Chapter 7 Reading AJEEMAL Book 2 Hausa Novels By Khaleeseart Abdullahi Raeys.txt Arewa Novels

AJEEMAL Book 2 Hausa Novels By Khaleeseart Abdullahi Raeys.txt

Author :  Khaleeseart Abdullahi Raeys Category :  Hausa Novels 001

Chapter   7 / 24

18K to 21K   out of 70.1K words

tasan kaunar da Kamal yakewa Nisha tabbas bazata taba bari wannan lamarin yafaruba gashi yazo mata time din da yariga ya makara wanda hakan yajawo tonu abunda aka rufe wanda dama duk daren dadewa zaibud'u,.

duk da sunso abi abun daki daki Amma zuwan Kamal duk ya cakuda abubuwa saboda shegen zuciya irin tashi Ammi hararo Kamal tayi wanda keta safa da marwa cikin dakin cike da damuwa, ba ji mawa Kamal yaji ki ciniyar bude geat aiko cikin sauri yafice ya taroshi cikin hanzari suka kariso shigo cikin bedroom din, ganin Nisha kwance idanuwanta arufe Ammi na gefen ta cikin damuwa yasa doctor fu'ad saurin karisawa kusa da bed din yana tambayan ba'asin meyafaru da ita, saidai ba amsa saima Ammi da ta kai kallon ta ga Kamal wanda shima itan yake kallo ta kuma cilla masa harara wanda ya sa shi sunnar da kai kasa cikin na dama jin shiru ba wanda ya samu daman ba shi amsa yasa yace su ba shi guri ya dubata ba musu Ammi tamike tafice Kamal ma ya rufa mata baya haka suka fito sumu sumu da su.

Gefe Ammi tazauna bisa sofa ta raf ka uban tagumi shi kuwa Kamal bai samu daman zama ba sai kaiwa da kawo yake tsakiyar parlourn, jim kadan doctor fu'ad ya fito wanda suna ganin fitowar shi yasa suka nufoshi suna tambayan shi ya jiki Nisha ya amsa musu da

"Shi is fine but baku bani amsa ba maiyayi causing dinta shiga wannan ya nayin doctor fu'ad ya kuma tambaya yana kallonsu Kamal dai har yanzu bai iya cewa komai Ammi ce ta saukar da ajiyar zuciya jin kyakykyawan labari Nisha na cikin koshin lapia, takalli doctor fu'ad ko ma wa tayi ta zauna kafin tayiwa doctor fu'ad nuni da ya zauna dan yi masa ba ya ni.

Dan muskutawa Ammi tayi tagayara zama kafin takalli doctor fu'ad wanda ya mata zoro yana sauraron abinda zata fad'i, doctor fu'ad kai ba mutumin da za abuyewa komai bane, kamar yanda kasani shekarun baya da suka wuce Hajj mama itace silan hada auran Ajmal da Heelah , to halinda ake ciki yanzu wasu kwanaki dasuka wuce Hajia tasake hada auran Nisha da Ajmal but tayanke hukunci ne cikin bacin rai bisa rashin kunya da rashin girmamawa da Heelah da mahaifiyarta suka zo suka gabatar kwanakin baya akan wata yar hatsaniya da ya faru tsakanin Raheelah da Nisha nan Ammi tashiga korawa doctor fu'ad yanda lamarin yakasance da kuma dalilin da yasa Hajia ta zarta da wannan hukunci ba tareda tayi la akari da afkuwan wani matsalaba
dan kauda kai Ammi tayi tana murza hannayenta irin na shiga damuwa tace,"

"Duk tsawon kwanakin nan inata kokarin na fahimtar da ita cikin natsuwa bisa auran Ajmal da ke kanta amma senaji nakasa maganar tayimin nauyi because bansan da wani ido zan kalletaba kuma bansan wani irin kallo zata mana ba bisa amanarta da mukaci nadaura mata aure da da' nmu ba tareda yarda ko amikamatrta ba , sam bamu san Kamal yana da ra ayi akantaba se yanzu yasameni da batun soyayyarsu wanda yanzu shiyayi causing wannan problem din banso ta tsinci lamarin ta wannan sigarba, Ammi tafad'i tana sunnar da Kai kasa ,

wani goron numfashi doctor fu'ad ya sauke tareda jinjina kai yana mai mamakin lamarin, yama rasa tacewa but tawata fiskar yaji dadin kasan cewar hakan because tun randa yafara ganin yarinyar ya yabawa hankali da nisuwarta koma ba komai yasan zata kula dashi sosai fiye da tuna ninsa to amma yanda zai karbeta amatsayin mata yake tunanin because koda yakarbeta amatsayin mata yasan Nisha bazataji dadin zama dashi especially yanda bai gama gamsuwa da itaba, dan gyaran murya Doctor fu'ad yayi kalli Ammi yana fadi'n

"Amma senake ganin kamar bai kamata acigaba da boye batun aure tsakaninsu ba duk da ita Nisha tasani yanzu shima Ajmal yana da hakkin yasan nauyin da aka daura masa or yayi accepted or rejected dan haka boyewa bashi dawani fa'ida kamata yayi yayi azauna dasu ko duk susan matsayinsu wannan shine shawaran da zan iya bayarwa doctor fu'ad ya fad'i yana kallonsu Ammi da kamal wanda yayi zoro daga gefe yana jimami, dan gyada kai Ammi tayi alamar gamsuwa da maganar tashi batare da ta iya sake cewa komai ba,

"so nizan wuce zuwa gobe zandawo naga yanayin jikin nata duk da ba wana matsala bane kawai tsoro da firgici ne yayi causing," doctor fu'ad ya fad'i tareda mikewa nan idonsa yasauka kan su Fadeelah da Reeda wanda suke tsaye bakin door Wanda basu ankara da suba balle susan da tsayuwarsu sungama jin komai jikinsu duk asanyaye cikin sauri suka kariso ciki suna kokarin nufa bedroom din dan ganin halinda Nisha ke ciki cikin hanzari doctor fu'ad ya dakatar da su gamida fad'in,"

"Please karku dameta yanzu because tana bukatan hutu, so kudan kara hakuri"

jiki ba kwari suka nemiguri kusa da Ammi suka zauna suka sanyata tsakiya kowaccensu tajin gina head dinta jikin shouldern Ammi cikin damuwa, doctor fu'ad binsu kawai yayi ganin yanda sun wani lagwabe jikinsu duk yayi sanyi dan girgiza kai yayi daga bisani yayi sallama da Ammi yafice Kamal ya rufa masa baya jiki amace, seda Kamal yaraka doctor fu'ad harbakin motar sa kafin sukayi shaking hand doctor fu'ad ya shige motarsa yamata key mai gadi yabude masa geat yafice daga bisani Kamal shima ya juya cikin gidan direct part dinsa ya nufa inda ya iske Nabilah bisa sofa tana danna wayarta jin motsin shigowar Kamal yasa tamike cike da murmushi but lokaci daya kuma murmushin ya kawar kan face dinta ganin Kamal cikin wani yanayin wanda bata saba ganisa cikiba,

Direct bedroom taga yajufa ko inda take bai kallaba aikuwa cikin sauri itama ta tashi tabi bayanshi, koda tashiga bedroom din bakin bed taga ya yazauna yayi juguk dashi hakan yasa Nabilah karisowa inda yake tadurkusa saman carpet tadaura hand dinta saman cinyarsa tashiga tambayansa meke damunsa amma se shiru yayi bai kulataba,

" Please ya Kamal kafada min meke da munka ni matace agareka bai kamata kaboyemin matsalar data damekaba"

"ko nice nayi wani laifin ban saniba kasanar dan" ganin yanda take masa magiya duk tashiga damuwa ganinsa haka yasa yace

"Please Nabilah banason yawan tambaya ni ba abunda yake damuna so kidena damun kanki" yana fadi'n haka yamike yanufi toilet jiki ba gwari Nabilah tamike tafito daga bedroom din takoma parlour tanemigu tazauna tana tunanin meyeke damun Kamal taganshi cikin wannan halin, jim kadan taga ya fito cikin wani shirin ya fice ba tareda ya kalletaba balle yace mata wani abin, komawa tayi ta kwanta kankance me hawaye suka shiga zarya cikin idanunta sam bataji dadin kasan cewar sa cikin wannan yanayin ba to kowani laifin tayi masa bata saniba kamata yayi yasanar da ita ba yadau zafi hakaba,.

Guraren karfe 9 na dare Nisha tasaki wani dugun nufashi kafin tashiga kiciniyar bude ido seda takarewa bedroom din kallo sannan tasauke ajiyar zuciya tadauka zata bude ido ta ganta agushewarta because yanda zuciyarta wani buguwa da karfi time daya sam ba tayi tsammanin bude ido ta ganta araye ba dakin shiru yake ba kowa sai ita kadai dake kwance anrufeta da blanket, yaye blanket din tayi ta mike zaune ta najin yanda kanta yai mata nauyi tamkar an aza mata kaya maganganun Ammi ne ya shigadawo mata cikin kai yana mata yawo cikin kwakwalwarta, cusa kanta tayi tsa kan kanun kafafuwanta tashiga rera kuka har da shashsheka.

Ringin din k'aran wayarta ne yasa ta tsagaita da kukan ta shiga leka phone dinta daketa faman ruri saman bedside table but kafin ta dauki phone din I kiran ya katse jawo wayar tayi tashiga duba mai kiran 5 miss call tagani daga kawarta salma wasu sabbin hawayene suka sake kwaranyo mata ganin k'iran salma wacce ta turo mata da IV dinta tun last week auranta cikin wannan week din Nisha ba k'aramin buri ta ci ba na auran kawarta salma sai dai kafin auran salma ita andaura nata auran wani sabon k'iranne ya kuma shigowa Nisha kamar baza ta daga k'iran ba saboda yanayin da ta ke ciki bazata iya magana ba harya kusa katsewa sannan ta dauka tare da kara wa akunne ba tareda ta ce komai ba,


"Haba Nisha tun yaushe naketa kiran wayanke ba kya picking kuma baki biyoniba ni ba wannan ba yaushe za ki zo ne because ya kamata a fara komai dakefa"

" Hello wai ko ba kya ji nane kam "salma ta tambaya jin shiru ba magana sai shashshekar kuka da ta ke ji kasa kasa

"Wai mai yake faruwane Nisha naji kinyi shiru inata magana kinyi shiru qalau kike kuwa, ?" dib Nisha ta katse wayar ta sake phone d'in saman bed tashiga rera wani sabon kuka ta na cikin wannan ya nayin sai ji tayi anturo door ana kokarin shigowa wanda yayi saurin mayar da ita sense d'inta cikin hanzari tashiga goge hawayen face d'in ta ta koma ta kwanta ta rintsa ido kamar mai bacci, cikin natsuwa HAJIA ta turo door ta shigo hade tura kofar ta rufe, girgiza kai Hajj mama tayi ganin Nisha kwance yanda suka barta kamar mai bacci saka makon zuwan ta bakin door din ta jiyo sautin shashshekar kuka wanda kuma Nisha ce keyi karisowa tayi kusa da bakin bed d'in ta zauna tare da shafo kan Nisha tashiga fadi'n

"Ki ga far ceni y'ar nan na yanke hukunci ba tareda izini yarda ko amincewarki ba nayi hakanne ba dan na cutar da ke ko saki cikin damuwa ba " tar Nisha ta bude ido jin Hajj mama ke magana ta na kokarin matsar kwalah
Manyan idanuwanta wayanda suka kumbura ta sauke akan Hajia wacce tayi sunkuye cikin kunya da na dama tana ta faman sharce , hawaye da gefen zaninta hankali Nisha tasuma kokarin gyara zama wanda yayi sana diyan dago da kan Hajj mama cikin sauri tashiga taimakawa Nisha wajan gyara mata zaman tana fadi'n

"Sannu 'yar nan ya jikin naki dan allah ki gafarce ni ba na son ki shiga da muwa sabida ni hak'ik'a nayi babban kuskure wajan yanke hukunci ba tare da sani ko yardarki ba amma dan allah,.. cikin hanzari Nisha tariko hanun Hajj mama wacce duk ta da burce ta shiga da muwa cikin sanyin murya Nisha tasuma fadi'n

"Please Hajia kidaina neman afuwa agareni aganina kun isa da ni shiyasa kuka zabamin miji kuma nasan ba dan kucutar da ni bane yasa kukayi hakan, inde nakasance daya daga cikin y'ay'an gidan nan to kunada kowacce irin dama akaina ba zabin da zakuce kunyi nace AA ko nayi musu please Hajia kidaina damun kan ki zabin da kukayi agareni shiya dace dani because ni yar kuce, Nisha ta karishe zancen da rintsa ido saboda hawayen da yacika idanuwanta,

"Aa Nisha kema kina da naki ra'ayin kuma kina da zabi, hakika naji komai daga bakin Ammi soyayyarku da Kamal wanda kuwa da nasan hakane kokusa ko alama da bazan fara wannan katubaran ba nide burina kikasance daya daga cikin sirikar gidan nan alakarmu dake takara kusanci sosai , hakika nice sila aurarraki dayawa daga cikin family nan saboda dauren family na , kama daga auran habu d'ana(Daddy) nina hada auran sa da yar wajan k'anwata hafsa wacce Allah ya azurta ta da yammata biyu Bilkilsu da Maryam, wanda daga baya Allah yamata rasuwa nina cigaba da rikeso lokacin Ina tareda mijina Alh Muhammad bature wanda shi balaraben saudia ne a saudia muke da zama acan na haifi y'ay'ana maza guda biyu Abubakar wanda muke kiransa da habu(Daddy) da Muhammad wanda muke cemasa modi(Abu) sai Rabi'atu itace karama,

Bayan rasuwar k'anwata hafsa can natafi dasu kasan cewar ita a Nigeria tayi aure kuma tana kusa da baffa Sani wanda yakasane wan mahaifinmune shiyarikemu yarenemu saboda mu marayune duk mahaifanmu sun rasu shiya cigaba da rikemu bisa amana kulawa da kuma nuna mana gata because iyayenmu sunada wadata sosai bamusan meye wahala ko taluciba alhamdulillah muna cikin rufin asiri bayan rasuwar baffana da kuma k'anwata ba karamin shiga damuwa nayiba because narasa dangina yanzu banida wasu family da wuce y'ay'ana 5 da mijina dan haka sena rungumesu muka cigaba da rayuwar farin ciki dajin dadi yayinda kowannesu yake karatu gurare daban shi Abubakar a Paris yake ban garan kasu wanci yayinda shikuma modi yazabi Landon ban garan likitanci sukuma y'ay'a matan agabana suke karatu because ni ban yarda da karutun y'ay'a mata awani gurin da ban ba shiyasama kikaga Fadeelah da Reeda suke karatunsu a maryam abacha komai zasuyi ido nakansu,

Bayan kammala karatun kowannesu yacika burinsa yayinda modi ya zama babban doctor nan kasar Landon din yake aiki yayinda yabude hakararren hasibiti nashi nakanshi dake gida Nigeria da sunana HAJIA MADINA hospital inda yarsa Heelah take ai kenan kuma ita take jagorantar asibitin ,shikuwa habu yazama babban dan kasu but shi rayuwarsa harta ban garan siyasa ya taba yayinda yashahara wajan kasu wancin gwala gwale anan kasar England yayinda ta ban garan siyasa yake na hanun daman shugaban kasa, ganin kowannesu yacimma matsayan dayakeso tsayawa yasa nabijiro musu da batun aure cewa kowannesu ya gabatar min da macen da yakeso kuma yakeda burin aure ban garan habu yanuna min shide tukunna bashida wanda yake so yanzu baisaniba ko nan gaba but azahiri yanda naga sunfi shakuwa da Balkisu kullum suna tare suna fira nayi tunanin soyayyace a tsakanin su but saiya tabbatar minda ba abunda nake tunanibane to amma banida zabi wannan alkawarine da nayiwa zuciyata hada auran su dukansu 4 saboda sake dankun zumunci because a ganina nagida bai koshiba ba abawa na wajeba,

Kasancewar modi shine babba senayi tunanin hadashi daHafsa because yarinyar akwai nitsuwa sosai ga hakuri but shi modi akwai taurin kai gaskiya wani lokacin baya jin magana ga fada ba kamar habu ba dan shi yanada saukin kai ga raha but shima wani time inya juye baka gane masa shiyasa nayi tunanin shikuma na hadashi da Balkisu (Ammi) Balkisu yarinyar tana da raha ga suruta kamar aku saide kuma akwai tsiwa wani lokacin shiyasa nake ga zasufi dacewa da habu tasu zaifi zuwa daya saboda ita Hafsa tanada shiru shiru sosai batafiye maganaba kuma itace karama akan Balkisu, koda nakawo shawaran hada junansu aure bawanda yakawomin cikas se modi dama nayi tunanin hakan domin kuwa yaki amsan tayin da namasa na auran Hafsatu yakawomin azurin yanada wacce suka d'aid'ai ta a Nigeria take da zama azirga zirgan dayake tsakanin Nigeria da london suka hadu, har ya gabatar min da hoton ta sunanta Jumanah azahirin gaskiya yarinyar bataminba Hafsatu naso na hadasu amma sam yadage se waccer yarinyar mai ido atsakarka ganin banasu natakura masa yasa nazuba masa ido yayi yanda yakeso yayinda shikuma habu ya amince da zabin da nayi masa, haka itama Rabi ta gabatar min da wanda take so saide shima asalinsa dan Nigeria ne shima babban dan kasuwane yau yanaca gobe yana nan but yafi zama Nigeria, dan haka aka daura aure kowannesu,


Koda aka daura aure modi cewa yayi a Nigerian zasu tareda domin acewarsa amaryarsa tace bazata zauna inda yakeba because bazatabar dangintaba saide shiyabiyota suzauna acan domin bazata zauna inda ba kowa nataba modi duk abunda tace masa kamar yanka wuka haka zaidau lamarin a tak'aice dai yabita can Nigeria acan suka tare , itama Rabi tana can tareda mijinta a Nigerian karatunta da komai ya koma can, nida maihaifinsu wanda yake kwance jinya da habu da amaryasa mukadai muka kasance anan duk da shima habun bai wani cika zama sosai ganin yanda Balkisu take zama cikin kadaici yasa nace yadinga tafiya da ita matsawar bazata takurawa aikinsaba dan haka seyabi maganata yakan tafi da ita sa'i da lokaci kasan cewa itama karatu take bawai ta kammala bane inda take bangaran alkalanci,

Hafsatu ita kadai takasan agabana da batayi aureba tacigaba da karatunta inda take da burin zama shahararriyar barrister saide kafin kammala warta tasamu miji inda wani malaminsu yanuna ra'ayinsa akanta ma'ana yanason ya aureta aikuwa ba bata lokaci akayi auran, saide kafin agama warware gajiyan bikin rai yayi halinsa watansu 3 yayi hatsarin mota Allah ya dauki rayuwarsa tadawo gida muka zamana yayinda ta cigaba da karatunta

alokacinda Balkisu take dauke da tsohon cikin Ajmal a wannan yanayin mijina Alh Muhammad bature Allah yamasa rasuwa bayanda Balkisu tahaihu ta santalo santalelen jarumi d'an wanda yaci suna Muhammad anakirasa da AJEEMAL idan kinji ance Ajmal ananufin abu mafi kyau, mai kya , kyakykyawa, tunda suka haifi Ajmal sama da shekara 8 sannan ta sake samun cikin Kamal wanda kusan tare suka haihu da Rabi tsakanin muhaiseen da Kamal bai wuce sati 2 ba Saida aka hafi muhaiseen bayan sati 2 aka haifi Kamal shiyasa tsakaninsu ba yawa wanda tunda taga haihuwan muhaiseen Rabi bata sake samun wani cikin ba shiyasa ta dauki son dunya ta dau rawa muhaiseen because shi kadai Allah yabata,

Kamal nada shaira 6 Ammi ta sake samun cikin yan biyun ta Fadeelah da fareeda ita fareeda sunan k'anwata taci yayinda ita kuma Fadeelah ni a kayiwa mai suna, ina matukar alfahari da family na mun zama tsintsiya madaurinki daya saidai gaba daya hankalina ya koma kan Rabi da Modi da suke Nigeria especially Modi da hankalinta ya kasa kwanciya da shi g'wara ita Rabi hanun namiji take but shi Modi ahanun mace yake saboda ita ta jashi sai yanda tayi da shi wannan abu yana d'agan hankali.,

Bayan da su Reeda da Fadeelah suka kammala primary School nayanke shawaran komawa Nigeria tushe na domin hankalina ya kasa kwanciya da rarrabuwan kan ahalina saidai Kamal da babban yayansu karatunsu yayi nisa shi Kamal yana Americans shikuma Ajmal yana Dubai kowannesu da inda yake karatu dan haka koda Habu ya dawo nake sanar da shi hukunci da nayanke na komawa Nigeria tun da dalilin wanda nake aure anan din Allah ya masa rasuwa dan haka zan koma mahaifata Habu baimusa mi ni ba saidai yace mu d'an basa lokaci domin duba mana gidan da zamu zauna, aikuwa cikin satin yazo ya nuna mana amincecen gidan da ya siya

7 / 24