Author : Binta Umar Abbale Category : Romantic Books
Ya sauke ajiyar zuciya me zafin gaske, a hankali ya mi'ke ya fita daga dakin, ta'be bakinta tayi tace"Zaka gama salau! salau! d'in naka ka dawo ka bada kai, idan laifi ne ai bani kadai ce mai lefi har da kai dan haka duk sai mu taru mu bawa junanmu hakuri."
Ta dauka, ba zai dawo dakin ba sai ta saki jikinta sosai bacci na kokarin daukarta taji alamun shigowarsa dakin yana kulle kofa, ta dan kalleshi ta ganshi cikin wasu pyjamas sky blue 'kirjinsa a waje dan be daure igiyar gaban rigar ba
Tsigar jikinta ta mi'ke da sauri ta mai da idanunta ta rufe tana takure jikinta gabanta kuma na d'an fad'uwa kad'an!
Ya jima kafin taji ya hayo bed din yana jan bargon jikinta......Sai kawai ta sakar mishi bargon dik ya janye ya rufe jikinsa dashi har da kanshi, shuru dakin yay na tsayin minti goma, ta bude idanunta a hankali sai taga dakin yay duhu, alamun ya kashe fitila, ta dan juyo a hankali tana kallonshi taga yanda ya wani takure jikinsa cikin bargo har da rufe kanshi, yau bai bada tazara mai tsayi ba a tsakaninsu, juyawa tayi a hankali ta dan dora hannunta kan babynta dake gabanta tana sauke ajiyar zuciya, Can wayarshi ta soma ringing, firgigit ta mi'ke zaune tana kallonsa ko zai tashi ya dauki wayar, taga ko motsi yaki yi, gashi sai kiran wayar ake.
A hankali tace"Ana kiran wayarka." Shuru yay mata sai da ta sake magana tukkuna yace."Ki dauka ki kashe wayar wannan halin da nake ci yasa na manta ban kashe wayar ba."
Murya a harhard'e yake magana."
Ta dan rankwafa ta jikinsa ta dauki wayar tana dubawa taga Zeey ce.
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar
*07084653262*alliya:
'Yr Bngr Sys
*81*
Wani matsiyacin tsaki taja me karfi ganin sunan Zeey kan screen din wayar, tuni ranta yay wani mugun 'baci taji zuciyarta na wani irin tafarfasa tamkar zata tsaga kirjinta ta fito waje haka takeji, hannunta na karkarwa ta datse kiran tana kara jan wani tsaki!! idanunta har sun kada sunyi jawur ranta bai ta'ba 'baci ba irin yau! Wai me matar nan take nufi ne? Jin tana ta jan tsaki ya sanya ya bud'e fuskarshi yana kallonta,tana rike da wayar tashi a hannunta sai dubawa takeyi.
Shuru yay mata dan shima jikinshi ya bashi Zeey din ce dama dai-dai wannan lokacin take kiran wayarsa shi abin ma mamaki yake bashi sam bata da zuciya ko kadan yana jin ko aure zaiyi ba zai aureta ba dan shi yafi son ya auri mace wacce tasan ciwon kanta ba me bibiyar maza da kanta ba.
Zeey Sarkin 'yan naci aikuwa sai ta sake kira second guda bata 'kara ba ta d'aga wayar a fusace! murya a sama tace"Ke! mahaukaciya idan kina cin 'kasa to ki kiyayi ta shuri wallahi! saboda rashin kamun kai da iskanci da wulakanci zaki dinga kiran waya duk daran duniya kina damun mutane? wallahi to duk sanda kika sake kiran me wayar nan sai nazo har inda kike naci miki uwa! ni *Wasilatu 'Yar gaske!* na wuce da tunaninki bana d'aukar rainin hankali! idan auranki zaiyi yaje ya aureki ban hanaba amma kada ki kuskura na sake ganin kin kirashi a waya lokacin da yake cikin gidanshi, duk sanda kika kuskura kika sake kiran wayarsa a dai-dai wannan lokacin sai na dauki tsatstsauran mataki a kanki wallahi."! A fusace! take maganar tana wani irin huci jikinta na kyarma tamkar wacce tasha tsumin 'yan bori sai faman hura hanci take.......Mi'kewa yay zaune da sauri yana 'kokarin fizge wayarsa, ta mike da sauri ta bar gurin tana cigaba da sauraran maganar da Zeey ke mata."
"Ke har wata abace da zaki ce zaki dauki mataki akaina to mu zuba ni dake shege kafasa aure kuma nida governor kamar anyi an gama sai dai ki mutu dan babban mutum mai 'kima da mu'kami gami da mutunci bai cancanci! ya zama miji a gareki ba." A fusace! tace"Da Uwarki ya cancanta."! Zeey ta mike zaune da sauri tana mamaki! kafin ma ta dawo daga cikin mamakinta taji muryar Wasila na fad'in "Nace da Uwarki ya cancanta!? Shegiya dabba! wacce ta rasa mashinshini! tana bin mazan mutane a waje, zan nuna miki isa da mu'kamina a gurin shi wanda kike ganin ban isa na zama mata gareshi ba, zakiji da kyau wallahi zai za'ba a tsakaninmu ni ko ke! shashasha! mahaukaciya kawai."! Tana karashe maganarta ta kashe wayar tare da fashewa da wani irin kukan ba'kin ciki da takaici.
Ya jima kanshi a 'kasa ransa yayi masifar 'baci! ashe dama yarinyar nan ba tayi hankali ba wannan ai shashanci da rashin hankali da zata tsaya tana gundume gudunmen ashar da wata ransa ya sake 'baci sosai da abinda tayi dan duk a ganinsa laifin ba na kowa bane nata ne tunda be ce ta daga waya ba cewa yay ta kashe masa waya.......A d'an kausashe yace." Kiyi min shuru kada ki tasar min da yarinya daga bacci."! Cikin 'kuluwa da tsabar bakin ciki ta kalleshi, tace"Sai me! idan ta tashi ai laifin ba na kowa bane naka ne ni wallahi tallahi nagaji nagaji! ana cutata kuma ace ba zanyi magana ba kawai ka za'ba ni ko wannan 'yar iskar mahaukaciyar matar dake kiranka a waya."
Cikin tsananin bacin rai yace."Ranki zaiyi mutukar 'baci idan kika sake yi min irin wannan maganar kece zaki tsara min abinda nayi niyya idan nace Zeey na za'ba me Za kiyi.!?
Aikuwa sai ta fusata sosai idanunta ya rufe shaf ta manta waye a gabanta ta dinga zazzaga masa rashin kunya da fad'in "To same? dan ka za'bi Zeey ka ajiyeni dama ai hausawa suna cewa duk wanda yaci moriyar ganga zai yada koranta dama ai nasan tuntuni bani kake so abinda ke jikina kake so, dan haka ko sakina ma kayi ni bazan damu ba dan nasan Allah yayi min baiwar da in na rabu da kai in auri wanda yafi ka komai da komai na rayuwa sai me? dama dole akayi min me zanyi da tsoho! (me saisayayyan kai Inji *Nafeest* Lol🤭) ta cigaba da cewa " ai dama kai d'in kwata kwata ba'asan aurena bane dama da Zeey din kafi dacewa." Kallonta yake wani irin gumi na tsiyaya a jikinsa, tunda yake ba'a ta'ba ci masa fuska irin y
au ba, wannan yarinyar shi takewa rashin mutunci da d'ibar albarka? wai shin ma duk me ya jawo hakane? tambayar kansa da kansa yake da yaga bashi da amsa ga wani irin ciwo da kansa ke masa sai kawai ya mike zai fita daga d'akin! tayi gaggawar tarar gabanta tana kuka da fad'in "Sai ka sakeni tunda kace ka za'bi Zeey dani wallahi na gama zama da kai dama baka cancanta dani ba."! Cikin wani irin yanayi na tsananin damuwa da rud'ani! ya kifa mata mariku masu tsakanin shiga jiki, ta zube akasan dakin tana rirrike kafafunshi ihu! take sosai wanda ya tashi su Hajja daga bacci duk sukayo waje cikin tsananin tashin hankali da damuwa.
Kafarsa yake janyewa tana sake ri'kewa duk tabi ta cikwiye masa a jikinsa
Ga wani irin jiri da ciwon kai na nema su zautar dashi.
Hajja ta dinga buga kofar d'akin tana fad'in " Innalilhi wa'ina ilaihi raji'un jama'a meke faruwa ne? Amadu Wasila ku bude kofar mana komai yayi tsanani maganinsa Allah."
Jin muryar Hajja ya sanya Wasila tayi zumbur ta mike tsaye, saboda yanayin kwarin jikinsa har sai da ta tureshi ta bude kofa a guje ta fita daga dakin ta rungume Hajja tana wani irin kuka da shashsheka! "Hajja! nagaji da wannan zaman nagaji kullum sai ya dokeni ya sani kuka kullum cikin 'kuntata min yake baya kulani baya sakar min fuska nayi masa lefi na bashi hakuri yaki hakura, kullum sai muna kwance budurwa zata kirashi a waya suyi ta hira kuma a gabana bashi da lokacina ko magana nake masa baya saurarata, yanzu da bakinsa yace" Ya za'bi budurwarsa a kaina, dama nasan haka zata iya faruwa tunda dani da iyayena duk be dauke mu da mahimanci ba sabida muna talakawa, dama budurwarsa tace ni bancancani da na zama matarsa ba dan haka ni kawai ya sauwa'ke min na huta da wannan zaman."!
Hajja tace"Subahanallahi Wasila daina irin wad'an nan maganganun sam basu dace ba, kiyi hakuri kinji ko ansan ba'a kyauta miki ba amma komai a sannu ake binsa dama ni tuntuni na fuskanci matsala a tartare daku dama kuma naso in zauna daku din gobe idan Allah ya kaimu kiyi hakuri kinji ko duk da kince anyi miki laifi amma ina so kiyi hakuri dan duk wacce kika gani a gidan mijinta hakuri takeyi, maganar saki ki daina yi tunda har Allah yasa kun fara haihuwa ke dashi ai babu maganar rabuwa shi kuma aure lokaci gareshi idan Allah ya 'kaddara mijinki zai 'kara wani auran babu wanda ya isa ya hanashi abinda kikeyi bai dace ba kin san bashi da lafiya amma a maimakon ki kwantar masa da hankali sai kuma tashin hankali haba Wasila." Hajja ta kare maganarta cikin damuwa da kuma tausasa harshe.
Wani irin bala'in shaushin matar ya turnu'keta! hakan da tayi yana nuna mata cewar tana goyan bayansa kenan! A fusace! ta shige dakinta ta bugo kofar dakin da karfi!!!!! Hajja da rashida suka bita da kallo cikin mamaki, dama Amadu shi tuntuni ya shigewarsa dakinshi tsabar takaici bai tsaya ya saurari sharrin da take shirya masa gurin Hajja ba abinda bata sani ba kuwa Hajja ko kad'an bata son abinda zai 'bata masa rai!
Wannan abinda tayi yay masifar 'batawa Rashida rai! bata ta'ba yin turrr! da halin 'yar uwartata ba sai yau, kamar ta fashe da kuka tace" Dan Allah Hajja kiyi hakuri."! Hajja tayi murmushi a hankali tace"Ai babu komai Rashida Wasila na cikin 'bacin rai a yanzu komai zata iyayi kishi ne ke damunta."
Rashida ta girgiza kanta rai a 'bace! tace"To Hajja kishi hauka ne ni wallahi banji dad'in abinda takeyi ba."
Hajja tayi hanyar daki tana fad'in" Rashida kenan wani idan kishinsa ya tashi mancewa yake da komai da kowa kada ki damu nayi mata uziri."
Rashida ta girgiza kanta ta nufi dakin Wasilan.....Zaune ta tarar da ita had'a tagumi! hannu bibbiyu tana zubda hawaye duk ta wani firgice!.
Rashida tace"Yanzu anti Wasila wannan abin da kikayi shine dai-dai? nifa dole na fada miki gaskiya saboda in kika kashe wannan auran ba kanki kawai kika cutar ba har damu! Ashe har kin manta da al'kawarin da kika d'aukawar su Mai allo, shin wai me mutumin nan yake miki? meye bai miki ba na jin dadin rayuwa? ina ruwanki da auransa! ya auri mata dubu mana kin san dai ba zaki ta'ba hana abinda Allah ya halasta ba, to duk wannan tashin hankalin da damuwa
r da kikeyi na banza ne wallahi, wai har Hajja zaki zum'burawa baki ki buga mata kofa kawai saboda tana fad'a miki gaskiya meye laifinta dan tace ki bawa mijinki hakuri tana jin tsoro kada ki kwana cikin fushin Ubangiji duk macan da take furta kalmar saki ga mijinta Allah na fushi da ita! ni wallahi anti Wasila wani lokacin idan kina wani abun har mamaki kike bani."
Murya na rawa rashida ta karashe maganar.
Maganganun ne suka sanya ta dawo hayyacinta nutsuwa ta shigeta sai ta dinga tunanin abubuwan da suka faru ita dashi a baya, gabanta ya buga da mugun karfi! kada fa yayi zuciya ya kara sakina irin na baya! abinda ta ayyana kenan cikin ranta..... Ta goge hawayen fuskarta tana kallon babynta dake bacci, Rashin kunyar da tayi masa ta tuna, jikina yay sanyi duk taji tsoro ya shigeta tasan halinshi baya barin takwana idan anyi misho sai ya rama kuma ta lura ranshi ya baci sosai, tsoranta Allah tsoranta Annabi kada ya saketa da jego! gashi ta daukarwa su Mai allo alkawarin zama dashi har abada.
Ta kalli rashida jiki duk a sanyaye tace"Rashida Wallahi raina ne ya 'baci shiyasa kuma nasan ko ke akewa irin haka ba zakiji dad'i ba, amma nima nagane ban kyautaba."
Rashida tace"Nifa a ganina duk wannan abinda ke faruwa tsakaninku rashin bashi kulawa ne da tun farko da ya nemi agajinki kina agaza masa kina rarrashinsa da lallabashi da biya masa bukatunsa to da duk haka bata faru ba, wallahi laifin ba na kowa bane naki ne."!
Murya na rawa tace"Rashida kema laifina kike gani ko."? Rashida tace" Wallahi laifinki ne kan me yasa ba zaki kwantarwa da mijinki hankali ba tunda dai kin san baida hakuri ta wannan 'bangaran."
Hawaye ta goge murya na rawa tace"Kina so na mi'ka masa jikinta ya lalatani."
Rashida tace"Nifa ba haka nace ba, kiyi masa dabaru ma ki biya masa bukata, kuma ni banga wani abu ba banda kin sanyawa ranki kinje asibiti an tabbatar miki da cewar gurin nan ya warke to kuma zaman me kikeyi ki bawa me hakki hakkinsa kawai kin tsaya wani abu wallahi kece mai babban laifi."
Wasila tayi shuru tana sauraran 'kanwartata, tace"Naji shikkenan jeki dan Allah ni nagaji da wannan maganar na hakura idan na mika masa jikina ya fatattakani ya watsar dani shikkenan tunda haka kuke bukata." Rashida ta juya ta fita daga dakin ranta a 'bace!
Wasila ta jima zaune tana sa'ke-sa'ke yanda za'ayi ta gyara kwa'bar da tayi dan jikinta yay bala'in mutuwa sosai tana jin tsoro kada gari ya waye ya shigo mata da takardar saki irin na farko........Jikinta a sanyaye ta dauki babynta ta nufi dakin nashi......A hankali ta tura kofar dakin ta shiga ta mai da kofa ta rufe, da haske kadan a dakin shima na karamar wayarshi ne ya kunna.
Yana kwance cikin bargo zazzabin gaske ne ya rufeshi a d'azu dai zazzabi 'karya ya 'kir'kirarwa kansa amma yanzu tsabar tension d'in Wasila ya zuba masa zazzabi me zafin gaske.
Jin zamanta kusa dashi ya sanya ya bude idanunsa da sukayi masa bala'in nauyi sunyi jawur yana haska fuskarta da hasken wayarshi
Marairaice fuska takeyi tana kalato hawaye.....Ya 'bara rai mutuka yace"Tashi ki fitar min a d'aki."
Hannunsa ta ri'ke murya na rawa jiki na rawa tace"Kayi hakuri."!!!!! Ya janye hannunsa yace."Kin shigo nan ma ki zageni ke ga mara kunya ko."? Girgiza kanta tayi tace"Ba haka bane wallahi nayi kuskure raina ne ya 'baci! dan Allah kayi hakuri bazan sake ba."
Yace." Zaki hanani aure ne."? Shuru tayi gabanta na fad'uwa.
Ya sake maimaita magabarshi, girgiza kanta tayi alamun a'a hawaye na sauka a kumatunta, yace."To cewa nayi ki d'aga waya ta ko kuma cewa nayi ki kashe."?
"Cewa kayi na kashe." Yace." To me yasa kika d'aga min waya."? ''Babu komai." tafada tana dan matse hannunta da nashi dake game! Yace."Zeey ba sa'arki bace ta girmeki nesa ba kusa ba kuma da zan aureta da tun kafin na aureki na aureta bana son rashin arziki da rashin mutunci wallahi duk sanda wani ko wata ya sake kirana a waya kika d'auka kika zageshi sai na sa'ba miki kuma idan kikayi wasa sai nayi aure domin nagaji da wannan rashin hankalin naki."
Hannunsa ta rungume a kirjinta tana shashshe'kar kuka tace"Dan Allah kayi hakuri na daina kada kayi min kishiya
Allah bazan iya had'aka da ko wace mace ba ina sonka ina kishinka duk sanda naga kuna waya da Zeey ji nake kamar na mutu saboda bakin ciki da takaici."
Yace."Kina yi min irin wannan d'abi'un zan zauna dake ke kad'ai ki sanja hali idan kina bukatar hakan." Tana sake matsowa jikinsa sosai tace"Na daina wallahi Yanzu kome kake bukata zanyi maka dama dan dai na haihu ne amma yanzu idan ka shirya nima a shirye nake.........Ya watsa mata wani irin kallo yace."Ban shirya ba tukkuna kije ki huta ba yanzu ba." Sai ta sake rungume hannunsa sosai a kirjinta tana marairace masa fuska.......
_Namiji tamkar yaro 'karami yake duk ta inda kika tafiyar dashi zai tafi kuma ba zaki sha wuya dashi ba Namiji ba'ayi masa kutse! ba'ayi masa dole ba'a nuna masa iko idan kikace zakiyiwa mijinki wad'annan da'bi'un zakiyi masifar shan wahala.........Wasila itace babbar mai laifi dangane da wannan rikicin da sukeyi Team din Wasila Afuwa Amadu nada masifar sau'kin kai kuma yana son Wasila ni banga laifinsa ba idan ma yana da laifi bai ka nata ba, yanzu gashi lokaci 'kankani ta shawo kansa duk da rashin mutuncin da take masa amma tasirin son da yake mata ya hanashi daukar mataki a kanta ko yayi niyya ma baya iyawa saboda yana sonta dan haka Wasila kiyi kokarin ganin kin rike mijinki da kyau idan ba haka ba na kawo mishi santaleliyar mace wacce tafi ki komai da komai da kike ta'kama dashi🤭🤭_
Littafin na kudi ne....!
Kika futar min da book keda Allah kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar
*07084653262*alliya:
'Yr Bngr Sys
*82*
Yace."Me yasa a sanda na nema baki bani ba sai yanzu da naji kwata-kwata bana sha'awa, kawai kije ki kwanta duk sanda na keso zanyi miki magana." Taji kamar ya da'ba mata wu'ka a ma'koshi yau itace ke masa tayin yin sex da ita yana kaucewa lallai yayi fushi da ita sosai! Jikinta a sanyaye ta saki hannunsa ta juya masa baya tana goge hawaye, Shima juya bayansa yay saboda baya so ya tsananta gurin kallonta domin kada ta rinjayeshi dan ya lura da rigar baccin dake jikinta me futar da tsaraici ce yana so ya tabbatar da shin da gaske tuban da tayi na gaskiya ne ko na karya dan ya daina yi mata rawar jiki ballanta ta cigaba da raina masa hankali.
Ganin ya juya mata baya yana jan bargon jikinsa ya sake sanyawa jikinta yin sanyi ta juyo tana kallonshi, wata zuciyar na bata shawara kawai tayi tafiyarta yayin da wata zuciyar ke cewa ki zauna dai ki cigaba da rarrashinsa kada kiyi fushi dashi.
Sai ta dauke baby zahra dake kwance a gefensu ta kwantar da ita a gadonta tayi mata addua a hankali ta dawo gadon ta kwanta kusa dashi tana nani'karsa, cikin bargon ta shiga ta zura hannunta ta rungumeshi sosai a jikinta tana sauke ajiyar zuciya,
Shima ajiyar zuciyar ya sauke yana dan sake takure jikinsa tsigar jikinsa na mikewa a hankali ya tura le'banshi na kasa a bakinshi yana dan cizawa shi kadai yasan abinda ke damunsa
Hannunta ta