Chapter 6 Reading DANGIN SA COMPELET HAUSA NOVELS BY MAMAN WALEEDA DA WALEED.txt Arewa Novels

DANGIN SA COMPELET HAUSA NOVELS BY MAMAN WALEEDA DA WALEED.txt

Author :  Maman Waleed Da Waleedah Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   6 / 33

15K to 18K   out of 97.7K words

fahimtar yananin da ya shiga ne adalilin ambaton *dangin sa* da tayi ne ya sa bata kuma ce masa komai ba har ya bace,


tj ne ya rako shi har gurin parking space, shima ba abinda yace masa kawai shiga motar sa yayi yai gaba a guje
"Allah ya sauke ka lfy ɗan uwana" ya firta a fili



sai dare sannan yaji zai iya magana, ɗauko wayar sa yayi ya kira tj akan ya same shi a hotel ɗin daya saba sauka, ba a wani ɓata lkc ba sai ga tj nan ya zo sai bayan da suka ƙara gaggaisawa ne sannan suka shiga abinda ya haɗa sun


aliyu ne yai wa tj bayanin halin da ake ciki na sace zainab ɗin da yayi, tj yai mamaki sosai amma kuma sai be ce komai ba don yasan halin ɗan uwan nasa
"to yanzu yaushe zaku lagos ɗin" inji aliyu

" gobe zan tafi in shaa Allah don dole zanje in samu ɗan uwan hjy dake agegen mu samu mu gyara wannan ɓaran ɓaramar da ka tafka"


harara aliyun ya bishi da shi, amma kuma yasan maganar tj gaskiyace, don haka sai bece komai ba
"ka zaɓi gida guda a cikin gidajena na agegen a bashi don bana son aje neman min auren mata a inda suke a raina ni" ba ce komai ba suka ci gaba da tattaunawar yadda bikin zai kasance daga ƙarshe sukayi sallama akan sai tj ɗin ya dawo zai kira shi yai masa bayanin yadda ta kaya
[7:42PM, 12/7/2017] ‪+234 806 803 7117‬: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀



By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)

🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺



Huguma grp 😘

Safiya huguma congrats on your completely ur amazing novel *da'iman* I hope u r going to blast us with yet another jzk sis



Page :11🌹


*Lagos*



Ko da tj ya je lagos direct gidan ɗan uwan hjyr ya wuce daga na suka wuce sai gidan su zainab da taimakon kwatancen drivern sa,

Sun samu baba sun masa bayanin kansu, kasancewar akwai ƴar sanayya tsakanin ɗan uwan hjyn wato alh idris da baba yasa ba su wani kai ruwa rana sosai ba suka shawo kansa

"to wai ma don me yasa aka sacen ta shine ban sani ba kuma nake neman ƙarin bayani"

"wato shi yaron nan da ka ga hoton su tare da ita babban mutum ne, to kasan duk manyan mutane dole ne bazasu rasa maƙiya ba, don haka duk wanda yake tare da ajaban dole a bashi tsaro na musamman barin ma da akace matar sa to wallahi za a iya halaka ta, gaji dalilin sa na ɗauke don ya kare ta daga halaka, don an taɓa kwatanta haka wata yarinya ta fito tace wai ita zai aure Allah yarinyar nan sai gawar ta, to gudun kar hakan ta sake faruwa yasa shi aikata hakan"



jikin baba sai yai sanyi
"amma duk da haka da sai yayi bayani ba ba wai yazo da dakarai ba ya sace min ƴa"
"ƙuruciya fa" inji alh idris





ran baba ya ɓaci sosai ace sai da ƴar sa ta kwana sha huɗu sannan akazo aka ce masa wai don tsaron ta aka sace ta, ranshi ya ɓaci sosai daga baya dai ya sauko kuma ganin irin bada haƙurin da suke yi


Sai bayan da baba ya sauko ne sannan suka gabatar masa da zancen auren nata da za a zo a ɗaura ran jumma'a me zuwa inda hali, nan ma baba sai da ya ɗan yi ɗan karamin hauka kana daga baya ya sauko ya fahimtar da su shi bai tanadi komai na aure ba, inda suka shaida masa basa buƙatar komai su za suyi komai har abinda za a ci da bikin,

"to ai shikenan ita zainab ɗin yaushe zata dawo"sosa kai tj yayi
"ai baba sai nan da wata uku in shaa zaka ganta kafin nan komai ya lafa"


"meeeeeyeeee ƴar tawa sam ban yadda ba na sanima ko siyar min da ita kuka yi wannan zamanin da ba gaskiya" wannan karon alh idris ne yayi magana


"haba haba haba shi in baka san shi ba ni ai kasan ni ka san gidana ka san komai nawa na ɗauka har ƴar ka ce take auren ɗan aminina (maryam), ya za ayi kace zamu sai da maka da ƴa, wallahi da alkhairi muka zo ba sharri" sai da yayi baba dogon turanci na lallami da ban baki sannan baba ya sauko ganin cewar ko savce tan zasu yi a yanzu dai yasan wanda zai bi don fara binciken inda yar tasa take



"to shike nan Allah ya shige mana gaba" gabaɗayan su suaka ansa da amin , tj ne ya gabatar masa da gidan nan ma baba ƙin karɓa yayi sai da ƙh idris yasa baki sannan ya karɓa, sun masa bayanin cewar suna son ayi bikin a gidan, inda angon zai gyara musu gidan su tare kafin jumma'ar


Bayan doguwar shawara an tsai ds tarewar su ranar laraba ana jibi ɗaurin aure,suka buƙaci baba da yazo aje aje ganin gida wani maƙocin sa ne ya rakashi don ganin gidan wanda ya kasance a unguwar daji dake agegen



Four bedroom Duplex ne gidan, yai kyau sosai sai dai ɗan alamar an daɗe ba kowa a ciki amma da ya ɗan sha kwaskwarima zai fito fes da shi, sun zazzaga cikin gidan daga bisani suka dawo da su baba gida tare da yi masa alƙawarin zuwa kashegari don akai shi ya zaɓi irin kayan da yake so ai mai gyaran gidan da shi





ko da baba ya koma gida yai mama bayani da farko ta ɗauka wasa yake yi sai da taga takardun gidan nan fa hankalinta ya tashi wai ita ce zasu koma gidan kansu a unguwar daji ma, mama ranar kwana tayi batai bacci ba burin ta gari ya waye ta je gidan ta gani sannan ta fesa wa ƙawayen ta masu zama a fƙat suna mata kallon matsiyaciya, ko misƙaƙa zarratin bata damu da abinda zainab ɗin baban yace ta shiga ba ita kawai taje gidan ta gani



kashegaɗi baba ne ya kira su maryam suma suka zo aka sake ɗora zancen daga farko, gaskiya hankalkn sj ya tashi sƙsai barkn ma da suka ji maganar gidan shike nan baba ya sai da yaya


ko da baban yai musu bayanin wanda ya zo da zancen sai hankalin su ya kwanta don sun san alh idris kuma sun san halin sa


sun je sun ga gida mama ce ta zaɓi irin furnitures ɗin da za a gidan sannan tj ya sallami baba ta ɓangaren kayan abinci da kuma ƴen hidomomin bikin, store ɗin su taf aka cika musu da shi, nan suka shiga hidimar bikin ƴar sa zainab sai dai muce Allah ya kaimu


*abuja*
*ajaban recidence*


yana zaune yana tunanin wai gobe za a ɗaura masa aure da wata shi a rayuwar sa bai taɓa kawowa wai zaiyi aure saboda fassara mata da yayi akan basu da tausayi da imani a ziciyar su, a kullum idan ya tuna ƙuruciyarsa sai yace to me zanyi da mace a rayuwata amma yanzu gashi hjy tai masa shigar sauri matar da baya iya musu da ita ta haɗa shida aure, ko yama za ayi auren da shi oho




tashi yayi ya ƙarasa haɗa kayan sa da zai sa a cikin ƴar trolley ɗin tasa ɗinki da tj ya kawo masa ya ɗauka yana Allah sarki ya za ayi in iya rayuwa ba kai, shi sam ma ya manta wai ango sabon kaya yake sawa da badan tj ya ɗinka masa ba da saidai yaji kunya


kwanciya yai da safe yana da flight don ma sai goma zasu zo kasancewar yace a bar sabon private plane ɗin nasa a kano idan ya ɗauko tj sai su zo su kwashi shi, tsohon kuma a ɗauko ƴen ɗaurin aure, kwanciya yayi don bayasa ya makara


ina can akwance bansan wai nar da ake toyawa a kaina ba, nima bayan na gama komai na na kwata saba'ul khair




***********

*lagos*


ranar lahadi da ƙarfe da ƙara sha biyu dai dai aka ɗaura aure wanda ya tara dubban mutane daga ko'ina naɗin duniya, duk abokanan ajaban ne, shagali aka sha sosai ba ga ɓangaren amarya ba baga na ango don tj be ɗauki auren ɗan uwansa da wasa ba, reception ya haɗa musu sosai na gani na faɗa wanda sukayi bayan ɗauri auren acikin garin lagos,


a ɓangaren mama ita ma ba sauƙi a lamarin nata duk da guturi tsomar da akeyi akan anyi aure ba amarya wannan bai hana mama haɗa gagarimin yinin ta ba don itama ace ta faso


ɓangaren ƙannena ma hankalin su akwance suka gudanar da sha'anin bikin kasanceqar alh idris ya kira su ya kuma yi musu bayanin dalilin ɓoye nin da aka yi kuma sun gamsu sosai. ko da daee yayi babu batun kai amarya don haka sai kowacce mace ta kama hanyar inda ta fito mudai sai dai muce Allah ya bada zaman lfy


***************

yana kwance akan gadon ɗakin da ya kama a hotel yana hutawa yana hutawa bazai iya komawa abj ba yau don a ajiye yake tiƙis, bayan duk sun sallami ƴen ɗauren auren da suka zo da badan tj ba da baisan ya zaiyi da mutane ba don wasu ma bai gayyace su bai ma san inda suka samu lbrn auren nasa ba ya manta cewar he is d famous *ajaban*


bugun ƙofar ɗakin yaji kamar za a ɓalla a hotel ɗin ake irin wannan bugun ya faɗa ranshi a ɓace don har ya fara bacci, a gajiye ya sauko ya buɗe yai mamakin ganin tj ne, kuka tj yakeyi sosai kamar ƙaramin yaro, girgiza tj ɗin yayi tare da tambayarsa lfy


"hjy ce Allah yai mata rasuwa yanzu nan"
shiru aliyun yayi duk wani service ɗin shi ya ɗauke
"wace hjyr" ya tambaya idon nan nasa yai ja jijiyoyin jikin sa sun tashi fuskar sa ma tai jajawur
"hjyr mu ɗan uwa uwar mu kuma kakar mu yau Allah yai mata rasuwa"
"tj kenan da magaribar nan fa sai da mukayi waya da ita tace min jikin nata da saukƙiya zaka kawo min zancen banza wai ta rasu"


Tj ne ya ƙara fashewa da kuka yasan sam dama aliyun bazai taɓa yadda ba in ba gani yayi ko kuma ji, wayar shi ya ɗauka ya kira ƙanwar mahaifinsa wadda itace take jinyar hjy ya sa a speaker, da kukan ta ɗauka
"tijjani ka gaya aliyun kuwa hjyrsa ta rasu " shine kaɗai kalmar da ji don ragowar bai ƙarasa jin zancen ba service ɗinsa gabaɗaya ya ƙarasa ɗaukewa


wai hjyrsa ce ta rasu to shi ya za ayi ya iya rayuwa babu ita matar da duk wani neman sa da faɗi tashin da yake yi don ita ne yanzu da ta mutu ta barshi da wannan uban dukiyar me zai yi da ita wa zai kashewa, wani irin kuka ne me ƙuna ya kwace wa aliyu wannda tunda yake bai taɓa yi irin sa, wayar sa kawai ya ɗauko ya kira pilot ɗin
"prepare d plane we r flying to kano"
"yes sir" inji pilot ɗin

tj ne ma ya iya haɗa musu kayan nasu don shi gogan tuni yai waje yana kuka sosai me ƙona zuciya yana tafiya yana kiran sunan hjy ta bai damu da yadda mutane suke binsa da kallo ba shiɗdai burin sa ya isa yaga ta farfaɗo har suka shiga jirgi ya ɗaga zuwa kano yana kukan sa me sauti tare da tausayi
[7:42PM, 12/7/2017] ‪+234 806 803 7117‬: 🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊
*DANGIN SA*
🕊🕊🕊🕊🕊
🥀🥀



By Mmn Walida nd Walid(mrs aliyu)

🎁 *nasibi writers association*🎁
*we shine with the smile of our readers so keep smiling* ☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺☺


Dis page is 4 u mmn farida 😁😁😁



Page :12🌹


Har suka je kano aliyu bai daina kuka ba direct tafkeken gidan sa na sharaɗa uuka wuce inda anan hjyr take zaune tare da tj da matar sa babban gida ne, a cike gidan yake taf ba masaka tsinke don kuwa hjyr ajaban ta rasu, har an mata wanka an haɗa ta an ajiye ta tun da mutuwar dare tayi sai da safe za ayi jana'iza ta,

Mace me mutunci da sanin darajar ɗan adam wai itace yau babu Allah ya jiƙanta, a zaune aliyu ya kwana tare da ƴaƴanta da kuma tj, ba wanda bai tausaya aliyu ba ganin halin daya shiga don ba wanda baisan tsakanin su da hjyr ba,


Kashegari da ƙarfe takwas na safe aka kai wa hjy jana'iza inda mutane suka dinga ɗurowa daga ko ina kamar gayyatar su aka ohhh duniyar nan sai kallo ko da aka binne hjy aƙiyi ne kawai ya tsaya akan kabarin nata da tj bayan kƙwa ya watse ya kasa tafiya wai hjyr sa a nan, ya shafe kusan awa biyu akan kabarkn kafin daga bisani tj ya ja shi da kyar suka koma don tabbas za a dinga zuwa yi musu gaisuwa



Tun a mota aliyu ya ba tj atm card ɗinsa
"gashi a dinga yin cefanen abincin sadakar ba sai an dinga tambaya ba, pls kuma a dinga yin wanda mutane zasu iya ci"
"akwai kuɗi a hannuna ai"harara ya dokawa tj ɗin wanda baisan lkcn da ya karɓa, ya za ayi yace tj ya yi cefanen gidan nan bayan Allah ne kaɗai yasan irin mutanen da zasu dinga zuwa bayan tj ɗin shi yayi hidimar bikinsa tas da kuɗin hatta da lefe shi sai a gidan bikin ma ya gani don ya ma manta da batunsa, kuma ya san a ƴaƴan hjyr babu me cewa zai yi wani abun shi zasu zubawa ido to don me zai ɗaurawa tj ɗin
"kasa a ɗauko masu dafa abinci daga hotel ɗina don tun jiya na kira manager ɗin nace ya ya rufe hoteƙ ɗin saboda masu zuwa daga nesa sai su dinga sauka a can sai su kuma cooks din su dinga yi mana abinci dan nasan mutanena zasu dinga zuwa ban Son a kawo min abinda zanji kunya"
"to wane irin abincin za a dinga fitowa da" tj ya tamabaya
"ko menene ma ban damu ba amma a tabbatar anyishi kala kala"
"tom in shaa Allah"



a cike ƙofar gidan take taf kamar ɗaurin aure ake ba masaka tsinke hango fitowar aliyu daga motar ne yasa mutane suka yuuuu kansa kowa so yake yi yayi masa gaisuwa kuma a san ya zo, ansawa kawai yake yi amma baya ma iya gane komai, wurk ɗaya ya samu ya zauna ya ci gaba da karɓar gaisuwa




zaman makokk akayi wanda sai wanda ya gani abinci ne ake fitowa da shi kamar ba a san darajar kuɗi, kullum sai anyank sa da raguna huɗu banda iyayen kaji



mutane sai cicciɗowa kawai suke yi daga kowane ɓangare taf gidan yake cika har waje gurin zama har kaɗan yake yi, ko da akayi sadakar uku tj ya so ya cire canopies ɗin da aka kafa a wajen gidan amma ganin yawan mutanen da suke zuwa gidan ne daga ance agri ya waye ne yasa aliyu yace a ɓarsu haka aka ci gaba da ciyar da mutane


ran da ta cika kwana shida ana gobe sadakar bakwai aƙiyu ya kira pilot ɗin sa yace masa ya shirya zasu tafi saudiya kashegari da daddare yes sir kawai yace



ranar sadakar bakwai kamar biki akeyi saboda tsabar cika abin har ya bawa tj haushi yawancin su ba mutuwar bace a gabansu ba sudai suci su ƙoshi shikenan, ana sallah isha aliyu yai wa tj sallamar da cewa ya tafi saudiya, aliyun yana tafiya, tj yasa aka kwashe canopies ɗin da tabarmin wurin an tashi daga zaman makoki



kashe gari da sassafe sai ga wasu alarammomi da malun malun ɗin su wai sunyi wa aliyj magana cewar zasu dinga zama suna yiwa hjy addua har sai tayi arba'in, wannan abun ba ƙaramin ɓatawa tj rai yayi ba tabarmi ya basu suka shinfiɗa a waje aka fara karatu, kafin kace me wurin ya kuma cika ba masaka tsinke wasu ma akan talkalman su suke zaune a cikin rana, ko ƙala baice musu yayi fice warsa


to rana fa ta ke hantsi ya fara duban ludayi alarammomi da ƴen zaman makoki aka fara jin yunwa tun suna sa ran akawo musu har suka ga la'asar tayi ba aɗɗa'am ba alamar sai suka fara zamewa da ɗaya da ɗaya kafin biyar wurin nan kamar anyi shara ba komai ko da tj ya dawo yaga

6 / 33