Chapter 3 Reading ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt Arewa Novels

ZAZZAFAN SO COMPLETE HAUSA NOVELS BY KARIMA TIJJANI MANSUR.txt

Author :  KARIMA TIJJANI MANSUR Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   3 / 40

6K to 9K   out of 119.4K words

dress mai kauri ta yafa bakin mayafin abayar ta fesa turare..

Tana fita falo ta hango mama acikin kitchen (kitchen en a falon yake)
Kamar mara gaskiya sai ta tsorata da suka had'a ido..
Ina zaki daga yin magariba?
cewar mama da ta d'an hade rai..

*I Need your comments to encourage me!*πŸ‘πŸΌ
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): β™₯β™₯β™₯β™₯
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
πŸ’”πŸ’”

Story and writing by:

*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*

*Dedicated to:*
*Unique In Your Love Heart Members.*


πŸ“„ *9*


*"Am* mama gidansu Ummi xani wani littafi zan k'arbo."
"To kiyi sauri ki dawo "
"Tom mama"
Ta fita cike da son ganin wanene wannan yake nemanta da farar magriba..
Tana tura gate ta hango motar a gefen dama na gidansu..
Motar ta had'u kamar yadda bashir ya fad'a mata.
An d'an bude murfin motar. Na ciki ya d'an fito da k'afarshi waje..
B'akin takalmi ne a k'afarshi da farin jeans.
Ahankali take takawa har ta isa kusa da motar.
Shiko hankalinshi na kan wannan wayarshi yana latsawa..
Ta d'an tsaya na kamar minti 1,sannan cikin sassanyar murya tace
"Assalamu alaykum"
Hakanne ya sa shi d'agowa ya kallo gefen da take..
Farin kyakykyawan saurayi,mai manyan idanuwa, dogon hanci gami da bak'in gashi sid'ik..
Ahankali ya dago fararen idanuwanshi kamar madara masu zara-zaran adon gashin ido (eye lashes) Ya mata sanyayayyen murmushi da jan leb'enshi madaidaita.
"Wa alaykissalaam"
Ya amsa sallamar. wanda muryarshi tasa Hafsah fad'uwar gaba.
Ahankali ya amsa kuma cikin nutsuwa yadda ita kada'i sautinshi ya jiyar.
Ya mik'o k'afafunshi gami da fitowa gaba d'aya daga cikin motar..
Ta danja gefe daf da bango ta tsaya. mamaki ne cike da xuciyarta to shikuma 'daga ina'?
Takowa yayi zuwa inda take ahankali cikin nutsuwa ya na fuskantarta har ya isa kusa da ita ya tsaya.
Ya hard'e hannayenshi a k'irji. wani tsadadden agogone a hannunshi gami da wani zobe na azurfa. a d'an yatsanshi na tsakiya.
Murmushi ya kuma mata, sannan ya lumshe idanunshi ya bud'e.
"Hafsah nah"!!
Gabanta ya fad'i taso ta tuno mai irin muryar nan a wani waje..
Ya kuma kallonta
"Am back to you again!
"Ina tunanin "This is the right time to you to accept me!
Kinga kene kika bani wannan lokacin..pls kada ki k'i karb'ana."
Ya fad'a yana had'e hannayenshi biyu alamar rok'o.
Ya k'ara cewa "kinji..? "pls..
Tayi shiru na wasu lokuta wato shine tabbas, saurayinta na 'Seven months'
Ita abinda ya bata mamaki shine: 'Meyasa a wancan lokacin bata lura da kyau da had'uwarshi ba?
Wannan ma ai yafita kyau..
Sai ta tuno da maganar jamila wancan lokacin.
"Hafsah wannan fa ba kalar wukak'anta wa bane"!!
Tabbas jamila taga abinda ita bata gani ba a lokacin.
"Baby kinyi min shiru "
"hum.. Tayi murmushi "AI nayi tunanine sai yanxu na gane ka"
Murmushi yayi na yin dad'i "da biki gano ni ba koh"?
"Yes."
"Yanxun fah?
Na gane ka, sai dai baka fad'amin sunanka ba wancan time en"
Ya d'an daga kai ya rufe ido sannan ya bud'e.ya naushi iska
"Oh shut!
Ya kama leb'enshi na k'asa ya d'an matsa..
"Lefin baki nane, amma ai kene u didn't even listen to me.!
Ta rufe bakinta da hannunta "No a lokacin islamiyya zamu ne.
"Ok so my name is Yusuf".
Ya fad'a kamar rad'a.
"Ok Nice name" tace.
Am mu shiga mota "mana koh?
Kamar ta musa sai kuma ta kasa don gaba d'aya salonshi da komai nashi ya tafi da ita..
Motar kuwa suka shiga duk da ad'an tsorace take.
Abba yayi tafiya amma tace wa mama baxata dad'e ba.
Nayi long waiting fa anan, since 5:55pm nake. Ya fad'a yana kallon agogon hannunshi. sannan yace 6:15pm.
Ta zaro ido "Sannu gaskiya,may be ina shiga gida daga islamiyya kazo. 5:50pm na dawo.
"No, don't worry , all this is because of you"
Ya fad'a yana kashe mata ido da'ya.
Kan tace wani abu taga ya dakko wata led'a.
Ya bude ledar kwalin wayoyi ta gani guda biyu.
Ya bud'e ta farko "I phone ce"
Ya mik'a mata wayar yana cewa "I missed you over" ko waya bakya dashi bare mu d'anyi hira Koh?.. To ki amsa wannan to"
Ta girgiza kai cike da tsoro.
Ya kalleta, ya Kalli wayar
"why baby?
"Ka.. Ka barshi abbanmu zai bban wayya..ai"kuma wanna tayi girma.."
"No ni sai na baki"
Ya fad'a cike da shagwaba.
Ta girgiza kai
"Thank u"
"Bakya so na Koh?
Ya fad'a yana nuna kanshi da d'an yatsa.
Ta girgiza kai kawai.
Ji take kamar tayi kuka, wacce kaddarar ce ta sata shiga ma cikin motar?
"Ok"
Ya fad'a yana cije lebenshi.
Ya Mayar da wayar tayi dakko d'aya karamar ko bude ta baiyi ba ya mik'a mata ita ya had'e rai sannan yace.
"You should accept this one"!
"Just for receiving my call."
Sai kuma ya sassauta murya cikin muryar bayyana damuwa yace.
"Don Allah"..
Kinga bamu da way of communicating.. Kuma fa nasha wuya da bana nigeria saboda Kefa!
Ta sa Hannu ta karb'a.
"Thank you"
Ta fad'a
"U deserve more my baby"! Ya fad'a Yana murmushi gami da lumshe idanunshi saboda jin dad'i.
Pls anjima xan kira wayar ki kunna ta.
'OK'
"Bari na shiga gida Koh?
Ta fad'a tana kallon shi.
"Uhum Uhum yana girgiza mata Kai"
Kamar yaro.
Hankalinta a d'an tashe saboda kada mama ta gane tace.
"Pls kaga mama bata san na fito ba"
Ya zubo mata manyan idanunshi
I won't let u go wallahi until..
A k'age tace" until what?
"U say u luv me!!
Ya fad'a cikin rad'a
To fa..
"I can't"
"U can't and I won't".
Ya fad'a ya na kashe mata ido da'ya.
Ta Kalli glass d'in motar ta ciki ta gane duhu yayi sosai.
Zatai magana kenan ta hango bashir yana tahowa ta dafe k'irji.
Ta kalleshi k'ok'arin kunna musu wak'a ma shi yake.
Bashir ya karaso ta b'angarenta yace yaya kizo inji mama"
Ta "kalleshi mama fa na kirana."
Shima yaji.
ya kalleta "U are lucky."
Ya bude mata motar ta fita.
Ya d'ago mata hannu "Bye bye."
"Na shiga uku bashir mama ta gane Koh?
Ya girgiza kai "a,a,
Yaya meye wannan"?
"Waya ya bani"
"Waya kuma??
Eh.. Bashir bannsan ya xanyi ba cewa yayi dole sai na karb'a dafa iPhone ce." ta fad'a tana zaro ido.
"Kaii yanxu fa?
Samsung ce k'arama.
To ki bo'ye.
"Yanxu mama tana ina?
Da xata aiko ni dai tana falonta kuma naga kamar wanka xata shiga.
Hafsah tayi ajiyar xuciya "Alhamdulillah"
B'oye wayar nan xan.
"Kema aunty mai yasa kika karba?
Daidai lokacin kuma sun shigo cikin gida, cikin sa,a kuma mama bata falon.
Tayi sauri ta shige daki ta yiwa wayar kyakykyawan b'oyo.
Sannan ta dawo falo cikin k'annenta suna kallo.
Can mama ta fito.
Me yasa kika dad'e.?
"Um wanka takene danaje" ta fad'a cike da rashin gaskiya.
Wai wanne littafine ma keda ba makarantarku d'aya ba..
"Um English ne wani assignment xan duba"
"Ki Fad'awa abbanku ya sai miki bana son are - are"
"Tom."
Mama ta kuma kallonta kamar wata ce wani abu xai kuma tayi shiru.

*Hajeeyah Kareemerh ce*

_I Need ur comments to encourage me!!_ πŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌ
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): β™₯β™₯β™₯β™₯
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
πŸ’”πŸ’”

Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*

*Dedicated to:*
*Unique In Your Love Heart Members.*

*GODIYA TA MUSAMMAMAN GAREKI BABBAR YAYA Bilkisu Tijjani Mansur THANKS FOR YOUR LUV AND SUPPORT*πŸ‘πŸΌπŸ˜˜
*Wannan page naki ne sai wanda kika ba*😜


πŸ“„ *10*


*KO* da Hafsah ta kwanta bacci tunani uku ne ya had'ar mata..
Na farko mummunan labarin data samu akan jamila ya tsorata ta sosai ya sanya mata tsoron shiga soyayya..
Na biyu kuma saurayinta na 'Seven months' daya dawo yau, hak'ika ganinshi da tsarin surarshi da wayewarshi ya chanja mata tunaninta akan soyayya... Da ta rufe idonta shi take gani,yayin da kalamanshi ke mata yawo a kunnuwanta..
Ahankali ta furta "My new found love"!!
Tayi murmushi tare da k'ara rungume pillow a k'irjinta lallai tayi farin gani ayau,bata tab'a tunanin samun kamar yusuf a cikin rayuwarta ba...
Sai dai me??
Gabanta ne ya fad'i da ta tuna da kyautarshi gareta wato (wayar daya bata)
"Innalillahi"
Ta fad'a ahankali wato wannan ne lokaci na farko data tab'a mallakar wani abu ba tare da sanin mahaifanta ba.
Bata daga cikin yara masu b'oye wa iyayensu komai.. Duk da wasu daga cikin 'yan ajinsu nayi... Misali sau dayawa idan ana hira zataji 'Basma yunus' tace "wannan wayar wani ne yaba ni amma ko maman mu batasan ina da waya ba.."
Ko wani zancen makamancin haka..
Sai take ganin "Ina iyayen nasu suke ??
Baxata tab'a iya b'oye wa mama komai ba..don koma ta b'oye mata sai ta gane, don mama bata da shamaki da ko ina a d'akin tana xuwa ta bud'e komai..
A hankali taji an turo d'akin..mama ce bisa al'adarta takan lek'o su duk tsakiyar dare domin duba su.
"Bakiyi bacci bane Hafsah"?
"Um yanxu dai na farka"
" Kin yi addu,a dai Koh?
"Eh"
"To kiyi k'ok'ari ki koma bacci gobe dai kin san da makaranta."
"To mama"
"Sai da safe" mama ta fad'a tana jawo mata k'ofar ta fita.
"Hum!!
Hafsah tayi ajiyar xuciya.
Wato yusuf dai ya had'u ko ta ina..duk yadda take bukatar mijinta ya kasance (A siffofinshi) Yusuf ya kai har da k'ari..
Ita kadai tayi murmushi tana lumshe ido,ahaka bacci ya sace ta...

*Washe Gari*
*A Makaranta*
Aji ne mai d'auke da dalibai kamar guda 30 ne kuma duka, mata ne kawai class SS 2b kenan.. Wanda SS 2a ya kasance na maxaa xallah.Haka tsarin makarantar yake..
Row d'in tsakiya desk na biyu shine maxaunin Hafsah, Itace a tsakiya.Su uku ne a desk d'in hajara Umar, sai Hafsah H. Hamid sai Fatima Mukhtar.
Saman desk en kuwa wata d'alibace Mai matsakaiciyar ki'ba fatarta coffee colour, uniform d'inta sunsha goga..
Surutu kawai take ta zubawa..
'Basma yunus kenan.' uwar rawar kai da gigi..
Tsit ajin yayi sakamakon shigowar Malamin English d'insu teacher Ahmad kenan 'Gajere Sai Fad'in Rai'🀣
Sunan da suka lak'aba mishi kenan..
Sam basma bata san da shigowar shi ba surutunta kawai take xubawa..
"Hey stupid !!
Go out from my class!!
Ya fad'a cikin wata tsawa daya sa ajin yin wani tsit, kamar babu halitta mai motsi acikinshi.
"Dim" basma ta duro daga desk en sannan ta tsaya chak a tsakiyar ajin ta kalli malamin ta wurga mishi wata uwar harara..
"I say get out"
Ya fad'a yana zare ido..
"Humm" basma ta fad'a tana hura hanci..ta k'ara galla mishi harara sannan ta fita..
Malamin ya d'auki marker sannan ya fara magana *to day our lesson is..*


Teacher Ahmad Ya iya koyarwa sai dai baya son raini, kuma baya son wasa da alama jininsu bai hadu ba da basma.Don ta tsani ya shigo,shi kuma ya tsani surutu..
Da aka fita break ne suka had'a dandalin hira. Duk da Hafsah bata fiya yawan magana ba,amma takan saka baki a hirar tasu wacce yawancinta ta samari ce ko kuma ta wani party ko birthday na wata da xa,ayi.
Basma ta d'Γ£kawa Hafsah duka abaya..
"Ku H. Hamid fa munafuka ce, sai dai ta zauna taji cikin mutane, amma ita baka tab'a jin hirar saurayinta!!.
Suka yi dariya "Hahh, gaskiya ne fa, ko dai rowa take mana ne..
"Hmm.. Hafsah kawai tace, sannan ta jawo basma ta rad'a mata a kunne..
"Ke biki saniba jiya nayi wani har ya kawomin I phone nak'i karba sai Samsung shima a gida ba,a sani ba..
Kut m... 😠
"Gaskiya H Hamid Baki da hankali.."
Basma ta fad'a cikin karaji..
(Kuji min ita da ake mata rada)πŸ˜’

"Me ya faru?
Dukansu suka tambaya.
"Wai don iskanci a bata I phone ta mana bak'in ciki"?😏
Ta fad'a tana dungurewa Hafsah kai.
Hafsah ta toshe mata baki, "ke basma ki bari don allah..
Sai lokacin Fatima Mukhtar tayi magana
"to Menene kawai daga bata waya sai ta karb'a?
"Eh mana, meye aciki?
Inji basma.
Babu ruk'ayya ta fad'a.
Basma taja hannun Hafsah zo muyi sirri k'awata.
"Yanzu ina wayar?
Inji basma sanda suka isa can layin baya suka keb'e.
"K'arama ce fa wayar, ni tsoro ma nakeji."
"Kinjiki tsoron me?
"Abbanmu."
ta d'anyi shiru sannan ta d'ora.
"Ya hanani kula samari fa"
"Hmm to ke bari zaki yi ya gane?..
"Ni dai gobe kizo da wayar."
"K'ilama yana ta kiranki kinki kunna wayar.. Ki kunna idan kinje gida dallah."
"OK zan kunna saboda kada yaji shiru ya k'ara dawowa don yau abbanmu zai dawo."
"Ki dai zauna ayi babu ke" basma ta fad'a tana dariya..
"Hahh" Don dai kawai ya had'u ne gayen, da babu ruwana dashi.
"Hahh" ta daki bayan ta. "H Hamid anji guys"!!
To bayan ta koma gida, aiki ta tarar mama nayi na tabar abba (wanda yayi wata 'yar tafiya zuwa Abuja na kwana biyu) ta zauna sukayi aikin ita da mama ko islamiyya bata samu zuwa ba.
Suna aikin mama najanta da hira Kala -kala kamar k'awarta.
Da la,asar abba ya iso suka tare shi suna mishi Sannu da zuwa ita da mama.
"Yawwa, sannunku ku ma."
Ya sauke kallonshi kan Hafsah "Baki je islamiyya bane.?"
"Aiki ta taya ni" cewar mama suna k'arasowa falo, sannan suka shiga wata k'ofa wacce shine falon mama had'e da bed room d'inta.

"Kije kiyi wanka kema"
Inji mama sannan suka shige d'akinta ita da abba.
Gidan yayi shiru dama k'annen nata suntafi islamiyya.
Mama da daddy kam suna da'aki.
Bayan tayi wanka a toilet d'in d'akinta ta d'an yi shafa sannan ta saka wasu pink d'in riga da wando jeans saka wata pink d'in turban ta d'aure kanta dashi sai tayi kyau sosai.
Hafsah kenan doguwa ce bata da k'iba kwata-kwata kuma ba siririya bace, tana da hasken fata mai ja,
tare da bak'in gashi dogo amma bai cika yawa ba.
Bud'e wardrop d'in can k'asan kayanta ta bincika ta d'auko ledar da kwalin wayar ke ciki.

Ahankali ta k'arasa ta sawa d'akin key. Sannan ta dawo ta zauna.
Akan gadonta ta mik'e k'afarta mai zara-zaran yatsu.
Ahankali kuma cikin tsoro take bud'e kwalin wayar 'yar k'arama ce mai kyau.
Ta kunna ta..minti kad'an ta kunnu.

Da SIM card akan wayar sai dai babu chaji kara d'aya ne kawai.
Ta saka wayar a vibrations sannan ta d'auki chajar wayar ta jona ta achaji ta koma ta kwanta tana jiran taji ankira wayar..amma shiru har lokacin sallar magariba.Ta mik'e ta nufi toilet don yin alwala...
Bayan isha'i ne mama tazo ta kirata. Allah yaso lek'owa tayi bata shigo ba.
"Ki zo ki raka abbanku shopping keda bashir."
Ta saki k'ofar data rike ta juya.
Ajiyar xuciya Hafsah tayi sannan ta mik'e ta d'ora after dress akan kayan jikinta tayi rolling da mayafi sannan ta d'auki wayar ta maidata kwalinta sannan ta mayar inda ta bo'ye ta da farko.
Jin muryar mama tayi a bayanta tana "kiyi sauri fa"
Ta tsorata sosai.Mama ma taga hakan sai dai bata ce komai ba.
Al,adar abbannasu ce zuwa dasu shopping musammaman ita da bashir idan k'annensu suna buk'atar wani abin suna fad'a musu idan xa,a shopping a tawo musu dashi.
Yana jan hafsah ajiki sosai duk da ita ba namiji bace..amma yana hira da ita ya bata labarin Yarintar shi da yadda sukai karatu a boarding school (makarantar kwana) yana nuna mata al,amran rayuwa sosai, niyyar shi shine ta sami kyakykyawan tarbiyya da kwaxo ta zamewa k'annenta kamar uwa.
Abba nason Hafsah sosai ya kan fad'a mata ma wani lokacin "Hafsah ina son ki" (idan tayi wani abu ya burgeshi) yana nuna mata ita wata ce kuma tana da girma Shiyasa yakan kirata da "Yaya." (wasu lokutan idan zai kira ta) yakan ce mata idan k'annenta sun mata laifi ko bashir ya kawo mata raini wani lokacin "Haba yaya aikece babba kiyi hak'uri mana, duk abinshi kin dai girmeshi. Kokuma "Ke fa babba ce, kiyi ha'kuri dole babba sai yayi ha'kuri kinga kece zaki zame musu abin koyi, ki kula da rayuwarki Hafsah kada ki dinga shashanci da shirme"..
Wannan ne irin kalaman abba yawanci a gareta, wanda suna tasiri matuk'a azuciyarta har suka sa mata nutsuwa da girma fiye da shekarunta, don baka tab'a ganin ta tana abu na shashashanci ko rawar kai irin na 'yan matan yanxu, musamman wad'anda iyayensu ke da sukuni irinta..
Komai takeyi cikin nutsuwa take yinsa, bata gaggawa, shi yasa ake ganin kamar tana da 'yanga'.
Ki dinga nutsuwa Hafsah mace da nutsuwa aka santa ki daina gaggawa a al,amra domin gaggawa aikin shed'ance"..
Wannan ne kalaman abbanta ko da Yaushe.
Tsaye ta tarar da abban a falo yai murmushi "To mu tafi koh"?
Sunzo fita daga layinsu kenan taga motarshi zata shigo. gabanta ya fad'i, ta dafe k'irji
"ya salam"
To sunje sunyi siyayya sosai, mama kuma ta bata sautu don tace yau basai taje ba.
Sai wajen 9:00pm suka dawo.
Yaran sai murna suke dama abban baizo da tsaraba ba.
Dariya kawai take so take ita dai ta wuce d'aki ta duba wayarta.
Abba ya kalleta.
"Ko kin gaji ne yaya?
Ta kad'a kai
To maza je ki kwanta ta mik'e ta nufi bedroom d'inta.
Sai da ta d'an watsa ruwa sannan tasa kayan bacci. Ta dakko wayar ta kashe fitila ta kwanta.
5 missed calls ta gani akan wayar.
Sannan da text akan wayar tana cikin dubawa, sai ga wani kiran..
Ta d'aga ta kara a kunne "Hello."
Muryarshi mai sanyi da dad'i ta daki kunnenta. Ta d'an muskuta, kafin tayi magana yace cikin shagwabar nan tashi.
"Haba baby nayi miki laifi ko na kiraki kink'i picking then nazo kuma kika cemin bakya nan, pls mena miki ne..??
Ta bude baki xatayi magana kenan, taga haske ya baibaye d'akin tayi saurin juyowa mama ta gani idonta akan wayar hannunta.. 😳
Shigowa tayi ta tambayeta waye yazo nemanta d'azu? sai ta fara kunna fitila so take suyi magana kan kada ta soma kula wani tunda tasan abbanta baiso..
To kuma tana kunna fitila taga abinda da bata tab'a zato ba... Hafsah da waya to waye ya bata?? dawa ma take wayar??
Ku biyo ni..πŸ˜‡

*Hajeeyarku ce*πŸ‘ŒπŸΌ
*Pls idan kunga typing error ko kuskure kuyi hak'uri ni sabuwa a harkar. Wanna ne first novel di'na..πŸ‘πŸΌ*
*Ina Godiya fans ☺*
*Pls I need your comments to encourage me!*πŸ‘πŸΌ
[1/11, 1:33 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): β™₯️β™₯️β™₯️β™₯️
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
πŸ’”πŸ’”

Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Karemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique in your love heart group members.*



πŸ“„ *11*


*Tsawa* Maman ta daka mata tare da kai mata duka, wanda yaja tsoro yasa wayar fad`uwa a kan gadon.
Caraf mama tasa hannu ta d`auka abin yana bata mad`aukakin mamaki bata tab`a zata ba.

Uban wa ya baki wayar nan."?

Iya rudewa Hafsah tayi ta har ta kasa bada amsa.
"Tashi zaune."
Ta qara daka mata wata tsawar.

Ta miqe cike da fargaba yayin da maman ta zauna gefe gadon.

Ta kafe ta da ido sannan tace, "Ki fad`a mini wanda ya baki wayar nan tun muna mu biyu, idane ba haka ba zan hadaki da abban ku. "
Zufa ta ketowa Hafsah, ya zata yi idan wannan zancen yaje wajen Abba, ai ta ka d'e

Gwara ta fad`i gaskiya tun suna su biyu da maman tunda an kama ta dumu-dumu ai bata da wata mafita.

Cikin Hawaye ta labartawa maman yadda wayar tazo hannunta, Sannan ta qare mata ta kalaman kare kai.

"Wallahi Mama ajye min yayi ya tafi shiyasa na karb`a, kuma Allah ranar na fara ganinshi."


Tana gama zancen, taji mama ta kama kunnenta kamar zata tsinka.
"Ki kiyaye ni Hafsah, wallahi duk ranar da na kuma ganin

3 / 40