ANA MALIK HAUSA NOVELS BY HUMAYRA BULAMA .doc

Author :  Humaira Bulama Category :  Top Hausa Novels 2025

Chapter   9 / 33

24K to 27K   out of 98.8K words

cinyar wani Hadiminsa yana yi masa tausa kansa kuma yana a kan wasu pillows na feathers masu asalin taushi.
Waya ce a hannunsa yana daddannawa kwata kwata baza ka ce hankalinsa yana a kan waenda suke bakin gadon ba, kamar ba buk atarsa ce ta kawo su d akinba.
Ya fi kusan mintuna ashirin Yayinda Hadiman nan mata su uku suke a tsaye kyarr! Ko numfashi da kyar suke jaa kafin da kyar ya magantu ba tare da ya kallesu ba hankalinsa yana a kan wayarsa ya ce  undress yourselves .

A take jikinsu ya d auki karkarwa kamar an jona musu wutar lantarki, dukda mutum d aya ce kawai ta fahimci me yake nufi amma ragowar suma sun d an fahimci yaren nasa& .
Kuka d ayar ta saka ta durk usa tana shirin yin magana ya yi fito, a take sannan da gudu wani hadimi ya shigo ya na zuwa ya durk usa a gabansa kansa a k asa
 Ka kaita mari
Kawai ya ce ba tare da shima ya kallesa ba.
Da a kaika mari d in da yake a cikin masarautar gara a kashe ka ta hanyar rataya a cikin kasuwar garin gashi a k aida idan ka shiga Mari sai ka yi shekara uku ma tukunna za a waiwayeka.
Kuka sosai ta fashe da shi jikinta yana karkarwa tana rok o tana mai neman yafiya a wajen wanda ita kanta ta san bai ma san mecece kalmar yafiyar ba!
A haka aka jaa aka fitar da ita waje babu tausayi babu jin k ai.

Yana fita waje ragowar y an matan suka shiga yin abinda suke tunanin yana nufi hankulansu a masifar tashe dan in dai har hakan yake nufi to alk iyamarsu ta tsaya ne saboda sun san me zai biyo baya sannan a al adar masarautar tun daga kan matan sarki har zuwa kan baiwa in dai a cikin masarautar kike aka yi aurenki aka kaiki gidan Mijinki ya tadda hanyarki a bud e to hukuncin kisa ne a kanki!
Matan sarki da wasu daga cikin masu asalin mulkin masarautar ne kawai ake yi musu d aurin rai da rai a kurkukun sarakuna ko
kuma a yi musu tozarcin da wata sai ta zab i mutuwa ma
da shi, amma ragowar kam musamman ma bayi a washegarin ranar ake tsiresu.

Tsindir haka suka yi suka tsaya a gabansa jikinsu na karkarwa.

Da camerar wayarsa yayi amfani ya gama k are musu kallo ta cikin wayartasa ta hanyar zooming kafin ya ce  su juya, nan ma ya gama k are musu kallo& &
Tsaki ya yi cikin d an b acin rai ya ce  get out!
Da sauri kamar za su zuba ruwa a k asa su sha don murna suka sunkuya suka rarumi kayayyakinsu suka fice a guje tib ir tib ir zannuwansu kawai suka samu damar yafawa suka fice suna masu k ok arin mayar da ragowar suna masu jero hamdala a zuk atansu.

Suna fita ya mik e tsaye cikin d an fushi ya kalli amintaccen hadimin nasa wanda ya yi saurin saukk owa ya sunkuya a gabansa.
Cike da izza sannan ka na iya jiyo b acin rai a cikin muryar tasa ya ce  is that the best you can find?

Jinjina kai Hadimin nasa ya yi ya ce  daga cikin dukkannin Hadimai kamar yadda ka buk ata, waennnan sune kawai muka samu masu irin shekarun dai da ka ambata& Dalilin kuwa shine ka san batun satar da aka yi a parlourn Gimbiya Zakiyya ya janyo an rasa dayawa.

Amma na ga wasu a cikin bayin masu lamba d aya& .

 To hell with them
Ya furta hakan cikin zafi, wanda ya sanya Hadimin na sa yin shiru.

Fuuuu! Ya juya ya fita ransa a b ace, a take Hadimin ya mik e ya bi bayansa yana fita wasu guda goma a cikin masu tsoron k ofar d akin suma suka take masa baya.
****************

BULAMA
'?
0806 402 1951
ANA MALIK!!
Book 01.
Page 07.

Humairah Bulama.
Mikiya writers Association.

Dije tana barin wajen azabar kararar k auyen su Sumayya ta sake k aimi a jikin Ma a. Duk dauriyarsa bai san lokacin da ya tafi kamar zai kifa ya damk i bencin dake ajjiye a gabansa da sauri ba, a take wani irin zazzafan gumi ya shiga tsattsafo masa fiye da farko ta ko wacce b ular gashi dake a jikinsa kamar wanda ya watsa ruwa.
Kad an ya rage bai kurma uban ihu ba, dai dai lokacin da su Oscar suke k arasowa wajen a guje sakamokon ganin halin da yake a ciki shi kuma bugun zuciyarsa ta fara sauyawa ya shiga janyo numfashi da kyar.

A machine suka goya shi suka nufi gida da shi wanda kafin su k arasa gidan Oscar shima ya goga, kad an kuwa ya rage bai zubar da su ba, suna isa ko gama cikakken parking bai yi ba ya diro a gigice ya afka d akin Ma a ya shiga toilet ya kunnawa kansa ruwa wanda hakan ya zamo masa kamar mabud in masifar k aik aiyi.
Allah ya so shi bai
kwab e kayan jikinsa ba dan a hakan sa ya fito yana zabga ihu kamar ba Oscar ba.
Ihun nasa ne ya fargar da Mama ta fito daga kitchen da wuri dai-dai Scorpion ya kamo Ma a yana tafiya da kyar numfashinsa yana fita da kyar sama-sama. Shi kansa Scorpion d in zuwa yanzu ya goga dauriya ce kawai yafi Oscar sannan shi bai zubawa kansa ruwa ba.

Mama tana ganinsu a haka ta nufesu hankali a masifar tashe.
Da kyar Scorpion ya iya cewa  karara ne Mama kar ki matso.
Dan haka ta ja ta tsaya sai
kuma ta k arasa ta je ta shimfid a musu tabarma Scorpion ya k arasa da shi kai
ya samu ya taimaka masa ya kwantar rigingine dan zuwa yanzu shi kam bai
ma san a wacce duniyar yake ba ga numfashi yana ta d ad d aukewa kamar mai
shirin barin duniyar.

Kuka Mama ta saki har ta mik e tana shirin ce musu su tafi asibiti sai kuma ta koma ta zauna dan ta san azaba da bak in ciki ne suke jefa shi a cikin irin wannan halin dan haka ta shiga yi masa tofi.
Kamar kuma wadda ta tuna wani abun sai ta mike ta ce  bara in d auko manja a zuba muku yana rage k aik ayin.
Da sauri Ma a ya ruk o gefen zaninta tana juyowa ya girgiza mata kai kawai.
Ta fahimci baya so ta bar wajen ne dan haka ta koma ta zauna ta ci gaba da yi masa tofi yayinda shi kuma ya lumshe idanuwansa kawai ya na mamakin Dije& .
Da mugun gudu Oscar ya afka cikin kitchen d in ya kinkimo galan d in manja ya shiga kwararawa kansa gaba d aya ya gigice, zuwa wannan lokacin shi
kansa Scorpion duk dauriyarsa ya fara murk ususu kamar mai
shirin fara breakdance, ganin dauriyar fa ba zata kaishi ko Ina ba gashi abin sake k arfi yake yi ya sanya ya mik e ya k arasa ya shiga shafawa jikinsa manja shima, kafin minti d aya sun yi nasha nasha abinsu da manja in ka gansu kamar ma su tallar maita.
Kuma har zuwa wannan lokacin a gigice suke dan su dai ba su ji alamun sassauchi ba.
Mama ita dai tanata kallonsu duk da halayyarsu amma sai da ta tausaya musu, dan haka kawai take ta binsu da sannu.
Shi dai Ma a bai ce komai ba kawai ya lumshe idanuwansa, chaaan! Kamar a mafarki Mama ta ga wani sassanyan murmushi ya sub uce masa.

Sai bayan kusan awa hud u tukunna da kyar aka samu k aik ayin ya d an lafa, ba wai
ya d auke gaba d aya bane kawai dai ya d an lafa. Har zuwa wannan lokacin Mama tana tare da su tanata yi masa tofi shima kuma ta bashi add u o i tace ya yi ta yi, idan ta yi salla ta idar ta yi addu a sosai ta tofa masa, ya d an ji dama-dama haka suma su Oscar da ta basu addu o i ta ce su yi ta yi, amma har zuwa wannan lokacin numfashin Ma a bai
dawo dai-dai ba kuma idanuwansa a lumshe suke& .
Lissafi kawai
yake yi yana mamakin Dije lokaci zuwa lokaci kuma yake sakin wani lallausan murmushin da yake shirin fara firgita Mama.. tabbas yau kam ya had u da wadda ta azabtar da shi cikin sauk i, abunda zaratan maza suka gagara yi yau gashi Yarinya k arama ta yi, dan tabbas shi kansa ba zai iya expressing kalar uwar azabar k aik ayin da ya kwasa a yau d in ba.

Sai da ta ga sun d an fara nutsuwa tukunna ta nemi jin ba asi, har Oscar ya bud e Baki Ma a ya yi saurin juyawa ya zuba masa rinannun idanuwansa da har yanzu basu kai ga fara dawowa dai-dai ba.
Shiru ya yi ya had iye
maganarsa, ya sunkuyar da kansa k asa zuciyarsa kamar zata fashe tsabar takaici! Tabbas yau idan Oga ya hanasa halaka Yarinyar nan wallahi watak il sai jininsa ya hau idan bai kamu da ciwon zuciya bama kenan! Ko da ace bai halaka ta ba to Yarinyar ko y ar gwal ce ya kamata a barsu su yi mata tambarin da har tsufanta ba zata tab a mantawa da shi ba.
Scorpion kam shi bai yi tunanin yi mata komai ba dama dan ya san Oga ba zai tab a bari ba (kamar kullum), amma fa shima ya shak a dan har yanzun bai gama dawowa dai-dai ba, wai kamar su ace wannan y ar Yarinyar ta haukata ta gigita a cikin k ank anin lokaci amma gashi da ikon Allah haka nan suna ji suna gani za su bar komai ya wuce saboda ba su isa yin komai a kai ba.
Shiyasa ya shiga zaginta da aibantata kawai a iyaka cikin zuciyarsa kamar wani Yaro dan ya san bai isa ya yi a fili ba.

Sai da suka sake nutsuwa tukunna Oscar da Scorpion suka ce masa  Bara su je su kimtsa
Ko da suka fita sai da suka bawa jama a tsoro Allah ma ya so su duhun dare ya iso, yayinda waensu ma da kyar suka iya gane su, haka nan suka wuce zuwa d akunan su da suke haya a wani gida mutane suna ta satar kallonsu dan ba su Isa su yi k iri-k iri ba.

Suna fita Mama ta mayar da kallonta ga Ma a wanda yake nan kwance a kan tabarma har yanzun idanuwansa a lumshe. Fuskar tasa ta k urawa ido a take ta ji duk ta muzanta! Babu wanda zai kallesa sau d aya ba tare da ya fahimci wayene shi d in ba.
Allah ya d aura mata matsanancin son d anta Ma aruf dan zata iya cewa babu wata uwa da take son d anta sama da ita a kaff fad in duniyar nan, shiyasa take jin tsoro a duk lokacin da irin wannan ciwon nasa ya tashi, kuma take gujewa duk wani abunda zai tada masa ciwon nasa, dan tana matuk ar jin tsoron abunda zai rabata da shi dan haka take kare duk wani abun da zai janyo b acin ransa, wanda hakan ya sanya take ganin kanta as selfish take kuma jin tsoron ranar da zata tsaya a gaban Ubangiji ta yi masa bayanin amanar da ya bata, ta san tana iyaka bakin k ok arinta kuma tana addu a ba dare ba rana amma tabbas wani abun har da kasawarta&
Addu a ta shiga yi masa sosai tana zaune a hakan& .ta jima tana addu a tana mai neman taimakon Ubangiji kafin chaan ta sauk e wata nannuyar ajiyar zuciya
 Babu aure babu sana a babu girma, ko yaushe Allah zai shirya min Ma aruf d ina??
Ta yi maganar da ita a tunaninta a zuciyarta ta yi ba ta san a fili ta yita ba.
A hankali ta ga ya bud e idanuwansa ya zuba mata su, wanda sai a lokacin ne ta fahimci ashe maganar tata ta fito fili.
A hankali ya gyara ya mik e ya zauna kafin ya d an k uraa mata ido sai kuma kawai ya mik e ya ce  Bara in je in yi sallolina
Daga haka ya mik e da kyar dan har yanzu k irjinsa bai dawo dai-dai ba. Ya wuce zuwa d akinsa.
Ta d an jima a zaune a wajen kafin chaan kuma ta mik e itama ta wuce bayi dan har an fara kiran sallar isha.


Cikin tsananin tashin hankali Inna ta nufi k arshen tsakar gidan inda mutanen da suka kinkimo Ya Muhammad suka nufa da shi.
Jikinta har karkarwa yake yi tana isa ta durk usa a gabansa ta shiga duddubashi a lokaci guda tana tambayar  mai ya same shi?
Wani Yaro ne ya ce  tare suke shi da Dije yana tambayarta  mai ya sa ta je wajen Ma a ta bari ya rik e mata hannu , sai kuma kawai ya yanke jiki ya fad i.
Difff!! Haka kowa ya d auke wuta hatta Kaka wadda take ta sababin  kar a wani d aga hankali ai hakan ba komai bane tunda dama an riga an san da zaman ciwon nasa na hauka .
Sheshshek ar kukan Dije ne ya ci gaba da tashi a tsakar gidan, cikin raunin da ba d abi arta ba ta matso tana zuwa ta durk usa a kusa da Inna tana cewa  Inna mu kaishi asibiti, kar yau ma ya s& 
Wani irin gigitaccen mari Inna ta sauk e mata wanda ya sanya ta yin shiru a lokaci guda kuma ta shiga shock! Ita da gaba d aya al ummar gidan na tsakar gidan da masu lab e dan waenda za su ce sun tab a ganin Inna ta sakawa Dije hannu k alilan ne a cikinsu, yawanci in zata hukuntata sai su kad ai da daddare take yi.

Cike da tsana Kaka ta ce  ai ba ki ga komai ba! Wallahi ba ki ji komai ba Halima wannan y ar taki sai ta saka ki kuka da ciwon zuciya, kuma yanzu ai kin makaro dan lokacin hukuntata ya riga ya wuce ko kin yi a banza dan shi reshe tun yana d anye ake tankwara shi idan ya riga ya bushe aka ce za a tankwara sa to karyewa zai yi.
Tsakanin Dije da wannan Yaro kuwa za ki ce na gaya miki wallahi komai ya riga ya gama wakana sai dai kuma kar a kuma!
Tana gama fad in haka ta juya ta shige d akinta zuciyarta fesss!! Idan akwai abunda take so a duniya to bai wuce ta ga Halima da y ay anta sun wulak anta sun tozarta ba.

Magana Dije ta yunk ura za ta yiwa Inna Minu ya daka mata wata razananniyar tsawa  wuce ki shige ciki!!!
Da sauri ta mik e tana kuka sosai ta shige ciki Hankalinta a masifar tashe ranta a b ace.

Tana wucewa Mallan ya ce  a kai masa shi d aki & ..
Tun daga nan Mallan ya rufu a kan Ya Muhammad shi da wani Yaron sa aka kira Likitan bayan layinsu shima ya zo amma ba a samu Ya Muhammad ya farfad o ba sai k arfe sha biyu na dare shima kuma da ihu ya tashi abunda aka fi gudu kenan dan duk lokacin da ya suma ya farka da ihu to sai an yi sama da wata d aya ana abu d aya.
Har wannan lokacin su Dije ba su rintsa ba haka wasu jama ar ma a cikin gidan dan d aya bayan d aya suka dinga shiga d akin Inna suna yi mata jaje tun suna d ari-d ari har suka ware suka shiga dannarta.
Kaka ita ma ba ta rintsa ba dan jira take ya farfad o a gama da shi Dije ta zo ta bar mata gidan d anta dan ta ce  wallahi tunda ta illatata to ta gama zama k ark ashin inuwa d aya da ita.
Dalilin ma da ya sanya ta d an d aga k afa shine kukan da Mallan ya saka mata..dan suna tsaka da yiwa ya Muhammad add ua bayan Maghrib sai gata ta zo, ta tsaya ta ce  ko Dije ta fita daga gidan ko ita ta tafi, shi kuma Mallan dama already hankalinsa a tashe yake ga shi shirun da ya ga Inna ta yiwa Kakar yau ya san definitely akwai matsala a gaba ga Ya Muhammad ya k i ko da motsi ne shiyasa kawai ya saka mata kuka wanda kukan da taga yana yi ne ya sa ta d an d aga masa k afa ta na jira ya gama ya zo ya same ta a yi ta ta k are.
Asabe kuwa ta na gefenta in banda famfo ba abunda take yi mata ita kuma tana sake hawa zuciyarta na d ad a yin zafi tana ji idan ba ta kori Dije daga gidan ba to ba ta haifu ba kuma ba ta haifa ba& &
Musamman ma da ta lissafa ta ga wannan d in dama ce ta same ta a b agas da zata yi amfani da ita ta zartar da k udirinta na shekara da shekaru, shiyasa ta zage dantse ta kuma saka a ranta tabbas ba zata yi sanya ba.

BULAMA
'?
0806 402 1951

ANA MALIK!!
Book 01.
Page 08.

Humairah Bulama.
Mikiya writers Association.

Ciki-ciki ya yi sallama ya d aga labulen d akin ya shiga. A zaune ya sameta ita kad ai kamar kullum tana karatun Alk urani.
Bata kulashi ba shima bai katseta ba bayan ya nemi waje ya zauna kawai sai ya yi shiruuu alamun ya yi zurfi a tunani.
Sai da ta kai aya tukunna ta yi doguwar addu a sannan ta juyo ta kama kanshi ta shiga yi masa addu o i& .
Sai da ta ida tukunna suka shafa a tare, daga nan d akin ya yi shiruuu& .bayaga d azu da suka gama shan azabar karara ta tayasu da

9 / 33