Author : Binta Umar Abbale Category : Romantic Books
biya bukatarka ni nafi karfin ka idan kuma ka tsananta to za'ayi mutuwar kasko dani da kai a gidanan, dan nayi rantsuwa da Allah babu wani d'an iska da ya isa ya rabani da budurcina akan hakan zan iya aikata komai."
Ya jima yana kallonta kafin yace."Ke! kina nufin kina sa budurci a yanzu, da har kike wani tada jijiyar wuya! okey to kar ki damu ba wannan bane manufata a kanki kawai dai yanzu na baki umarni kan ki nutsu kana kuma muje ciki na sanar miki da abun al'ajabin da ya faru dake."
Taji wani irin shocking ya kama jikinta shin wai wannan wane irin abun al'ajabi yake so ya fad'a mata ne? Ji tayi wata jarumta tazo mata a take tace"Muje amma akwai sharad'i idan ka kusance ni sai nayi maka illah." Yace."Na yarda." Gaba tayi tana gurd'ewa ga lifayar tsabar wahala duk ta warware sai silmiyowa takeyi tana gyarawa gashin kanta duk ya baje a kafadarta ribbon din ya fad'i a bakin mota......Bayanta yake bi cikin nutsuwa yake 'kare mata kallo warwarewar lifayar ya sanya ya fahimci kayan dake jikinta t_shart ce mai karami hannu sai dogon wando na jins amma ya da'me ta d'am-d'am! ya fito mata da mazaunai tamkar suyi magana....Dauke kanshi kawai tayi yai saurin wuce ta yaje ya bud'e kofar palon....Yana tsaye ta 'karaso da hannu yayi mata alama ta shiga ta tsuguna tana kwance takalminta dake mai igiya ne... Nan ma kasa tsayuwa yayi saboda yanda ya hango brest dinta sun bullotso ta saman d'amammiyar rigar dake jikinta sai ya shige palon ya tsaya...Ta shiga ya mai da kofa ya rufe da key.
Had'uwar palon da 'kayatuwarsa sam! bashi ne a gabanta ba burinta kawai ya fad'a mata abun al'ajabin ko ya nuna mata ta zuba masa furgitattun idanunta
Cikin wani irin taku iske inda take tsaye ya zura hannunsa cikin aljihu dubu biyar d'in sadakinta ya zaro ya kama hannunta ya sanya mata kana ya kalleta ido da ido yace."Ri'ke sadakin auranki da kyau!! Yau! ni *Ahamdu Musa* na cika d'an halak na tashi daga sunan gwauro na 'yantu na cika cikakken namiji inda nayi tattaki 'kafa da 'kafa na iske har Garkin Gargo na d'aura aure da Wasilatu 'Yar gaske Kawunki Malam mai allo yace na baki sadakin ki a hannunki ki lissafa su dubu biyar ne."!
Yana gama maganarshi ya sakar mata hannunta kud'in suka watse a kasan palon.....Bai damu ba ya nufi bedroom dinshi hankalinsa kwance.......Da wani irin mamaki take kallonsa har ya bude dakinsa ya shiga tana kallonsa tana jinn sautin miryarsa na amsa kuwwa a kunnanta *"Wannan shine sadakin auraki Ni Ahamdu Musa nayi tattaki kafa da kafa na iske garin Garko na daura aure da Wasilatu 'yar gaske na tashi daga sunan gwauro na 'yantu Kawun ki Malam mai allo yace na baki sadakin ki da hannuna."* Wannan maganganun kawai takeji a cikin kunnanta kamar yanzu yake fada mata idanunta tsaye a kofar dakinshi.......Kimanin minti goma tana tsaye a gurin tana jajanta maganar gani take ma kamar mafarki take sai da ta kai idanunta kan kudin da suke watse kasan kafet, sannan gabanta ta sake faduwa ta tsuguna kamar wacce kwai ya fashewa a ciki ta dinga daukar kudin tana hadawa guri guda tsaf! ta lissafa su dubu biyar.......
*"Ni Wasilatu ni aka daurawa aure da sadaki dubu biyar sai kace bazawara!! Bazawarar ma mara gata da galihu tir'kashi!!!! A fusace! ta mike! ''Karye ne wallahi! Ni Wasilatu nafi karfin ayi min wannan wulakancin Ni za'a daurawa aure ban sani ba Wallahi wannan auran dashi da babu duk d'aya a gurina."!!! Sai ta nufi kofar dakin nasa gadan gadan!! hannunta rike da 'kudin sadakin auran na ta."*
*'YAR BANGAR SIYASA!!*
🌺 romantic love story🌺
*NA:*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*🌍Manazarta Writes asso*
_'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_
~~~~~~~~
*NA KUDI NE.......!*
_Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_
*NA SADAUKAR MUKU DA WANNAN PEGE 'DIN*
Rahima Aliyu
Hauwwa Saudia
H.Rabi 'kofar bai
Fatima Yakubu
Nafisat Ahamad
Zahra Kaduna
Fatima Binta
Jamila Abubukar
Mum Basma
Maimuna bichi
Ummu Yusif
Atou Tabalak
Anty Zeey Kazaure
Zainan Khabir Ishak
Jamila Yusha'u
JiddatulKhairi
_*Kuna da yawa sosai masoya wanda baiji sunanshi ba afuwa zamu hadu a gaba ina mutukar alfahari daku masoya Ubangiji Allah ya 'kara 'kauna ta gaskiya*_
~~~~~~~~~~~~~
*Free Pege20*
Lest Free Pege
A fusace! ta buga 'kofar d'akin ta shiga, yayi hanzarin juyowa jikinsa sanye da rigar wanka da alama yayi shiri tsaf wanka zai shiga dan yana daf da bakin toilet din....Idanunta a rufe ta durfafo inda yake tsaye yana kallonta ga mamakin sa sai yaga ta d'aga hannunta dake ri'ke da kud'in zata watsa masa yayi hanzarin ri'ke hannun! suka tsaya suna kallon junansu.....Sai yanzu ta lura da irin kayan dake jikinsa, rigar wanka ce mai bud'ad'addan gaba kuma bai daure ba ya sake ta faffad'an kirjinsa mai cike da yalwar gashi yana a bayyane kuma karamin wando ne a jikinsa wanda da ya d'ameshi.
da sauri ta sunkuyar da kanta 'kas! gabanta na masifar fad'uwa Ganin yanda wandon jikinsa ya masifar matse shi ba ta ta'ba ganin zahirin namiji ba sai yau! Har yanzu hannunsa na rike da nata wanda kudin ke ciki yana watsa mata wani irin kallo yace."Kar ki kuskura kiyi min watsi da kudi a d'aki idan kikayi sai ranki ya 'baci! hakkin ki ne kije dasu duk wanda ki kaga damar bawa ki bashi wannan bai dami kowa ba." Hannunta ya saki ya kama hanya zai shiga toilet d'in! aikuwa ta watsar da kud'in kasan dakin tana fadin "Wallahi wannnan auran dashi da babu duk daya suke a gurina ka kwashi kudin sadakin ka bana sonka bana ra'ayin auran mutum irinka da har zakaje har mahaifata kasa a dauro maka aure dani to yanzu ba gobe ba sai ka sake ni dan wannan budurcin nawa na mai rabo ne." Da jarumta take maganarta kuma tsakaninta da Allah take....Ya juyo cikin wani irin yanayi yana bin kudin da ta watsar a 'kas! wato dai sai da ta watsar masa da kudi a d'aki saboda taurin kai!! Nufar ta yayi cikin tsanani na 'bacin rai!!
Sosai ta tsorata! da ganin yanayinsa sai ta soma ja da baya yana sake tunkarar ta tana sake matsawa gabanta sai duka yake yana daka haka suka dinga yi har sai da suka dangane da jikin bango. (Garu) d'aga hannu yayi kamar zai mareta! sai tayi saurin kauda fuskarta ta sanya dukanin hannunwanta ta kare tana sakin 'karamin ihu!! Shiru taji ta bud'e idonta a hankali tana kallonshi ta kafar hannunta yana tsaye daf da ita ya dafa hannunsa guda a jikin bango ya tokare ta sannan faffadan kirjinsa dake bud'e yana gogar hannayenta, 'Das!d'as gabanta yake fad'uwa lokaci guda ta rasa miyau! a bakinta ya bushe kamas!!! Sai zare ido takeyi wani irin tsoronsa ne ya shige ta mussaman yanda taga zahirin hallitarshi sai ta ganta wata 'yar ficika a tsakaninsa ya za tayi idan wannan 'katon mutumin ya hau ta duka.
"Ashe rashin kunyarki ta banza ce! tunda har kika razana tin kafin nayi miki hukunci." Shiru ya dan yi yana kallonta yanda take kyarma! sai uban gumi take hadawa Murmushi ya saki mara sauti ya girgiza kansa kana yace." karki kuskura nayi sabo da dukan ki ko marin ki zaki sha wahala, aure ni nayi ra'ayin na aureki saboda na karya al'kadarinki kin shiga gidan redio kin zageni kin aibatani kinyi min kazafin na zina kawai saboda ki bata min suna a idon mutune to bukatarku bata biya har yanzu da mutuncina a idon mutane na aureki da mummunar niya ba zan munafurce ki ba amma kuma mutunci da 'kimar wannan dattijon ya sanya na janye kudirina a kanki! karyi tunanin ko zanyi wata mu'amular aure dake domin naji baki da wani zance da magana sai na budurci ki sani da budurcinki da babu duk daya suke a gurina domin bashi ne a gabana ba, zan killace a cikin gidana ne domin na taimake ki da wannan yawace yawacen da kikeyi kinga ke idan 'yar halak ce godiya ce zata biyo baya a tsakaninmu dalili kuwa na 'yan taki na aureki tare da killace ki guri guda, magana ta karshe da zanyi miki itace maza ki kwashe kudinki da kika watsar min 'kasan d'aki! ruwanki ne kiyi amfani dashi da kanki ruwanki ne ki bayar sadaka bai dami Ahamdu ba."
Bakinta mutuwa yayi murus! sai dai Ubab hawayen dake ambaliya a fuskarta, tayi tayi ta d'ago fuskarta ta kasa saboda yanda taji duk wani alkadari nata ya karye amma Ahamdu yayi mata wulakancin da ba zata ta'ba mantawa dashi ba....Cikin tsawa yace."Kin kwashe kudin ko kuwa."! Hucin maganarshi ya daki fuskarta tunda har yanzu yana kusa da ita ta ina zata wuce ya babbake hanya.....Idonta ta zuba masa tana motsa baki! Ko kusa ko alama bata bashi tausayi ba sai ma wani irin tsanarta da yake ji, ya kauce daga jikinta yana nuna mata kudin da hannunsa.....Tsugunawa tayi ta dinga binsu daya bayan daya tana tsincewa tana sha'kar hanci ta gama ta mike tsaye ba tare da ta juyo ba......Tsaki yaja mai sauti ya wuce toilet abinsa.
Yana shigewa toliet din ta fara dube dube a dakin kan mirror dinshi ta nufa ta hau duddubawa key take nema ba ta ganshi ba tayi d'age sosai tana lalube saman wardrobe dinshi, ganin tana wahala sai tayi nufin dauko drowar guda itama ta'ki daukuwa saboda yanayin katakon ba na wasa bane.....Da sauri ta bude wardrobe din tana dube dube can ta hango rigarshi da ya cire a rataye ta ciro tana zazzage ta babu komai a ciki sao gilashinsa da kuma carbinsa mai ma dannai.....Ta mayar da rigar a gaggauce! ta bude drowars ta fara dubawa nan taga tarin mukulai ba tare da 'bata lokaci ba ta d'aukesu ko rufe drowars din ba tayi ba ta fice daga dakin...Yaji lokacin da ta bude dakin ta futa sai jikinsa ya bashi a gaggauce ya cigaba da watsa ruwa a jikinsa ya dauro towel ya fito, nan yaga dakin a hargitse duk ta baza masa kaya....Ya fito palo da sauri, a take yaga kofar palo a bude bayan yasan ya rufe ta da key! Shaf ya manta towel ne a jikinsa da takalmin wanka ya fita a haka can ya hangota suna dambarwa da Masu gadi......Sosai ranshi yayi masifar 'baci! ganin yanda ta zakalkale tana musu masifa har da marin daya daga cikin yaranshi sai dungure masa kai take wai dole sai sun bude mata kofa ta fita!! Taku biyu yayi da niyar zuwa gurin towel dake kugunsa ya kwance nan ya tuna ashe daga wanka ya fito a gurguje ya koma ciki ya zura jallabiya ya fito, sai dai me!? 'Karamar 'kofa ya gani a bude Wasila ta shammace su ta fita.....Wasu daga cikinsu sun bi bayanta, Sauransu ya dinga zabgawa masifa kamar ya yari baki sai bashi hakuri sukeyi suna fadin"Wallahi shamtarsu tayi ta bude karamar kofa ta fita......Hadi ne ya paka mota a inda yake ya kar'bi key din motar rai a 'bace! ya shiga da gudu ya fice daga gidan.......Can ya hangota ta kusa fita daga Estate din tana wani irin gudu Su Garba na binta a baya....Yaji duk lamarin yarinyar ya fuce masa da kai wannnan zubda mutunci dame yayi kama, da ya sani ya shiga yi ace wannan ce matar auranka tana gudu maza na binta.
Wani wawan burki! yaci a gabanta! Tsabar wuya da galabaita ya sanya ta zubewa a gurin tana mai da nuffashi!! Ya bude mota ya fito rai a 'bace! sai ta yunkura cikin zafin nama zata sake arcewa da azama! ya sanya mata kafarsa guda a tsakanin tata sai tayo kanshi zata fad'a! yayi saurin matsawa ta kirjinta ya daki jikin motar....Ta dago kafadunta tare da juyo da ita ba tare da 'bata lokaci ba ya kife ta da wani wawan mari! wanda sai da taga gilmawar taurari ta dinga jin dum!! dum!! a kunnenta....Luuuu!! tayi zata sake kifawa a jikinsa ya kauce! ta sake dukan motar a zabure!! ta bude idonta ta dinga ganin zatinsa dishi dishi a cikin idonta.....Kawai sai wasu lafiyayyun hawaye suka wanke mata fuska.....Motar ya bude ya tankad'ata ciki ya mayar da murfin ya rufe kana ya zagaya mazauninsa ya shiga yaja motar,
Su Garba kuwa dama tuni sun juya..........Gate din a bude yake dan haka kawai sai ya shiga da motar duk suna tsaye ciro cirko ya tsai da motar ya tsaya yana musu fada da gargadi kan duk wanda yayi kuskuran sake barin ta ta futa daga gidan to a bakin aikinsa." Dukaninsu suka shiga bashi hakuri tsabar haushi bai ma tsaya ya sauraresu ba ya fuzgi motar a guje ya wuce.
Yanayin parking ya fito hade da bude kofar da take tana kwance ruf da ciki kan site gashinta ya wargaje yayi buyaya lifayar ma ta cire dan saura kadan ta rabu da jikinta, Tsawa ya buga mata kan ta fito masa daga mota! shiru yayi ya sake kwatsa mata wata tsawar yaji shiru, sai da yayi magana sau biyar ba ta amsa ba, ya zura jikinsa cikin motar ya burkitota fuskarta ya tsirawa ido yana kallo....Idanunta a rufe ruf! dai-dai da gashin idon baya motsi! yaji faduwar gaba kadan ta kamashi Hannunsa ya dora a kirjinta minti biyu ya dauke! da sauri! ya kara hannunsa saitin hancinta nan ma yayi minti biyu babu alamun nuffashi a tare da ita....Babu shiri ya tattaro ta jikinsa ya taraiyaye ta daukar jarirai yayi mata ko motar bai rufe ba ya nufi cikin gidan da ita, hankalinsa a tashe.
*_TO JAMA'A NAN NA KAWO 'KARSHEN FREE PEGE NA WANNAN LITTAFIN GA DUK MAI BUKATAR CIGABA DA KARANTAWA SAI YA DUBA BAYANAN DA NAYI A SAMA KAZO KA BIYA KUDINKA KA KARANTA DOMIN KAR AYI BABU KAI WANNAN LABARI DAI YANZU MA AKA FARA AKWAI TAFIYA A GABA WANNAN D'ANDANAN GISHIRI NE..........HAR KULLUM INA FAD'A CEWA KUD'IN KARATU KIKA BIYA BA NA MALLAKA BA IDAN KIN YARDA KIZO KI BIYA KI KARANTA IDAN BAKI YARDA DA WANNAN TSARIN BA TO DAN ALLAH KAR KIZO KI BIYA KI FUTAR MIN DA BOOK KI RUSA NI KIYI ZAMANKI NAGODE SANNAN DUK MAI BUKATAR KARANTA NOVLS DINA AKWAI COMPLETED KAN FARASHI MAI SAU'KI KAR KU MANTA DAI HAUSAWA NACEWA SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA_*
'WADANNAN SUNE LITTAFAN NAWA
*NANA KHADIJA*
*YARO DA KUDI*
*GIMBIYA BALARABA*
*TSANTSAR BUTULCI*
*BABBAN YARO*
*LADIDI KWADAGA*
*MASHAHURI*
*SADAUKI OMAR*
*RUWAN DARE*
*NI DA YAYA SADAM*
*'YAR BANGAR SIYASA*
Kar ku manta da cewar ni Binta Umar Abbale nice mamalakiyar wad'annan novels din.....Saboda haka ga duk wani mai bukatar ya karanta completed dinsu sai ya nemi numbar ta ya biya ya karanta hankali kwance, Ina kara tunasar daku cewar kada kuje ku biya wani ko wata kudin wannan novels din dana jera muku 'karya yake 'karya take zasu siyar muku da hakkin da bana su ba kumai ba zama lallai su baku complete ba shikkenan sunci kudinku a banza, hanya mafi sauki anan ita ce ku tuntu'be ta wannan numbars din nawa
*08089965176*
*07084653262*
Masha Allah masoya sai naji ku🙋🏻♀️
*'YAR BANGAR SIYASA!!*
🌺 romantic love story🌺
*NA:*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*🌍Manazarta Writes asso*
_'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_
~~~~~~~~
*NA KUDI NE.......!*
_Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_
*NA SADAUKAR MUKU DA WANNAN PEGE 'DIN*
Rahima Aliyu
Hauwwa Saudia
H.Rabi 'kofar bai
Fatima Yakubu
Nafisat Ahamad
Zahra Kaduna
Fatima Binta
Jamila Abubukar
Mum Basma
Maimuna bichi
Ummu Yusif
Atou Tabalak
Anty Zeey Kazaure
Zainan Khabir Ishak
Jamila Yusha'u
JiddatulKhairi
_*Kuna da yawa sosai masoya wanda baiji sunanshi ba afuwa zamu hadu a gaba ina mutukar alfahari daku masoya Ubangiji Allah ya 'kara 'kauna ta gaskiya*_
~~~~~~~~~~~~~
*Free Pege20*
Lest Free Pege
A fusace! ta buga 'kofar d'akin ta shiga, yayi hanzarin juyowa jikinsa sanye da rigar wanka da alama yayi shiri tsaf wanka zai shiga dan yana daf da bakin toilet din....Idanunta a rufe ta durfafo inda yake tsaye yana kallonta ga mamakin sa sai yaga ta d'aga hannunta dake ri'ke da kud'in zata watsa masa yayi hanzarin ri'ke hannun! suka tsaya suna kallon junansu.....Sai yanzu ta lura da irin kayan dake jikinsa, rigar wanka ce mai bud'ad'addan gaba kuma bai daure ba ya sake ta faffad'an kirjinsa mai cike da yalwar gashi yana a bayyane kuma karamin wando ne a jikinsa wanda da ya d'ameshi.
da sauri ta sunkuyar da kanta 'kas! gabanta na masifar fad'uwa Ganin yanda wandon jikinsa ya masifar matse shi ba ta ta'ba ganin zahirin namiji ba sai yau! Har yanzu hannunsa na rike da nata wanda kudin ke ciki yana watsa mata wani irin kallo yace."Kar ki kuskura kiyi min watsi da kudi a d'aki idan kikayi sai ranki ya 'baci! hakkin ki ne kije dasu duk wanda ki kaga damar bawa ki bashi wannan bai dami kowa ba." Hannunta ya saki ya kama hanya zai shiga toilet d'in! aikuwa ta watsar da kud'in kasan dakin tana fadin "Wallahi wannnan auran dashi da babu duk daya suke a gurina ka kwashi kudin sadakin ka bana sonka bana ra'ayin auran mutum irinka da har zakaje har mahaifata kasa a dauro maka aure dani to yanzu ba gobe ba sai ka sake ni dan wannan budurcin nawa na mai rabo ne." Da jarumta take maganarta kuma tsakaninta da Allah take....Ya juyo cikin wani irin yanayi yana bin kudin da ta watsar a 'kas! wato dai sai da ta watsar masa da kudi a d'aki saboda taurin kai!! Nufar ta yayi cikin tsanani na 'bacin rai!!
Sosai ta tsorata! da ganin yanayinsa sai ta soma ja da baya yana sake tunkarar ta tana sake matsawa gabanta sai duka yake yana daka haka suka dinga yi har sai da suka dangane da jikin bango. (Garu) d'aga hannu yayi kamar zai mareta! sai tayi saurin kauda fuskarta