Chapter 8 Reading AJEEMAL Book 2 Hausa Novels By Khaleeseart Abdullahi Raeys.txt Arewa Novels

AJEEMAL Book 2 Hausa Novels By Khaleeseart Abdullahi Raeys.txt

Author :  Khaleeseart Abdullahi Raeys Category :  Hausa Novels 001

Chapter   8 / 24

21K to 24K   out of 70.1K words

mana a gida Nigeria cikin babban birnin kano gidan yayi kyau fiye da tunanin mai tunanin dan haka sai muka soma shirin komawa Nigeria , .

Koda muka dawo Nigeria muka sauka agidan da Daddy ya siya mana gidane mai kyau na alfarma babu abunda babu acikinsa komai na bukata an ta na daishi acikin gidan sai dan abunda da ba arasa ba bayan kwana biyu da zuwan mu na bukaci Daddy da ya kira Modi ya sanar dashi zuwan mu saboda ni inna kirashi baya shiga saidai shi ya kirani wani sa'i bayan lokacin watakil shi akwai yanda suke sadarwa kwana biyu da yin hakan aikuwa Modi ya turo da wata kyakykyawan mota acewarshi ad'ibomu akawomu inda suke aikuwa hakan akayi duk mukayi shiri muka shiga motar da ya aiko domin mu shi kuwa Habu motarsa na bayan mu yanabin duk inda yaga munyi har Allah yasa muka isa gidan Masha Allah gidan da modi yake rayuwa aciki yanada kyau matuka Saida kyansa zai biyo bayan wanda Daddy ya siya mana Wanda muke kokarin fara gina sabon rayuwa a ciki, balaifi anyi mana kyakykyawan tarba an gabar mana da abubuwa kala kala kama daga a bubuwan ciye ciye da na lashe lashe.

Alhamdulillah naga d'ana cikin aminci da kwanciyar hankalin da alamu shima yaji dadin ganin mu tare da jin kyakykyawan labari dawowar mu Nigeria Saida abun lura dashi tun shigowar mu Modi ke tabin Hafsatu da kallon bakinsa keson cewa wani abin ita kuwa Hafsatu ba ta shima take ba hankalinta gaba daya yana kan yarinyar da ta ke ta shiga tana fice wajan d'a wainiya da mu duk wani abunda ake da bukata ita ke samarwa cikin hanzari kaida ka ga yarinyar baka kalar y'ar aikatau ko wahala ba kyakykyawan yarinyace kuma ga hankali yarinyace karama da bata wuce sa'arsu Fadeelah 13 year's sai girman jiki da suke da shi kai ka ce yan 20 year's.

Gaba daya nima hankalina sai ya karkata yakoma kan ta nan nefa nake tambayan Modi tunda nazo banga giftawar jininsa ko guda daya ba nan yake sanar dani duk suna can ture suna karatu but nan da karshen shaikara zasuyi hutu zasu dawo insha allah daga nan zai gabatar dasu gareni amma ga k'anwarsu Nabilah Abu yafad'i yana nuna min Nabilah wacce tasunnar da kai kasa tana jiran abata umarni tayi nace dashi yanzu wannan din yar kace na tambaya da mamaki dan k'wata k'wata ba zakayi tunanin yar gidan bace duba da yanda taga Jumanah tana ta tsawata mata d'an kuskure kalilan zata hantare ta gaba daya dai yanda take mata zakayi zammani aikatau take wanda kuwa ba haka bane, nan ya fara neman da nayafe masa ataikace dai yayi aure shaikarun baya da suka wuce auran bai jimaba matar tarasu saka makon jinya da taita fama dashi wanda aka kasa gane kan lamarin har Allah ya karbi rayuwarta.

Tabbas Modi ya shayar dani ruwan mamaki ban dauka zai iya mai dani ba a bakin komai na keba a garesa da har zai iya kula wani al amarin ba tari da nasa ni ko naji labari ba ban bi takanshiba ballai nasan sauran zancen da yake natashi na nufi gurin jikata tare da janyo ta jikina wanda ya sanya yarinyar sakin wani kuka mai tsuma zuciyan mai saurare gwanin ban tausayi take parlourn ya dau shiru bawanda yake magana daddy tunda muka shigo parlourn bayan gaisawa bai iya sake cewa kala ba ya zubawa sarautar Allah ido yana ganin yanda dan uwan nasa gaba daya ya koma sususu, fareeda da Fadeelah kawai na kallah na basu umarni dasu je ciki su ta ya Nabilah hada kayanta domin kuwa tare zamu tafi zama yakare mata agidan nan, amma Jumanah ba kunya babu tsoron Allah tashiga mita mai ya sa za adauke Nabilah daga gidan bayan ansan ita ta ke mata hidman cikin gida saboda Jumanah tamkar y'ar aikin ta haka ta dauki Nabilah duk wani ayuka na gidan ita takeyi amma ban bi takan ta kan surutan ta ba su Fadeelah suka hada kayan Nabilah suka fito muka wuce har muka fice daga parlourn HAJIA Jumanah mita ta ke wa Modi mai ya sa bazai dakatar damu daga kokarin tafiya da Nabilah da mukeson yi ba shikuwa Modi ya kasa tsaida mu kuma ya ka sa jure mitar da matarsa keyi haka muka tafi muka barso,,.


Turo door din da a kayine ya sa HAJIA da ka ta wa daga labarin da take bawa Nisha suka shiga zurawa door din ido don ganin mai shigowa, ganin Ammi ne tashigo bakinta dauke da sallama yayin da hannayenta ke dauke da trary din abincin tashigo ta tsaya daga gefe tana aikawa Nisha da kallon tausayawa kafin ta ce

" Hajia ya ka mata ki je ki ki kwanta kihuta ni because kin ga ke ma ba k'oshin lapia ga re ki ba d'an numfasa wa Hajj mama tayi kafin ta gyada kai takByalli Nisha tare da shafo gefen face d'in ta tana fadi'n

"Zan tafi saida safe ki kula da kan ki" gyad'a kai Nisha tayi daga haka Hajj mama ta mike ta fi ce daga bedroom fadi'n

"To yanzu bari natafi na baki guri ki kwanta ki huta good night" Ammi tafad'i tana yi wa Nisha kyakykyawan murmushi itama Nisha murmushin yak'e ta shigayi tana g'yad'a kai daga haka Ammi tafice daga bedroom din cike da jin dadin yanda Nisha ta sake jiki, nan Nisha ta koma ta kwanta because jikin ba k'wari kuma amace duk wannan sa kewar da Nisha tayi taci abinci cikin raha da rashin damuwa kawai ta danne zuciyarta ta ne because bata son su dinga shiga damuwa ta dalilin ta but Allah kadai yasan kukan zucin da ta ke.

Washe gari da asuba Nisha yanda taga dari haka wa ye wan gari because bacci ya kasa daukar ta gefe Fadeelah da Reeda sai bacci suke cikin kwanciyar hankalin amma ita bacci ya kasa ziyartarta sam tunani duk yabi ya adda bi k'wanyarta ta kasa gaskata wannan lamarin wai ita aka daura wa aure da Ajmal papan Aheel mutum da Sam baya kaunar kasan cewar ta atare da shi in ba ya ka sance dole ba taya ma zata iya kasan cewa da shi tare da wannan ma sifaffiyan matar tashi Heelah mai bala'in kishin tsaya duk time din da taji wannan al'amarin tasan saita konata da ranta, haka Nisha ta dinga juyi saman bed ta juya nan ta juya can daga karshe taga kwanciyar ya gagara haka yasa ta sab'ulu daga saman bed tanufi bathroom because asuba tayi anata kiraye kirayen sallah ga mai niya .

Wanka tayi sosai daga bisani ta fito ta naimi duguwar gown sannan ta sanya hijab tare da shinfida sallah tashiga jera salloli, karan ringin din wayar Fadeelah wata sai ta arlam na asuba shine ya tashesu daga nan nauyan baccin da suke, koda suka tashi idanuwan su ne ya sauka kan Nisha wacce ke zaune bisa sallaya bayan idar da sallolin ta tashiga yin lazumi ko waccen su mikewa tayi tasakko daga bed daya bayan daya sukayi alwala suka fito suma suka ta da sallah gefen Nisha, koda suka idar da sallah sukayi addu'a daga bisani suka mike Fadeelah tanufi bakin bed ta zauna yayin da Reeda ta ne mi saman sofa ta zauna gaba daya suka tusa Nisha a gaba suna kallo wacce kanta ke sun ku ye gaba daya yinin jiya bai musu dadi ba du ba da ya nayin da y'ar uwarsu ta kasance a ciki na rashin jin dadi ta wani ban ga re kuma ba karamin farin ciki suke da kasan cewar wannan lamari ba ko ba komai alak'a ya kara karfi tsakaninsu.

Jin shirun ko wannen su ya sa Nisha juyawo suka hada ido da su Fadeelah wanda ya sa su ka yi saurin sakar mata murmushi, itama Nisha murmushin ta mayar musu hade da jawo alqur'ani mai girma ta shiga karanta ko damuwar da ke zuciyarta zai kawo , tayi nisa cikin karatun yayinda kakejin yar siriruwar muryanta wanda ka ke ji kamar ana busa sarewa tsabar zakin muryar ahankali ta ke karatun saboda gudun shiga hakki, sai guraren 7:30 kafin ta samu daman tsagai tawa time din har su Reeda bacci ya sake kwashesu daga inda suka k'ishin gid'a ita Fadeelah ta G'yara kwanciyar saman bed itakuwa Reeda ta mike saman sofa sunata baccin su, ajiye alqur'ani Nisha tayi tare da ninke sallayan ta ya ye hijab din da tarufu ta nemi ma ya fi ta sanya bisa kanta tanufi hanyar fita daga bedroom din direct kitchen ta nufa ko zata tarar da barka cikin kitchen din but sai ta tarar ba ta ciki kamar bata fito ba kenan sometimes zaka iya tarar da ita guraren 6: ta na aikace aikace

Harta wu ce za ta koma sai kuma taji kamar shashshekar kuka ana jan akanci da surutai kasa kasa da ya ke kofar Barka yana gefe da kitchen shi ya sa Nisha ta jiyo sautin, ba da wani jin kiri ba Nisha ta matsa jikin door din Barka tare da murda handle din kofar ahankali bakin ta dauke da sallama ta tura kofar ta shiga, ko da Nisha ta shiga bedroom Barka a zaune ta sa me ta bisa sallaya tana addu'a yayin da ta daga hannuwa sama tana rokon Allah jin motsin shigowar mutum ya sa Barka saurin shafa addu'a tare da mutstsike hawayen face d'in ta tashiga k'irk'iro murmushi tana kallon Nisha yayin da ta kariso gefenta ta t'suguna

"Baba barka lapia kuwa mai yafaru?" Nisha ta tambaya tana kallon Barka wacce ta ke mammatse ido cikin damuwa,

"Bakomai y'ar nan lapia qalau na ke ya yau baki koma baccin ba kenan ya jikin naki ashe bakiji dadi ba Barka tashiga jero mata tambaya ta na murmushi da nuna ba wani da muwa da ke damun ta,

"I'm okay but sai na ke ga kamar kinada damuwa because ga face din ki ya nuna hakan"

"Lah ke kuwa y'ar nan mai zai da me ni a duniyar nan da ya wuce tsofa da tunanin mutuwa yau ko gobai" girgiza Kai kawai no Nisha tayi dan ba wai ta gamsu bane dan yanayin da taga Barka ciki ba ta saba ganin ta haka ba infact ma bata taba ganinta cikin damuwa ba balle harta kaiga zubar hawaye kullum cikin walwala da raha tareda wasa da dariya ta ke, d'a n numfasa wa Nisha tayi tana fadi'n

"Shikenan daman naje kitchen ne ban sa me ki ba shine nace bari na duba ki a bedroom din ki muje na ta ya ki aikin kafin Ammi ta fito idan kuma bakijin dadine sai na karba miki aikin

"Tab rufamin asiri y'ar nan kin gani qalau na ke yanda baki da koshin lapia ko aikin ban isa ki ta yani ba kije kiyi kwanciyar ki kihuta" tura baki Nisha tayi tare da b'ata fiska tana fad'in

"Nifa lapia ta kalau muje kawai Nisha tafad'i tare da juyawa tayi gaba Barka nabin bayanta tana murmushi hade da girgiza kai tana tunanin halin kirki irin na Nisha, karfe 8:30 Ammi tazo kitchen d'in ta tadadda Barka tare da Nisha sunyi nisa cikin aiki daga bakin door din kitchen din ta tsaya tana kallonsu ba k'aramin jin dadi ta yi ba kuma hankalinta ya k'ara kwanciyar ganin yanda Nisha ta sa ke sosai kai ka ce ba abunda ya faru hankali kwance su ke hiransu da Barka suna raha,

"Sannun ku da aiki" Ammi tafad'i time din da ta karisa shiga kitchen din duk juyo sukayi suna kallon Ammi wacce ta ke ta zuba murmushi kamar gonar auduga, cikin nishadi Barka tashiga dagawa Ammi gaisuwa sai da suka gaisa kafin Nisha tashiga mika nata gaisuwan

"Ina kwana antashi lapia"

"lapia qalau kyakykyawan y'ata ya kwarin jikin? ashe har kinfito kuma kika shiga wahalar da kanki"

"Wallahi kinga nima sai da na ce ta bari taje tayi kwanciyar ta ta huta amma taki kinsan mutumiyar ta ki akwai son aiki" Barka ta karbi maganar murmushi Ammi tayi gamida shafo gefen face d'in Nisha tana fadi'n

"Allah dai yamiki albarka but tafi wayance shashashon da basu da aiki sai bacci da danna phone zanga ya zasu kare da mazajen nasu idan basa bukatan y'an aiki kamar yayansu" dariya Barka tayi tana fad'in

"Aiko dai"

Nisha dai shiru tayi tana murmushi wanda bai kai zuwaci ba because yanzu bata da aikin da ya wuce murmushi yak'e ko dariyan dole saboda k'wata k'wata hankalinta ba akwance ya ke ba kwai dai danne zuciyarta ne karta nuna damuwarta afili tasasu cikin damuwar su ma, Ammi kallon Barka tayi tana fadi'n

"So fatan breakfast ya zama ready? but zanje nayi wanka na shirya asamar min da breakfast please"

"To ba damuwa yanzu kuwa" Barka ta amsa cikin b'arin jiki irina karb'an umar nin nan, daga haka Ammi ta juya ta fice daga kitchen d'in, ba bata lokaci Nisha da Barka suka shiga gabatar wa da Ammi breakfast d'in ta bisa dining table guraren 9 Nisha ta zame daga kitchen d'in ta fito tanufi hanyar fita daga parlourn.

Side din Ajmal ta nufa security da ke can gefe ganin Nisha na karisowa yasa ya mike da sauri ya shiga kiciniyar bude mata door din parlourn sai da tayi masa sannu kafin ta sa kafa tashige, shi kuwa security sai zuba murmushi yake harda na sayarwa kafin ya maida kofar ya rufe, bakowa cikin parlourn shiru kakeji kamar ba masu rayuwa ciki, direct kitchen ta nufa yau ta ci sa'a bubu uban tarkacen wanke wanke da Heelah ta saba tarawa cikin kitchen d'in da alamar jiya bata musu mahaukacin girkin da ta sa ba ba da yanzu kaga kitchen kaca kaca da tarin wanke wanke, ba tare da bata lokaci ba tashiga gyara kitchen d'in ta tsaftace shi daga bisani tashiga daurawa Ajmal breakfast mai dan sauki because ta gaji sosai,

Daga ban fitowa tayi ta dauki vaccum cleaner ta shiga tsaftace parlourn k'wata k'wata parlourn bai cika dutti ba kamar ba a zama cikin sa, tana ga mawa da parlourn sai kuma ta shiga haurawa upstairs,

Bedroom din Aheel ta nufa tabude ta shiga wani murmushi ta sake har kullum dakin Aheel ya masifar burgeta especially kyawawan Teddy's d'insa masu kya da ban sha'awa duk ya watsasu ko ina har saman bed, karisawa tayi ta zauna bisa gefen bed din lokaci diya tasaki wani murmushi mai sauti big teddy bear d'in da Aheel ya yake kwanciya da shi lokacin shitaga ya sanyawa Teddy bear d'in shi dariya ne ya kufcewa Nisha tare da daukan teddyn tana kallo, daga bisani ta rungume Teddyn kafin ta maida shi ta ajiye nan tashiga g'yarawa Aheel shin fidarsa tareda tattare masa kayan wasa da Teddy's d'insa guri guda kafin ta fito ko door d'in Ajmal ba ta kalla ba balle tayi tunanin ta shiga ta g'yara du ba da gargad'in da Heelah tayi mata akan shiga bedroom d'in mijin ta so duk randa tayi katari ta shiga tofa sai d'an buzun ta shiyasa ma ta dawo downstairs ta koma kitchen domin ci gaba da aikinta ,

Guraren 9:35, motar Ajmal ya sako kai cikin gidan time din da mai gadi yabude masa geat sai yayi parking kafin ya fito ya nausa kai cikin side din shi har security ya taho da niyar bude masa door Ajmal ya dakatar dashi sau da dama yakan hanasu yi masa duk abunda yasan zai iya wa kansa tofa yafi gane yayi da kanshi shiyasa bude masa door mota ko door din parlourn ko wani rakiya private bai cika son amasa hatta door din office d'insa da hannunsa yake budewa baya bukatar taimakon kowa sai dai irin wani taron biki ko taron siyasa ko wani taro na musamman da zai kasan ce awajan to nanne yake bukatan girmamawa kasan cewar shi shugaba koma shararren dan kwangila,.


Yana shiga parlourn saman table d'in parlourn ya ajiye key d'in motarsa tare da phone d'insa daga bisani shi kuma ya zauna bisa duguwar sofa ya mike yana sauke ajiyar zuciya remote ya dauka ya kunna television, dai dai time d'in da Nisha ta fito daga kitchen hanunta dauke da tray d'in abincin ganin Ajmal da tayi zaune bisa kujera ya kurawa TV ido yana kallon News channel, shi kuwa jin motsin mutum ta ba yanshi ya sa shi ju ya wa suka hada ido .

Kallon kallo suka shiga yiwa juna daga bisani Ajmal ya dauke kai ya maida shi kan TV yayin da ita kuma Nisha tashiga ta kowa ahankali ta kariso tsakiyar parlourn tare da ajiye tray d'in abincin bisa table kafin ta dago kai ta kallai shi.

"Ina kwana antashi lapia?"

Kamar bazai amsa ba amma kamar wanda akasa dole daker ya motsa baki ya amsa mata da

"Fine"

Mikewa tayi da nufin tashi ta fita but sai ta ji ya ce

"Zo nan"

Jiki asanyaye Nisha ta dawo ta t'suguna ta sauraron mai zaice,

"Mai yasa kika daina g'yara bedroom d'ina" Ajmal ya tambaya yana tsareta da ido daker ta iya motsa labenta wajan fad'in

"Am., damman Aunty Heelah ce ta ce karna sake shiga inba haka ba zata karya kafata" Nisha tafad'i kanta sun kuye, saura

"Nina saki aikin ko ita ?" Ajmal ya tambaya yana b'ata fiska tare da hade gira, cikin rawar murya Nisha ta amsa da

"Kai.,kkaine"

"So kar nasake miki tambaya akan hakan "

"To" Nisha ta amsa tana g'yada kai nan yayi shiru na dan wani lokaci bai sake magana ba ita kuma Nisha kanta na sun kuye jin shiru ya sa tayi tunanin ya gama korafin nashi hakan yasa cikin hanzari Nisha ta sake mikewa da shirin barin parlourn still sai ji tayi ya sa ke fad'in

"Come back ban ce kitafi ba" Ajmal ya fad'i yana hararota , cike da k'osawa Nisha ta dawo ta kuma duk'awa ba karamin ga jiya tayi ba tana bukatan ta huta but ya tsaida ita yana mata surutai gaba dayaa sai taji haushinsa ya kamata duk abubuwan da take masa ba gani yake ba, jin knocking anturo door yasa Ajmal da katawa daga maganar da yake kokarin yi ya kurawa door din ido don ganin wa ke

8 / 24