Chapter 9 Reading AJEEMAL Book 2 Hausa Novels By Khaleeseart Abdullahi Raeys.txt Arewa Novels

AJEEMAL Book 2 Hausa Novels By Khaleeseart Abdullahi Raeys.txt

Author :  Khaleeseart Abdullahi Raeys Category :  Hausa Novels 001

Chapter   9 / 24

24K to 27K   out of 70.1K words

shigowa haka babu excuse.

Doctor fu'ad ne ya turo door ya shigo bakinsa d'auke da sallama ganin haka yasa Ajmal g'yara zama time d'in da doctor fu'ad ya karisa shigowa ya nemi guri ya zauna face d'insa cike da fara'a yana kallon Ajmal da Nisha wacce tayi sunkuye da kai tana d'urk'ushe saman carpet tayi ladab

" Yallabo'i amin afuwa nashigo babu karban izini Doctor fu'ad yafad'i yana kallon Ajmal wanda shi d'in ma shi yake kallo, Ajmal bai ce masa k'ala ba dan yasan halin doctor fu'ad ko yaushe cikin tsokana da wasa yake

" Ina kwana?" Doctor fu'ad ya tsinci y'ar siriruwa muryan Nisha tana mai d'aga masa gaisuwa cikin kankan da kai .

" Lapiya qalau ya jiki naki " Doctor fu'ad ya amsa yana mai tambayar ta dagowa tayi ahankali kafi ta amsa masa da cewa

"Da sauki"

" but now naje duba ki aka shaida min kina nan shine nabiyo naga yanayin jikin naki but alhamdulillah naganki garau dake masha Allah" murmushi kawai Nisha tayi masa tana g'yada kai becauseause ta kosa ta tafi shikuwa Ajmal mamaki maganganun doctor fu'ad yayi because dama tambayar da zai mata last kenan, Ajmal komawa yayi ya kuma manne wa bayan shi da jikin sofa yana kallon Nisha karfin yayi gyaran murya hade da fad'in

" Sai nace ki zuba abincin" mamaki Doctor fu'ad ya shigayi ganin mulkin mallaka da Ajmal ke yiwa marainiyar Allah sid'i sid'i Doctor fu'ad ya ga Nisha tamike a sanyaye ta nufi kitchen wasu plates da spoons Nisha ta kuma dau kowa ta dawo ta bude foodflast tashiga serving dinsu wani daddadan kamshin na musamman ya shiga gauraye parlourn fried chips with plantain and vegetables soup with roasted chicken ga sandwich with pancake gefe kuma ga lemon iced tea Nisha sai da ta gama serving din ogan nata kafin ta janyo wani plate din tasoma kokarin serving din doctor fu'ad

"No karki wahalar da kanki kibarshi kawai zanyi serving da kaina tunda kin sallami mai gidan naki ya wadatar" wani kallo Ajmal ya dago yabi doctor fu'ad dashi kafin ya maida hankali kan abincin sa ya suma ci ,

"Za,.zan iya tafiyaiki "

Nisha ta tambaya tana kallon Ajmal yayinda ya kai yayinda ya kai lallausan pancake bakinsa g'yada mata kai kawai yayi ba tare da yayi magana ba cikin hanzari Nisha tamike ta fice daga parlourn sai turo baki ta ke shi kuwa Doctor fu'ad an barshi da mamakin abokinsa ganin yanda ya tusa yar mutane gaba yana bata umarni cikin isa da gadara wai dan ma bai san matsayinta gareshi ba ,yarinyar akwai hankali da nitsuwa kuma ba maisun ha ya niya bace balle yawan magana ,.

sam baya so Ajmal ya dauki halhakinta da yawa because yasan halin Ajmal na ko in kula especially yanda yaga yamai da yarinyar tamkar mai masa hidamane y'ar aiki kawai yana fatan akan yarinyar nan Ajmal ya fahimci maiye soyayya kauna da kuma yadda akejin shaukin wadda akeso ya fahimci rayuwar aure da kuma ma'anarta, a iya sanshi da Ajmal duk bai fahimci wadannan a baben ba kuma ya kasa tsayawa ya fahimta , haka ma ta ban garan aurataiyya bai daukeshi da wani mahimmanci balle ya tsaya ya fahimci yanda alamuran suke tafiya but ya tsaya ya na ta wahalar da kanshi

"What are you thinking?"


Wani dugun numfashi doctor fu'ad yaja yana mai kallon Ajmal wanda ya tsare shi da tambaya kafin ya saki wata murmushi yana fadi'n

"Nothing" daga nan ya kai hanu shima ya dauki lallausan sandwich wanda ya ke hango shi tamkar zane

"Tun shigowa na hancina ya cikaro da kyakykyawan kamshin abincin nan nasan cewa ba gama garin delicious ake gabatar waba ashai amaryar muce ta karbi office " Doctor fu'ad ya fad'i yana kallon Ajmal ta gefen ido kafin ya danna daddad'an sandwich cikin bakinsa. shi dai Ajmal har wa yau bai kullashi ba dan yasan Doctor fu'ad inya fara zuba kamar fanfon kasuwa yake bakin ba burki kuma cikin maganarsa ya dinga sa wasa da tsokana aciki.

"Bana manta wani delicious da naci time da Raheelah ke amarya only one spoon but ranan kwana nayi ina zaryan toilet I hope HAJIA karama ta iya kayatattun delicious irin haka like Nisha ba girman parlour ta ke kamar Heelah ba "

Doctor fu'ad ya sauka layi sai barin magana yake maybe dad'in girkin Nisha ke sa shi wannan zuban, Ajmal bai san sannan da ya saki wani murmushi mai sautin ya na kallon doctor fu'ad da ke ta kada kai ya na ta faman surutu shi dai a iya sanin shi k'anwartashi ba ta da mara ba da Heelah duk ba abunda suka iya sai dai ta iya zuban surutu kamar shi

"Please kaci abincin kadaina surutun nan haka" murmushi doctor fu'ad yayi gamida da dan buga head d'insa kadan yana fad'in


Sorry fa dad'in girkin ne yasa nake ta surutu ban sani ba , honestly mutumi na yarinyar nan ta tsa moka daga k'angi ta taimake ka yanzu kayi bye bye da ordern restaurant, cikin ta kaici da maganganun Doctor fu'ad yasa Ajmal da katawa da cikin roasted chicken din da yake ya ya b'alli tissue paper ya shiga goge hannayenshi kafin ya koma ya jingina Jikinsa da kujeran yana hararo Doctor fu'ad

' wai ta tsamoshi daga k'angi ta na taimakesa, shi inbama na sihar da Ammi ta yi masa akan yarinyar da kuma nuna tana bukatan mu amalarsu tare ba da mai zaisa ma kafarta ya fara tako side din shi tun kafin zuwanta yana rayuwarsa ba cikin k'angi ko taimakon wani ba zuwanta ba zai canza komai ba kuma k'angi da taimako da yake fadi'n duk wani bauta ko hidama da take da shi biyanta zaiyi dan baya bukatar hidimar da ta ke masa a kalle shi a fiskar taimako ko fita daga k'angi,' Doctor fu'ad ganin kallon da Ajmal ke yi masa yasa shi ya saki sakin murmushin kasa kasa

"Naji kana tambayar ta ya jiki mai ya sa me ta" Ajmal ke tambayar doctor fu'ad because kasan cewarta a k'ark'ashisa zaiso sanin damuwa ko matsalarta, zame hanu Doctor fu'ad yayi shima ya shiga goge hannayenshi kafin ya gyara zama yana fad'i

"Eh to da farko dai a sumammiya naje na sa me ta Ammi da kammala suna ne suke kaiwa da kawo bisa kanta but da na duba ta bakomai bane fa ce tsorita ne da firgici duba da yanda zuciyarta ta ke bugu yana kaiwa da kawowa shiyasa mu likitoci muke da d'a wayar da kai ba kowace irin magana akeso adinga fad'awa mutum kai tsaye ba ko ya tsinci magana kamar daga sama ma'ana baiyi zato ko tsammanin jin maganar ba especially mutum mai saurin razana tsoro ko firgici ba kasan halinda zai fada ba like ita Nisha ,.

" Ammi Kamal? su sukayi coursing matsalar kakeso kace" Ajmal ya tambaya yana mai tsare doctor fu'ad da manyan idanuwansa

"Kusan haka but Ammi ta fada min dalilin faruwan hakan wanda lamarine da ya shafi tsakanin ka kai da Nisha , is very confident Ajmal ya gyara zama yana fad'in

"Ina jinka banaso kana tsayawa yayin maganar ka dunkule min zance cikin kalama daya," murmushi Doctor fu'ad yayi gamida fadi'n

"Bana tunanin zai dunkulu ta kalma daya shi yasama banso na sanar dakai yanzuba because banzo da Shirin yi maka bayani yanzu ba nayi tunanin wa re wani time da ban dan tattauna maganganun because tattaunawar is very important cikin rayuwarku kai da ita but why not na sanar dakai yanzu nasan zaka saurareni kuma zaka fahimce batuna kuma ka dau shawaran da zan baka, ".

Ajmal ya k'osa ya ji kan zance but shi kuma doctor fu'ad sai dugun ba yani yake da ma fa matsalar su kenan likitoci nan ba zasu tsaya su maka zance kai tsaye ba sundinga kwane kwane kkenan harsai mutum ya hasala

"Look idan zancen ba fa'idar na sani kabarshi kawai ina da abubuwan yii" Ajmal ya fad'i ciki takaici da bacin rai ya mike yana kokarin tafiya cikin hanzari doctor fu'ad ya kamo hanun Ajmal yana fadi'n

"I'm sorry mutumina zauna na maka bayani" because yasan halin mutumin da saurin hasala komawa Ajmal yayi ya zauna cikin hade gira ya ce

"I'm hearing you talk " cikin na tsuwa tare da kawar da wasa alamarin doctor fu'ad ya shiga zaiyyanu zantuka da labarain da ya samu da Ammi game da batun auransa da Nisha,..

______Tun bayan da Nisha ta fito da ga side din Ajmal ta nufi sashinsu a kokarin ta na shiga parlourn time d'in kamal shima ya sako kai da nufin fitowa nan suka game da juna gefensa dauke da Nabilah wacce ke biye da shi , ganin su da tayi sai da kirjinta ya d'an buga. ja ba ya Nisha ta yi ta matsa gefe kad'an tana kallonsu, Kamal fiska dauke da murmushi ya suma tambayar ta

"My sister! Ke muka shiga dubawa yanzu but ba mu tadda ke ba.

" Ya jikin naki" Kamal ya ya tambaya yana duban Nisha cike da murmushin nasa da baya yanke sai wani ikon Allah

"Da sauki Nisha ta masa cikin sanyin murya, jinjina kai kawai Kamal yayi yana fadi'n

"Masha Allah haka akeso" kafin ya juya ya kai kallonsa ga na Nabilah gamida fad'in

"Ni zan wuce sai na dawo take care of yourself" g'yada masa kai Nabilah tayi tana fadi'n

"Allah ya tsare"

Daga haka Kamal ya wuce ya nufi compound d'in gidan daidai parking space ya shiga motarsa tare da yi mata key mai gadi yabude masa geat yafice. har yabar ha raban gidan Nisha binshi da kallon ta fad'a tunani ba k'aramin mamaki Kamal ya ba ta ba kwata kwata ba wata damuwa kan face d'insa gani tayi duk tafishi shiga da muwa da kad'uwa, but shi hankalinsa akwance yake kamar ma ba shi da wani damuwa.

'kodai kwai da ma wasa yake da hankali da tunaninta ba wani sonta ya ke ba but ya cusa mata soyayyarsa da ra'ayinsa da sha'awar fara sabowar rayuwa tare da shi ' jin anruko hannayenta yasa ta dawo cikin hankalinta da tunanin da ta ta fi time din idonuwanta har sun ciko da k'walla tab.

Nisha kallon Nabilah tayi wacce ke rike da hannayenta duka biyu tana kallonta cike da murmushi tana fadi'n

"Idan ban ta kura kiba inaso mu dan tattauna wasu maganganun da ke amma fa in ban shiga time d'in ki ba, girgiza kai Nisha tayi tana fadi'n

bakomai" still Nabilah ba ta da ke hannun Nisha ba fiiiii Nabilah ta ja hanun Nisha suka nufi sashinta.

Ko bayan da suka karisa shiga parlourn Nabilah ta zaunar da Nisha bisa kujera kafin Nabilah ta koma dining area ta hadu musu coffee ta dawo ta mikewa Nisha cup d'in zazzafan coffee shekeke Nisha ke bin Nabilah da kal kafin ta karbi cup ta rike still idanuwanta ba su dainabin Nabilah da kallon mamaki ba ita kuwa Nabilah sai murmushi ta ke ta zubawa Nisha kafin itama ta nemi guri kusa da ita ta zauna tare da kai coffee d'in cup bakinta.
Sai da ta kurb'a zazzafan coffee d'in kafin ta kalli Nisha wacce ta sa ke baki ta na kallonta kamar hoto ta kasa shan coffee d'in da Nabilah ta ba ta

"Ki sha mana kin tsaya kina ta kallona kamar ba ki sanni ba "Nabilah ta fad'i gamida murmushi ta cigaba da shan coffee d'inta kafin itama Nisha ta kai bakinta jikin cup ta suma sha. dan kadan Nisha ta shaa ta sauke cup d'in ta sa ke Kai kallonta ga Nabilah ta na son jin dalilin da yasa ta jawo ta nan da kuma maganan da ta ce zasu tattauna, Nisha muryan Nabilah taji ta suma magana da cewa

" Tun bayan da naji tsakaniku da da ya Kamal na ji duk ki yai yan da na ke miki ya kau infact ma ko auranki ya bijiro da shi bazan wani damu sosai ba duk da kasan cewa ta macece mai kishi sosai especially akan abunda nakeso kuma nake matukar kauna ranar. farko da na fara ganinku tare a guest house d'in Daddy naji kishi sosai raina kuma ya baci harma nayi tsammanin wani abu tsakanin ku wanda kuma bai kamata nayi wani zargiba but time din idona yarufe naita fadan maganganun da bai da ce na fa de su ba akan zargin da ban da hujja ko tabbaci, Sam awance lokacin banason ya Kamal fada cikin yanayinda ya Kb yayi nisa aciki duk da abaya ya dauki wani ban gare irin na rayuwar Kb,.

Juyowa Nabilah tayi tana fiskanta Nisha ta cigaba da fadi'n

Kasan cewa na taba rayuwa cikin gida nan wanda shine sana diyar haduwata da Kamal time din da ya dawo daga American HAJIA ta sa aka shirya kayataccen waliman taron dawowar jikokinta dakuma murnar haduwar ahalinta, Kamal da KB makaranta daya suke karatu but ba wanda ya San Dan uwansa ko ya taba ganin hoton dan uwansa balle su shaida junansu.sai bayan haduwarsu aliyafar ne sannan ne suka shai da juna nima sannan ne na ga ya Kamal mukayi amanna da juna kasan cewa ina rayuwa cikin gidan su shiyasa muka shaku alakarmu ta kara karfi sosai wanda kowa ya fahimci hakan.

Kamal mutum ne mai fara'a sosai da sun wasa tsokana da ban nishadi wanda shiyasa na kara sa ke sosai na fara mance duk wata damuwa na Kamal ba kamar babban yayansu Wanda ke da fiskar fusatattu sam bayi da fara'a sai mutum ya ci sa'a yake iya tuzali da murmushi ko da dariyansa ballai ma ba na zaton yana murmushi balle wani dariya shiru yake maganan bata da mai Shi ba infact ma duk inda yake da hayaniya ko ake surutu wajan tofa baya zama yafi kadai tuwa shi ka dai Sam ba yi da son ha yaniya ni tsoronsa na ke ji sosai ko ido ba na yarda muhada da shi time d'in da nake rayuwa gidan nan but karfin hali irin na Aunty Heelah haka ta dinga cusa kanta cikin rayuwarsa da nuna sha'awar soyayyarta gare shi amma shi sam baya bata fiska ita kuwa Aunty Heelah sam babu kunya cikin idonuwanta zaman turai ya ba ta ta duk wata kunya da akasan ya mace na dashi to ga Aunty Heelah kam babu infact ma ba ta sanshiba.

Dabi'un da Aunty Heelah ke yi cusa kai ba kwarjini kiri kiri ba kunya haka take binshi wani sa'in abun har kunya ya ke bani ,ba ni kadai ba ma kusan kowa yana hankalce da tarkon da ta fad'a duk da sunsan wannan cusa kai da shige masa da ta ke baya waiwayarta ballai yasan halin da ta ke ciki because ba yida lokacinta harkan gabanshi kawai yake kamar baisan da lamarin ta ba amma Hajj mama duk ba ta yi la"akari da ta ban garansa ba yana da ra'ayinta ko aa hajia ta sa aka shirya bai konsu duba da yanda Aunty Heelah ta k'walla fa rai da shi ta nuna sha'awar so da kaunarta gareshi,.

Ya Ajmal duk da bai nuna interested akan Aunty Heelah ba but bai nuna ya na da ja ko musu a kan abunda HAJIA ke kokarin yi ba time d'in da Aunty Heelah ta kammala karatunta a kasar England aka tsaida ranar auransu already ya Ajmal ya Kammala masters d'in shi dan haka aka tsaida ranar auran tare da na Aunty Hafsatu kanwar ammi acewar hajia tunda har mahaifina zai iya cin amanarta yayi wani auran har asamu karuwa amma ace bai iya fada ma ta ba kuma bataji labari ba to yanzu bashida ikon da zai da katar da ita daga hukunci da tayanke na auran Aunty Hafsatu koya amince ko bai amince ba yana so ko baya so duk da abaya ya bijirewa hakan ba da son rantaba, bayanda da Aunty Hafsatu ta kuma gidanmu da zama amatsayin matar Abu to bayan wasu lokaci jima na koma gida na cigaba da da Auntynsa hafsatu.

Aunty Hafsatu tana da dadin zama sosai ta rike ni bisa amana tana kula Dani sosai tamkar wacce na fito daga cikinta kulawar da take ba ni ko mahaifiyata tana raye iya kulawar da zata ban kenan, ba kamar sanda na ke hanun mommy ba time d'in jinke gidan kamar ba na mahaifina ba kamar ba cikin gidan na girma ba gidan ya zam ta tamkar akan k'aya na ke saboda ita time din ko yan aiki hana mahifina tayi ya kawosu ninake komai a gidan ga tsan g'wama da kyara na zama tamkar bora acikin gidan, wanda kuwa ba haka ta kewa su Aunty Heelah da yaya KB ba duk da nayi farin ciki da ban kasance ta bani irin tarbiyan da ta taso da yayanta ciki ba gaba daya ta ga ma sangartasu ba ta k'wab'ansu duk abunda suke so shi sukeyi walau mai kyau ko mara kyau .

Sun kuyar da kai Nabilah tayi saboda wani hawayen da ke kokarin zubu mata na tuna wahalar da ta sha ahanun mommy gaba daya Nisha jikinta sai ya kara yin sanyi gaba daya tausayin Nabilah ya kamata wato kowa da yanda ake jarabashi arayuwa, parlourn ne ya dau shiru ba wanda ya yi magana cikin su jim kadan Nabilah takuma dagowa ta kalli Nisha tana fadi'n

Kiyi hakuri bana kiraki Dan na baki labari ko surutu abunda ya shafi rayuwa ta bane sai d'an kinzama daya daga cikin family gidan nan kina da right din kisan wani ban garai da yashafi ahalin nan da kuma yanda rayuwar familyn ke gudana, because Kamal ya bani labarin komai daran jiya ganin yanda hankalinsa ya tashi sosai ya kasa nitsuwa wanda nima yasa nakasa nitsuwar hankalina ya kasa kwanciya har sai da ya labar ta min abunda ke faruwa matsayinsa na mijina kwantar masa da hankali tare da bashi shawarwarin da zai Kara matar dashi damuwarsa ya manta da ya cireki daga zuciyarsa ya manta ya ta bata jin wani abunda ya Dan ganci soyayya da ke because ke ba rabunsa bace ke matar yayansa ne yanzu alkar ku zaima yanzu yan uwan ta ka ne kawai ba batun so

9 / 24