Author : Jamila Janafty Category : Romantic Hausa Novels
School ce Kashe Motar yayi ya Fito Yana Gyara zaman Caot Din Jikinsa Lokaci Daya yana Duba agogon Fatan Dake Hannunsa Pass 8.
Da Baba Megadi suka Fara gaisawa kafin kai Tsaye ya Fara Taku Zuwa Kofar da zai sadashi da ainihin Babban Falon Gidansu Motar Abba yagani da Direbansa yana Tsaye yana Jiransa alamun Shima yau bai Fita da Wuri ba,Barayin su Saudart ya kallah bama su Lura dashi ba ganin Haka yasa ya Dakata ya kwalama Junior kira.
Waigowa Sukayi Duka Atare Jin Muryansa da Sauri suka kwashi Gudu Zuwa Wajensa Atare suka Hada Baki Suna Fadin"Sannu da zuwa Yaya Dacta..And Happy Birthday.."
Suka Fada Suna Mirmishi Yara ne Masu kama da Zain kamar an Tsaga kara Barin ma mace Saudart yar Shekara Goma Sha Uku a Duniya yayinda Junoir yake dan Shekara Tara aduniya Cikin mamaki da Mirmishi yake kallonsu Kafin ya Dafa kawunansu,yana Fadin"Kai...Waya gayamuku yau Birthday Dina..? And kuma meys Hanaku zuwa School yau
.?
Saudart ce tayi Saurin Cewa"Yaya Dacta Jiya aka bamu Hutun Meadteam Break Sai Monday zamu koma.."Kumatunta ya Shafa yana Fadin"Daz Gud Anty Kumatu kamar Nene na baki Madaran yara sai kiba ki ke Karawa Saudatu.."Dariya Junior ya Kwashe Dashi Ita kuma sai ta bata Rai kamar zatayi kuka Tana Hararanshi,Ganin Haka yasa Zain ya Riko Hannun Junior yana Fadin"Kai karka kara mata Dariya ok..?
Kai ya gyadamai Yana Kokarin Danne Dariyansa kafin yace"Yaya Dacta Nene ce ta gayamana yau ce Ranar Zagayowar Haihuwarka..."Kai ya Jinjina yana Fadin"Dama nasan Itace Kadai agidan bata Manta Ranar Haihuwarta ba..."
Yafada kai Tsaye yana Rike Hannayensu Dukkansu Suka Nufi Cikin Gidan Suna Tafe Suna mai Hira Suna Dariya da Haka sukayi Sallama a Babban Falon Gidan Zainab ce Kadai ke Zaune Tana kallo Gefe Daya kuma Tana Danna Wayarta Dake Hannunta tana Jin Sallamarsa ta mike tana Ihu Tana Fadin"Happy Birthday To U...Happy Birthday Happy birthday To u Yaya Dacta..Nene Fito ga Yaya Dacta yazo..!.
Take Fada gabadaya Fararan Hakoranta Suna Waje Jin Haka yasa Wacce aka kira Da Nene ta Fito Daga Cikin Bedroom Dinta Tana Fadin"Maraba da Da" irin na Nene Dan albarka.."Take Fada cikin Tsantsan Farinciki,Wata Gajeruwar mata na gani mai Kiba kadan Ashekaru bazata wuce 48 aduniya ba Fara ce Tas Tana da Zanen Biyu Biyu agefen Fuskarta Akallon Farko in kayi nata Zaka Fahimci Tana da Saukin kai da Wayewar Zamani.
Zain da Farinciki ya Cika Ransa ya Saki Hannun Su Saudart ya Tafi ga Nene ya Ramkwafa zai Gaisheta da Sauri ta Dagosa Tana Fadin"A"a kul Dan albarka Babban Mutum Mun Tashi lafiya...? Barka da Zagayowar Ranar Haihuwa Son..Allah karama Rayuwa albarka Dama yau muke Shirin in baka zo ba zamu kwasa muje chan Gidan naku muyi Shagali Wasu sai jin Haushi Suke Suna Fadin Shirmen Banza.."
Tafada Tana Nuna Umman Zareena da baki Wacce ta Fito Daga Kitchen,Dauke da Mug din Ruwa a Hannunta Doguwar Mace Ba Fara ba Chan tana da Haske,A kallan Farko in kayi mata Zaka Shaida Mahaifiyar Zain ce Saboda yanayin kamarsu da Juna Ashekaru itama Bazata gaza 49 ba Aduniya Tabe baki Tayi bayan Ta kallesu Tana Fadin"Kwa ji Dashi dai..'.
Yana Dariya ya Juya yana Fadin"Umman Zareena ina kwana.."Tana kallonsa Tace"Lafiya lau Dacta...Ina Kwanan Diyata..? Yana Sosa kansa yace"Tana lafiya Umma..Tare muka Fito ta Shiga School ammh Tace In ta gama abunda take Daga Gidan Alhaji Tsoho nan zata zo gaida ke.."Yafada yana yar Dariya Mirmishi Umma ta saki Tana Fadin"Na sani...Allah ya kawomin Ita Lafiya ina kewarta Daga Ita Har Zafeera ban ji su ba kwana Biyu,Jiya dai mun yi mgana da Zareena..!
Nene Tayi karaf tace"Wannan dai ya"yan naki Sai dai nace kinyi Sa'an Haihuwa Ya"ya Suna Mantawa da Uwarsu Abu dai Baiyi Dadi ba.."Tafada tana Dariya Umma tace"Au ke saboda naki Yaron na gabanki..? Allah kawomin Halimatuna lafiya..!
Tafada Tana Juya zuwa Shashen Megidan Wato Alhaji Usman Abubakar Saulawa,Zain ya saka Baki ya Kirata.."Umma baki ji ba..!ta waigo tana kallonsa Cikin Shakiyanci yace"Umma baki min Happy Birthday ba yau fa nake Cika Shekara Dai Dai Har Talatin aduniya fa Umma.."Wani Dogon Tsaki Taja Kawai Tana Fadin"Rabani da Saka kaina Cikin Shirmenka kai da Uwarka.."Daga Haka ta wuce su Nene suka Rakata da Dariya Harda Yaran Itama da Mirmishin ta Shige Akan Fuskarta.
Tana Wucewa Nene ta Jashi ya Zauna kan kujera Tana Fadin"Ina Zuwa Yarona.."Tafada Lokaci Daya ta wucewa Kitchen Zainab ta kariso Tana Fadin"Yaya Dacta Don Allah yau ka bari a Shirya kayattacen party for u agida nan plz..!
Kallonta yayi yana Fadin"Kefa yarinyar nan na Lura yar son Bidi"a ne fa.."Yafada yana Hararanta Dariya ta Saki Tana kokarin mgana Nene ta Fito da wani katon Cake a Hannunta Su Junior suka Saka Ihu mamaki bai Kama Zain ba Domin Duk Shekara Sai Nene ta Shiryamai Ranar Haihuwa koda baya Gari zata yi Shagalinta agida su Kirashi Vidoe call Suna Tayashi Murna.
Kan Center Table Din Dake Tsakiyar Falon taja ta Daura Cake din,su kuma su Zainab da Saudart suka je suka kwaso kananan Baloon din da suka Hadashi Tun Jiya suka zo suka watsa Afalon Lokaci Daya Suna Sakin Wannan Abun mai kamshi da kuma Farfatsi asama yana Sauka Bisa kan Zain Din Lokaci Daya Suna mai wakar Happy Birthday bakinsa yaki Rufuwa da Farinciki Haka bakin Nene Sai da suka gama Tace su Dakata Zain ya yanka Cake.
Har gaban Cake din Taja Hannunsa Takai Ta mikamai karamar Wukar Hannunta ya karba yana mata Dariya Duka Hannuwan Kannensa yahada da Na Nene zai yanka Cake din Yaji Dagachan Abaya Ana Fadin"Yaron Nene wannan Son kai yayi yawa Shikenan Haka akeyi sai ka yanka Cake ba Umma zareena ba Abba kuma ba Ita Firstlove din Taka..?
Dukkansu suka waiga Jin muryan ABBA,farin Karkkafan Namiji ne mai Cikar kamala da Zati kenan,In ka gansa zaka Fahimci nan Zain ya Debe Tarin Dattako da kamalan Fuska Harda Haiba da kwarjini,afizge Suna kama na jini,Da Duka Ahalin nashi yana ashekaru ba zai gaza 58 ba Sanye da Riga da wandon Shadda Harda Babban Riga kansa Sanye da Hula Umma na Gefensa Rike da Karamar Jakarsa na Briefcase Tana Mirmishi.
Ganinsa yasa Zain ya Washe baki yana Fadin"Sabahul khair Abba.."Fara takowa sukayi gabansu Lokaci Daya Yana Fadin"Lafiya Likitan Mata na Nene Kuma angon Halimatu ko..? Yafada Cikin Zolaya Lokaci Daya Yana kallon Nene kafin ta samu Zarafin mgana ya Rigata da Fadin"Kin kyauta..Munga Son kai Hajiya Nene masu D"a...Kawai Sai ku yanka Cake dinku ku kadai Salon Rowa kada muma ayanko a saka mana Baki Toh Wlh baku isa ba gamu munzo Dale ajiramu ayanka Damu kuma aci Damu badai Fadi kawai ake Happy Birthday ba muma mun iya.."Ya karishe Fada Cikin Barkawanci da Zolaya.
Gabadayansu Suka sakamai Dariya yana Kallon Junior yace "Ko ba Haka Ba Basiru..'Baki ya Tura yana Fadin"Ni fa Abba ba Basiru bane Sunana Am Bashir Usman Abubakar Saulawa by Name.."Abba yace"Kai Don Allah..? Maimaita me kace Sunanka.."Yafada yana karkatamai Kunni Cikin Haushi Junior yace"Bashir Usman Abubakar Saulawa Abba.."Gabadayansu suka kara Sakamai Dariya Ganin Idanuwansa ya kawo kwallah ne yasa Umma ta Jawo sa Jikinsa Tana Fadin"Kyalesu Junior na Abba ke son Taba min kai ko? Kowa ya sani Sunanka Bashir ne ba Basiru...!
Sai da suka gama Dariyan Nasu kana Abba ya karkace kai yana Fadin"To mu yanka Cake din mana Sauri nake Meeting gareni 10 fa.."Nene tace"Taci albarkacin ka ABBa...Da naso Sai Yar nata tazo sai su yanka nasu mugani.."Zain na Mirmishi yace"Kamar kin sani Nene..Ragowan data Hadamim Jiya yana nan zata Zo Dashi..Su yanka ita da Mamanta.."
Nene tace"Kaji ko Abba..? Gaskiya bamu so Leken Asiri.."Tafada Tana Dariya Umma tace"Mugani..? Wannan cake din ba bai kai kyan na Diyata ba na sani..? tafada tana Leke Cikin Barkwanci Bata Rai Nene Tayi zatayi Mgana Abba yace"Meye na Fushi..? Bar ta ta yanka taci Itama in yarta Tazo Dashi ataru ayanka aci sai a Tantance Tsskanin na Uwar Da na matarsa wanne yafi Dadi.."Abba yafada yana Dariya Zainab ta kada baki Tana Fadin"Gud Idea Abba.."
Dole ba Yadda Nene Zatayi suka Hadu suka yanka Cake Zain ya Dinga Dauka Daya Bayan Daya Yana Basu Nene aka fara Bamawa Itama ta bashi Tana Fadin"Allah ya albaeci Rayuwarka da Farinciki yarona..Zunubanka na Baya Allah ya yafe maka Allah yasa wannan Shekaran Daka Tunkara Alherin Allah ya Lullubeka.."Gabadayansu suka amsa da Ameen Daga Ita ya bama Umma itama ta bashi Tana Fadin"Duk da Mamanka ta Riga ta gama cewa Komai..Ammh Nima zan ce..Allah yayi maka albarka Likita.."Tafada tana Shafa kanshi Mirmishi yayi yana Jin Wani Farinciki kafin ya Furta..'Nagode Umma..!
Daga Ita sai Abba ya Bamawa Daya Dauko karami kin karba Abba yayi yana Fadin"Nene ji Son kan D'anki.? Wanda ya baki katon Gaske yama Fi karfin bakinki ammh ni kalli nawa Wani karami Wanda iyakarsa bakin Saudatu.."Yafada yana kauda kai Dariya suka sakamai Kafin ZAIN ya yanko wani kato kana Abba ya Karba ya Turamai baki Har sai ya Fi karfinsa Ya batamai Gefen baki me yaran zasuyi in ba Dariya ba Zainab na Gefe Tana Daukan Vidoe tana Fadin"Dole su Anty Zareena susha Takaichi in suka ga Wannan Show din..'
Haka ya bi kannen nashi Duka ya basu suma suka Bashi,Suna yi Suna Barkwanci Suna Dariya Suna gamawa Abba yace"To angama..? Ni bari na Tafi office saura na anjuma in Firstlove tazo da nata.."Yafada yana yar Dariya Umma tace"Kwarai..Bazamu yanka ba sai ka Dawo Abban Saudat..'
Nene tace"Oho dai Sauran yarona ne..Tunda Jiya sai da ya Fara yanka Abunsa kuma yaci..'Umma tace'Naji ba komai..Ai ni na Koyar da ita kyautatama yaron naki..'
Nene tace"Nima ai na Koyar dashi Rike Diyar naki..Ke kanki kinsani Samun irin mai Nagartan Dana sai an Tona.."Umma tace'Nima fa..Ai ya sani Diyata Badaga Baya ba.."
Abba ya mika Hannu yana Fadin"Nidai bani Jakata Nagode..Bari na Tafi in kuka Fara wannan Jayayyan naku kan ya"yan naku ba kwaji bakwa gani..na Tafi sai na Dawo.."Gabadayansu suka Rakashi da Adawo lafiya Zain ya Biyosa yana Fadin"Abba gidan Tsohon nan zaka Fara biyawa kafin ka wuce ko..?
Abba yace'Eh Zaka ne..? Yafada bai Tsaya ba Da Sauri Zain yace"Eh Abba..Dazu Firstlove ke Fadamin Haddir ya Fadamata yana Fama da Mura.."
Bai samu bashi amsa ba Sai da Suka Fito Daga Falon kana Yace mai.."Yanzu sai karfe nawa zaka Tafi asibitin kenan..? Yaron Nene adaina Wasa da aiki fa..!
Yana Sosa kai yake Fadin"Ba Haka bane Abba...Akwai Likitoci asibitin kaima ka sani..Kuma ina zuwa zan Fara addenting din Patient.."! Abba na Mikama Direbansa Jakarsa yana Fadin"kardai abarsu Jira..Kakanka na alfahari Dakai ya kamata ka daina Shiriritarka.."Da Sauri Zain ya Budemai Murfin Motan yana Fadin"Insha Allahu Abba..!
Sai da Yaga Fitar Motan Abba kana ya Shiga Tashi yabi Bayansa Tsakanin Gidan Iyayen nashi da Gidan Alhaji Tsohon ba Nisa Duka Anguwa Daya ne ko a kafa zaka iya zuwa..Kusan Tare suka isa da Abba Tare suka kuma Jera suka Shiga Babban Falon na Alhaji Tsoho kana ganin yanayin Gidan zaka Fahimci ma mallakin Gidan Yana da Tarin Ilimi.
Suna Shiga Suka iske Haddir yagama Dubashi yana Shirin Tafiya ne Suna Shigowa da Sallama Alhaji Tsoho ya Dago yana Kallonsu Lokaci Daya yana Gyara Zaman Siririn gilashin Dake karamai karfin gani Farin Dattajo mai Yalwar Fara"a Da Dattako,yana Zaune Bisa Wata kujeran alfarman Daga Tsakiyar Falon,Sanye yake da Wata Farar Jallabiya Rantsatsiya mai kyau irin ta Saudiya,Gefe daya kuma Yana Rike da Wata karamar Sanda kamar ta Axurfa wacce ke karamai karfin Takawa,Akallan Farko in kayi mai zaka Fahimci Tsantsan Haibansa da Zatinsa Uwa Uba Nasabansa da Nagartansa,Dr Abubakar Bashir Saulawa kenan a Shekarunsa na Haihuwa Kimanin 93 kenan a Dunya Farin Gemu Duk ya Lullube kansa da Sajensa Gabadaya Ammh Fatarsa bata Yamutse ba kamar na Wasu Tsoffin Saboda Tana Samun Jin Dadi da kulawa Daga ya"yansa Uwa Uba kuma Tsantsan Ilimin Dake Tare Dashi Both Boko da Arabi.
Da Mirmishi Bisa Fuskarsa ya amsa Sallaman nasu yana Fadin"A"a Muryoyin wa nake ji kamar ta Usmanu Bin Fodiyo da Babban Likitan Mata Iyayenmu Dr.Zainullahi Usman Abubakar Saulawa Mijin Halimatu Sa"adiya..."Yake Fada Gabadaya Hakoransa Suna Waje Domin Babu Hakoransa ko Daya Daya Fita.
Haddir Dake gefensa Sanye da Suit Black and White sai Rigar Likitancinsa Lapcoat Daya Dora asama yace"Kaji Tsohon nan Da wani Dogon Sharhi..Kana Nufin baka gani ne sai Daukan Murya..? Lalle ka Fara Tafiya Tsoho..!
Ya Fada yana Dariya Dakuwa Abba yamai yana karisowa Cikin Falon Lokaci Daya Tana Fadin"Kaga Naka nan Hadiru mu kam Tsohon mu sai ya Bar Duniya da Idanuwansa Insha Allah.."Yake Fada yana Zama Kusa da Alhaji Tsohon Cikin Girmamawa ya Shiga gaisheshi Haddir da Zain suka Sarke Hannun Juna Suna Dariya Mirmishi Alhaji Tsoho yayi yana Fadin"Kyalesa Usmanu Bin Fodiyo Haushi yake ji Domin nace in ya wuce wannan Ramadhan Din bai kawomin Matar Aure ba sai na Bugamai Kidan Gauro ka ganshi nan Shine yake ta wani kunci Toh ba wasa nake ba Jira nake Karshen Satina nan yayi Ubanninka Su Taru zan Musu bayani in ma Baka lafiya ne Gwara Tun Wuri ka Fada anema maka mgani..!
Da Sauri Haddir yace'Waye bai da lafiya..? Ni wlh Lafiyata kalau.."Yafada yana wani Bata Fuska Zain da Alhaji Tsoho Suka Fashe da Dariya Lokaci Daya Abba na Tayasu Duka Haddir yakai ma Zain Abaya yana Fadin"Ameobo..."Shidai Zain Dariya kawai yake ya Duka ya bama Alhaji Tsoho hannu Sukayi musabaha Yana Fadin"Likitan kwakwalwa ya Mura..? Jiya Firstlove ke Fadamin Baka ji Dadi ba..?
Alhaji Tsoho yace"Wlh...Naji Dama yanzu Muran ma Tayi Sauki Uwargida da Amaryata Suna Kula Dani..'Yafada yana Mirmishi kafin ya Cigaba da Fadin"Wato Iyayen naka Zainullahi sai dai nayi musu Fatan Gamawa da Duniya lafiya kawai Jiya nan suke Har Dare da Kayan Dubiyarsu Tare da Feefesun kazan su Wanda yaji Citta namu na masu Mura..Lalle ban yi Nadamar Aurama Usmanu Su Arana Guda ba Aisha da Fatima Allah yayi musu albarka Allah kuma ya albarkaci Zuru"arsu.."Gabadayansu suka amsa da Ameen kafin Zain yace"Wai ina Matas ne ban ji Motsinta ba.."
Alhaji Tsoho zai yi mgana kenan Sai ga Wata Farar Dattijuwa ta Fito Daga Cikin Kitchen Dauke da Silba Cike da Damammiyar Fura,Kallo Daya zaka mata ka Shaida ita ta Haifi Alhaji Usman Saboda yadda Yake kama da Ita,Itama Ashekaru bazata wuce 70 ba,Ammh bazaka Fahimci haka ba sai ka Kura mata ido saboda jin Dadi Hajiya Amina Kenan Wacce Ya"ya da Jikokinta ke Kiranta da HAJIYA MAMA..!
Tana Karisowa Cikin Falon Tana Fadin"Ga ni nan Ango na ina chan ina Dama ma wannan Tazurun abokin naka Fura ne ina Tsausayamai kada yaje aiki Bai ci komai ba.."Tafada tana Dire silban Gaban Haddir Tana Fadin"Gashi nan...Megida ba Cefene na gaji da maka Bauta..Ka nemi mata kayi Aure kafin na Dauke maka kafa Atoh..'Jan Silban yayi yana Fadin"Ke kuma shikenan sai kimin Tonin Silili gaban wannan Tsohon Mijin naki me Tafiya da Sanda ko..?
Alhaji Tsoho yace"Kwarai..Kuma yafi wani mai kafan amfani Tunda ni Har yau ina Cefane.."Hajiya Tayi Dariya Suna gaisawa da Abba da Zain kafin Haddir yace"Au haka kika ce ko..? Bari na koma Wajen Baba Tabawa Ita zata yi Mijin Dani.."Hajiya mama tace"Eh Jeka tana Kitchen ka sameta ita kam zatayi Kayan Megida ba Cefane sai Wahala."Zain sai Dariya yake Haddir na Hararansa ya Dauki Furansa zai bar Falon kenan Alhaji Tsoho yasa baki ya Kirashi Ya Dawo kallon Abba yayi yana Fadin"Tayani Gayamai Usmanu..Kila kai yaji mganarka ace yau Dan Aliyu Yana Garinan ga Gidanka ga Gidana Ammh bazai zauna ako Daya ba Sai yaje ya kama Haya Shi gashi ba Mata ba..? Kaniyarsa yake achan Usmanu..? Maza ka gayamai komai yake Ciki ya Tattaro ya Dawo Gidanka ko Nan Gidan da Zama ban lamunci Zamansa awannan Gidan ba Tunda ba mata gareshi ba..!
Yafada Cikin Alamun ba Wasa yake ba Abba ya Jinjina kai yana Fadin"Hakane Alhaji Tsoho..Kai Haddir maza ka Tattaro kayanka Ka zabi Gidana ko Nan Gidan ka Dawo ka Zauna Zamanka achan baida wani amfani Tunda Kana da Wajen da zaka Zauna.."Hajiya Mama ta karbe da Fadin"In yana so ya samu sakewa..Yayi Aure..!
Fuska ba Walwala Haddir yace"Toh Abba Dama Abunda yasa na kama Chan Gidan naga yafi kusa da asibiti ne.."Alhaji Tsoho yace"Wannan Ba Hujja bace..Da zai saka ka Zauna kai kadai..Sai Mutane surika Munana maka Zato Tunda ina da Tabbacin ansan kana da Mu anan garin Zamanka achan bai Dace ba kayi yarda muka ce kawai ."Kai ya kada yana Fadin"Shikenan Weekend zan yi parking..Zan dawo nan daman Wannan Tsohon matar naka Tana So tana kaiwa kasuwa..!
Yafada yana Hararan Hajiya Mama Shewa ta saki Tana Fadin"Ja chan Me zan Dakai..? Kaga Sabon Megida nan,Megidana akwai Cefane.."Tafada Tana Dafa Zain Dake gefenta Shima ya Dafata Harda Ma Haddir gwalo Abba yace"Hajiya mama Ayi ma Tsohon mu haka..?
Hajiya Mama tace"Me za"a Fasa..? Shima Tawaye yake neman yayi min da Halimatu Kullum sai tazo Gidan nan kaga Sun Hada kai suna ta kus kus in kuma bata zo Zata kirashi a waya ko Aikomai da wannan kawomai wannan Kaga fa in batazo ba ya Dinga Damuna da Fadin Oho Aminatu yau Halimatu Shuru ko lafiya..? Bari na Kirata..!
Abba na Dariya yace"Au Ramawa kikayi kenan kema kika kwace mata miji kenan..? Hajiya mama Tace"Eh mana Taji In Da Dadi itama.."Alhaji Tsoho yace"Hoho Aminatu...Ina Laifin Halimatu kinsan Bakin Tsoho sai da Gishiri Gishiri kuma Kus kus Din Da kikace munayi labarin Iyayenta nake bata Ina gayamata kyawawan Halayansu da na sani Lokacin da muka Zauna dasu Suna Raye..."
Allah ya Jikan Umaru da Abdullahi da Duka Musulmab da Suka Rigamu gidan Gaskiya.."Gabadayansu suka amsa da Ameen sai kuma Jikinsu yayi sanyi Alhaji ya Cigaba da Fadin"Haske da Rahma yakai musu..Bayin Allah ne masu Zuciyar Zinare Na Sha Gayama Halimatu Ta Debo Wasu Daga Cikin Hallayan Mahaifiyarta Maryama.."Hajiya Mama tace"Ba Shakka...Allah ya Hadamu a Aljannah Dasu.."Gabadayansu suka amsa da Ameen Ameen kafin su Cigaba da Hiransu Jefi Jefi Abba bai Jima ba yayi musu sallama ya Tafi Zain kuma sai da ya Tsaya Suka Sha Furan da Hajiya Mama ta Damama Haddir Duk da yadda ya Dage kan bazai Sha ba Bayan sun gama suka Tafi Kitchen suka gaisa da Baba Tabawa Wata Yar Dattijuwa ne aiki take Gidan Alhaji Tsoho Tun Tana Matashiyarta Har Girma ya kamata an Riga da an zama Daya Dayake Baba Tabawa irin yan gudun Hijiran ne ba wasu Dangi ne Alhaji Tsoho ya Zame mata Tamkar Uba Duka su Zain Agabanta suka Taso Ita tayi Wahala dasu In Aka kawosu Hutu Gidan na Alhaji