Chapter 16 Reading BAYA DA KURA BOOK COMPLETE BY NANA HALEEMA.txt Arewa Novels

BAYA DA KURA BOOK COMPLETE BY NANA HALEEMA.txt

Author :  Nana Haleema Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   16 / 27

45K to 48K   out of 80K words

online.



Magana tayi mata ta zauna jiran amsa shiru bata amsa ba kuma tana ganin ta online sai ta tura mata voice note tana cewa, "Duk abinda ya samu Mama akan tunanin ki Yaya Allah bazai barki  ba nima bazan yafe miki ba wallahi, kwanan Mama bakwai a asibiti amma sau Waya kika je, inda babar su Bily ce da kullum kina can dan ki faranta mata rai. Bakya kwana ma a gida baki san halin da take ciki ba, wallahi ki kiyayi duniya domin tana gab da kai ki ta baro ki" tana gama faWa ta tura mata ta kashe datar tayi lamooo tana tunani.



Mama na jin ta duk abinda take cewa tayi murmushi ta share hawayen idanun ta cikin so da ™aunar ta, babu yadda zata iya haWa matsayim Manal da Mubeena a zuciyar ta, ta ko wanne Sangare ita Win ta daban ce. Abinda yake tayar mata da hankali yanzu a ina Mubeena take kwana?.



Mubeena kuwa duk kiran da ake mata tana gani kawai bata yi niyar Wauka bane, lokacin da Manal take mata message tana kan yin waya da Baby shiyasa ma bata bi ta kanta ba hankalin ya yana ga soyayyar sa da ta gama mamaye mata jikin ta cikin lokaci kaWan. Bata iya tsallake duk abinda tace saboda kar ransa ya Saci kamar yadda shima a nasa Sangaren yake jin ta a jikin sa har ya ™agu ya dawo kawai saboda ya ganta.



Daga can Sangaren yace, "Baby." Ta amsa da cewa, "Na'am Baby."

"Gobe zan dawo me zaki tanadar min?." Tayi murmushi tace, "abinda ka ke sl." Yana kallon ta tana kallon sa kasancewa video call yace, "ni ke kawai nake so."

"Ni ai taka ce Baby."

"Ina so goben ya kasance na musamman, da fatan a Sangaren ki hakan zai kasance ko?." Tayi murmushi tace, "sosai ma kuwa."



Murmushi ya mata tace, "Wai kuwa Baby matan ka nawa? A ina kake da zama?." Yayi ΄ar dariya yace, "sai yau kika tambaya?."

"Sai yau naji ina so na sani."

"Mata na biyu, yarana takwas. Maza uku mata biyar."

"A ina suke zaune?." Yace, "mu bar zancen nan Baby, ni yanzu ki ji dani kawai." Tayi dariya tace, "to me kake so?."

"Ke mana. Da zan zamu abinda nake so gobe ina sauka daga lagos na ganki a gidana a zaune da nayi farin ciki."



"Kar ka damu zanyi abinda ka ke so."

"Da gaske zaki zo?." Ta amsa masa da Uhum ya dinga murna yana farin ciki a haka suka raba dare suna waya kafin ta kashe ta tashi daga falon ta koma Wakin Bily tana zaune tana karatu, ta wuce ta kwanta bata ce mata komai ba itama bata ce mata ba.



Nana Haleemad'ώ>Ψφή<Ψϋί



*BAYA DA ˜URA.*

Fitattubiyar2025



  ©ώNana Haleema.



Wattpad@Nanahaleema

Arewabooks@nanahaleema11



Masu nema daga farko ku shiga wannan link din https://whatsapp.com/channel/0029VaLsFSiGZNCrecIWUc36



_Kina neman inda zaki siyi abinci mai daWi? Kina ™iyar yin girki gashi zaki yi ba™i?, kina neman inda zaki yi order abinci mai daWi wanda zaki fita kunya?. Masu abinci suna suka tara, akwai abinci mai daWi akwai a lallaSa. Kina son ki siyi abincin da zaki Wauka a saudia ki ke? Kuna son ku siyi abincin da in kuna ci zaku dinga murmushi saboda daWi da khamshi?. LEEMARS_DELICIOUS itace kat a wannan Sangare, tazo muku da nau in abinci kala-kala na gargajiya da na ™asar waje. Tana siyar da Mandi rice, chicken biryani, funkaso, alelen gwangwani, bread pocket da sauran su._



_me ku ke jira? Maza ku garzaya shafin ta na instagram domin ku ganewa idanun ku, ku danna wannan link din domin yin magana da ita kai tsaye. Ko ku neme ta a number wayar ta da take ™asan rubutun nan._ call/whatsapp 09030398006 https://www.instagram.com/leemars_delicious?igsh=MWRzZWtnYXM4ZHB2dw%3D%3D&utm_source=qr



Kar ku sake a baku labari, siyan na gari mai da kuWi gida.



*BOOK 1*

*Page 018.*





Da safe Mubeena da wuri ta shirya ta taho zuwa gida, lokacin da ta shiga gidan Mama da Manal suna zaune kamar ko yaushe suna cin abinci a kwano Waya da alama sai lokacin suke karyawa. Yatsine fuska tayi ganin tuwo ma suke ci abinda ta tsana gabaWaya  a duniya, ta ™arasa da sallama Mama na jin maganar ta taji hankalin ta kwanta amma bata nuna ba har ta ™araso ta zauna tcae,



"Mama ina kwana, ya jikin ki?. Naje asibitin lokacin kina kwance kina bacci gashi muna da jarabawa a makaranta shiyasa ban dawo ba." Mama kamar tana kallon ta tace, "ki dinga jin tsoron Allah Nusaiba, ba haka mahaifiyata take ba, a ko yaushe in na tuna sunan ta kika ci ina dana sanin saka miki sunan ta a rayuwata." Mubeena ya zauna tana zunburo baki tace, "Mama nace makaranta naje fa, kuma me nake yi don Allah?."



Mama tace, "babu abinda kike yi Mubeena, komai kike yi daidai ne." Ta kalli Manal da take kallon ta itama ta zabga mata harara Manal ta taSe  baki bata ce komai ba.



Baba ne ya shigo ya shirya da alamun tafiya wajan nema ganin Mubeena sai yace, "A'a Mubeena."

"Na'am Baba, Ina kwana" ta faWa tana gaishe shi ya amsa yana faWin, "ina kika shiga?."

"Baba makaranta ce fa ta Soye ni, kuma ina nan zoo road gidan su Bilkisu ™awata a can nake kwana saboda tare muke karatu." Baba yace, "Allah ya taimaka, zo ina son ganin ki" ya faWa  yana yin cikin gidan ta tashi rai a Sace ta bishi ta zauna yace,





"Mubeena shi wannan rawar kan da kika saka a gaba ba komai zai amfana miki a rayuwa ba face dana sani, mu da kike rainawa kina ganin baki dace ace iyaye ki bane saboda kina da kyau mune gatan ki yanzu da nan gaba. ac1n ran da kike sakawa mahaifiyar ki kema ganin ki shine burgew?kin san da Sacin ranki a ciwon zuciyar babar ki? Kin sani?."



Mubeena tayi shiru batayi magana ba yace, "Ki bi duniya a sannu, shi kuWi da kike gani ba komai bane face takardar, ba kowa Allah yake bawa ikon amfanar ba sai wanda y zaSa. In kina ganin mahaifiyar ki bata dace dake ba saboda tana da lalaurar ido da kuma tana aurena saboda bani da kuWi kuma sannan itama bata da kuWi kin yi kuskure, baki san wacece mahaifiyar ki ba, in zancen kuWi ake kafin a lisaafo wanda kike bi saboda kuWi za'a lissafa ta a jerin su. Koda yake ke ba wannan lissafin kike ba, baza kuma ki gane inda na nufi  a yanzu ba wata™ika sai nan gaba. Abinda nake so dake Mubeena ki nutsu kiyi hankali ki tabbatar da abinda kike aikawa ba burge bace ko kuma darajar ki bane, babu inda wannan hali zai kai sai tashar dana sani."



Mubeena bata ce komai ba tayi shiru ya mi™e yace, "nasiha nake miki matsayin uba a wajan ki, in kin Wauka Mubeena ke zata amfana, in baki W'auka ba shima ke zata cuta. Allah yana gani ina iya bakin ™o™arina wajan na miki tarbiyya mai kyau, na barwa Allah lamarin ki ina kuma faWa masa kullum. Ki sani ha™™in mahaifiyar ki ba zai bar ki ki zauna lafiya ba, ba kuma zai bari ki samu abinda ki ke so ba. In ma yawo ki ka fara ki sani kafin ke anyi irin ki dubu, babu wacce tayi riba a yawon banza, a ™arshe da ciwo suke ™arasa rayuwar su a wula™ance" ya faWa yana fita. Baki ta turo bayan ya fita ta fito tsakar gidan ta zauna tana kallon su kamar basu san tana wajan ba saboda babu wanda ya tanka mata.



"Assalamu alaikum" aka faWa ana shigowa duk suka juya a tare ita da Mubeena. Manal ganin wanda ya shigo sai tayi dariya tace, "Laaa Yaya Harun." Dariya yayi shima ya ™araso yace, "Manal." Mama jin muryar haruna sai tayi murmushi tace, "Mutanen ™asar Riyad ne a tafe kenan." Yayi dariya ya zauna kusa da Mama yace, "mu ne wallahi Mama, ina kwana."

"Lafiya lau Haron, saukar yaushe?."

"Šazu da safe nazo, ashe bBaba bai faWa miki ba."

"Ya sha'afa. Ya hanya?."

"Alhamdulillah Mama, ya ™arfin jikin? Baba yace jiya kika dawo gida daga asibiti."



Mama tace, "Da sau™i Haruna, naji sau™i sosai."

"Allah ya ™ara Lafiya" ta amsa da amin ya kalli Manal yace, "nifa fushi nake dake ko kiran wayar nan ma bakya yi ki nemi." Tayi dariya tace, "wayar tawa ce sai a hankali Yaya, ba wani damuna tayi ba ko datar na saka na shiga na kalli video abinci na kashe shine aikina."

"Daman ke ai babbar mai dafa mana abinci ce." Sukayi dariya a tare ya kalli Mubeena da bata ma san ya shigo ba kamar zai mata magana sai ya share ta ganin ta kawar da kanta gefe.



Ji tayi yana kallon ta a jikin ta sai tace, "Sannu da zuwa" ya amsa bai kalle ta ba ya saka hannu aljihu ya Wauko waya ya mi™awa Manal yace, "ga waya na tawo miki da ita a cigaba da kallon abinci, shiyasa na bayar a gaban Mama nasan zaki ce Mama baza ta bari ba" ya faWa yana kwaikwayon muryar ta sai sukayi dariya har Maman.



Mama tace, "Haruna harda hidima haka? Waccan wayar ma kai ne ka bata fa."

"Babu komai Mama, Manal ai ™anwata ce da nake ji da ita." Manal ta karSi wayar tana duba ta cikin murna tana kallon jikin wayar, ba™a ce ta gabaWayan baya an saka Samsung S10.



"Na gode sosai Yaya,Allah ya saka da alkhairi ya kai mu bikin ka mu sha biki." Yayi dariya yace, "Amin Manalin Mama, sannan duk sanda datar ki ya ™are ki faWa min zan saka miki ki cigaba da kallon abinci, dan so nake ki iya sosai nan gaba ki zama shararriya a duniya."

"To Allah ya biye bakin ka Yaya."

"Amin ™anwa, zan saka a duba makarantar koyar da girki ma ki fara shiga tun yanzu. Akwai wacce na biiya miki online ma wajan wata Leemars_Delicious, ta iya girki ina ganin ta a Ig shiyasa da naga zatayi online classes sai na tura mata kuWin, zata saka ki a group ki koya da kyau ™anwata."



Mama tace, "A'a Haroun kar hidimar tayi yawa kuma."

"Haba Mama, Manal da ™anwata ce dan nayi mata ai ba komai bane." Mama tace, "haka ne, Allah ya saka da alkhairi." Ya amsa da amin.



Wayar Mubeena aka kira ta Wauka wayar ta duba ganin mai kiran sai bata Wauka ba, hanyar fecewa kawai take so ta samu amma babu dama.

Haroun ne ya kalli wayar hannun ta amma sai bai yi magana ba  fa tashi ta shiga falo shi kuma yau sallama ya fita.



Haka ta kai bayan azahar a gidan gabaWaya a takura take gashi tana ta kiran Baby bai Wauka ba duk ya damu. Sai da akayi sallar la'asar sannan taga message Win sa an saka, _Sorry baby, kina ta jira na ko? Na dawo ina gida a kwance bana jin daWi sosai Baby. Kizo ki ganni._ hankalin ta ya tashi sosai ta kira shi a lokacin ya Wauka tace, "Baby me yake damun ka?." Murya can ™asa yace, "ZazzaSi ne Baby, gashi ina gida ni kaWai ko abinci bansamu naci ba."

"To baby ka saka ayi maka take away mana."

"Babu kowa Baby, ban san ya zanyi ba ji nake kamar zan mutu."



Cikin tashin hankali tace, "to yanzu ya za'a yi?."

"Ki zo ki ganni Baby, ganin ki kawai zai saka naji daWii." Shiru tayi bata amsa ba yace, "amma in baza ki iya zuwa ba ki damu babu komai." Mubeena tace, "A'a zan zo, sai dai bazan jima sosai ba kaga yamma tayi."

"Okay Baby, gashi babu kowa balle ma turo a Wauke ki. Bara na kira driver na duk inda yake yazo ya Wauko min ke." Ta amsa da to ta kashe wayar tana tunanin ta wacce hanya zata bar gidan su.





     Mubeena da ta fito daga Waki ta ga Mama ita kaWai zaune da alama Manal  gidan su Surayya sai tace, "Mama an yi mana  kiran gaggawa daga makaranta zanje na dawo." Mama tayi tsaki tace, "tambaya ta kike daman in zaki fita Mubeena? Wacece ni da zaki nemi izinina?."



Mubeena tace, "Mama kiyi ha™uri in dan na kwana a gidan su ™awata ne kike fushi dani." Mama bata ce komai ba tayi mata banza Mubeena tasan bazata cs komai ba hakan ya saka tace, "Mama zanje na dawo yanzu" tana faWa ta fice bata ma jira mai Maman zata ce dan driver ya fara yimata waya.



Tana fita ta Wauki wayar ta sakaa kunne tana yin titi da sauri. A lokacin Manal da Haruon suna tsaye suna kallon ta yace, "Manal waye ya bawa Mubeena wannan wayar ta hanun ta?." Manal tace, "Wallahi ban ma kula da wayar hannun ta ba." Haroun ya girgiza kai yace, "babar waya ce sosai fa, a hannun yaran masu kuWi ma bata da yawa saboda bata jima da fitowa ba, kuWin ta yayi miliyan uku da wani abun wallahi."



Gaban Manal ya faWi tace, "Yaya miliyan fa? A ina Yaya ta samo ta? Ko dai sata tayi ko kuma ta ™awar ta Bily ce?." Ya girgiza kai yace, "bama ce ba, amma zan faWawa Baba maganar dan wannan ba abinda za'a bari bane, shi ya tambaye ta a ina ta samu wayar." Manal cikin tsoro tace, "ni na fara jin tsoro."

"Kar ki damu, kar ki sanar da Mama wannan ki bari na faWawa Baba." Jiki a sanyaye ta amsa yace, "jeki gida na tsayar dake" ta amsa da to ta juya ta tafi tana tunanin waye ya bawa Mubeena wayar fin naira miliyan 3?.



Bebi kuwa ranar bai samu ya fita da wuri ba dan daren jiya sai dare ya dawo gida saboda theater da suka yi a babban asibitin Murtala. Bayan ya tashi daga Murtala asibitin su ya wuce, yana shiga kawai sai Manal ta faWo masa a zuciya musamman inda take tsaye tana yi masa murmushi a lokacin da ransa yake Sace bai tsaya ya saurare ta ba ya wuce.



Numfashi ya sauke yana inda yake tsaye yace, "gabaWaya ta™i barin tunanina."

"Wacece ta™i barin tunanin maka?" Hamza ya faWa yana kallon sa ya juya ya kalle shi yace, "har ka fito kenan?."

"Mun fito, sai yanzu ka shigo?."

"Uhum, na jima a can ne kuma kasan jiya muna team work shiyasa ban samu ma na fita da wuri ba."



"Wacce ta™i barin tunanin naka naji kana maganar? Kodai an samu madadin Rumana ne?." Bebi ya girgiza kai yace, "bana ce ba, haka kawai na kasa mantawa da ita musamman....." sai kuma yayi shiru yace, "forget it kawai. Ina Huzaifa?."



Huzaifa da yake tunkaro wajan yace, "gani, da labari ne?." Hamza yace, "akwai labari, da alama wata ta kama zuciyar Bebi fa." Huzaifa yace, "haba don Allah, da gaske?."

"Wallahi da gaske, shi kaWai naji yana zancen ya kasa mantawa da ita kuma shima ya faWa min."



Huzaifa yayi dariya yace, "Wacece wannan Bebi?." Kallon Huzaifa yayi kafin yayi magana ya riga shi yace, "kamata yayi kayi hanzarin ko wacece a yi a wuce wajan saboda damuwar Rumana." Bebi yace, "nifa bance son ta nake ba, kawai dai na kasa mantawa da ita ne, nasan kuma saboda abinda nayi mata ne bayan wannan babu komai" ya faWa yana barin wajan ya ™arasa inda office Win sa yake ya shiga duk suka biyo bayan sa.



Bebi ya kalle su yace, "ina da wanda zasu zo nan fa meye na biyo ni?."

"Sanar damu zaka yi wacce wannan ta kamo zuciyar ka haka?." Bebi yace, "ku bari na tabbatar sai na faWa muku amma yanzu ban tabbatar ba." BuWe ™ofar akayi aka shigo da takardu Bebi yace, "kun gani ko? Patients Wina sun zo sai anjima" ya faWa yana karSa ya zauna suka fita ya fara duba mutane.



Sai bayan ya kammala sannan yayi shiru yana tunani zuciyar sa na bugawa a hankali da ya rufe ido fuskar Manal yake gani musamman ranar da ta saka black hijab tana dariya. Numfashi ya fesar daga bakin sa yace, "wai me hakan yake nufi ne? Daga Wan sabawa da ganin ta sai na fara tunanin ta? Meyasa na kasa mantawa ne?."



Glasses Win idon sa ya cire ya ajjiye amma bai daina jin wannan bugun zuciyar ba yayi shiru ya zubawa waje Waya ido yana kallon inda ta zauna ya saka mata magani a ™afar ta.

"Oh my god!" Ya furta a hankali ya rasa ma tunanin da zaiyi yaji daWi.



A cikin asibitin yayi sallar magriba ya tashi ya buWe window yana kallon masu shigowa da fita iska na shigowa kaWan da khamshin ganyayyaki. "To wai har magana sau nawa muka yi ne da zan saba da ita haka? Adnan me kake yi ne?" Ya faWa yana sake kulle ido ya buWe sai ya kulle window Win ya Wauki key na mota ya fito ya shiga ya tafi gida.





**** Mubeena tayi mugun tsorata tana zaune tana kuka da shima yana kusa da ita yace, "Haba Baby, meye na wannan damuwar haka? Kawai hug ne da kiss ba wani abun kika yi ba, kuma gashi kin taimaka min na samu Lafiya amma meye na shiga damuwa haka?."



Mubeena tsoron ta ya riga ya gama bayyana ™'arara tace, "Ba abinda kace zanyi ba kenan, ni dai gaskiya banji daWin hakan ba, bamu yi hakan da kai ba.

"Nima ban san hakan zata faru ba ai Baby, shau™in son ki ne ya warkar min da rashin Lafiya, da kuma murnar maganin ki kusa dani shine har hakan ya faru. Amma babu komai kar ki damu, baza'a saka ba wannan Win ma kuskure ne."



Mubeena jikin ta gabaWaya ya gama yin sanyi ta kalli dan™walin ta da yake gefe da mayafin da ta sako yace, "muje kiyi wanka ko?." Ta girgiza kai tace, "A'a sai naje gida."

"Kiyi a nan, in kika bari sai a gida za'a ce wankan me kika yi kina dawowa daga unguwa, nan yafi kwanciyar hankali tashi muje" ya faWa yana ri™o hannun ta suka ™arasa inda banWaki yake yace, "ki shiga kiyi wanka da kin fito sai a kai ki."



Kai ta daga ta shiga ciki yayi murmushi bayan ta shiga

16 / 27