YAR BANGAR SIYASA BOOK COMPLETE By Binta Umar Abbale .txt

Author :  Binta Umar Abbale Category :  Romantic Books

Chapter   12 / 57

33K to 36K   out of 169.7K words

ta sanya dukanin hannunwanta ta kare tana sakin 'karamin ihu!! Shiru taji ta bud'e idonta a hankali tana kallonshi ta kafar hannunta yana tsaye daf da ita ya dafa hannunsa guda a jikin bango ya tokare ta sannan faffadan kirjinsa dake bud'e yana gogar hannayenta, 'Das!d'as gabanta yake fad'uwa lokaci guda ta rasa miyau! a bakinta ya bushe kamas!!! Sai zare ido takeyi wani irin tsoronsa ne ya shige ta mussaman yanda taga zahirin hallitarshi sai ta ganta wata 'yar ficika a tsakaninsa ya za tayi idan wannan 'katon mutumin ya hau ta duka.


"Ashe rashin kunyarki ta banza ce! tunda har kika razana tin kafin nayi miki hukunci." Shiru ya dan yi yana kallonta yanda take kyarma! sai uban gumi take hadawa Murmushi ya saki mara sauti ya girgiza kansa kana yace." karki kuskura nayi sabo da dukan ki ko marin ki zaki sha wahala, aure ni nayi ra'ayin na aureki saboda na karya al'kadarinki kin shiga gidan redio kin zageni kin aibatani kinyi min kazafin na zina kawai saboda ki bata min suna a idon mutune to bukatarku bata biya har yanzu da mutuncina a idon mutane na aureki da mummunar niya ba zan munafurce ki ba amma kuma mutunci da 'kimar wannan dattijon ya sanya na janye kudirina a kanki! karyi tunanin ko zanyi wata mu'amular aure dake domin naji baki da wani zance da magana sai na budurci ki sani da budurcinki da babu duk daya suke a gurina domin bashi ne a gabana ba, zan killace a cikin gidana ne domin na taimake ki da wannan yawace yawacen da kikeyi kinga ke idan 'yar halak ce godiya ce zata biyo baya a tsakaninmu dalili kuwa na 'yan taki na aureki tare da killace ki guri guda, magana ta karshe da zanyi miki itace maza ki kwashe kudinki da kika watsar min 'kasan d'aki! ruwanki ne kiyi amfani dashi da kanki ruwanki ne ki bayar sadaka bai dami Ahamdu ba."
Bakinta mutuwa yayi murus! sai dai Ubab hawayen dake ambaliya a fuskarta, tayi tayi ta d'ago fuskarta ta kasa saboda yanda taji duk wani alkadari nata ya karye amma Ahamdu yayi mata wulakancin da ba zata ta'ba mantawa dashi ba....Cikin tsawa yace."Kin kwashe kudin ko kuwa."! Hucin maganarshi ya daki fuskarta tunda har yanzu yana kusa da ita ta ina zata wuce ya babbake hanya.....Idonta ta zuba masa tana motsa baki! Ko kusa ko alama bata bashi tausayi ba sai ma wani irin tsanarta da yake ji, ya kauce daga jikinta yana nuna mata kudin da hannunsa.....Tsugunawa tayi ta dinga binsu daya bayan daya tana tsincewa tana sha'kar hanci ta gama ta mike tsaye ba tare da ta juyo ba......Tsaki yaja mai sauti ya wuce toilet abinsa.


Yana shigewa toliet din ta fara dube dube a dakin kan mirror dinshi ta nufa ta hau duddubawa key take nema ba ta ganshi ba tayi d'age sosai tana lalube saman wardrobe dinshi, ganin tana wahala sai tayi nufin dauko drowar guda itama ta'ki daukuwa saboda yanayin katakon ba na wasa bane.....Da sauri ta bude wardrobe din tana dube dube can ta hango rigarshi da ya cire a rataye ta ciro tana zazzage ta babu komai a ciki sao gilashinsa da kuma carbinsa mai ma dannai.....Ta mayar da rigar a gaggauce! ta bude drowars ta fara dubawa nan taga tarin mukulai ba tare da 'bata lokaci ba ta d'aukesu ko rufe drowars din ba tayi ba ta fice daga dakin...Yaji lokacin da ta bude dakin ta futa sai jikinsa ya bashi a gaggauce ya cigaba da watsa ruwa a jikinsa ya dauro towel ya fito, nan yaga dakin a hargitse duk ta baza masa kaya....Ya fito palo da sauri, a take yaga kofar palo a bude bayan yasan ya rufe ta da key! Shaf ya manta towel ne a jikinsa da takalmin wanka ya fita a haka can ya hangota suna dambarwa da Masu gadi......Sosai ranshi yayi masifar 'baci! ganin yanda ta zakalkale tana musu masifa har da marin daya daga cikin yaranshi sai dungure masa kai take wai dole sai sun bude mata kofa ta fita!! Taku biyu yayi da niyar zuwa gurin towel dake kugunsa ya kwance nan ya tuna ashe daga wanka ya fito a gurguje ya koma ciki ya zura jallabiya ya fito, sai dai me!? 'Karamar 'kofa ya gani a bude Wasila ta shammace su ta fita.....Wasu daga cikinsu sun bi bayanta, Sauransu ya dinga zabgawa masifa kamar ya yari baki sai bashi hakuri sukeyi suna fadin"Wallahi shamtarsu tayi ta bude karamar kofa ta fita......Hadi ne ya paka mota a inda yake ya kar'bi key din motar rai a 'bace! ya shiga da gudu ya fice daga gidan.......Can ya hangota ta kusa fita daga Estate din tana wani irin gudu Su Garba na binta a baya....Yaji duk lamarin yarinyar ya fuce masa da kai wannnan zubda mutunci dame yayi kama, da ya sani ya shiga yi ace wannan ce matar auranka tana gudu maza na binta.


Wani wawan burki! yaci a gabanta! Tsabar wuya da galabaita ya sanya ta zubewa a gurin tana mai da nuffashi!! Ya bude mota ya fito rai a 'bace! sai ta yunkura cikin zafin nama zata sake arcewa da azama! ya sanya mata kafarsa guda a tsakanin tata sai tayo kanshi zata fad'a! yayi saurin matsawa ta kirjinta ya daki jikin motar....Ta dago kafadunta tare da juyo da ita ba tare da 'bata lokaci ba ya kife ta da wani wawan mari! wanda sai da taga gilmawar taurari ta dinga jin dum!! dum!! a kunnenta....Luuuu!! tayi zata sake kifawa a jikinsa ya kauce! ta sake dukan motar a zabure!! ta bude idonta ta dinga ganin zatinsa dishi dishi a cikin idonta.....Kawai sai wasu lafiyayyun hawaye suka wanke mata fuska.....Motar ya bude ya tankad'ata ciki ya mayar da murfin ya rufe kana ya zagaya mazauninsa ya shiga yaja motar,


Su Garba kuwa dama tuni sun juya..........Gate din a bude yake dan haka kawai sai ya shiga da motar duk suna tsaye ciro cirko ya tsai da motar ya tsaya yana musu fada da gargadi kan duk wanda yayi kuskuran sake barin ta ta futa daga gidan to a bakin aikinsa." Dukaninsu suka shiga bashi hakuri tsabar haushi bai ma tsaya ya sauraresu ba ya fuzgi motar a guje ya wuce.


Yanayin parking ya fito hade da bude kofar da take tana kwance ruf da ciki kan site gashinta ya wargaje yayi buyaya lifayar ma ta cire dan saura kadan ta rabu da jikinta, Tsawa ya buga mata kan ta fito masa daga mota! shiru yayi ya sake kwatsa mata wata tsawar yaji shiru, sai da yayi magana sau biyar ba ta amsa ba, ya zura jikinsa cikin motar ya burkitota fuskarta ya tsirawa ido yana kallo....Idanunta a rufe ruf! dai-dai da gashin idon baya motsi! yaji faduwar gaba kadan ta kamashi Hannunsa ya dora a kirjinta minti biyu ya dauke! da sauri! ya kara hannunsa saitin hancinta nan ma yayi minti biyu babu alamun nuffashi a tare da ita....Babu shiri ya tattaro ta jikinsa ya taraiyaye ta daukar jarirai yayi mata ko motar bai rufe ba ya nufi cikin gidan da ita, hankalinsa a tashe.










*_TO JAMA'A NAN NA KAWO 'KARSHEN FREE PEGE NA WANNAN LITTAFIN GA DUK MAI BUKATAR CIGABA DA KARANTAWA SAI YA DUBA BAYANAN DA NAYI A SAMA KAZO KA BIYA KUDINKA KA KARANTA DOMIN KAR AYI BABU KAI WANNAN LABARI DAI YANZU MA AKA FARA AKWAI TAFIYA A GABA WANNAN D'ANDANAN GISHIRI NE..........HAR KULLUM INA FAD'A CEWA KUD'IN KARATU KIKA BIYA BA NA MALLAKA BA IDAN KIN YARDA KIZO KI BIYA KI KARANTA IDAN BAKI YARDA DA WANNAN TSARIN BA TO DAN ALLAH KAR KIZO KI BIYA KI FUTAR MIN DA BOOK KI RUSA NI KIYI ZAMANKI NAGODE SANNAN DUK MAI BUKATAR KARANTA NOVLS DINA AKWAI COMPLETED KAN FARASHI MAI SAU'KI KAR KU MANTA DAI HAUSAWA NACEWA SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA_*




'WADANNAN SUNE LITTAFAN NAWA




*NANA KHADIJA*
*YARO DA KUDI*
*GIMBIYA BALARABA*
*TSANTSAR BUTULCI*
*BABBAN YARO*
*LADIDI KWADAGA*
*MASHAHURI*
*SADAUKI OMAR*
*RUWAN DARE*
*NI DA YAYA SADAM*
*'YAR BANGAR SIYASA*


Kar ku manta da cewar ni Binta Umar Abbale nice mamalakiyar wad'annan novels din.....Saboda haka ga duk wani mai bukatar ya karanta completed dinsu sai ya nemi numbar ta ya biya ya karanta hankali kwance, Ina kara tunasar daku cewar kada kuje ku biya wani ko wata kudin wannan novels din dana jera muku 'karya yake 'karya take zasu siyar muku da hakkin da bana su ba kumai ba zama lallai su baku complete ba shikkenan sunci kudinku a banza, hanya mafi sauki anan ita ce ku tuntu'be ta wannan numbars din nawa
*08089965176*
*07084653262*


Masha Allah masoya sai naji ku🙋🏻‍♀️




[07/08, 11:49 pm] +234 803 238 4602: 'Yr bngr Sys.
*21*
Kan makeken bed dinshi ya shimfidata a gaggauce ya bude ma dai-dai cin firjin dake gefan bed din ya dauko goran ruwa mai sanyi ya bude murfin ya tsiyaya a hannushi ya soma yarfa ma a fuska, sai da yayi haka sau uku tukkuna ta sauke wata nannauyar ajiyar zuciya numfashinta ya dawo amma kuma idanunta a rufe ruf sai dai gashin idanunta dake motsi.....Tsayuwa yayi a kanta yana me 'karewa fuskarta kallo, Tunda yake da yarinyar bai ta'ba tsayuwa ya kare mata kallo ba irin yau! tana da masifar kyau! wanda sai ka dade kana kallonta zaka fahimta babu abunda yafi tafiya da hankalinsa irin karamin bakinta mai dan tudun le'be dai-dai sumba, bai san sanda ya tsotsi leb'anshi ba ya dan lumshe idonsa tare da sake budesu a kanta, karaf! suka hada ido lokacin ta bude nata idon yayin saurin dauke kansa yana dan ja baya daga kusa da ita.....Cikinta ta rike da hannuwanta tana rintse ido hawaye ya soma shatata! "Wayyo cikina wayyo cikina! wayyo cikina."!!!! Abunda take ta fad'a kenan tana matagugu kan bed din......Sai ya tsinci kanshi da kid'imewa ya zauna kusa da ita yana kokarin rike hannunta ta fuzge! da 'karfi! tana cigaba da murkususu da kiran cikinta.....Hayewa yayi bed din ba tare da ya sani ba ya rirrike ta jikinsa sai kyarma! yake " Menene! ina ne yake miki ciwo sannu daina kuka ko kin bugu ne."? Duka ya jero mata wannan tambayar lokaci guda.....Shiru tayi masa ta sane ta dinga kwanciya a jikinsa tana mutsika masa jikinta anashi tana kuka da kiran cikinta......Bai san sanda ya zura hannunsa cikin rigarta ba yana shafa kasan mararta muryarshi sanyi kalau! yake magana "Sannu daina kuka bari na duba miki magani ina kin buga gurin da jikin mota dole yayi miki ciwo mybe ma yunwa kikeji ko."? Ba tace komai ba sai aukin tureshi da takeyi daga jikinta yana sake rirriketa shi duk a tunaninsa da gaske take cikinta ciwo yake.....Ya mike da sauri yans fad'in" Bari na duba miki magani dare yayi yanzu da na kaiki an duba ki.''' Yana fita taja tsaki ta mike da azama! taje ta rufe kofar dakin tabar key din a jiki.....Komawa tayi ta kwanta tana sa'ka wacce zata fisheta.


Ya dawo dakin hannunsa rike da maganin ciwon ciki duk ya had'a uban gumi yana jan kofar yaji a kulle gam! gam!! Turus yayi da maganin a hannunsa yana tunani Babu shakka yarinyar nan yaudararsa tayi.....handle din ya sake murdawa yaji a rufe gam! gashi bedroom dinshi ne duk wasu abubuwan bukatunsa na ciki.....Wato tana so yayi mata magiya ta bude kofar shi kuma ya dauki alkawari kan sai dai ta gaji dan karan kanta ta bude tunda ya gane manufarta.....Wani bedroom din ya nufa ranshi a 'bace! amma yarinyar ta shammace shi gashi wayoyinsa na dakin hade da sauran makullan gidan.....Idanunsa suka sauka kan key din dake jikin kofar dakin da yake ciki....Da sauri ya mike ya isa gurin ya zare key din ya nufi dakin....Koda ya zura key din sai yaki shiga yayi yayi nan ya fahimci tabar key din a jiki. Ya juyo yana girgiza kai agogon bango ya kalla karfe daya na dare har da wani abu yarinyar nan ta hanashi bacci.....Idanunsa ne suka sauka kan pose dinta dake can bakin kofa yayi saurin isa inda take ya dauka tare da zama kan kujera yana budewa.....Wayarta babba da karama ce a ciki sai turaranta da wani zobe na gold a cikin gidanshi sai 'yan kudinta wanda basu wuce dubu takwas ba zuwa goma....Ya kunna wayar yana dube dube a ciki.


Tana kwance ta 'kurawa cilling ido tana tunanin yanda za'ayi ta kubutar da kanta daga hannun Ahamdu, ta mike zaune da sauri tana dube dube! sai yanzu ta tuna da pose dinta....Tsaye ta mike lifayar jikinta na hard'e tayi gaggawar cireta ta jefar a gurin babu ruwanta da yanayin kayan dake jikinta ta durfafi kofar futa.....Har ta murda kofar zata futa sai kuma ta fasa tsoro takeji kar ya ritsata ta k sanya kunnanta jikin kofar wai ko za taji alamun motsi taji tsit! a hankali ta murza key din ta ja kofar ta bude.......Yana zaune kasan kafet tsakanin kujeru shine dalilin da ya sanya ba ta ganshi ba sai ta fara dube dube a palon....Ya zuba mata idanunsa yana kallonta tar cikin jan 'kwan dake palon mai hasken tsiya.....Can yaga ta nufi bakin kofar futa domin anan take tunanin ta yar da Pose din nata....Ya mike a hankali ya iske inda take hannunsa rike da pose din nata....Tana juyowa suka buga karo goshinta ne ya daki kirjinsa......Tayi masifar razana!!! da sauri tayi nufi guduwa ya tare ta tare da matseta a jikin labule......." 'Kas tayi da kanta kunya ta isheta sai yanzu ta fahimci a yanda ta fito tama manta shaf da kananun kayane a jikinta.


"Kallonta kawai yake yi ya ma rasa abunda zai ce mata sai bin sasan jikinta yake da kallo yana ayyana abubuwa da dama a kanta.


Pose din dake hannunshi ta zubawa ido....Ya dage mata gira tare da fad'in" Kin bude kofa ne sabida kizo ki dauki jakarki ko."? Tayi shiru yace."Kin yaudareni da ciwon ciki kin kulle min daki....Daga taimako sai sharri ya biyo baya kinga dake bani da alhaki a kanki da kanki kin bude kofar wai ke me wayo ko? Okey jakarki gata a hannunta zan baki abarka amma zan dauki abu biyu a ciki."


Hannu ta kai da sauri zata fuzge! yayi sama da jakar yana kallonta sai d'age! takeyi Yace."Ki daina wani wahalar da kanki Ba komai zan dauka ba a ciki illah wayoyinki dukaninsu babu ke babu amfani da waya sai kinyi hankali."


Ido ta zare! hannunta na kyarma sai rirrike hannunsa takeyi tana so ta fuzgo pose din....Dariya ta bashi ganin yand ta dage tana d'age! 'kafafu Ya d'an ture ta daga jikinsa yana matsawa, Biyo shi tayi muryarta na rawa "Allah sai ka bani waya ta." Abunda take fada kenan tana rirrike masa riga....Ya 'bata fuska da fad'in"Idan ba ki daina tatta'ba min jiki ba sai na 'bata miki " Wallahi kinji na rantse ke da wayar nan har abadah sai nayi niyya nan gaba na yarda da hankalin ki sannan zan yarda ki rike waya."


Dajin wannan magana tashi sai ta fashe da kuka" Wallahi ban yarda ba haka kawai zaka takura min ka shiga rayuwa ta kace ba zan rike waya ba, Idan ka cuzguwa rayuwata nima sai na cuzguna maka kuma na fada maka wannan auran dashi da babu duk daya suke a gurina Gwara kawai ka sallame ni naje na cigaba da harkokina."


Ko kallonta baiyi ba ya cire mata agogonta da turaranta ya ajiye mata kan kujera ya nufu bedroom dinshi yana fadin"Wahala ce bata isheki ba yarinya sai kiyi tayi ke kadai, Ahamdu bashi da lokacin ki." Yana shiga dakin ya murza key ta tsaya jikin kofar tana bugawa ya share ta kawai ya kwanta bed din shi tare da rufe ido bacci yake ji sosai bayan haka kuma ga gajiya ta dabaibaye shi......Tun yana jin bugun kofarta sama-sama har ya daina ji bacci yaci karfinsa.......Itama da ta gaji da dukan kofar sai ta silale kofar dakin tana kuka da kiran sunan Allah shiru palon tsoro da farga duk ya isheta haka dai tayi kwance bakin kofar dakin ga sanyi Ac yayi yawa a palon tsoro ya hanata taje ta rage, Yanda taga rana haka taga dare domin a kunnanta aka soma kiran assalatu.






Kika futa da book din nan na barki da Allah kika karanta baki biya ba kema ke da Allah! Whasap numbar
*07084653262*




*BINTA UMAR ABBALE*
[07/08, 11:49 pm] +234 803 238 4602: 'Yr bngr Sys
*22*
Yana fitowa da shirin zuwa masalaci yaci tuntube da ita a bakin 'kofa yayi saurin matsawa yana dan haske ta da wayarshi, ta bude idanunta da suka ci kuka suka 'koshi ta zuba a kanshi....Wani irin mugun haushinsa da tsanarsa ne ya kamata haka kawai ya daukota ya rufe a gida yana azabtar da ita, Da sauri ta mike tsaye! yayi saurin kaucewa ya bata hanya ya dauka dakin zata shige sai yaga tayi kansa ta cikwokwiye shi tana kuka." Ka dauke ni ka mayar dani inda ka dauko ni ba zan iya wannan rayuwar ba bana sonka kan me yasa zakaje ka sanya a daura maka aure dani ai wannan zalinci ne, Wallahi gwara na kashe kaina kan in zauna da kai na tsaneka." kuka take hai'kan! tana sake rike masa riga sai shigewa jikinsa takeyi gashi ya dauro alwala.
Yanda take gunjin kuka ya nuna masa da gaske takeyi abunda take fada har cikin ranta yake......Sai yaji rashin dadin hakan ranshi a bace ya ture ta daga jikinshi ya bar gurin da sauri! ta kuma mikewa a guje ta cimma sa ta baya ta rikeshi tam ta zagaye 'kugunsa da hannuwanta kirjinta na gogan bayanshi.....A zabure! ya juyo ya hankade ta hade da kifa mata mari! da hannu ya nuna ta "Kika sake kika 'kara ta'bani sai ranki ya 'baci! wallahi ba zan sake ki ba za kiyi ta zama a cikin kunci da bacin rai! ke da kin dauka nima sonki ne? Allah ya sawake na fada miki domin na karya alkadarinki yasa na aure ki shashasha kawai."! Juyawa yayi ya shige dakin....A gurguje ya sake sabuwar alwala yana jan tsaki ko yaya ta ra'bi jikinsa sai yaji sauyi a tare dashi abinda bai taba faruwa ba dashi.....Tana durkushe tsakiyar palon ya fito ko kallonta baiyi ba

12 / 57