Chapter 23 Reading BAYA DA KURA BOOK COMPLETE BY NANA HALEEMA.txt Arewa Novels

BAYA DA KURA BOOK COMPLETE BY NANA HALEEMA.txt

Author :  Nana Haleema Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   23 / 27

66K to 69K   out of 80K words

ya bari an office amma yaso yaje yaji kwakwaf dan ya ™ure Adnan.



Bebi bai sake ganin Manal ba itama bata kuma ganin sa bar bayan la'asar, a lokacin Maman ta farka kuma ance shi zata sanarwa, sai a sannan ta ™wan™wansa office Win ya amsa daga ciki ta shiga da sallama ya amsa bayan ya Waure fuska sosai tace, "Dr Mamana ta farka."

Ba tare da ya kalle ta ba yace, "reception ake zuwa a faWa."



jin abinda yace ta kalle shi sai tace, "Okay, thanks." Ta faWa zata fita sai taji yace, "wait." Ta kalle shi yace, "ina zuwa." Bata sake magana ba ta juya tana mamakin hali irin nasa, gabaWaya ya canja kamar ba shi ne suke hira a waya da zahiri ba. Takun sa taji a bayan ta kafin ta shiga Wakin ma ya riga ta ya saamu Mama ta farka tana kwance ya ™arasa yace, "Sannu Mama." Mama tace, "Adnan ne?."

"Shine Mama, ya jikin?."

"A asibiti muke kenan. Da sau™i, ciwon yayi sau™i sai kaWan da nake ji."



Adnan yace, "Zaki daina shima in sha Allah, damuwa ce ta miki yawa shine ya haifar da wannan ciwon. Sai Ana ha™uri ana kawar dakai a kan dukkan lamura, ina ance komai sai an damu a kansa zuciyata baza ta zauna lafiya ba. Kuma shi wannan ciwo ko ya Sacin rai yake baya iya Suya sai ya bayyana."

Mama ta girgiza kai tace, "Haka ne Adnan, na gode. Ina Manali?."

"Gani Mama" ta faWa murya na rawa. Mama tace, "Manal meye na kukan gashi ai na tashi ko? Kina ina?" Ta faWa tana mi™a mata hannu Manal ta ™araso ta ri™e hannun Maman tana kuka.



Mama tace, "meye na kukan kuma Manal? Ai naji sau™i yanzu ciwon kaWan nake ji."

"Mama Wazu ko magana bakya yi, hankalina ya tashi na rasa ya zanyi."

"To ki yi ha™uri na samu sau™i, ki gode Allah da ya haWa mu da su Adnan." Murmushi yake yana kallon su suna burge shi sosai domin akwai soyayya da sha™uwa a tsakanin su sai ya fita dan yaga sun manta ma dashi.



Bai jima da komawa office ba ta sake dawowa da sallama ya amsa a lokacin yana zaune da laptop yana dannawa ya kalle ta bayan ta shigo tace, "sorry na kuma dawowa, Mama tace zamu iya tafiya gida?." Kallon ta yake yi kafin yace, "zauna." Bata musu ta zauna ya tashi ya Wauki ruwa da kansa ya bata yace, "sha." Ta karSa tasha kaWan ta ajjiye yace, "ki dawo nutsuwar ki."



Manal tace, "a nutse nake."

"Mama ta samu lafiya kar ki damu, ki dinga ™o™arin ganin bata shiga damuwa ba ko tunani, duk abinda kika san zai saka ta a damuwa ko tunani kiyi ™o™arin ki ga bai faru ba kina ji?." Ta Waga kai alamun eh yace, "anytime, anywhere wani abun ya faru just call me, in banyi picking ba ki ta kira na har sai kin tabbatar na Wauka, kin gane?." Ta Waga kai alamun eh.



"Mama zata zauna a nan har sai gobe da safe, saboda ta sake samu sau™i sosai sai ku koma." Kai ta Waga kai ta yun™ura zata tashi yace, "ki koma ki zauna."

"Zan faWawa Mama sai gobe ne."

"0n kin koma tayi bacci." Ta kalle shi tace, "ya akayi ka sani?." Ya kalli agogon hannun sa yace, "Lokacin tayi baccin ne yayi." Ganin bata amince ba sai yace, "kije ki duba, in kin tabbatar tayi baccin ki dawo."



Fita tayi taga Maman tayi bacci kuwa sai bata koma ba saboda kiran sallar magriba da ake yi, sallah tayi tana zaune kusa da Maman Baba ya dawo ya shigo Wakin suka cigaba da zama kafin ya fita lokacin i'sha tayi sallah itama Bab ya dawo yace, "Manal baki ci abinci ba, gashi Dr Adnan ya faWa min zata kwana a nan saboda ta sake warwarewa gobe sai mu koma gida."

Manal tace, "Bana jin yunwa ma Baba."

"Zaki ki yunwa Manal, zan saka nemo miki abinda zaki ci."

"Allah bana jin yunwa."

"Ai kwana zaki ko kin manta ne?."



Ta girgiza kai tace, "Ban manta ba, basai naci komai ba." Baba yace, "To shikenan." Suna nan zaune har tara na dare sannan Baba ya tafi ya barta bayan ya tabbatar da Haroun ya tawo.



Ita kuma ta fito ta zauna a kofar Wakin tayi tagumi kamar wata marainiya. Huzaifa da yake niyar tafiya gida ya gano ta ya ™araso yace, "Manal ba dai jikin Maman bane?." Tayi murmushi tace, "A'a Dr, bacci ma take sosai."

"Haka ake so, zan wuce ni gida amma Bebi yana nan nasan zai kula da komai."

"Allah ya saka da alkhairi."



"Kar ki damu an zama Waya ai." So yake ya tambaye ta maganar Bebi amma sai ya kasa sai daga baya yace, "kin san waye Bebi Win?." Ta Waga kai alamun eh yace, "Yauwa, duk abinda yake damun ki ki sanar dashi."



Ta amsa da to yayj mata sallama ya tafi badan haka yaso ba yaso yaji meye ala™ar su da shi. Tana nan zaune sai ga message a wayar ta ya shigo ta buWe taga Adnan ne yace, _ki tashi daga nan ki shiga Wakin da kika zauna Wazu, sai zuwa sha Waya Mama zata farka._ kallon wajan tayi taga baya nan, abin bai bata mamaki ba ta san bazai wuce ta camera ya ganta ba, tashi Win tayi ta shiga dan ta gaji da zaman.



Tana shiga ta zauna akan kujera babba ta jingina, buWe ™ofar akayi aka shigo sai ga wata nurse da abinci tace, "Dr Adnan yace a kawo miki." Murmushi tayi ta karSa tayi godiya ita kuma ta koma. BuWe pack din abincin tayi shinkafa ce basmati fara tass ga miya a wani pack Win sannan ga salad mai yawan gaske yaji uban cucumber.

Fara ci tayi a hankali taci rabi ta tashi ta sha ruwa a water dispenser ta dawo ta zauna tana murmushi a zuciyar ta.



Knocking ™ofar aka yi ta amsa ya buWe ya shigo ta kalle shi ya kalli abincin yace, "baki ci ba?."

"Naci, ya ishe ni, na gode."

"Šazu kafin nazo waye ya kawo ku nan?."

"Dr Huzaifa ne, shi na kira na sanar dashi, na ruWe na manta ma ba faWa maka."



Ya girgiza kai yana kallon ta yace, "baki taSa bani labarin kina da number Huzaifa ba, bayan nace miki bana so kiyi min hiding komai." Manal da mamaki tace, "ban Wauka ya shiga ciki abinda kake nufi bane, beside na jima ina da number shi tun muna zuwa babban asibiti, ina kiran shi a waya in yana nan muje in baya nan sai mu fasa zuwa." Ya girgiza kai yace, "Baki bani labarin ala™ar ku tayi girma haka ba ai."



Manal tace, "yana da kirki sosai har yaso ya fika, yana Wauka na kamar ™anwar sa nima ina Waukar shi Yayana. Kai tsaye zan iya kiran shi kafin na kira ka." Ran Bebi ya sosu sosai bai magana ba ta kuma cewa, "Saboda wani lokacin kai sai aga kamar baka son ma ayi maka magana." Ya sauke numfashi yana kallon ta ta ™asan ido cikin ™unar rai yace, "shi kuma wanda ma gan ku da safe tare fa? Sau biyu ina ganin ki dashi akan titi kuna hira, shi kuma waye Win ki? Shi ma yafi ni Win ko?."



Nana Haleema>ĜBŬd'ŝ



*BAYA DA ˜URA.*

Fitattubiyar2025



     İŝNana Haleema.



Wattpad@Nanahaleema

Arewabooks@nanahaleema11



_Kina neman inda zaki siyi abinci mai daWi? Kina ™iyar yin girki gashi zaki yi ba™i?, kina neman inda zaki yi order abinci mai daWi wanda zaki fita kunya?. Masu abinci suna suka tara, akwai abinci mai daWi akwai a lallaSa. Kina son ki siyi abincin da zaki Wauka a saudia ki ke? Kuna son ku siyi abincin da in kuna ci zaku dinga murmushi saboda daWi da khamshi?. LEEMARS_DELICIOUS itace kat a wannan Sangare, tazo muku da nau in abinci kala-kala na gargajiya da na ™asar waje. Tana siyar da Mandi rice, chicken biryani, funkaso, alelen gwangwani, bread pocket da sauran su._



_me ku ke jira? Maza ku garzaya shafin ta na instagram domin ku ganewa idanun ku, ku danna wannan link din domin yin magana da ita kai tsaye. Ko ku neme ta a number wayar ta da take ™asan rubutun nan._ call/whatsapp 09030398006 https://www.instagram.com/leemars_delicious?igsh=MWRzZWtnYXM4ZHB2dw%3D%3D&utm_source=qr



Kar ku sake a baku labari, siyan na gari mai da kuWi gida.





*BOOK 1*

*Page 26.*





Manal ta kalle shi cikin mamakin abinda yace tace, "ka gan mu da safe? A ina to?." Ya jingina da kujera ya Wora ™afa kan Waya yace, "ki bani amsa." Manal ta yatsine fuska tace, "Yaya Haroun ne, Yayana ne, kuma ka san shi."

"Baki bani labarin kina da Yaya ba."  Kallon sa tayi tace, "komai sai na faWa maka?, kuma ranar da kazo gidan mu ya kira ni a waya ai na faWa maka ko?."



Da ido ya bata amsa ya kulle shi ya buWe alamun eh ta kawar da kai tace, "kai ba komai ka faWa min ba ai" ta faWa tana kallon agogo kafin tace, "Lokacin tashin Mama yayi kamar yadda kace, zan koma wajan ta." Baice mata komai ba ya ta fita yayi murmushi bayan ta fita, Allah kaWai yasan yadda yake matu™ar farin ciki in yana zaune gashi gata. Sau uku kawai suka zauna tare amma bazai manta da wannan ranakun ba gaskiya.



Kamar almara tana shiga taga Mama ta farka dan tana zaune ma ta ™arasa tace, "Mama kin tashi?."

"Eh Manal, ina kika je?."

"Ina zaune a wani Waki a can ma naci abinci."

"To zo ki taimaka min nayi sallah, dare yayi ko?."

"Eh Mama, har ta wuce tayi." Mama tace, "Subahanallahi." Taimaka mata tayi ta sauka tayi alwala ta tayar da sallah.



Sai bayan ta idar Manal na zaune Mama tace, "Manal ina ganin hasken Wakin nan da kaWan-kaWan." Manal tace, "da gaske Mama? Kina iya ganin Wakin nan?" Ta tambaya a ruWe da farin ciki.  Mama tayi murmushi tace, "ina iya ganin hasken Wakin amma ba sosai ba."

"Bara naje na faWawa Dr ko akwai abinda za'a yi." Mama tace, "yi zaman ki ki huta, Mubeena bata zo ba ko?."



Manal tace, "tare muka zo sai Baba yace ta koma gida." Mama bata ce komai ba tayi shiru Manal tace, "Mama abinci fa?."

"Bar shi Manal naci da safe."

"Safe kuma Mama? Bafa kici abinci ba kwata-kwata."

"Yanzu in nace zanci a ina zaki samo? Sai dai ki faWawa Adnan a kawo min kuma ni bana so. Yaron nan bai fa aure ki ba har yanzu, kin ce baki gama tunani akan zaki iya auren sa ba ko baza ki iya ba, tun yanzu muna Wora masa wahalar rashin lafiyata?, ko ya aure ki kula dani ba a kansa yake ba balle bai aure ki ba. Da na san ma shi zaki kira da ban faWa miki bani da lafiya ba. Matsayin sirikina yake a yanzu, bai aure ki ba baza'a dinga Wora masa wahala ba. Ko ya aure ki ha™™in kula dani ba a kansa yake ba."



"Assalamu alaikum." Aka faWa daga bakin ™ofa mai share-share na asibitin ya shigo da leda a hannun sa yace, "Barka da dare, ya mai jikin?." Manal ta amsa ya mi™a mata yace, "Gashi in ji Dr Adnan." Manal ta karSa tayi godiya ya fita ta kalli Mama tana buWe

abincin tace, "gashi ya aiko dashi."



Mama ta girgiza kai tace, "Bana jin daWin haka Manal, nauyin sa nake ji wallahi."

"To Mama bani nace masa ya kawo ba ai."

"To sai ki bani naci."



Manal tayi murmushi ta koma kusa da ita ta buWe mata tana ci. Sai bayan ta gama cin abincin Adnan ya shigo da sallama ya kalli Mama yace, "Mama ya jikin?."

"Da sau™i sosai Adnan, har ciwon ma na daina ji." Manal tace, "Mama tace tana ganin hasken Wakin nan." Mama ta taSa ta tace, "Manal!." Manal tace, "Mama bazan iya shiru ba, kiyi ha™uri."

"Daman ke ai bakya iya shiru." Manal tayi murmushi Bebi yace, "Ana samun cigaba sosai, zan aiko da magani yanzu ki saka mata a idon ta, sannan akwai glasses da zan baki tana amfani dashi."



Manal tayi murmushi tace, "To" sai ta kalli Mama tace, "Mama kin ji ko? Kar kice na takura miki da magani wani sabo za'a bayar." Mama tayi murmushi ita nauyin ma Adnan Win take ji, Bebi ya fita ba jimawa aka aiko da maganin ta sakawa Maman suna ta hira sama-sama.



Adnan ya gama komai amma bazai iya tafiya ba haka ya kwana a asibitin, har bakwai na safe yana asibitin a lokacin ake medication nurses suna bi Waki-Waki suna bawa a marasa lafiya magani.



A lokacin Huzaifa yazo da mamaki yake kallon motar Bebi ganin inda ya barta jiya, ya shiga ciki yaga dai yana nan kuma gashi da kayan jiya da alana kwana yayi, ya bishi da kallo yace, "Daman kwana kayi?."  Idanun sa lumshewa suke saboda bacci Adnan yace, "Uhum! Yanzu zan tafi."



"Wai saboda Manal Win ka kwana ka yini kana aiki?." Kallon sa yayi bai ce komai ba Huzaifa yace, "ai na gama fahimtar itace wacce ka ke so Win, daga yi maka wasa jiya ka canja."

"To ka fahimta kuma kake tambaya ta? Kasan dai babu inda zan iya zuwa ko?." Huzaifa yayi dariya yace, "lallai soyayya tana wahalar da kai." Baice komai ba ya fita ya barshi ya shiga inda su Manal Win suke a lokacin ma Baba yazo suka gaisa ya bawa Baba glasses Win yace, "Wannan zata dinga amfani dashi, zai taimaka mata wajan gani in sha Allah."



Baba yace, "mun gode sosai Adnan, Allah yayi albarka." Yayi murmushi kaWan ya kalli Manal a lokacin ta kalle shi sai tayi masa murmushi ya Wauke kansa yace, "zan wuce gida yanzu, akwai wanda zai kai ku gida in kun gama shiryawa zai zo ku tafi." Mama tace, "ai mun gama ma mu tafi kawai." Adnan ya girgiza kai ya fita. Jim kaWan sai gashi tare da wani suka fita gabaWaya suka shiga mota ya tafi kai su shima ya hau mota ya tafi gida dan bacci yake ji matu™a.



Koda ya koma gida ko wajan Mama bai iya zuwa ba kai tsaye Waki ya wuce ya cire kayan jikin sa ya kwanta nan da nan bacci ya Wauke shi. Sha biyu na rana wayar sa ta tashe shi ya kalla yaga daga asibiti ne, kamar bazai Wauka ba sai kuma ya Wauke abinda akace masa ya saka shi sauke wayar ya mi™e da™yar ya shiga wanka.



Da sauri da sauri yake shiryawa ya gama ya fita ya gaisa da Mamy ya shiga wajan Mama Mimi tace bata nan ya hau mota ya koma asibitin, kansa har ciwo yake saboda bai samu bacci ba.



      Mama tayi wanka taji daWin jikin ta sosai suna zaune da Manal Maman su Surayya ta fita a lokacin Mubeena tazo ta zauna tace, "Mama ya jikin?." Mama tace, "da sau™i."

"Allah ya ™ara lafiya." Ta amsa da amin kafin Mama ta kalli Manal tace, "Baki faWa min ya kike ji a zuciyar ki akan maganar Adnan ba, har yanzu baki yanke hukunci ba?." Manal tayi shiru jin shirun Mama tace, "Ni dai ina miki sha'awar auren sa, duk ke zaki yanke abinda kike ganin daidai dake ne, amma ni kam ina so ki aure shi. Duk da ban san ya kammanin sa suke ba, amma yanayin maganar sa zai baka tabbacin nustuwar sa a zahirance."



Manal tayi murmushi a zuciyar ta tana ayyana daman ai shi zan aura in sha Allah, a zahiri sai tace, "Na yanke hukuncin ai Mama." Mama tace, "faWa min to mana."



Manal tayi dariya tana Soye fuska tace, "To Mama ki gane abinda nake nufi mana." Mama tayi dariya dan ta fahimta tace, "to na gane, Allah yasa shine mijin ki, Allah ya sa ya zamar miki na gari Manal. Burina daman ki samu mijin da zai kula min dake kuma na tabbatar kin samu." Tayi murmushi tana jin daWi a zuciyar ta.



Manal tace, "Mama bara naje wajan Surayya kin ji Mama tace bata da lafiya." Mama tace, "to yi sauri, duk da nasan zaki je ki bata labarin Adnan ne." Tayi dariya ta saka mayafi da takalmi ta fita. Gidan su Surayya Win ta shiga ta samu Mama zata aike ta farkon layi kawai suka fito tare suka jera suna hira.



A hanyar su ta dawowa da yake rana ce babu mutane sosai suna ta hira Manal taji an kira sunan ta daga baya, ta juya ta kalli wanda ya kira ta dan bata san shi ba hakan ya saka ta mamakin a ina ya santa. Ya ™araso yace, "Barkan ki, nasan baki sanni ba ko?." Bata yi magana ba yace, "Abokin Adnan ne ni, sunana Mujahid."



"To sai akayi me?" Ta faWa tana kallon sa. Yayi murmushi yana kallon ta yana kuma yaba kyaun ta yace, "in kina tantama zan nuna miki shaida" ya faWa yana Wauko wayar sa ya nuna mata hoton su ta kalli screen Win wayar yace, "abokin sa ne ni sosai, in kika tambaye shi zai faWa miki.."



Manal ta Waga ™afa zata tafi yace, "Nazo na sanar dake wata gaskiya akan Adnan. Manal Tsakani da Allah ba wai yana son ki bane, Adnan ´ar masu kuWi yake burin aure daidai shi, yana amafani dake ne saboda kina da kyau daga zarar ya samu abinda yake so shikenan zai mama gaban sa. Zan iya cewa kece mace ta goma da Adnan zai yaudara domin wannan halin sane, kar kiyi mamaki ko tunani akan wani abu kiyi tunani akan rayuwar ki."



Ya sake cewa, "na zaSi na sanar dake ne saboda naga ke marainiya ce mai kula da mahaifiyar ta, kiyi baya da Adnan kar ki amince da duk wani daWin bakin sa in ba haka ba nan gaba kaWan zaki dana sani" yana gama faWar hakan ya shiga mota ya tafi ya bar Manal tana kallon motar.



Kallon Surayya tayi Surayya itama ita take kallo tace, "kar wannan yayi tasiri a zuciyar ji, irin mutanen nan ne masu so lallai sai sun raba mutum da wanda yake so. Ni ban Wauka ana korarwa maza wacce suke so ba, na zata mata ake yiwa suma kuma daga na jikin ka yake faruwa. Don Allah ki share kawai mu wuce, da ganin wannan bana kirki bane, in haka

23 / 27