Chapter 28 Reading Zainazain Book 1 Compelet by janafty Arewa Novels

Zainazain Book 1 Compelet by janafty

Author :  Jamila Janafty Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   28 / 43

81K to 84K   out of 126.5K words

Tana kallonta,Cikin bayyana Bacin Ranta ta saka Duka Hannuwanta Ta Tallabi Fuskar Zaina Tana Fadin"Dago ki kalleni nan Halima..!

Tafada Cikim kakkausan Murya jin Umma ta ambaci Sunanta yasa Zaina Ta Dago da Jajayen Idanuwanta da suka kumbura Tana Binta da kallo Cikin Nuna kauna da Tsausayi Take fadin"Tunda kika taso na Taba nuna miki wani bambamcin Da zaki ji cewa bani na Haifeki ba..?

Ta Fada Tana kallonta Girgiza kai Zaina Tayi Hawaye suna kwararan mata Umma ta Cije baki Kafin ta Cigaba da Fadin"Toh meyasa kike Tunanin baki da kowa..? Kalleni nan Halima kina da kowa ni Fatima nice Uwarki Abban su kuma Shine Ubanki Har gobe,Kidaina Tunanin baki da wanda zai Shiga Lamarinki Ni nan zan iya Shige miki gaba akomai Wlh Na Daukeki Tun baki Cika Shekara Biyu ba aduniya Halima Na Rike Tamkar Diyar Data tsaga Jinina ta Fito Keda Zafeera da zareena Ban Taba Jin bani na Haifeku ba ina muku kallon Shakikan ya"ya ne Saboda Haka ki Sani Bazan Taba bari Acuci Rayuwarki ba..Zan Tsaya miki Tsayin Daka Har sai Zainullahi YA SAKE KI..!

"DAM! gaban Zaina ya Buga da Sauri Ta kara ware idanuwanta kan Umma kafin ta zaro Ido Cikin Dishashiyar murya Tana Fadin"Ya Sake ni kuma Umma..?

Sakin Fuskarta Umma Tayi Ta Mike Tana Fadin"Tabbas sai ya Sake ki..Bazan yarda kiciga da zama da Mayaudari mazinaci irinsa ba..Ya baki Takardanki Bayan kin gama idda kina karatunki Allah zai kawo miki Wani Mijin Mai Nagarta kiyi Auranki..Ammh ban Zan Juyar da kai Ina gani ki ciga da zama da Wanda bai san Darajan Kansa ba Ballatana yasan Darajan ki ba.."Baki Hamgame kawai Zaina kebin Umma da kallo da wani bugawar Numfashi Hade dana Zuciya Lokaci Daya kuma da wani kaunar Umma da Kimarta Suka karu acikin Idanuwanta Tana Tunanin Aduniyan nan akwai masu Hali irin na Umma..? Masu maida Dan wani nasu Su Ki nasu..?masu bayyana Laifin nasu saboda wani bare..? Bata Taba Jin Irin Mai Halin Umma ba Bata Taba ji ba.

Cikin mamakinta ta kara Bude baki Tana Fadin"Umma Saki fa kika ce..? Firstlove bazai Taba sakina ba Nasani.."Da sauri Umma Ta waigo Tana Fadin"Dolensa ya sake ki ko yana so ko baya so.."Kuka kawai Zaina ta kara saki Kamar wacce Aka Daka Umma ta Cije baki Tana Fadin"Gwara kiyi kukan Rabuwa Dashi..Da ki zauna Dashi Ki Cigaba da kuka Har karshen Rayuwarki ba Halima..!

Daga Haka ta Fice Daga Dakin Ta bar zaina na wannan kukan,Kukan wani Hali zata Shiga in aka Rabata da Firstlove..? Wata zuciyar tace mata ke kuma sai ki zauna Dashi..Kina kallon Dadirosa Ta Haihu Kuma ya aureta ya Hadaku Gida Daya Tare in Hakan ta Faru ya zakiyi..? tuna Haka yasa sai Da Taji kamar Numfashinta zai Dauke Cikin ganin Jiri Jiri Ta mike Ta Fada Bisa Gado Tana Fadin"Bazan iya Jurewa ba...Allah gani gareka...Hasbunallahu Wani"imal wakil.."

Take Fada Tana wani Gunjin kuka mai cin rai da kuma Saka Tsausayi ga zuciyar mai Sauraro.

******

Haddir gida ya koma ya kwana Cikin Halin Damuwa kamar yadda Ta kasance ta Bangaran Kowa da kowa Gari na waye Tun Safe ko tsayawa Karyawa bai yi ba Duk kuwa nacin da Hajiya mama Ta Dinga mai kan ya Tsaya ya karya bai tsaya ba ya Wuce asibiti,Adaidaita ya Hau Zuwa asibitin Tunda Motarsa na Wajen zain kuma Tun Jiya Daya Dawo yayi ta Kiran Layinsa Tun Tana Ringing baya Dauka Daga karshe sai ma yajita a kashe ya Shiga Tashin Hankali Dakyar yaga Safiya Saboda Zullumi Yana Tunanin Kila Zai samu Zain din acikin Asibitin sai kuma yaje bai sameshi ba Kuma Dr Peter ya Tabbatar mai Tun jiya bai saka Dr.Zain acikin idanuwansa,ba Kuma gama Motarsa nan a Haraban asibitin Tun Jiyan nan Daya barta bai Dawo ya Dauka ba, Hakan ya Tabbatar da cewa Zain Bashi a kusa Zuciyarsa ta Fara Rawa Yana Tunanin to yana ina..?

Tunanin zuwa Gidansa ya Shigeshi Ko patient ko Daya bai Tsaya Dubawa ba ya samu Mai adaidaita ya Hau zuwa Lowcost Gidan Zain Yana zuwa Bayan ya sallami mai adaidata ya Fara Buga Kofar get Din Tanimu maigadi yazo ya Budemai ganin Shine Yasa ya Fara Washe baki yana mai Kirari bai ma Tsaya Sauraransa ba,Ganin Motarsa A Haraban Adana motoci ya Tabbatar mai da Zain yana Cikin Gidan ko Takan Tanimu maigadi bai bi ba,ya Nufi Kofar da zata Sadashi Da Falon Gidan Har yana cin Tuntube Tanimu megadi Abun ya Dauremai kai ganin irin wannnan Saurin da Haddir yake yi Da kuma yanayin Dawowar da Zain yayi Jiya ya Tabbatar mai da Cewa ba Lafiya.

Haddir yana Shiga Falon gidan yaji Shuru Tun Daga nan yake Kiran Sunan Zain ammh sai yaji Shuru Hankalinsa ya kara Tashi,Shi kuwa Zain yana Cikin Bedroom dinsa kwance Cikin Wani Hali yana jin Kiran sa da Haddir yake ammh kuma bazai iya Tashi ba Ballatana Har yayi mgana,Ammh yana Fatan Allah ya bashi Ikon Shigowa ciki Domin yana Bukatar Taimako.

Allah ya karbi addu"arsa Domin kai Tsaye Bedroom din ya nufa yana Fatan Allah yasa Zain yana Ciki,Da Farko Knooking Din Kofar ya Farayi jin Shuru yasa ya Turata ta Bude ya Shiga yana Wurga Idanuwansa zuwa Cikin Dakin Cikin Ikon Allah sai Idanuwamsa suka Hango Masa Zaim kwance cikin Bargo ba yarda  yake ya Dunkule atsakiyar gado acikin Bargo Hankalin Haddir ya Tashi Da Gudu ya karisa Kan gado ya Dago zain yana Kiran sunansa Cikin Tashin Hankali,Ammh Zain baya iya mgana Jikinsa yayi zafi Hakoransa suna Haduwa Waje Daya Hawaye kawai suke Zubomai ta Gefen Kunnuwansa,Hankalin Haddir ya Gama Tashi Ganin Halin da Dan"uwansa kuma Amininsa Yake Ciki,Cikin Tashin Hankali Ya Dagosa ya sakamai Filo ya Jingina yana Binsa da sannu Toilet ya Shiga ya Debo Ruwan sanyi a karamin Baho ya sako karamin Towel yazo yana Goge ma Zain Jikinsa Daga kansa Zuwa Kirjinsa Bayan ya Sabule Vest Din Dake Jikinsa Bai barsa ba sai da yaga Jikinsa ya Rage zafi kana Zain kuwa kansa kawai yake Dafewa Cikin azaban Ciwon da Radadi Lokaci Daya Yana Zubar da Hawaye masu Zafi Haddir na Faman Sharemai Shima kamar yayi kukan yake Fadin"Kagani ko Zain..? Dama irin wannan Lokacin nake jiye maka..!

Yake Fada Shima yana Share kwallar Kwantar Dashi yayi ya Maida Komai cikin Tiolet Key Din Motarsa ya gani nan saman gadon ya Dauka ya Fice Da Gudu Yana zuwa ya kunna Motar ya Budeta ya Shiga ya Bata Wuta Cikin Gaggawa yayi ma Tanimu megadi Hon ya Bude mai Get ya Fice Daga Gidan,Wani Phamarcy Dake kusa Da Gidan yaje ya Siyo Mganguna da allurai Da kuma Drip Cikin gaggawa ya Dawo yazo ya Sakama Zain Ruwan bayan yayi Mishi alluran Ruwan Sai da ya sakamai masu Sinadaran Abinci Guda2 Kanana Bayan sun kare ya sakamai Babba Guda Daya Harda alluran Barci yayi mai kafin Lokaci Kadan Barci ya kwashesa Sai Lokacin Haddir ya Numfasa Gefen gadon ya koma ya zauna yana Kallon Zain yadda Zufa ta Fara Ketomai alamun zazzabi ya Fara sauka Remot ya Dauka ya Kunna mai A.C saboda Iska ya koma Kasan Cafet din Bedroom Din ya Zabga Tagumi Yana Bin Dakin da kallo Madubin Dakin ya kalla Shake da kayan Kawa na mata,Ga Jakunkuna da Takalman Zaina,Kan gadon ma Kayan Barcinta ne yana Tunanin kila zain ya Daukosu,Yanzu ina amfanin Haka..? Wa gari ya waya..? Da aace Zain yabi Shawaransa da Duk haka bai Faru ba..

Yana nan zaune har 1pm na Rana Tayi,Ya tashi ya Shiga Tiolet din yayi alwala yayi sallah bayan ya idar Lokacin Ruwan Daya sakama Zain din ya Kare sai yaCiremai ya sakaamai Dayan Har yanzu yana Ta barci alluran barcin bata Sakeshi ba,Fita ya sake yi Wani Restaurant yaje yayo Takeawaya Guda Biyu yazo yaci Daya bawai Domin yana Jin Ci ba sai Domin kada Shima yunwa tamai illah sai kuma Zain Wamda ya Dinga zama Dashi ba bai Farka ba sai Gabda La"asar,Kuma alhamdulillah Zazzabin ya sauka Ciwon kanma Babu Shi ya Taimakamai yayi wanka ya Dauro alwala yazo ya Rama Salolin Da suka Subucemai Kafin Haddir ya gabatar mai da abinci jalop din Shinkafa ce kadan yaci sai Madaran Yoghourt,sai Rabin kaza matsamai Haddir yayi yaci Sosai ya bashi mganguna yasha Ya koma ya kwanta Ya Lumshe Ido kawai yana Tunanin Rayuwa sai chan ya Bude yana kallon Haddir Dake gefensa yana Duba wayarsa Cikin Muryan Ciwo da Kasala yace"Firstlove Bata Dawo Gida bane..?

Kallonsa Kai Tsaye Haddir yayi kafin yace"Tana Gidan Abba..Domin Bata agidan Alhaji Tsoho.."Daga haka ya Tsuke bakinsa Shima Zain din kai ya Rausaya yana Fadin"Nasani Daman bazata zo ba...Itama zata Gujeni Allah na Tuba.."Yake Fada yana Sharan kwallah Haddir na kallonsa bai yi mgana ba Domin bashi da Abun cewa.

Suna nan Zaune Har barci ya Fara Fizgan Zain din sai ga Kiran Mama Safiya ta wayar Haddir Tana Fadin yana ina ne..? Gasu Gidan Abba Usman zasu wuce Jin haka yasa yace ma Zain bari yaje ya Dawo Daganan Daya Fita Bai zame ko"ina ba sai Gidan Abba Yana zuwa ya Iskesu Duka aharaban Gidan,Daddyn Abuja da Mama Safiya sai Hamdiya,Dasu Umma sai Abba Da Zareena wacce ke Rike da yarta Su Baban kaduna sun Dade da Tafiya Inna Rukayyah ma Ta wuce Inna Hannatu ne kadai sai Gobe Zata bi Jirgi ta koma Kowa kagani Fuska ba Walwala Dadyn Abuja da Abba sun kebe sai bashi baki yake Hakama Mama Safiya sai bama Su Umma Hakuri suke da kuma Nuna musu Yadda Da kaddara ya zama Dole ga Dan Musulmai,Umma Dai Tana Jin Mama Safiya ne kawai Nene ce ma ke Fadin bakomai Haka Allah ya kaddara Ita kanta zaina Mama safiya Tayi Ta bata Hakuri Tana chan suka barta Tana kuka wanda Ta wuni yinshi inda Hawaye suna karewa da Tuni Hawayen Zaina Sun Dade da karewa.

Zuwan Haddir yasa suka Dakata ya Rankwafa yana gaida Iyayen nashi mata kafin ya karisa wajensu Abba ya Duka yana Gaishesu Abba ya amsa Cikin Sanyi,Daddyn Abuja ne ya kalleshi yana Fadin"Kai ina Ka Shiga ne Tun dazu Alhaji Tsoho na nemanka bai ganka ba..? Ko ka Shiga asibiti ne.?

Kansa na Kasa yace"A"a Daddy nadai Shiga da safe na Fita...Zain ne naje na samu agida Yana kwance ba lafiya.."Daddyn Abuja yace"Ashha Subhanallahi..Meya Sameshi..? Haddir yace"Wlh Daddy Zazzabi ne mai zafi da Cowin kai sai yunwa kuma ammh yanzu da Sauki nayi Attemping Dinsa ya samu sauki na Barshi ma yana ta barci.."Daddyn Abuja ya Jinjina kai yana Fadin"Allah ya bashi lafiya..Ka Zauna ka kula Dashi..Sai Hakuri..'

Abba yace"Dom me zai zauna ya kula da wanda bai san Darajan kansa ba Aliyu..?Kawai saboda Shashasha irin na Zain sai Haddir ya ijiye zuwa aikinsa saboda kula Dashi..ya kyaleshi In ma Mutuwa Zai yi ya mutu..Wanda Yaja Ruwa Shi Ruwa kan Duka.."Abba ya Fada Cikin Bacin Rai,Daddyn Abuja yace"Assh..Abu baiyi Dadi ba..Haba Ya Usman Hannunka fa baya Rubewa ka yankeshi ka yar..Har yau har gobe Zain Danmu ne domin wannan Kaddaran Ta Faru babu Abunda zai Sauya Yana nan a matsayin Namu ne.."Cikin Fusata Abba yaja wani Dogon Tsaki yana Fadin"In ka Ga Hannunn
Naka ya Rube baka yankeshi ba Aliyu bai Dame ka bane..Ni kam wannan Rubabban Hannun nawa na yankeshi na Yardashi..Kuma na samu salama kai Hadiru ka wuce suwa sabgoginka ka kyaleshi koma miye ya Faru shi ya Jawo..!

Daddyn Abuja zai kara mgana Abba ya Dagamai Hannu yana Fadin"Allah ya kiyaye Hanya Aliyu..Ammh awannan Karon Ko Alhaji Tsoho bai isa ya Hanani Nuna ma Zain yaci Amanar yardan Da nayi mai ba.."Daga Haka bai kara mgana ba ya Rabashi ya wuce cikin Gida Fuu Su Umma suka Bishi da kallo Kamar yadda Haddir da Daddyn Abuja suka Bishi da kallo Har ya Shige Cikin Gida.

Numfashi Daddyn Abuja ya Saulke kafin ya Dafa Haddir yana Fadin"Take gud Care of Him Son..."Kai ya gyada mai yana Fadin"Insha Allahu Daddy.."Kai ya Jinjina yana Fadin"Allah yayi muku albarka..'Ya amsa da Ameen kafin yace"Yima Mamanka Mgana tazo mu tafi.."Daga Haka ya Shiga Gidan Baya Dama Direbansa ne ya kawosu Haddir ne ya karisa Gabansu Umma yace ma Mama Safiya tazo Daddy Na Jiranta Hamdiya ma Zareena ta yi ma sallama dasu Umma Ta wuce ta Shiga Gaban Mota Mama Safiya Tayi musu sallama tazo ta Shiga Mota Direba yaja Suka Fita Daga Haraban Gidan Bayan megadi ya wangale musu get suka Fice.

Daga Umma Har Nene ba wacce Tayi ma Haddir mgana suka Juya Zuwa Cikin Gida,Zareena ma Bata tsaya ba, Ta juya ta koma Cikin Gida ajiyar zuciya Haddir ya Sauke kafin ya Fada Motarsa ya Fice Daga Cikin Gidan.

Su Umma na Shiga Falon Suka Iske Abba na kai da kawo acikin Falon Hanayensa Goye abayansa yana ganin Shigowarsu ya Dago Cikin Bacin Rai yana Fadin"Fatima Da Aisha..!

Gabadayansu suka Zubamai Ido Suna kallonsu Zainab ma Dake Daki Tare da Zaina sai da ta Fito Jin yau kai tsaye Abba ya Kira Sunan Umma da Nene wanda basu Taba jiba da wayansu ba sai yau Haka ma Zareena Gabanta sai Fadi yake Allah yaasa Jalal yabi su Saudart zuwa Islamiya.

Cikin kakkausan Murya da zallar Bacin Rai yace"Ban amince ba kuma ban yar jema Daya Daga cikin ku Zain yazo Gidan nan Ta Daga ido ta kalleshi ba.."Yafada yana nuna su da yatsa Umma dai batayi Yunkurin yin mgana ba Nene ce Ta marairai ce Tana Fadin"Saboda me Abba..? Zain yana da wasu iyaye ne bayan mu..?

Cikin Tsawa yace mata"Eh mana yana Dashi..In ba ya maidamu wasu Shashashu ba Taya Taya Zai aikata irin wannan Dabi"ar bamu sani ba Karuwa fa ya ijiye Dadirowa fa Aisha Ahakan kuma muke zaman iyayensa..!? Ina Ban Amunce ba Ko yazo Gidan nan kada wacce ta mai mgana ku Rabu Dashi...Tunda ya Riga ya gama Cutar da Zuciyoyin da suka yarda Dashi..Yaci Amanarmu Mu iyayensa kuma yaci amanar amatarsa,Ku kyaleshi ni da kaima zan mai iyaka Da Shigomin Gida Tunda ba Da kudinsa na ginashi ba..!

Nene Taji Hawaye sun kawo mata Cikin Sagewar Numfashi Ta Bude baki zatayi mgana Abba ya Dakatar da ita da Fadin"Karki kara cewa komai...Umarni ne na baku ba Shawara ba..Har ke Zareena ban Yarje miki ki Saurareshi ba.."Daga Haka kawai ya wuce Fuu zuwa Dakinsa Umma ta Cije baki wani Abu na Suyanta acikin Ranta Ta mara mai Baya Nene ce ta Sulale nan Tana kuka Zareena ma Haka Zainab ma Tana Tsaye Tana Hawaye,Sadiq kuwa da Shigowarsa kenan Dakinsa kawai ya wuce yana jin Tsausayin Yayan nashi Har Cikin Ransa.

Zaina kuwa Tana Tsaye Daga Bayan Zainab Daga Cikin Dakin Bata Fito ba Taji Duka Abunda Abba yace sai ta kara Rudewa da Shiga Tashin Hankali Taya Ya Abba zai yanke wannan hukuncin..? In yace haka ina Ya zain zashi..? Tasan Duk Harda Saboda Ita Abba ya Dauki wannan matakin Sai Taji kamar Jiri na Dibanta zata Fadi baya Tayi ta koma Kan gado Ta zauna Tana Sharan Kwallah Tana Jin Zuciyarta na Bada wani Sauti Mara Dadi Fat! Fat..!






*Shakira...*
*ZAINAZAIN..!*
_(Is a love Story and Betrayal)_

*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janaftyshakira*❤️


*BOOK 1*
    
               2️⃣1️⃣

"Da Sauri Nene ta mike kamar Zata Tashi sama ta Wuce Dakin Umma Zareena da Zainab suka Bita da kallon mamaki,Kada kai kawai Zareena Tayi ta mike Tana Rangaji ta wuce Dakin Datake sauka in tazo Ganin Gida Zainab ma Baya Taja ta koma Cikin Dakin Tana Sharan kwallah Turus Tayi ganin Zaina Kwance kan gado tana Kuka mai cin Rai Da kuma Raunana Zuciyar mai Sauraro.

Itama nan Kasan Cafet din Zainab Ta Sulale ta Maida Hannayenta ta Tallabi kanta Tana Cigaba da Tsiyayan Hawaye,Domin bata da wani karfin Gwiwan Hana Anty Zaina kuka Domin Abun kuka ne ya sameta Dole abarta ta koka ko Zataji Saukin Abunda ke Damunta acikinn Ranta ita Fa kenan Data ke kanwarsa Taji Zafi Abun ya Raunana mata Zuciya Ballatana ita Matarsa Da ta kasance abokiyar Sirrinasa gabadaya.

Umma na Shiga Cikin Dakinta Ta maida kofa ta Rufe Lokaci Daya Tana sakin wani Siririn kukan Daya ke neman kwace mata Tuntuni Tana Boyewa,Shi ta saki yanzu Domin Abun yana Fito mata Daga kasan Zuciyarta ne kukan Bakinciki da kuma Tsausayin Zaina Gefe Daya kuma Tana jin wani Daci acikin Ranta In ta Tuna Abunda Zain ya aikata a matsayinta ta uwa Dole ne Tafi kowa Shiga Tashin Hankali game da wannan lamarin Duk da Tana Boyewa bata son Kowa ya Fahimci Ta Damu da Abunda ya Danganci Zainullahi din.

Nene Ta Dade tsaye kanta Tana kallonta Bata sani ba,Har Shigowarta Bata sani ba ballatana wamzuwarta acikin Dakinta Tana ganin Tana kuka Tasaki Mirmishin Takaichi kawai Domin ko Umma Taso Boye Damuwarta ita awajenta bazai Taba Boyuwa ba ba Tun yau ba tasan Cewa Duk Cikin Ya"yan da Umma ta Haifi Tafi Son Zainullahi kara ce kawai da kawaicin Dan Fari Da kuma Tasowar Da yayi ba ahannunta Ba yasa bata Shiga lamarinasa ammh Tabbas Soyayya Uwa da Da'nta Ko Uwa taso ta Boyeshi baya Boyuwa Allah zai bayannashi Wannan kukan Datakeyi bana komai Bane nashi ne Da kuma Bakincikin Matakin da Abba ya Dauka game da lamarin.

Ganin Batama san da Tsayuwarta ba yasa tayi gyaran Murya Wanda  ya karkato da Hankalin Umma Zuwa Fahimtar ba ita kadai bace acikin Dakin Kafin ta waigo sai da Tayi Saurin Share Hawayenta saboda Bataso wani ya ganta Tana kuka kana ta Juyo Cikin Sanyi Jiki ta Sauke kallonta kan Nene wacce ta kura mata ido Tana kallonta Cikin Tsausayi da wani irin Girmanta Da Nene take gani acikin Idanuwanta.

Yake Umma Tayi Tana Fadin"Ya akayi ne Hajiya Nene..? Tafada Cikin Zolaya Dama wani Lokacin Haka Take Kiranta Nene bata saki Fuskarta ba tace"Meyasa kika yin mgana kan Hukuncin da Alhaji ya yanke kan Zain..?

Wani kallo Umma Tayi mata Tana Kokarin Boye Abunda ke Ranta Tana Fadin"Meyasa ni kuma zanyi mgana Nene..?Yana da Damar da zai iya yanke ko wani Hukunci Tunda Dagamu har shi muna Karkashin Ikonsa ne..Kuma Banga Illah kan Abunda ya yanke din ba Nene..Yana da gaskiya bai kamata ka kara Sauraran Wanda ka bama yarda ba ya Cutar dakai ba..."

Ta Fada Tana kokarin maida kwallar cikin Idanuwanta Nene tayi Dariyan Takaichi kafin tace"Naji Hukuncin yayi miki Dadi Ammh Umman Zareena Meyasa kike kuka..?

Umma Tayi Saurin Cewa"Ina kukan Tsausayin Halin Da Yata Halima Take ciki ne Nene...Ina Matukar Tsausayamata Tana da kananan Shekaru ayanzu haka Tayi

28 / 43