Chapter 10 Reading AJEEMAL Book 2 Hausa Novels By Khaleeseart Abdullahi Raeys.txt Arewa Novels

AJEEMAL Book 2 Hausa Novels By Khaleeseart Abdullahi Raeys.txt

Author :  Khaleeseart Abdullahi Raeys Category :  Hausa Novels 001

Chapter   10 / 24

27K to 30K   out of 70.1K words

ko wani kauna ba.

Sannan ke ma ina mai baki shawara ki mance da Kamal ki fiskanci rayuwa auran da zaki fara da wanda zai zama shine jigo yanzu cikin rayuwarki duk da kin tsinci rayuwar auranki ta wani siga da ban kuma ina tayiki alhinin hakan ina kuma taya ki bankincikin kasan cewar Aunty Heelah amatsayin wacce zaki zauna da mijin ta ku zama kishiyoyin juna.,




Ajeemal

Page70

By oum amreesh

Page 72

_______Nasan halin yar uwata sosai tamakar yanda nasan yunwa cikina ina mai baki shawara ki dage da addu'a sosai har lokacin da Allah yasa ta fahimci ma tsayinki awajan mijinta , ina fatan Allah ya yayyafawa lamarin ruwan sanye komai ya tafi daidai cikin kwanciyar hankali because nasan Aunty Heelah da kuma hali irin na ta, akarshe nima zan sanyaki cikin addu'ata kuma ina rokonki da kidaina guduna haka nan nima ki dauke tamkar yanda kika dauki su Reeda nima ki daukine daya daga cikinsu because muriga munzama daya yanzu Nabilah ta fad'i ta na riko hannayen Nisha,.

jiki a sanyaye Nisha g'yada kai tare da sunnar da kai kasa maganganun Nabilah duk ya sa ke kashe mata jiki tsoron ta ya k'araru matuk'a bata san ya zata fara fiskantar wannan k'addaran auran ba sam ji ta ke ina ma duk wanda nan abubuwan da ke faruwa da ita ya kasan ce mafarkine ba gaskiya ba da kuwa inta farka bazata sake komawa wannan baccin ba girjinta sai bugun goma goma yake da ga Heelah har mijin nata tsoron su ta ke ballai kuma yanzu da ta ke kokarin fara rayuwa cikinsu wani irin yanayin zata tsinci kanta a tare da su a tuna ninta dukansu babu mai rang'wamen fiskar da zataji saukin mu'amala dashi. rintsa ido idanu Nisha tayi tana furzar da wani irin zazzafan ajiyar zuciya ta shiga karanto wasu addu'oi a hankali tana jin zuciyarta dan sanyi kadan kad'an kamar ana yayyafa mata ruwan sanyi,

ganin halinda da ta shiga yasa Nisha ta bawa Nabilah tausayi nan ta cigaba da tausan ta tare da bata shawarwari masu kyau wadan da zasu amfane ta, haka wunin yau Nisha ta yi shi cikin sanyin jiki har wani zazzabi zazzabi ta ke ji ya dawo mata, da dare bayan sun kammala dinner sun zauna bisa parlour suna fira kamar yanda suka saba, wanda nan Ammi ke shaida wa su fareeda ce wa Saturday and Sunday suna da private class na koyan girke-girken zamani kasancewar bikinsu yana ta karatuwa kuma ba abunda suka iya na ciman zamani ballai na gargajiya wacce zasu nishadantar da mazajensu Dan haka ta yanke shawaran kaisu akoya musu delicious kala kala saboda afita kunya shi ya sa ta ware wadan nan kuwanakin because sauran lokutan basu da lokaci saboda karatunsu, ranar murana gurin su Fadeelah ba a cewa komai.

Suna tsaka da firanne wayar Nisha ta shi ga k'ara alamar kira nan Nisha ta kalli screen d'in wayar salma ce ke kira duk duk da kasan cewar tun safiyar ranar ta ke ganin k'iran ta but takasa dagawa because bazata iya magana dan ta San da ta fara magana zata fashe da kuka shi ya sa ta ke gudun ta d'aga mata hankali ana tsaka da shirin bikinta dan ta san duk wani damuwarta damuwar salma ne haka duk damuwar salma da muwarta ne sun d'auki juna tamkar jini d'aya sam basu yi tsammanin rabuwa haka lokaci daya ba, abaya da suke rayuwa tare basa kwana d'aya ba su ga junansu ba ba tare da dalili mai karfi ba amma gashi yanzu sun rabu sai ayi wata basu ga junaba sai awaya kawai suke haduwa , yan zunma kifa wayar ta yi gefenta kanta kasa ta ci gaba da murza Dan ya tsanta tana ta karatun zuci

"Ba kiran ki ake awayar bane?" Hajia ta tambaya tana kallon Nisha, Nisha dagowa tayi ahankali ta kalli Hajia gamida g'yada mata kai tana fadi'n

"Eh kirane "

"Waye ya ke kira ki ? d'auka ki je bedroom ki amsa kiran mana kar mu da meki da ha yaniyar mu" ba musu Nisha ta dauki phone d'inta ta nufi bedroom tareda neman guri ta zauna ta shiga kiran salma time d'in idanunta haar sun kawo ruwa, ba wani dugun rigin carab salma ta dauki wayar ta suma magana.

"Haba Nisha why ba kya picking call d'in sai kinga dama duk kinsa hankalina ya tashi wai mai take faruwane "salma ta shiga jerowa da Nisha tambayoyi dan ko sallama ba tayi ba.

"Bakomai" Nisha ta amsa mata can kasan ma koshinta,

"Ko bazaki samu zuwa bikin nawa bane kika kasa fad'a min"

"Eh " Nisha ta ce time d'in da ta ke dab da fashewa da kuka

shiru salma tayi na Dan wani lokaci ba wanda yace kala acikinsu.

"Nisha kodai dunyar tayi miki dad'in da zaki iya watsi danine haka daga jiya zuwa yau na kiraki ya fi akirga but ba kya picking yanzu koma naji yanzu kuma da muke magana sai na fahimci kamar baki son magana na da meki , ko dai wani laifin na miki duk da nasan yanzu munyi nisa da juna bana tunanin hakan, dan wani abune ya ke faruwa da ke ya kamata ki fad'a min because ni abokiyar fad'a wa matsalar ki da damuwarki ne ko abunda ya shafeki please ki fad'a min in wani abunne ke da munki" nan fa taji Nisha saki wani kuka waiwai kamar karamar yarinya, ba k'aramin ta shin hankali salma ta shiga ba jin yanda Nisha komai ta ke kuka kamar wata k'araman baby nan Salma ta rude ta shiga tambayarta ba sanin kukan but ba amsa, tambayar duniyar nan salma tayiwa Nisha amma ta ki kulata, nan Salma ta ka tse wayar daga haka Nisha ta kwanta saman bed d'in ta ci gaba da koke koken nata a hankali ba tare da sautin ya fito anlura da halinda ta ke ciki ba.

Sai da ta yi kukan ya isheta kafin ta g'yara kwanciya dan ko kayan jikinta ba tasamu daman canzawa ba taja blanket ta rintsa ido tana sauke ajiyar zuciya kanta harya suma ciyo saboda kukan da ta sha yau ko tunanin kiran Ajmal taji ko yana da bukatan wani abin duk da tasan bai cika bukatan wani abin da dare ba infact ma bai cika dawowa da wuri ba koma ba dan hakan ba bazata bi ta kanshi ba, ta masa na Allah duk da ba wani koshin lapia garai ta ba, da safen nan ba k'abisa da aramin gajiya tayi ba ga kuma haushinda ya kuma bata tana cikin wannan yanayin har bacci b'arawo ya sace ta, washe gari karfe gusan 10 Nisha ta kammala ta shiga jerawa dining table kamar yanda ta sa ba parlourn shiru sai karan TV da ya ke ta aiki sai kuma ita da ta ke ta faman Kai kawo tsakanin kitchen da dining area tana shirya breakfast ,.

Nisha harta gama komai ta kimtsa ko ina ba kwalkiyan ko mutum daya da taji duk da tayi tsammanin tun shigowa ta zata ci karo da Heelah ko ta ji motsin ta but sai ta ga sabanin haka wanda hakanne ya bata daman yin aikinta cikin na tsuwa, ta nufi upstairs direct bedroom d'in Ajmal ta nufa ta g'yara masa kamar yanda yayi korafi, tana zuwa bakin door d'in ta shiga yin nocking a hankali bugu daya zuwa biyu ba ayi magana ba hakan yasa ta murda handle door d'in ta ku tsa kai bakinta dauke da sallama ta karisa shiga, .

bedroom din ba kowa ciki duk da anrage light d'in dakin ba komai ta ke iya gani ba d'an haka ta karisa cikin tsakiyar dakin ta nufi switch light d'in ta kunna nan haske mai kyau ya gauraye bedroom d'in nan fa idonta ya hango mata Aheel da ke kwance yana sharan bacci yana rugume da pillow kamar kamar zai shige ciki ya rungume shi tsam ajikinshi Nisha ba ta san sanda ta saki murmushi ba tana mai kallon kyakykyawan face d'in Aheel mai kaman antsaga kara da papanshi, karisawa tayi ta zauna bisa bakin lallausan bed d'in sai da ta lumshe ido tsabar taushi da laushin bed din, cike da murmushi Nisha ta kai hannu ta shafo gefen face d'in Aheel, kamar wanda ya yake jira a taba shi aiko tar ya bude idonsa bisa face d'in Nisha Aheel na ganij Nisha zaune gefen shi tana ta zuba masa murmushi, shima washe mata baki ya shigayi cike da farin ciki ganinta ya fad'a jikinta tare da rungume ta, cikin farin ciki da kyawan yaron Nisha ta dinga shafa bayanshi a hankali kafin ta dan zame jikinta daga nasa ta shiga tambayarshi


"My little yau ba school ne naga Kanata bacci har wannan time d'in, "washe baki ya kuma yi yana fadi'n

"Laaa Aunty jiya fa mukayi hutu, kuma hutu mai yawa aka bamu har 3 weeks Aheel ya fad'i ya na nuna da yan tsun hanunsa uku murmushi Nisha ta tayi gami da fadi'n

"Good tasu muje to baccin ya isa haka" , nan ta juya masa baya alamar ya hau bayanta shikuwa cikin zumudi ya dale bayan Aunty Nishansa tare da sakalo face d'insa gafen wuyarta yana ta dariyan jin dadi daga haka suka fice daga parlourn bedroom din Aheel suka nufa ta sa ya cire wannan tausasun kayan baccin da ke jikinsa ta bashi dan k'aramin towel ya daura yashiga bathroom domin ya wanke jikinshi yayinda ita kuma ta nufi wardrobe ta dauko masa kyawawan kaya t shirt and jeans rigar white color sai black jeans tana jin yanda Aheel ke ta wasa cikin toilet Dd'in yana tsalle tsalle yana wasa da ruwa ganin bayida niyar fitowa yanzu yasa no Nisha mikewa tashiga toilet d'in ta taimaka masa yayi wankan kafin suka fito ta kimtsashi tare da sanya masa kaya kafin ta jawo hanun shi suka nufo downstairs.

Dining table ta nufa dashi ta zaunar da shi ta dauki plate ta sanya masa breakfast duk abunda ya nuna ya naso shi ta sanya masa ta tura masa gabansa ya suma ci, daga haka ta zame jiki ta koma bedroom din.dining zuciyarta daya tunfi toilet domin fara wanke shi murda handle d'in tayi ta shiga , zaune yake cikin bathtub yayi tsam da ranshi idanuwansa a lumshemaganganun Doctor fu'ad sai d'a masa yawo cikin kunnuwa su ke sam ya kasa gas gata maganganun sa because yasan doctor fu'ad dasa zulaya cikin lamauransa in ba daga wajan su Daddy ko wajansu hajia ya ji bataun kai tsaye daga gare suba bazai taba gas gata hakan ba, idan kuma harta tabbata hakan lamarin bazai taba daina bashi mamakiba.

ko Time d'in da aka aura masa Heelah ba waii dan ba yi da ikon hanasu ko da dakatar da su bane kawai ya kyalesune ya zuba musu ido ba wai dan ya rasa yanda zaiyi bane but hakan ba shi zai basu daman jogana masa wannan wata mace ba especially wacce baisan wacece ita ba bai kuma san daga ina ta ke ba ballai asan asalin wacce ita, turo door din toilet d'in da akayine yasashi bude ido da sauri don ganin wake kokarin shigo masa bathroom ba neman izini, Nisha ya gani ta shigo kai tsaye wacce itama da alamar ba ta lura da shi ba because toilet d'in yana da girma sosai tamakar parlourn wani gidan fiskarta dauke da fara'a takarisa gaban katafaran mirror da ke cikin toilet d'in da ya ke fara kallon mutum yayinda ya shigo tsayawa ta yi tana hango kanta ciki rabunta da ta tsaya ta kalli kanta madubi harta mance time d'in kallon kanta ta ke sosai tana karawa tare da shafo face d'inta ta jikin mirror ganin tayi har wani kumatu tayi kuma ta kara haske sosai.

tabbas itama yau tayi mamakin yanda taga yanayinta ya canza gaba daya hutu ya zauna mata haka ta dinta juya lallausan hannayenta tana kallo kamar ataba jini ya fito time daya kuma fara'a ta ta dauke face d'inta ya koma face d'in jimami saka makon tunawa da maganar salma na cewa

'duniya yayi mata dad'in da zata iya mancewa da ita'

duk da ba ta yi tsammanin wannan furcin daga gare ta ba because ita dai a iya saninta bawani jin dad'in da zata tsinci kanta aciki ta kasa tunawa da aminiyar ta kawar yarinta abokiyar cin mushe su kashe su bunne tare wasu zaffan hawayene suka gangaro mata kafin cikin hanzari ta shiga goge hawayen ta suma waige waige don fara aikin da ya kawota kar ogan nata ya zu ya taddata anan tana ta karanta wasikar jaki, wani ihu Nisha ta kawo sake tana sallati gamida rintsa idanunta because ganin Ajmal time d'in da ya mike ya na kokarin daura towel bisa waist d'insa tana kuma yin baya ganin Ajmal tsaye cikin bathtub yana kokarin daura towel bisa waist d'insa, baya Nisha ta kuma yi da sauri idanuwanta a rintsai jikinta sai k'yarma ya ke a aikuwa sai timmm kakeji ta zame santsin tailed ya zamar da ita a zafafe ta ta kuma mikewa tanufi door sai da ta bude ido kafin ta murda handle d'in tafito ta watsa aguje ta fice.



Ajeemal
Story and writing
by
oum amreesh

Page 72



Aheel na zaune bisa dinning table yana breakfast kamar yanda Nisha ta barshi sai ganin Auntynsa yayi tafito fuuu kamar wata mota ta wuce ta fi ce da gudu daga parlourn ko waiwaye ba ta yi Aheel bin ba yanta yayi da kallo tare da kai kallonsa upstairs dan ganin mai ta ke wa gudun dan ba k'aramin tsoro ta ba shi ba sai zare ido ya ke amma ba kowa da ke biye da ita nan ya shi ga zamowa daga kujeran da nufin bin bayanta but sai ya ji muryan mom d'insa ta kira sunansa wanda ya sa ya mai da hankalinsa garaita ya shiga washe mata baki tare da kokarin karisawa gareta yayinda ta ke sakkowa ta na sanyi cikin kananun kaya wata half vest sai d'an wani gajeren wando iya gwiwa ta tufke gashinta a tsakiyar kanta sai lilo ya ke bayanta ta yi kyau da ita, Cike da murmushi ta kariso ga Aheel ta re da sa hanu ta sun kuci d'an nata tana fadi'n

"Good morning in this morning my love"

Morning Mommy Aheel ya fad'i gamida kwantar da kai jikin mommynsa

" What are you doing here" Heelah ta tambaya tana mai kallon Aheel ta na kuma kallon dining table d'in da kawata shi da kyawawan girke-girke kala-kala ta shaida wannan aikin Nisha ne nan ta shiga hararo abubuwan da ke jere bisa dining tana tabe baki nan Aheel ya shiga zamowa daga jikin mom d'insa kafin Heelah ta direshi akasa ta na kallonshi.


"Mom taho ki zauna kiye breakfast Aunty Nisha na ne ta yi mana delicious mai dadi " ta ho ki zauna ke ma " Aheel ya fad'i cike da murna yana washe baki gamida jawo mata kujera alamar ta zauna but Heelah sai Jan wani banzan tsaki tayi tana tabe baki tana kallon Aheel da ke ta rawar Kai wai Aunty Nishansa tabdi.

"Come and seat Mom" Aheel ya kuma fad'i yana kallon mom d'in nasa wacce ke ta faman hararo shi da shi da table d'in gaba daya tana fadi'n

"Kai da Allah rabu da ni mai zan zauna na ci a wannan tsiyar Allah kaidai yasan hade haden da ta ke cikin girke-girken nan da ta ke tana jan hankulanku da tunanin ku ku ke ta wani ribibi a kanta ta ga ma siye zuciyoyinku da yin nasara a kanku to nikam na fi karfinta ta Allah ba ta mutum ba muna fukar banza kawai Heelah ta karisa fad'i hadai da jan wani dugun k'wafa zuciyarta ta sai zafi ta ke ita ta rasa ya zatayi da wannan yarinyar gaba daya ta shige mata hanci da k'udunduni juya baya tayi yayinda ta hade hannayenta a k'irji ta na kada kai ta na tunano irin hanyar da zatabi da Nisha, shikuwa Aheel shiru yayi jikinsa duk yayi sanyi ganin yanda mom d'insa ke ta surfa masifa akan Auntynsa duk da baisan inda zantukan na ta suka do sa ba baikoma fahimce ta ba.

Shiru yayi ya na ta kallon mom d'insa da ke tsaye ta na ta kaiwa da kawowa ta kasa zama gefe guda kuma ya hangi papansa wanda ya ke sakkowa daga upstairs yana sanye cikin kyakykyawan black suit and black shoes sai bakin glass da ya sanya ya tushe idanuwansa, da gudu Aheel ya taho ya d'ale jikinsa time d'in da ya gama karisowa, cike da murmushin nan na shi Ajmal ya dago Aheel ya sunbaci kumatunsa kafin ya sauke shi kasa karfin Aheel ya ja hanun papansa suka zauna bisa dining table Ajmal ko kallon inda Heelah ta ke baiyi ba ballai ya San da tsayuwarta ya nemiguri ya ya zauna,

Heelah tunda ya sakko ta ke binshi da kallo harya karisa dining ya zauna kafin ta tabe baki gamida matsawa kusa da shi ta ja kujera ta zauna ta na fad'in

"good morning dear"

"Morning" Ajmal ya amsa cikin cool voice na shi ya na mai kokarin kai hanu dan serving din kanshi cikin hanzari Heelah ta a ga je shi ta shiga serving d'insa shikuwa bai dakatar da ita ba because ya na bukan hakan , tana gama serving d'insa itama tayi serving kanta ta zauna ta tusa plate agaba tana ya mutsa fiska sai ka ce wanda aka ce ta ci dole gefe kuma Ajmal breakfast ya ke cikin kwanciyar hankali yayinda Aheel ke gefe shima sai kada kai ya ke time din da ya ke shan daddad'an yoghur fruit ya na santi wayar Ajmal ne ya shiga ruri alamar Kira wanda ya sa shi dakatawa daga breakfast din ya kai kallonsa ga phone din ya kalli screen din wayar dan ganin mai kira, sharewa yayi ya ci gaba da cin abincin sa Heelah sai mika wuya ta ke tana kokarin hango sunan da ke makale jikin screen

10 / 24