Chapter 20 Reading BAYA DA KURA BOOK COMPLETE BY NANA HALEEMA.txt Arewa Novels

BAYA DA KURA BOOK COMPLETE BY NANA HALEEMA.txt

Author :  Nana Haleema Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   20 / 27

57K to 60K   out of 80K words

tace, "ashe zaka kwana baka ci ba wallahi." Ya taSe baki Mama tayi dariya tace,

"Kema dai , ai da sai kice ya jira ki zaki dafa masa, in kana son girki na kira Rumana nace ta kawo maka."



Ya girgiza kai yace, "A'a Mummy ™yale ta, zan san abinda zan ci" ya faWa yana tashi ya fita. Mama tayi dariya bayan ya fita tace, "duk zilliyar ka sai ka auri Rumana Adnan." Farida bata ce komai ba dan itama ba so take yi ba.



Sai bayan sallar magriba sannan yayi wanka yayi kyau cikin manyan kaya kamar jiya, yana ta ™hamshi mai sanyi dan shi baya ™hamshi mai Waukar hankali, baya son turare mai ™arfi kowa ya san da wannan indai kuna tare. Falon ya shiga ya tarar da Mama da Farida dasu Mimi duk sun na nan ganin sa sai suka tsaya kallon sa dan ya yi musu kyau sosai.



Farida tace, "Sai ina?." Mimi ™asa-™asa tace, "Kamar dai mai zuwa zance" ta faWa tana kulle bakin ta tana dariya.



Mama ta kalle shi tace, "ma sha Allah Bebin Mummy, kayi kyau sosai, ina zaka je haka?." Yayi murmushi Yace, "zanje wani waje mai mahimmaci Mummy, kiyi min fatan samun nasara" ya faWa yana ™arasowa inda take ya cire hular kansa ya tsiguna a gaban ta Wora hannun ta a kana tace, "Allah ya bada nasara, ko ina kaje kai ne mai nasara ai Adnan."



Ya mayar da hular ya tashi ya kalli Farida da suke gulmar sa ita da su Kausar yace, "me kuke cewa?."

"Cewa nayi yanzu wata™ila dan wata kayi wannan kwaliyyar ko?, Ko da yake Kausar tace ko wacece bata san wanda zata Wauko bane shiyasa".



Yayi ΄ar ™aramar dariya yana kallon su yace, "munafukai." Ganin har dar1ya yayi sai suka suka yi  dariya suka samu ™arfin guiwa Mimi tace, "wallahi kayi kyau Yaya, kuma yau naji kana khamshi kuma naga baka son turaren."



"Na gode. ™aryata ni ki keso kiyi kice daman dai ina sakawa ko?." Ta girgiza kai tace, "A'a, kawai dai nayi mamaki ne da na ji ™hamshin yanzu, ban taSa jin khamshin mai yawa haka a jikin ka ba, nasan ana ji amma sai anzo inda ka ke sosai."



"Ke dai munafuka ce, to dan kin ji turare a jikina sai ki cigaba da sakawa kizo inda nake" sai ya faWa cikin wasa suka yi dariya. Mama dai kallon sa take tace, "wannan kwaliyyar kamata yayi ace ta Rumana ce, ina zaka je haka ne?."

"Zan sanar dake Mummy sai na dawo" yana faWa ya fice suka cigaba da gulmar sa suna dariya.





Nana Haleema>Ψφή<Ψϋί>ΨBέ



*BAYA DA ˜URA.*

Fitattubiyar2025



  ©ώNana Haleema.



Wattpad@Nanahaleema

Arewabooks@nanahaleema11



Masu nema daga farko ku shiga wannan link din zaku samu. https://whatsapp.com/channel/0029VaLsFSiGZNCrecIWUc36





_Kina neman inda zaki siyi abinci mai daWi? Kina ™iyar yin girki gashi zaki yi ba™i?, kina neman inda zaki yi order abinci mai daWi wanda zaki fita kunya?. Masu abinci suna suka tara, akwai abinci mai daWi akwai a lallaSa. Kina son ki siyi abincin da zaki Wauka a saudia ki ke? Kuna son ku siyi abincin da in kuna ci zaku dinga murmushi saboda daWi da khamshi?. LEEMARS_DELICIOUS itace kat a wannan Sangare, tazo muku da nau in abinci kala-kala na gargajiya da na ™asar waje. Tana siyar da Mandi rice, chicken biryani, funkaso, alelen gwangwani, bread pocket da sauran su._



_me ku ke jira? Maza ku garzaya shafin ta na instagram domin ku ganewa idanun ku, ku danna wannan link din domin yin magana da ita kai tsaye. Ko ku neme ta a number wayar ta da take ™asan rubutun nan._ call/whatsapp 09030398006 https://www.instagram.com/leemars_delicious?igsh=MWRzZWtnYXM4ZHB2dw%3D%3D&utm_source=qr



Kar ku sake a baku labari, siyan na gari mai da kuWi gida.



*BOOK 1*

*Page 022*



Bebi sai da yayi sallar i'sha sannan ya ™arasa ™ofar gidan su Manal, Baba ya gani ya fito daga masallacin da yake farkon layin yana shigowa a ™asa yana jan charbi, ganin sa sai ya fito daga motar Baba da ya hango shi sai yayi murmushi ya ™araso yace, "Adnan ka ™araso?."



"E Baba, barka da dare" ya faWa yana du™awa ya amsa yana cewa, "barka dai likita, ya aikin naku?."

"Alhamdulillah."

"To ma sha Allah. Muje ciki" Baba yayi gaba yana bin sa a baya.



Sai da suka shiga soron gidan su Manal Win sannan yace, "anyi sa'a ma yau ma da wuta, kasan da yake ni ban amince da wani taWi a soro ko a mota ba gaskiya, nafi gane a shigo har cikin gida in ta kama a tsakar gida ma a zauna hakan yafi min kwanciyar hankali." Bebi ya girgiza kai cikin jin daWi da gamsuwa yace, "haka ne Baba." Tare suka shiga gidan babu kowa a tsakar gidan a share tiles Win yayi tass sai ganyen bishiya da ya faWo ™asa, gidan shiru kamar babu kowa.



˜aramin falon da suka shiga jiya nan suka sake shiga an gyara shi sai khamshi yake kaWan kaWn Baba yace, "ka zauna a nan zan turo maka ita yanzu nan." Bebi yayi godiya ya zauna Baba ya fita dan ya kiran Manal.



Yana zaune yana danna wayar sa yaji sallamar ta ya amsa yana Wago kai ya ganta cikin ba™in hijjabin da ya ganta a asibiti, shine lokacin da ya kasa mantawa ko yaushe tunawa fuskar ta yake a wannan lokacin. Shaf ya manta kallon ta yake yi, yaso yayi controlling emotion Win sa a kanta amma ya kasa ashe har ta ™araso ta zauna daga gefe a kan carpet Win da yake falon sai ji yayi tace, "ina yini."



A lokacin ya dawo hankalin sa ya dake kamar bashi ba dan ya shagala da kallon ta shi kansa ya sani yace, "kin yini Lafiya? Ya jikin ki?, I hope kin samu Lafiya sosai?."



Jin tambaya har uku da yayi mata lokaci Waya sai ta kalle shi suka haWa ido ta shagwaSe fuska tace, "to wacce zan fara amsawa?. Na yini Lafiya, naji sau™i, eh sosai a samu Lafiya." Jin ta amsa masa duka a tare yadda ya tambaya sai yayi murmushi sosai yana jin wani nishaW a zuciyar sa, ya gama lura shagwaSa a jinin ta take kowa ma yi amsa take yi.



Ganin yana murmushi abin ya bata mamaki tana kallon sa a ranta tana ayyana daman ya iya murmushi yake kullum fuska a Waure fuska.



Ya girgiza kai yace, "Adnan Mu'azzam shine sunana, nasan kin san aikina ni likitan zuciya ne." Ta girgiza kai bata ce komai ba ya kalle ta yace, "Baba ya sanar dake dalilin zuwana nasan da hakan, haka kawai Allah ya saka min ke a zuciyata na kasa mantawa dake har sai da nazo gidan nan jiya na samu Lafiya."



Bata ce komai ba yace, "Manal bana son ™arya, duk wani abu da kika sani ya shafe ki ki sanar dani kar ki yi min ™arya kat ki Soye min wani abu. Manal ™arya tana sakawa naji mutum ya fita daga raina lokaci Waya, dan haka kar ki Soye min komai a kan ki. Bazan ce lallai sai kin so ni ba, in kina da ra'ayina daman haka nake fata, in bakya yi haka Allah yayi daman." Yayi shiru yana kallon ta dan yaga yanayin ta amma bai fahimci komai ba yadda take haka take yace, "meye a zuciyar ki?."



Ta girgiza kai tace, "babu komai. Amma ni masu aikin ku basa burge ni, likita bai taSa burge ni ba, so bana tunanin...." Sai tayi shiru bata ™arasa ba.

Yayi murmushi yace, "Kina da wanda kike so?." Ta kalle shi ya Waga mata kai yace, "na faWa miki bana son ™arya ko Soye-Soye, ina son magana kai tsaye."



Tayi ΄ar dariya tace, "™arya ba halina bane, bazan kuma fara daga yau ba."

"Okay Answer me."

"Ni bana dashi, dan bani da wannan lokacin, kula da Mamana shi na saka a gaba."  Ya girgiza kai cikin jin daWin hakan yace, "Zaki iya saka Adnan zuciyar ki?."



"Sai na duba naga yuwar hakan" ta faWa bata kalle shi ba. Yayi murmushi yace, "haka ne, amma nasan you most love him." Sai tayi dariya tace, "really? For what reason?."



"Saboda na yarda da kaina." Tayi murmushi bata sake magana ba yana kallon ta, Allah ya sani yana sonta matu™ar so, daga lokacin da ya fara sonta soyayyar ta tayi masa kamu sosai musamman yanzu da take gashi gata tana kuma murmushi tare da magana mai sanyi cikin muryar ta mai za™i.



HaWa ido suka yi sai yace, "Ki bani phone number ki." Ta kalle shi ido cikin ido kamar zata yi magana sai ta fasa ya mi™a mata waya ta karSa tana saaka number kira yana shigowa taga an rubuta Rumana.



Mi™a masa wayar tayi ya karSa ganin wace take kiran sai ya ajjiye bai Wauka ba suka yi shiru babu mai magana a cikin su. Kallon ta yake yi yana ji farin ciki sosai a zuciyar sa, Allah ya sani yana son Manal so mai yawa. ˜ara wayar ta yi ganin mai kiran sai ta Wauka tace, "Yaya."



Bai ji me akace mata ba sai yaji tace, "subscription din ya ™are." Cikin shagwaSa yaji ta kuma cewa, "nidai Yaya kawai ka shigo yanzu, in kace sai gobe ni bana so na kai gobe ban gama ba" ta faWa kamar zatayi kuka. Sai yaga tayi murmushi tace, "to ina jira." Ta yanke wayar ta ajjiye tana murmushi yana kallon ta sai suka haWa ido ta sake faWaWa murmushin tace, "na tafi?."



Wani irin abu yake ji a zuciyar sa na tasowa yana game ilahirin jikin sa, ko ba'a faWa ba yasan kishi ne hakan ya saka shi zuba mata ido kawai yana kallon ta. Allah ya sani yana da kishi shi kansa ya sani. Ya sauke numfashi domin ya san kishin Manal sosai, zuciyar sa zafi take yi jin tana waya da wani.



Ya sauke numfashi yace, "Manal you have to be careful ba komai nake iya controlling a kai ba lokacin. Kina waya a gabana hakan zai bai min daWi ba."

Manal ita mamaki ma yake bata daga zuwa zance zuwan farko sai a dinga kafa mata sharaWi kamar mijin ta?. Sai magana yake yi dan ita bata Wauka ma yana da magana haka ba, wai ba komai yake controlling ba kamar wanda yake auren ta. Ta kalle tace, "Yayana ne." Bai bata amsa ba sai kallon ta da yake yi tana kallon sa kafin ya janye Idon sa yace, "Ban san kina da Yaya ba."

"Ynzu na sanar da kai." Ya kalli gefe ya kulle ido ya buWe, in ba soyayya ba taya wannan yarinyar zata zauna a gaban sa yana faWa tana faWa?. Ya tabbatar ko Mimi zata iya girmar ta, amma itace yana faWa tana mayar masa inda sune da yanzu zanen yatsun sa sun bayyana a fuskar su.



Sake kallon ta yayi ta sauke kai ™asa tana wasa da wayar ta yace, "sai da safe."

"Allah ya tashe mu Lafiya" ya faWa tana tashi itama ya ajjiye kuWi a inda ya tashi baice komai ba ya fita ta bishi da kallo, ita dariya ma ya bata wallahi da mamaki, daga zuwa zance sai a fara mata zancen bana son kaza ba'a son kaza.



A haka ta koma cikin gidan Mama tace, "Manal ina fatan kin amince dashi?."

"Wanne irin na amince Mama? Kina ji yana kafa min sharaWi daga zuwan farko?, shi baya son ™arya kuma yana da kishi kamar wanda ya haife ni ko yake aurena."



Mama tayi dariya tasan halin Manal Win ta bata son rainin hankali sannan akwai faWa duk da kuma akwai surutu kamar aku tace, "ai ya faWa miki gaskiya ne Manal, gwara ku saba tun yanzu."



"Yaya Haroun ne fa kawai yayi min waya dan na Wauka muna waya shine ya dinga kallona irin zai zane Win nan fa Mama, shine aka fara cemin ana da kishi" ta faWa tana dariya.



Mama ma dariyar tayi tace, "kema da laifin ki meye na Waukar waya a gaban sa?."

"To Mama Yaya Haroun ne fa?."

"Na sani ai, amma ai ba™o ne dake sai ki bari ai kin fito sai ku gaisa."



Manal tayi dariya Mama tace, "kina jin a zuciyar ki zaki iya amincewa dashi?." Manal tace, "gashi nan dai Mama, bashi da fara'a ko kusa ni sai jiya da yau naga dariya, sannan yana da shariya da faWa."



Mama tayi dariya sosai tace, "Manali ta kenan, Nidai ina miki sha'awar aure sa duk da bana ganin rashin fara'ar tasa." Tayi dariya itama tace, "to Mama zamu gani dai" ta faWa tana tashi ta shiga Wakin su ita da Mubeena tana dariya dan bata Soyewa Mama komai.





Shi kuwa farin ciki farin ciki, Sacin rai Sacin rai haka ya koma gida, bai yi niyar shiga wajan Mama bama ta window ta gano shi ta kira shi ya shiga ta bi shi da kallon tuhuma tace, "zance kaje ne Bebi?."



Ya kalli Maman alamun bashi da gaskiya zaiyi magana tace, "in ma can kaje na faWa maka kayi ganganci, kana Satawa ko wacece lokaci ne domin kuwa kai mallakin Rumana ne, ya kamata ka san da wannan tun ba yanzu ba, babu wata mace da zata zama mallakin ta matu™ar Rumana tana da rai. Sannan gobe ba jibi, kaje ka samu Yayan mahaifin ka aje gidan su Rumana a nemo maka auren ta, kar kayi min bayani akan wata mace na riga na faWa maka tun ba yau ba. Indai ina raye baka da mata sai Rumana ka jingine ko wacece a gefe, in kuma ban isa da kai ba dai zan gani" tana gama faWa masa haka ta koma ciki. jikin sa yayi sanyi sosai, gashi soyayyar Manal tayi masa kamun da bazai iya ha™ura da ita ba, gashi kuma dole yayi abinda Mama take so, to ya zai yi?.





Yana shiga Waki zama yayi a kan kujera ya zubawa waje Waya ido cikin rashin sanin abinda zai yi, tashi yayi ya shiga Waki ya canja kaya zuwa ™ananu ya fito ya hau mota ya wuce asibiti.



Yana shiga da Dr Hadiza suka haWu zata fita tace, "barka da zuwa Dr." kai ya Waga mata kawai ya wuce ciki a reception ya tarar da Huzaifa yana niyar tafiya ganin ya wuce shi sai yabi bayan sa daman akwai abinda zai faWa masa.



HaWuwa suka yi da Hamza ya fito daga maternity yace, "Ga Bebi Win can yazo, muje muyi masa zancen ko?." Ya amsa suka wuce suka same shi a tsaye ya juya baya ya harWe hannayen sa a ™irji Hamza yace, "Yauwa Bebi kana ji, akwai machine Win nan da aka siyo to custom sun kama shi a jirgin ruwa, don Allah ka yiwa Abba magana bazai rasa sanin wani ba a sake su don Allah. In machine Win nan yazo mune asibitin farko da muka fara mallakar sa a kaf nigeria." Huzaifa yace, "Akwai sabbin ma'aikata da muke tunanin Wauka this year, shima yana da kyau ka nutsu mu duba cv Win su mu gani, ni nan da wasu kwanaki zan je Qatar Daddy yana son ganina, kaima kace min akwai contract Win ku da india."



Sai a sannan Bebi ya juyo ya kalle su yace, "kuyi abinda ya dace kawai, zan samu Abba na sanar dashi zancen machine Win. Amma batun wani members kawai ku yi." Huzaifa ya kalle shi yace, "akwai damuwa ne?."



Kamar jira yake yace, "Na rasa ya zanyi, Mummy tana cewa in ma akwai wacce nake so na ajjiye ta a gefe indai tana raye bani da mata kamar Rumana. Na shiga tashin hankali sosai, na farko bazan iya tsallake maganar ta ba, na biyu bana son Rumana a yanzu, na uku yarinyar da nake faWa muku Allah ya Wora min ™aunar ta fiye da tunanin ku. GabaWaya komai baya min daWi."



Hamza yace, "to kayi ha™uri ka aure su duka su biyun." Ya kalle shi yace, "wallahi bana son Rumana, in na aure ta kamar tayi nasara a kaina ne, kullum gadarar ta sai na aure ta ko bana so."



"Haka zaka yi ha™uri kayi na dan ita na dan saboda Mama, ita kuma waccan Win ka ha™ura da ita in da hali." Ya girgiza kai yace, "bazan iya ba wallahi, baku san abinda nake ji a kanta ba shiyasa ku ke cewa haka. Ban taSa son wani abu lokaci Waya kamar yadda nake son ta ba, bana so na rasa ta. Bana son Satawa Mummy rai, in akwai mai son farin cikin Mummy ni ne, amma....!" Sai bai ™arasa ba yayi shiru yana sauke ajiyar zuciya.



Sun lura yayi rauni sosai, da alama abin ya taSa shi har zuciyar sa yake maganar. Huzaifa yace, "Ka cigaba da addu'a kawai, kar ka daina sauraren ita sabuwar saboda kana sonta, in duka matan kane sai ka aure su. Ni a shawara ta in Mama ta matsa ka samu kuyi magana kace mata zaka auri Rumana amma ta bari ka fara auren ita wacce ka ke so Win daga baya sai ka aure ta, zata iya amincewa saboda tasan baka yi mata ™arya sannan kuma itama Rumana an bata dama ta farko har ta auri wani bakai ba, duk da lokacin kana sonta ba'a matsa mata ba aka bari ta auri wani ba kai ba, kaima ya kamata a baka wannan damar."



"Anya Mummy zata amince kuwa? Bata da burin da ya wuce na auri Rumana."

"Zata iya amincewa mana ai ba ™in auren nata kayi ba ka fahimta?."



Ya kalli Huzaifa yace, "to ™arya nayi mata kenan ko da gasken zan aure ta Win?."

"Zaka aure ta mana, kaima ai baza yi mata ™arya ba?." Ya girgiza kai yace, "wai kasan yadda na tsani batun aure akan yarinyar nan?." Hamza yace, '"mafita kake nema, zancen ka tsana duk bai tashi ba ai Bebi. Dan Mama zaka yi ba don ita ba." Ya sauke numfashi yayi shiru baice komai ba dan bai san abinda zaiyi din ba.



Mujahid yana tsaye a bayan su yana jin duk abinda suke faWa,yazo ya yi masa albishir akan yayi nasarar fara soyayya da ™anwar sa sai yaji abinda yafi soyayya da ™anwar sa ma dadi, yana tsaye yana girgiza kai a zuciyar sa tana faWa masa ba mutuncin ™anwar sa ya kamata ya taSa ba, wacce yake so ya kamata ya fara da ita domin shima abinda yake

20 / 27