na karanto mata tsoro da kuma neman abinda zata fad'awa Abba.'
'Ta d'an runtse idonta, kawai sai photon, abinda ta gani ya hasko cikin idonta, bata san lokacin da ta fashe da kuka ba, tama manta gabansu abba take.'
'Abba ya fusata, ya kawo mata duka, mama da zuciyarta ta shiga rud'u ta tare shi tana cewa, "Don Allah kada ka daketa ka kyaleta ta yi magana.'
Cikin fad'a Abba ya fara magana
"In kyaleta koh, kina sangarta ta koh? "Don iskanci daga tambayarta sai ta hau yiwa mutane kuka"?
"Yayi kyau, shikenan ki goyi bayan ta!"
'Ya Mike fuu yayi daki, yabar Hafsa durk'ushe a wajen, har ya dakko abinda ya zo nema ya dawo ya fice cikin sauri.'
'Mama da tun sanda ya shige tayi shiru ta rasa abin da zata cewa Hafsah ma.'
'Har wajen tsawon minti biyu, sannan maman ta k'irkiro abin cewa, cikin tsawa ta yi mata magana.'
'Zaki fad'i inda kika je ko sai nayi ball da ke anan wajen.'?
Hafsah ta d'ago a razane, har yanzu k'wallar bata daina d'iga ba.'
"Basma aka kwantar um.. a asibiti shine aysha,mukaje..Asibiti duba ta.."
'Tana dire zancen mama ta d'auka.
"Karya kikeyi"
"Wallahi Hafsah idan baki fad'amin gidan uban da kika je ba sai na k'arya ki anan."
"Wallahi, Mama can muka.."
Ta, doka mata tsawa.'
"Dubiya da tsakar ranar nan koh,?.. To uban meye ya kumbura miki ido, fuskarki tayi ja ehe."
"Um, wallahi tun jiya mama nake ciwon ido dama."
'Mama tayi shiru, ba, wai don ta yarda da shiryayyen zancen Hafsah ba, kawai dai ta shiga rud'ani ne.'
'Kuma akace,' 'Mace' tana da rauni.' To agurin mama, raunin shine yayi tasiri, sai tunanin ta ya chanja gabad'aya zuwa wani layi daban.' Bisa wani karatu da zuciyarta tayi mata.'
'Ta fara tuno abubuwan da suke faruwa tun had'uwar Hafsah da Yusuf.'
'Zuwan Hafsah gidan Hajiyah na k'arshe, sai babban tashin hankalinta 'ranar bikin uncle abdallah, fitar da hafsah tayi ita da wani.'.. To yau ma gashi ta fita ba,a sani ba, kuma yadda mama ta kiyasta tafi awa d'aya bata gidan.'
'Don ita kanta maman wajen awarta d'aya da dawowa. Mamaki da tsoro suka mamaye ta data ga gidan a k'ulle.'
'Duk da tana da 'Spare' na muk'ulli acikin jakarta, hankalinta bai kwanta ba sai da tayi ta zagayen mak'ota tana cikiyar ko Hafsah ta shigo.'
'A farko tunaninta ko ta gaji da zaman shiru ta shiga mak'otan, duk da tasan Hafsah bata da tsoron zama ita kad'ai cikin gida sannan kuma bata da shige shigen mak'ota.'.
'Ashe ita Hafsan ta tafi wani wuri can abinta.' To ina taje kenan,? Ita da wa,?
'Allah ya kiyaye kada dai Hafsah na k'okarin kama wani layi na daban ne.' idan ta duba zata ga gaba-d'aya Hafsah ta canja dabi,u.'
'Zaman shiru
yawan tunani sai kuma b'oye b'oyen da ta tsiri yi mata yanzu, sai fita bada saninta ba.'
'Wanda ada ba haka bane.'
'To Meyake faruwa? ka da dai ace ansami wani ya gurb'atawa 'yarta tunani da kuma tarbiyyar da suka dad'e suna tattalinta.'
'Wannan tunanin na Mama, ya jawo abubuwa da dama..'
'Sallamar Hajiya ita ta farko da Mama daga dogon tunanin da ta tafi.'
'Ta amsa cikin sanyi, ta fara yiwa Hajiya sannu da zuwa.'
'Yawwa inji Hajiya, Hajiya ta zauna, sai lokacin ta lura da Hafsah, zatayi magana Mama ta hau gaisheta.'
"Sai da ta amsa, cikin sakin fuska, sannan ta juyo ga Hafsah,
"Ke kuma fa?
'Kinyi wani jugum dake ba kya gaida mutane"?
'Hafsah ta d'ago tare da dai dai ta fuskarta.'
'Hajiya sannu da zuwa, ina wuni.'
"Lpia lau"
'Hajiyan ta amsa, sannan ta dire tambayarta,
"Me akayi miki ne.'
'Kunya ta hana Hafsah amsawa, ita da tayi laifi kuma ake tambayarta me akayi mata'??
'Mama ta cafe zancen'
"Laifi tayi."
'Hmm ko da naji, sai wani wuk'i wuk'i kike da ido kamar mara gaskiya."
"Ashe kuwa baki da gaskiyar."
'Mama taji gabanta ya fad'i rashin gaskiya kuma.'? To me Hajiya take nufi,?
'Kada dai ta gano wani abu, game da Hafsah, tun da dai ita Babba ce.'
'Nan lissafin Mama ya k'ara jagule wa.'
'Ta mik'e ta nufi kitchen don debowa Hajiyah abinci.'
'Lokacin kuma aka kira sallar la,asar, saboda haka Hajiya ta mik'e don yin alwala, ta kalli Hafsah,
"Ja,ira sai ki tashi an kira sallah.."
"Naji yace kin k'are boko koh."?
"Ai, ashe bokon naku bana k'arau bane, kin gama secondira"
'Hafsa ta gyad'a kai.
"To Allah yasa albarka."
'Ta mik'e ta nufi d'akinta, tana godewa Allah, da Hajiya tazo da tuni har yanzu Mama na faman tuhumar ta.'
'Maimakon tayi alwala, sai alhinin abinda ya faru ya danne k'arfinta ta kwanta ta fashe da wani matsanancin kuka, tana jajanta wa kanta, wannan cin amana da aka dad'e anayi mata, da sai yau, Allah ya nufa ta sani.'
'Taci kuka ta goge Allah har ta tausaya wa kanta, babban abinda yafi tasar mata da hankali shine,
'Yanzu a wanne matsayi take gun Yusuf.'?
'Ashe Yusuf duk soyayyar da yake karanta mata ta k'arya ce.'?
Ita data rik'i Basma aminiya, shine zata ci amanarta.'?
'Ashe da gaskene sauyin data dinga gani a wajen Basma.'.. Wayasan lokacin da suka d'auka suna aikata haka,?
'Sun ninke ta abai-bai.. 'Ta k'ara rushewa da kuka, har da dukan 'pillow' saboda alhinin raina mata tunani da akayi.'
'Gaskiya sun raina tunaninta, takaicinta ajinta da aka zubar mata ranar birthday d'in Basma.'
'Ta tabbatar rabin 'yan class d'insu sun je, kuma an kira Yusuf da saurayinta, amma saboda su tabbatarwa da mutane sun rainata, kuma ita ba komai bace a wajen yusuf.'.
Yasa suka yi hakan.. '
'Tayi kuka har kanta ya fara ciwo, idanunta, sukayi jajir kamar an watsa mata barkono.'
'Har kiran sallar magariba bata fito ba, tana ta aikin kuka, amma babu shashsheka sai hawaye dake fitowa daga cikin idanunta, wand'a kana gani kasan tana cikin k'uncin zuciya, da taikaici.'
'Tana jiyo tafiyar hajiyah, amma ko lek'awa parlour bata yi ba.'
'Ta dai tashi tayi sallah sannan ta koma ta kwanta.'
'Mama kuma fushi take da ita, don haka ko lek'o ta batayi ba.
'Can kuma bangaren, mama tunani tayi kamar bata kyauta ba data hana abban hafsah dukan Hafsar, bai dace ta dinga katse mishi hanzarin ba, akan dukkan matakin daya ga ya dace ya d'auka akan Hafsar tun da ita ta gaza.'
'Ta saba tun da can bata dukan Hafsah, bare kuma yanzu da ta zama budurwa sosai.'
'Ba kuma, don hafsan tafi k'arfinta bane, sai don shi dukan bashi da amfani.'.
'Amma to ya ta iya, wani lokacin dole sai an had'a da dukan, musammaman yanzu da Hafsah ke neman 'bujirewa, ta kama wani layi na daban.' A tunin maman, 'Wanda zancen Abba da mutane yayi tasiri akanta har ta ke zargin wani mummunan abu ayau ga Hafsan wato fad'ar da ake na,ππ» 'BA,A SHEDAR YARAN YANZU'..
B'angaren zuciyar mama na wassafo mata wani abu, wani b'angaren na k'okarin korewa.'..
'Haka ta tilasta wa zuciyarta sai ta binciko gaskiyar zarginta. Hafsah ta gudu gidan Hajiyah tayi zance kuma ta tabbatar a d'akin uncle abdallah tayi zancen.' sanan ta fita da saurayi bada sanin kowa ba ranar biki, yau kuma ta fice yawonta (idan ma ita kad'ai d'in ta fita) batare da sanin kowa ba. 'Wanda dukka wad'annan halayen ba nata bane ada ba zata iya koda kwatanta yinsu ba, to Yanzu to 'Me TAKE SON ZAMA.'?
'Wai don ma mama bata ji halin da uncle abdallah ya gansu ba ranar.'
'Da akwai matsala inji Mama.'
'Iya k'arfin tunanin mama kenan..'πππΌππΌ#Hajeeyah Kareemerh.'
'Shiko Abba sai bayan anyi sallar magariba, sannan ya shigo gida.'
'D'akin shi ya wuce maman ta kai mishi abinci can, bai nuna mata komai ba ya saki jiki da ita har sukayi hira.'
'Bai sako mata zancen Hafsah ba sam, kuma tasan halinshi so yake ya barta tayi nata k'okarin, don haka tayi azamar chanja hirar tasu ta sako ta abinda yafi damunta ayanzu wato 'lamarin Hafsah.'
"Am Abban Hafsah baka tambayeni ya mukayi da Hafsah taka ba."?
'Cikin rashin bawa zancenta muhimmanci yayi d'an murmushi mai sauti.'
"Hmm to ai wannan ke da ita ne.
"Me yayi wa Abba zafi,? 'Bake tayiwa laifi ba, kin barta jiran gida ta fice nata sabgar,? to ni me ye nawa kuma ciki."??
'Nan da nan fuskar Mama ta sauya taji zafin kalamanshi fiye da tunani. 'Da bazata tanka ba sai kuma taga asarar hakan, don haka ta had'iye fushinta, tace,'
"Idan tamin laifi ai kaima ai tayi maka, kuma ko ba haka ba ma ai kafi kowa iko da ita."
"Hmm, ta yaya? Bayan gaki, kefa kika haifeta."
"Haba Abban Hafsah don Allah ka daina fad'ar haka."
"Hmm da Hakane Amina, ai da baki nuna min wai kada in tab'a miki 'ya ba koh'?
'Subhaanallah, wallahi ba haka bane, wallahi bada wani manufa bada manufa nayi hakan ba.'
"Hmm to ai shikenan nima bacewa nayi wani abu ba.
'Ki mata abinda ya dace kawai."
'Yana fad'a ya mik'e don fita masallaci sallar isha'i.'
'Hankalin mama ya tashi, tayi da na sanin hakan data mishi, data bari ya d'auki mataki akanta, ita gani tayi dukan bai da anfani, kuma ta tsorata da dukan da yayi wa Hafsan kwanaki.'
'Shi abinda kake tunanin zaiyi fushi akai to, ba,a kanshi yake fushin ba.'
'Yanzu ya zatayi idan ya zare hannun shi daga kan Hafsah'??π³
π
'Mama kenan'!ππ»
'To shima abba, a b'angaren shi, ba wai cire, hannun nashi zai yi ba.'
'To idan yayi haka mekenan yayi, ai kanshi yayiwa.'
'Dole ne ya sa ido akanta ko dan hak'k'insu akanshi yake, bare kuma yafi sonta akan dukan 'ya'yanshi.'
'Kawai ya kyale mama ne, don kuma da gaske abinda ta mishi ya b'ata ranshi sosai.'
'Amma shima da akwai nashi tunanin akan matakin daya dace kan Hafsah.'
'Koda aka idar da sallah bai nemi hanyar gida ba, ya jima yana addu,a kan Allah ya taimake shi akan tarbiyyar Hafsah, 'Don yasan addu,ar ita ce komai bawai wani k'okarinshi ko fad'anshi ba..'
'Yasani tarbiyya da akwai wuya amma, kuma yasan yayi iya kokarinshi, sai kuma yanzu da wani keson wargaza mishi komai.'
'Shi dake tuninshi daban da na mama, yayi amanna tabbas 'Soyyaya' ce ke dawainiya da Hafsah har bata tsoron fushinsu yanzu, ya lura tanayin duk abinda zai zamar mata maslaha ne ga soyayyar ta ko menene kuwa zai biyo baya.'
'Shi abba ba takaicinsa bane soyayyar data fad'a, a,a abinda yake b'ata mishi rai shine kalar yaron data nacewa.'
'Ya tabbatar ba na nunawa bane in banda haka meyasa ya kirashi, yak'i zuwa.'?
'Amma yanzu ya zamar mishi wajibi ya nemi yaron koda a waya ne, don maslahar shi.'
'Saboda haka yasa a ranshi gobe zai kira shi..'
'Da wannan tunanin ya kamo hanyar gida.'
'A gidan kuma, yaran ne suka dami mama bayan ta fito daga d'akin Abba, 'Wai ina yaya.'?
'Nace muku tana d'aki meye zaku dameni.'?
"Mama bata da lafiya ne..?"
'Inji Mufida.
"Ban sani ba, kije ki duba mana." 'Cewar mama cikin fushi.'
'Mufida ta mik'e ta nufi d'akin Hafsar.'
'Tana kwance sai juyi take.' Bayan ciwon kan daya addabeta yanxu kuma ciwon mara take fama.'
'Ga kuma uwa uba ciwon da aka haddasa mata cikin zuciyarta.'
"Yaya, Yaya, wai baki da lafiya ne?
'Ta d'ago jajayen idanunta, ahankali ta bud'e baki murya a dashe saboda kuka tace, "Eh Mufida, bani da lafiya."
"Kaii, amma baki fad'awa mama ba.?
Bari inje to in fad'a mata.
'Tana yunk'urin ce mata a,a, amma ina, ai tuni ta fice.'
'Daidai sanda ta dawo falo lokacin Abba ya shigo yaji tana cewa.'
"Mama