Chapter 6 Reading AJEEMAL Book 2 Hausa Novels By Khaleeseart Abdullahi Raeys.txt Arewa Novels

AJEEMAL Book 2 Hausa Novels By Khaleeseart Abdullahi Raeys.txt

Author :  Khaleeseart Abdullahi Raeys Category :  Hausa Novels 001

Chapter   6 / 24

15K to 18K   out of 70.1K words

tana kallon mutumin yasanya hanu yana taran ruwan yana kaiea baki da alamar yaji k'ishin ruwa seda yasha yakoshi sannan yashiga wanke fiskarshi datayi baki abar tsoro seda ya wanke face dinsa sannan yajiyu yakalli Nisha wacce ke gefe ta zuba masa na mujiya tana kallonshi, kauda kaiyayi yacigaba da wanke gabban jikinshi but jin motsin mutum kusa dashi yasa ya dakata ya kallo inda take idonta cika tab da kallo amma bakinta se murmushi yake yana barin cewa wani abin daker bakinta ya iya furta

"Abba?abbana kaine haka" Allah nagode maka Nisha tafad'i yayinda take matsowa gareshi da sauri yaja baya yana kallonta cike da mamaki amma bai iya cewa kalaba ganin haka yasa Nisha sake fadi'n,"

"Abba baka ganeni bane yarkacefa Nisha"tafad'i tana kuma tinkaroshi da kokarin fadawa jikinsa cikin murna but seyaga yasake ja dabaya 'to ko ta canzane bai iya ganetaba' tashiga tambayan kanta "


" Abba fa nice Nisha dinka ka kalleni da kyau nice , gamamakinta setaga ya watsa aguje yashigayin gudu itama cikin sauri tashiga bin bayanshi duk da ruwandq ake gudu yake sosai tamakar yaga wani abin tsoron itama Nishi se karayin saurin take but yamata nisa sosai , wata tsadaddiyar motane taga yaz o yasha gaban Abba aka bude murfin kofar motar aka kutsa abbanta ciki bataga ko suwayeba suka jashi csuka maidakofar suka rufe sukaja motar sukatafi dashi,

"Innalilahi wa'ina ilaihi rajuun"
Firgit Nisha ta tashi daga mafarkan da tashigayi tana kuma maimaita" inna lillahi wa'ina ilaihi rajuun abbanaaaaaaa!" bedroom din tashiga bi da kallo nan ta ganta wance kan gadon Aheel wanda tun kawoshi yakwanta yashiga rigimar sede su kwanta tare dalilin dayasa ta kwanata a domin ta samu yayi bacci seta sulale ta tafi but se bacci mai nauyi ya dauketa hardasu markin umma da Abba gaskiya mafarkin da tayi da Abbanata da irin halinda takaganshi ba karamin daga mata hankali yayiba, duk da sassanyan AC dake aiko cikin bedroom din but zuba take sosai kallon Aheel tayi wanda ya yabaje yanata sharan baccinsa wayarta tazaro tashiga duba time 4 na asuba zaro ido tayi tasakko daga bed din tanufi downstairs cikin sauri

ahanzarce take sakkowa daga benen koda ta karisa sakkowa se tsayawa tayi jinin jikinta yatsaya cak yabar aiki ganin Ajmal kwance saman duguwar sofa yana sanye cikin kyakykyawan jallabiyar shi yana karatun Qur'an tacikin phone dinshi , saka makon jiya da takawo Aheel basu ganshi a parlourn ba shima kuma Aheel bai nemi papan nashiba ya nace mata sede sukwana tare harda yar kukanshi karta tafi tabarshi atsorace tajuya cikin sauri zata koma atunaninta bai lura da itaba but setaji yace

"You! come back here, "nan Nisha tashiga mis mis da ido tana Shirin kuka ita tarasa wani tsautsayim bacci mai dugun zango ya kamata cikin side din Ajmal ahankali tashiga takowa, jikinta sai rawa yake gaba kidaya bata hayyacinta saboda mafarkin da tayi gaba daya hankalinta atashe take kuma tana cikin tsoro sosai hankalin takarisa inda yake tadurkusa saman carpet kanta na kasa gaba daya zufa yagama wanketa tas gashin kanta duk ya manne jikin face dinta yayinda da idonta kuwa hawayene fal ciki suna kokarin gangaruwa kumatunta sosai take sunkuyar dakai saboda hawayen dake kokarin zubu mata, kallo Ajmal ya tsareta dashi sosai yake bin sumar kanta da kallo baki wuluk dashi se wani shainin take

jin shiru baice komai ya tusata agaba yasa ta dago kai ahankali ta kai kallon ta gareshi daidai time din da sirarun hawaye suka sauka kuncinta ganin kallon da ya kafeta dashi kamar mai Shirin ganu wani abu a face dinta yasa tamaida kanta kasa tarasa shirun me Ajmal yayi yana kallonta ko wani irin kallone yake mata haka takasa ganewa kode kallon tuhuma yake mata na kasan cewa da tayi a side din shi,

"Aheel ne ya bukaci na tayashi kwana bayaso natafi nabarshi shine..,,, dakatar da ita yayi da ga surutan da kefaman jero masa because ba a bunda yakeda bukatan tambayar taba kenan dama yasan Aheel da fitina ayanda ya kwallafa rai da Auntynsa dayake fad'i wataran cewa zai ta dawo side din ma gabaki daya yasan halin d'ansa Ajmal yanason d'ansa sosai yanda Aheel keson Nisha yake kaunar kasancewa da ita da kuma kulawar da Nisha take bawa Aheel yasa Nisha tasamu sassauci daga tsana dakuma ki dayake mata abaya , shiyasama yanzu bai cika fargaban halinda Aheel yake ciki ba because yasan akoda yaushe tana kasancewa da shi kulawar da take bashi ko uwar data haifaishi Heelah bata bashi ,

Aheel raunin mahaifinshine baiso alakar Aheel da Nisha tayi nisa haka bas because Ajmal hankalisa Sam yakasa kwanciya da yarinyar yakasa karbarta kamar yanda agdn suka karbeta hanu biyu wani tunani yake da ban akanta da kuma shakku , wani lokacin kuma tausayi take bashi yanda take wasu abubuwan cikin tsoro da rawar jiki kamar mara gaskiya wannan yana daya daga cikin abunda yasa yakeda alamar tambaya akanta,

"you can go"

abunda Ajmal yace kenan , kamar jira take because tagaji daga dukawan da tayi dan haka cikin sauri tamike tafice taname goge hawayen face dinta , lumshe ido yayi tareda tunanin cikin zuyarshi yarasa meyasa yarinyar sometimes cikin fiskar damu take yanzuma harda hawaye yagani saman kuncinta Wanda yasa yakasa tambayar takamar yanda yayi niya lallai akwai bukatan sanin wacce ita da kuma labarin ta, mikewa yayi danufin haurawa upstairs kamar ance ya daga kai sukayi ido biyu da Heelah wacce take tsaye tundazu daga saman bene tana kallonsu kauda kai yayi irin na ko inkula tareda haurawa upstairs yana kokarin nufan bedroom din Aheel Heelah kamar jira take yagama karisowa tayi sauri shan gabanshi tana fad'in

"ahala wannan stupid girl din harcikin dare kanada bukatar ta , wai nikam me kuke nufine because nakasa ganewa lamarinku , Heelah ta tsareshi da tambaya cikin yanayin tuhuma but bai kulataba yaka kauce mata danufin ci gaba da tafiya amma se ta sake shan gabanshi tana cigaba da fad'in

"ina magana kashareni to mezai hana ka aureta da irin wannan maden da kukewa juna... damko gashinta dayayi da karfine yasa tahadiye sauran maganar da take kokarin yi tashiga kiciniyar kwace kanta

" a kullum ina fada miki kidinga nan na de harshenki daga warwareshi da kike kina furta abunda kikaga dama ni ba d'anki bane kuma niba sa'anki bane so be careful with me yana fadi'n haka ya kuma jijjiga gashin kanta da karfi kafin yayi wurgi da ita gefe yawuce yanufi bedroom din Aheel domin tabbatar da lapian shi, koda yashiga yasameshi cikin aminci yana tashan baccinsa harda minshari dan matsawa yayi kusa da bed din nan yaci karo da hulan Nisha da ta mance saman bed din Aheel wanda bata lura da shiba a takaicema batasan baya kantaba tsoro da far gaban mafarkin da tayi da kuma baccin da yasaceta a bedroom din Aheel side din Ajmal besa ta lura da shiba ,

hanu yasa yadauki hular yana jujjuyata daga bisani ya ajiye ya gyarawa Aheel blanket yarufishi dakyau kafin yanufi hana hanyar fita, koda yadawo parlourn ba takoma bedroom din ta cikin kuka , bedroom din shi yashiga daga bisani ya ajiye phone dinsa kafin ya nufi toilet danyin alwala domin time din sallah ya kawo kai yana idar da alwalan yafito da nufin shiga masallaci koda yafito suka hadu da Kamal wanda yafito shima danufin tafiya dan haka suka hade hanya suka tafi a tare duk da kasancewa masallacin a gidan yake but se kafita geat kafin ka iya shiga masallacin because kofar tawaje take ba ta cikiba,

Nisha kowa cikin hanzari tashige bedroom dinsu tasamu duk suna bacci Fadeelah nabisa gado Reeda yayinda Reeda kuma tamike saman sofa tana bacci slowly kamar mara gaskiya tadauki towel direct toilet suma kokarin shiga sekuma ta tsinkayi muryan Reeda wacce tayi likimo ta kira sunanta , Nisha tsayawa tayi jikinta duk asanyaye , karisowa Reeda tayi tana mai karewa Nisha kallo wacce ta jingina kanta da jikin bangon dakin cikin damuwa

"yadai Nisha Ina kuma kikaje bade a side din ya Ajmal kika kwanaba because bamu iya ishashshen bacci ba tareda keba, Nisha fada mata yanda sukayi da Aheel tayi irin rigimar da ya shiga mata sede sukwana tare bacci ya dauketa garin rarrashinsa but bata san time yaja hakaba,

" Alright no problem sede kuma kamar yanayin ki nagani cikin damuwa what's wrong? girgiza Kai Nisha tayi tana fadi'n

" Bakomai"

"okay"

Reeda tafad'i tareda ja baya domin bata damar shiga toilet da takeda niyar yi , Reeda komawa tayi tazauna bakin bed da tunanin keyasamu yar uwan tasu taganta haka bade yayan nasu bane yamata wani abin haka Reeda tazauna tana ta sake sake har Nisha tafito daga wanka hade da alwalan because ta kammala period dinta dan dama tarega Fadeelah farawa wardrobe tanufa ta zaro riga da hijab ta sanya daga nan tashin fida sallayan ta tada sallah ganin haka yasa Reeda Jan wani goron numfashi sannan itama tamike daga zamar da tayi tanufi toilet tayiyu alwala tanemi hijab ta sanya ta jera da Nisha itama ta tada sallahr daidai shigowar Amma domin tayar dasu sallah kamar yanda ta saba but setaga yau yaran nata sunyi hankali yau suntashi da kansu sun hutar da ita Fadeelah kawai ta hango saman bed ta baje se bacci take wacce tasan matsalar ta murmushi kawai Ammi tayi tafice da ga bedroom din tanufi nata dakin,

kamar yanda kowa yasani yau jirgin Goggo rabi zai daga zata koma karfe 10 na safe bayan kammala breakfast gaba daya family suka kasance compound din gidan domin sallama da Goggo rabi because yau zatatafi Hajia Ammi Nabilah gefe su Reeda banda agogo sarkin aiki Heelah tun farar safiya tafice daga gdn, su Fadeelah sunyi jigun jigun dasu lamari babu dadi zasuyi miss din Goggo rabi comedy bazasu sake ganintaba kuma se biki dama bawani zuwa takeba sosai se sa'i da lokaci, sekuma wani taro mai mahimmanci biki ko suna, Nisha da bata santaba abaya yanzu setaji yanzu tafi kowa shakuwa da ita , an kammala sanya kaya a mota komai ya zama ready,

" To saduwan alkhari se biki kuma in Allah yanuna mana muna cikin rayayyu " Ammi da Hajia suka shiga fad'in

"Amin " daga nan Goggo rabi tashiga daga musu hanu suma suka shiga daga mata hanun daga bisani tashiga rantsatstsiya motar Ajmal wanda dashi acikin rakiyar kuma a motarshi shiyake but Kamal ke driving dinsu se Ajmal ke gefensa muhaiseen da Goggo rabi suna daga gidan baya nan Kamal yayiwa motar key mai gadi yabude musu geat Kamal yaja motar suka fice, harsuka fice Fadeelah da Reeda basu daina bye bye ba sun sake baki se daga hannu suke

"To malamai sun bacewa ganinku daga hanun ya isa haka" Ammi tafad'i tana hararosu yayinda tajuya tanufi cikin gida,su Reeda sauke hannun sukayi jiki asanyaye ko wannensu ya nufi muhallin shi ,

,...... rayuwa yanzu yayiwa Nisha kullin huhun goro kullum cikin tunani da far gaba take tunanin mahaifinta da sanin wani hali yake ciki kullum shine aikinta hatta kyakykyawan cin abinci ta dainayi alwalantama ba kamar da ba wanda yasa hankalin su Hajia ya dawo kanta ganin canjij da sukayi atareda ita, but sun tambayi mai yakawo sauyi a tareda ita mai yake damunta setace "babu"

dan haka sesuka daina tambayan suka cigaba da janta ajiki cikin kulawa tareda wasa da dariya domin a tunanin su kewar mahaifiyar tane ya dawo mata sabo, wanda kuwa ba haka bane yanzu ba abunda take ga umma da yawoce addu'a gareta da fatan dacewa ga mahaliccinta tunanin ta daya shine tasamu hanyar fita daga gidan nan because taji gidan ya ishe tunaninta ya koma kan abbanta tun mafarkin da tayi da ashi da kuma halinda ta ganshi yana bukatan tai mako sede duk hanyar da tabi na kokarin barin gidan abu yaci tira because ko barawone yasamu nasaran shigowa gidan nan tofa fita zaiwuya agareshi matukar da kafarshi zaifita , sede in ba cewa zaiyi domin security ne abaje ko ta ina gashi ko kyakykyawan bacci basayi balle kasamu daman silalewa , gashi su gdn bawani fita akeba kullum ana jikin gida duk wani shopping din gidan barkace kezuwa tareda wasu securities din,

but tabarwa kanta sanin cewa ta tsaida lokacin tafiya tabar gidan nan ko ta halin yayane domin taje gurin tushenta wannan karon tashiryawa Mami koda tsiya tsiya setaga mahaifinta sai tafad'i inda ta kai Abba because taga alamun ba gaskiya alamarinta,

ranar wani lahadi da Nisha takasa mancewa dashi cikin rayuwarta tana kwance tana kwance bisa sofa cikin bedroom dinsu Fadeelah da Reeda sun kaiwa Aunty Nabilah ziyara kamar yanda suka saba sunacan sunata zuba mata surutu wanda hakan bakaramin dadi yakewa Nabilah hakan yana mata dadi sosai kasan cewar su kawaye yan uwa uwa uba kuma tana auran yayansu , but rashin jin dadinta daya takasa gane meyasa Nisha ke gudunta bata zuwa tareda su Reeda suna hira kodai ta dauka haryanzu tana fushi ko kishi da itane ita sam duk ta yada wannan mukaman zuciya daya tariketa yanzu ,

koda ace ya Kamal auranta zaiyi yanzu bazata wani damuba because yanzu yarinyar tausayi take tun wancen lokacin but itade tadaina kishi da ita musamman yanda Kamal yake kulawa da ita sosai ko bacin rainta bayason ganin yanzu duk wani abunda yakeso ko zaisashi farin to itama tana son shi saboda tsantsan so da kaunar da take mishi zataso duk abunda yakeso koda ita bai mataba, ta rintsa ido tana ta faman tunanin da tasaba koda yaushe tadaurawa kanta tunani da damuwa bude ido tayi tazauna tareda dafe goshinta cikin tafin hannunta , nan ta sakalo kafarta kasa ta sakko daga sofan tanufi window,

daga labulen window tayi tana ta kallon geat inama ace ana bacewa da tabace yanzun nan because duk tunanin ta ya ta al laka ga barin gidan motsin shigowar da tajine yasa tamaida da hankalinta ga door din ganin Kamal tsaye bakin door din face dinsa yayi jawar idonsa duk yacika da kwallah yasa tajiyo gabaki daya tana kallonshi tareda karisawa inda yake tsaye, kallonshi take sosai cike da mamaki mutumin da kullum yake cikin raha da dariya but yau face dinsa ya canza

"ya Kamal what's happened naganka cikin wannan yanayin? "
Nisha ta tambaye shi ciki kaduwa Amma setaga ya juya baya yadafe hanunshi jikin bangon dakin ya sunkuyar dakai kasa

" Ya Kamal kasani cikin damuwa naganka cikin yanayin da ban saba ganin ka ahakaba, please kasanar dani damuwarka"

"Nisha dama ke ba tawa bace " ras gaban Nisha yafad'i jin abunda Kamal ke fad'in

" but meyasa zakace haka ni takace mana Nisha tabashi amsa cikin damuwa narashin sanin dalilin dayasa yazo mata cikin wannan yanayin yana irin wannan maganan,

"Ke batawa bace Nisha because da aure akanki kika boyemin kuma nazo miki da soyayyata kika amsa ba tareda sanin igiyar aure ne akanki ba , why kika boyemin baki sanar da niba why Nisha? Kamal ya fad'in cikin daga murya gamida damuwa da baccin rai yana tambayan ta,

Nisha turos tayi tana kallon shi da mamakin maganganun da yake fitowa daga bakinsa, 'anya ya Kamal yana cikin hankalinsa kuwa Ammi tagani tazo da sauri kusa dashi ta dafa shoulder dinsa tana fadi'n

"Kamal mekakeyi haka ne? kamata yayi ka tsaya kaji abunda zan fad'i ba kafito ka kyaleniba yayinda nake magana kasaita natsuwarka mana haba Ammi tafad'i cikin sigan fad'a


"Ammi idan kowa zai boyemin ita bai kamata ta boyemin ba because tasan inasonta kuma na baiyana mata soyayya na agareta ta amsa batare da ta fad'amin matsayin taba, am,.

"Ya isa haka Kamal itama ba tasan komai gameda auran nan ba haka zalika shima Ajmal baisan da auranta akanshi ba iya tsakanimu magnar ta tsaya sai kai yanzu da kabijiromin da batun soyayyarku da na nemi na fahimtar da kai kaki saurarata". Ammi tafad'i cikin sigan shiga damuwa sam bataso abun ya kasance ta hakaba taso abi abun asannu ahankali but taurin kai irin na Kamal yakasa fahimtarta balle ya saurareta gashi yanzu yasa tayi subul da baka sirrin ciki yafito fili,

"Innalilahi wa'ina ilaihi rajuun" abunda Nisha take furtawa kenan ahankali yayinda ta dafe goshinta wanda takejin yamata nauyi saitaji mak'ok'oronta ya bushe yawun bakinta ya kafe dib

' Aure! Aure dai ' Nisha keta maimaita wa cikin zuciyarta ba jimawa idonta tasuma ganin walkiya walkiya haske haske hazo hazo kankance mai dakin yafara jiyuwa mata kafin su ankara tafad'i kasa sumammiya, sallallami sukashiga yi harsuna gwaral wajan karisawa wajanta tso da fargaba duk ya dabai bayesu

"Kaga irinta ko Kamal ga irinta nan da ka saurareni munyi maganan cikin nitsuwa da duk haka bata faruba da batajiba bare hankalinta ya tashi yanzu ga abunda taurin kanka ya haifar", Ammi tafad'i cikin rudu da tashin hankali

"Please Ammi kibar wannan maganan yanzu bashine solution ba mudagata mukaita asibiti don aceci lapiyar ta because karwani abin ya sameta"

Kamal yafad'i cikin rikicewa da tunanin mezaije ya dawo

"Kamal kira doctor kira doctor fu'ad please kirashi da sauri"

"Why not bazamu kaita asibiti ba?"

"Zaka sake taurin kainne ko zakayi abunda nace "

Ammi tafad'i a tsawace , cikin hanzari Kamal yamike yazaro phone dinsa cikin pocket dinsa marmaza yashiga dealing number doctor fu'ad yana dagawa Kamal yasanar dashi ana bukatarsa agida yana gama sanar dashi ya katse wayar ya kalli Ammi yana fadi'n

"Ammi taimaka min mudagata izuwa bed kafin doctor fu'ad din yakariso ba musu Ammi tasa hanu suka sunkuci Nisha wacce ke maga shiyar kamar macecciya suka daurata saman bed Ammi tazauna kusa da ita ta janyo hanun Nisha ta daura bisa nata tana murzawa idon ammi duk ya ciko gaba daya tausayin yarinyar ya kamata ita dama kwata kwata bataso al amarin nan ya kasance ba Hajia ce tayanke hukunci ba tareda tayi la akarin abunda zaije ya dawo ba da ace

6 / 24