SO MAHADIN RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVELS PDF BY BILKISU Z YAU.txt

Author :  Bilkisu Z Ya'u Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   24 / 31

69K to 72K   out of 90.7K words

"lallai Abba duniyar nan cike take da abubuwan ban tsoro, in har baka mutu ba zakai ta jin abubuwa kala-kala, amma Allah baya bacci gashi nan be tab'ar dakai ba saboda kyawun zuciyarka, kuma shi kawu Sunusi da sannu zai girbi abinda ya shuka."



Abba yace "a'a na yafe mishi fatana Allah yasa ya shiryu kafin Allah ya d'auki ranshi," Amir yace "Abba kai wane irin mutum ne?" Abba yace "me kwad'ayin samun aljanna."



Amir yace "Abba ka shirya kai da Umma muje gidan su Amira taga iyayena," Abba yace "to my son yanda kace haka za'ai," ko da isarsu gidan suka tarar da gidan a gar'kame da suka tambaya aka tabbatar musu cewa masu gidan sun tashi gaba d'aya.



_Topha tashin hankali wanda ba'a sa mishi rana_







Muje zuwa







*πŸ…±K CEπŸ˜˜πŸ’‹*
πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜









RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (πŸ…±K)*
```(Autar marubuta)```





SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```





*πŸ‡ΈπŸ‡¦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```πŸ€œπŸ€›





*MAMAN LABYB*
(Mamie nah)
*Kina raina a koda yaushe, tuni kika she'ke zuciyata da 'kaunarki ke ta daban ce, halin kirkinki ma daban ne, ina 'kaunarki 'kauna ta gaske kuma ta har abada, matsayinki ya zarce hakan gunaπŸ˜πŸ˜˜πŸ’‹*






*~MOMYN KADEEJA*πŸ§•
*Momyn kadeeja albarkacin 'kaunar da kike gwada min tare da d'umbin kulawarki kan littafin nan, na baki wannan page d'in kyauta kiyi yanda kikaga dama dashi, in kikace ba me karantawa ma sai ke kad'ai ta zauna,πŸ˜‚ ina godiya sosai da comment d'inku ina jin farin ciki sosai wlh akai.πŸ™πŸ˜πŸ˜˜πŸ’‹*






*Idan so yai so ko masoya na nesa da juna zuciyoyinsu na raya musu abu guda game da juna, ikon Allah kenan😍 yanayin 'karfin so a cikin zuciyar masoyan gaske kenan😍😍😍😍😍*






PAGE 175 to 180





Amir ya fad'i nan 'kofar gidan yaita rusa kuka kamar 'karamin yaro, sai a yau yake ganin wautarshi da kuma rashin kyautawarsa akan share lamarin Amira da yayi, cikin sauri ya d'ago ya kalli mahaifinshi tare da ri'ke mishi hannu yace "Abba wai sun tashi aketa ce mana fa, ina suka kai min matata to? Abba ka taimakeni a nemo inda suke, wallahi Abba in babu Amira bazan iya cigaba da rayuwa ba.



Jiri Amir ya fara ji, ya dafe kanshi da hannu bibbiyu, ya tafi taga taga zai fad'i Abbanshi yai sauri ya rungumeshi, yaita jijjigashi amma ina ya sume, cikin sauri securirty's d'insu suka kamashi aka sa a mota suka shiga sai asibiti.



Haka Amir yaita faman jinya ya mugun sawa kanshi damuwa, a koda yaushe yanzu bashi da wajen zuwa sai unguwar su Amira, ya samu 'kofar gidansu yaita rusa kuka, kullum aikinshi kenan, iyayenshi har sun saba duk in suka ga basu ganshi ba to nan suke nufowa, kuma suna zuwa zasu ganshi.



Babu inda bai je neman Amira ba amma babu ita ba labarinta, kullum cikin tunani yake duk yabi ya fige, iyayenshi duk sun rasa gane kanshi, saida ya zagaye dukkanin station d'in garin ya bada hotunanta ga duk wanda ya ganta ko yaji labarinta, amma har yau ba bayani.



Sunyi yawon shi da security's masu yawan gaske amma shiru kake ji ba wani bayani a kanta.



Bayan kwana biyu, Amir ne kwance kan jikin Ummanshi tana shafa kanshi tare da rarrashinsa kan ya rage sa damuwa a cikin ransa gashi nan sanadinta ya kamu da hawan jini kar ya zama silar kamuwarshi da ciwon zuciya.



Suna cikin magana sai ga Abba ya shigo, 'karasowa yai inda suke ya kalli Khadija yace "Sannunku da gida My Love, My Son ya kake, ya jikin naka?"



Gaba d'ayansu suka had'a baki wajen yi mishi sannu da zuwa, ya amsa musu sannan yace "na sameku lafiya?" suka sake had'a baki wajen fad'in "lafiya lau."



Zama Abba yai kusa da matarshi, sannan ya dafa Amir dake kwance kan jikinta, yace "Amir ji yanda ka rame ka lalace, haba Amir, da damuwa da sawa rai suna maganin kowace irin damuwa da tuni sunyi mana tamu maganin damuwar, amma a maimakon haka sai muka ri'ki takobi na gaske wato addu'a makamin mumini, wannan addu'ar da muka ri'ka itace tasa Allah ya dubemu da idon rahma yaji tausayinmu ya bayyana mana kai, saboda haka ka dage da addu'a muma muna tayaka, tunda ba mutuwa tayi ba menene na damun kanka za'a gansu insha Allah."



Amir ya share hawayen dake kwararowa daga cikin idanunshi, sannan ya kalli mahaifinshi yace "Abba Amira ta zama jigo na dukkanin rayuwata, zan jure komai amma akan Amira ban yin baya, Abba wallahi na sani Amira tana cikin damuwar rashina fiye da wadda nake ciki a yanzu, abinda ke sakani kuka kenan idan na tuno Abba bana son damuwarta ko kad'an, wallahi tunda naji zuciyata na zafi itama ta-ta tana can tana mata zafi," yana kai nan a zancenshi ya sake fashewa da kuka.



Abba da Umma sun tausayawa yaronsu matu'ka, domin bai b'oye musu komai ba cikin labarin rayuwarsu da Amira, kuma duk wanda yaji labarinsu dole sai ya tausaya musamman ma Amir wanda ya rayu cikin mawuyaciyar rayuwa.



Nan dai suka 'kara bashi baki, da 'kyar suka samu yai shiru, suna cikin hira shi dai bai saka musu baki, da haka ma bacci ya d'aukeshi.


………………………………

B'angaren su Amira kuwa har yanzu ta kasa dawowa asalin Amirarta, sannan koda yaushe Nura cikin sintirin zuwa wajenta yake, kan dole take sauraronshi shima dan yana mata zancen Amir ne, amma sam bata 'kaunar a dameta yanzu, a hankali tun tana gundura dashi har sabo ya shiga tsakaninsu, dama kowa ya sani cewa muddin mutum yana yi maka zancen wanda kake 'kauna akoda yaushe kuma yana yabawa masoyin nan naka zakaji zuciyarka ta sha'ku dashi, to haka ce ta faru da Amira.



Zaune Amira take gaban Dad d'inta shigowarta kenan falon Dad d'in nata wanda ya kirata a waya yace tazo yana son magana da ita.



Koda ta shiga ta tarar harda Mum d'inta a falon, gefe ta samu ta rakub'e kamar wata marainiya, sannan tace "Dad gani," Dad ya kalleta yace "Doughter abinda yasa nai kiranki shine Nura ya tabbatar min da yana 'kaunarki, mahaifinsa kuma yazo neman aurenki wajena dan hak.........." be kai ga 'karasawa ba Amira ta mi'ke tsaye cike da matsanancin b'acin rai had'e da razana, sannan ta kalli Dad d'inta tace "Dad Nura fa kace!!! to wallahi ban tab'a 'kaunar Nura ba a cikin raina, kuma har abada bazan 'kaunaceshi ba, wai ma Dad ba akan talaucin Amir ka 'kishi ba kuma ka tsaneshi, but why kake so yanzu in auri talaka wanda ubanshi ke aiki a 'kar'kashinka? gaskiya bana 'kaunarshi, kuma ko zanyi aure a nan gaba bazan tab'a auren talaka ba sai irin wanda kakeso mu gani zasu iya ri'ke maka ni kamar yanda Amir talaka bawan Allah ya ri'keni ko kuwa."



Dad yace "naji Nura talaka ne shi amma ai yana da asali ko, to shikenan in har baki amince da Nura ba to ki zauna da shirin cewa cikin satin nan zan kawo miki duk wanda naga dama."



Amira tai murmushin takaici sannan tace "Dad wallahi ka sauya gaba d'aya, amma ba komai, ni bazan 'ki yi maka biyayya ba akan koma waye zaka had'ani dashi, saboda ba auren so zanyi ba, duk wata so da 'kauna mutum d'aya tak zan iya ba mawa su, kuma na rasashi, to wallahi ba na biyunshi a zuciyata, zanyi maku biyayya kan duk wanda zaku had'ani aure dashi Dad," tana kai nan a zancenta ta fita daga d'akin a guje tana kuka lambun gidan taje ta zauna kan kujera tare da had'a kai da guiwa, ta cigaba da kukanta.



kanta na du'ke tana cikin kukan ne taga alamun mutum a kanta, tana d'agowa taga Nura ne, maida kanta tayi tare da cigaba da kukanta.



Nura ya du'ka kusa da ita yana rarrashinta tare da yi mata magiya kan ta sanar dashi abinda ke faruwa, Amira ta d'ago tace "Nura idan kana tunanin sabon da mukai da kai akwai d'igon 'kaunarka a raina to wallahi ka daina, bana 'kaunarka gwara ma ka janye wannan maganar, Nura ya numfasa yace "yanzu akan wannan kike kuka, ni banma san anyi zancen ba, tabbas ina 'kaunarki kuma na fad'awa mahaifina amma sam bance yazo yai maganar a gidanku ba, indai kan wannan ne ki kwantar da hankalinki ki daina kuka maganar ta wuce, Amira ta d'ago kai cikin kuka tace "ina fa ta wuce Dad yace ko kai ko kuma ya zab'a min koma wanene."



Nura ya numfasa cikin sauri dabara ta fad'o mishi a rai, yace "tunda abun ya zama haka me zai hana ki amince ni ki aureni, ni kuma na d'aukar miki al'kawari da zarar mijinki Amir ya dawo gareki wallahi zan sakeki ki aureshi, da wannan shawarar suka amince kuma a tare sukaje Nura ya sanar dasu amincewar Amiran ita kuma Amira ta baiwa Dad d'inta ha'kuri kan abinda ya faru d'azu, amma iyayenta sunsha mamaki kan canjin ra'ayinta lokaci guda, musamman yanda suka ga ta tayar da hankalinta akai musamman ma akan zancen Nura d'in, to koma dai menene su hakan yai musu dad'i, ba tare da b'ata lokaci ba aka sa ranar aure sati uku kacal, a ranar da aka tsaida rana ma Amira taci kuka kamar me, ita in aka barta tunda babu Amir rayuwarta ita kad'ai zata 'karasata.



Abba da Umma kuwa sun yanke hukuncin dawowa kano da zama, tunda dama Amir ya fad'a musu acan yai makaranta, to so suke su koma can ya cigaba da karatunsa ko Allah zai taimakesu ya rage tunanin da yake yi.



Koda suka tuntub'eshi da maganar be yi wata-wata ba ya amince da zancen dama garin ya isheshi tunda ba masoyiyarshi a ciki, amma sai yace wa iyayenshi in suka tafi kuma Amira ta dawo fa? mahaifansa suka ce mishi ai sun rarraba hotonta ga jami'ai, ana ganin sun dawo a ranar za'a basu labari, da haka ya amince suka fara shirin tafiya kano.



A yau talata su Amir dirarsu kenan a garin kano, kuma a yau talatar dai aka shaida d'aurin auren Amira Ahmad Tukur da Nuraddeen.





_'ka'ka-k'ara 'ka'ka ko wannan wainar ya za'a toyeta oho, ina fatan masu karatu basu manta da mahaukacin kishin Amir baπŸ˜‚_









Muje zuwa









*πŸ…±K CEπŸ˜˜πŸ’‹*
πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜









RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (πŸ…±K)*
```(Autar marubuta)```





SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie)```





*πŸ‡ΈπŸ‡¦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)```πŸ€œπŸ€›






PAGE 180 to 185






Daga shigowarsu cikin garin kano suka tabbatar da cewa lallai shagalin biki ake, kuma shagalin ma na 'ya'yan hamshak'an masu kud'i.



Abba ya kalli matarsa yace "da alama cikin garin nan shahararren biki ake kuma k'ayatacce."



Umma tace "gaskiya kam da alamu, haka suka k'arasa inda zasu je suna tafe suna hira ba tare da Amir yace musu ci kanki ba, har suka k'araso gingimemen gidan Abba dake cikin g.r.a a kano.



Ko da su Amir suka dawo garin kano da zama babu abinda ya canza zani daga gareshi, domin kuwa har yanzu bai ga masoyiyarsa ba, kuma bai dena tunanin da yake yi a kanta ba, da shelar nemanta a ko'ina, kuma a kanon ma duk inda yasan sunyi rayuwa tare da Amira can yake zuwa ya zauna yaita kuka, idan ya tashi da safe gidan shi yake zuwa yaita tuno abubuwan da suka wakana tsakaninsa da masoyiyarsa yana kuka tare da surutai kamar zararre, koda yake mai yin soyayya tamkar zararre yake musamman idan tazo maka da k'alubale me zafi irin na Amir da Amira, daga nan kuma idan ya tashi sai ya wuce d'aya gidan Amiran shima yaita kuka, yanzu a can yake wuni sai dare yake komawa gida, abun duk ya damu iyayensa, su sun dawo dashi nan domin ya samu sauk'i ashe zuwansu nan ne ma zai k'ara sakashi cikin wani mawuyacin hali.



Shawara suka yanke akan a sakashi a makaranta amma itama ba wadda sukayi shi da Amira ba.



Koda suka tuntub'i Amir da zancen makaranta sai ya amince kai tsaye, amma ya dage akan cewa shi lallai wadda yake yi ada a nan kanon ita yake so a saka shi, babu yanda suka iya cikin k'ank'anin lokaci aka gama mishi komai ya fara zuwa.


…………………………………

B'angaren Amira kuwa a ranar da aka d'aura aure a ranar suka tare a wani tangamemen gida, wanda Dad ya mallaka wa Amiran shi halak malak.



A daren ranar bayan an kaita kowa ya watse saura shigowar ango sai Amira ta tashi cikin sauri ta gark'ame k'ofa, ta fad'a kan gado tasha kukanta ba me rarrashi, idanunta duk sun kumbura saboda tsabar kukan da take sha a kullum tun ranar da aka saka ranar aurensu har zuwa yau da aka kawota gidanta na aure.



Ko da Nura ya shigo da abokanansa babu kalar magiyar da be yi mata ba akan ta bud'e k'ofar amma tak'i, dole haka abokansa suka juya kowa da abinda yake sak'awa a ransa, Nura yai musu rakiya ya dawo ya ajiye ledar kajinawa da lemuka da ya siyo a gefe, ya kwanta a d'aya daga cikin kujerun dake falo.



Yana daga kwance ya kira mahaifinsa yana fad'a mishi abinda Amira tai mishi yau, daga can d'ayan b'angaren mahaifin Nura yai murmushi, sannan yace "haba Nura, yau fa aka kawota gidan, kuma kasan dai bata sonka, to a hankali ya kamata ka bi da ita har mu samu mu cimma burinmu a kansu ita da mahaifinta, mu yagi rabonmu mu k'ara wuta," sun jima suna hira da mahaifinsa yana k'ara d'ora yaron nasa akan muguwar hanya, daga k'arshe suka yi sallama.



Washe gari Dad d'in Amira ya kira Nura gidansa ya bashi makullin sabuwar mota, sannan ya bashi takardun wani kamfani nashi ya bashi su halak malak, Dad ya d'ora da cewa "wannan ba komai bane akan abubuwan da zanyi maka a gaba muddin ka kulamin da 'yata," Nura yaita godiya sannan suka yi sallam ya fito yaja sabuwar motarshi d'aya daga cikin security kuma ya ja mishi tsohuwar suka taho zuwa gida, a hanya ne ya kira mahaifinsa yake sanar dashi abinda Dad ya bashi yanzu, sai mahaifin Nura yace "kaga abinda nake fad'a maka ko," Nura yace "wallahi Dad na gani, wai harda wani in kula mishi da 'yarshi yanda ya kamata," mahaifin Nura yace "eh yanzu ai kyautata mata da zaka yi shi zaisa mu samu komai cikin sauk'i a wajen mahaifin nata, tunda ka samu sabuwa zanzo ka bani d'ayar taka tunda tawa dama duk ta tsufa, Nura yai dariya yace "to sai kazo ai in komai ya kankama ma har jirgi sai a baka ba mota ba Baba," Baban nashi yace "yauwa na gode Allah da ka fahimci komai yanzu ka dawo kan hanya, ai duk fafutukar nan da kaga inayi duk saboda kai ne Nura na," nikam naci kaji uban wofi sai kace dukiyar da guminsa ya tara ta.



*BAYAN WATA 'DAYA*

Abubuwa da dama sun faru, ciki kuwa har da komawar Amira makaranta, sedai kuma ikon Allah basu tab'a had'uwa da Amir ba, kuma hakan ta faru ne sakamakon canza kos da Amiran tayi, mijinta Nura shi ke kaita ya kuma dawo da ita, duk wata kyautatawa na mata da miji suna yiwa juna musamman ma shi Nuran, amma duk da haka Amira ta kasa barinshi ya kusanceta, a wautarta ganin hakan take kamar cin amana ga Amir, tunda ita har yanzu zuciyarta bata daina bata yana raye ba.



Yau alhamis, shigowar motar su Amira kenan cikin harabar makarantar, a yayin da shima Amir be dad'e da shigowa ba yana daga cikin motarshi a zaune amma k'ofar motar a bud'e take, k'afarsa d'aya tana ciki d'aya kuma tana waje, yana zaune yana abinda ya saba wato tunanin Amira, kamar ance ya d'aga idanunsa kawai sai akan Amira, gani yake kamar gizo take yi mishi kamar yanda ya saba gani, shiyasa ya 'kura mata idanu, can kuma sai ya murza idanunsa ya sake murzawa ita d'in ce dai yau Allah ya gwada mishi zaune cikin mota, tabbas wannan Amirarsa ce, ya fad'i da 'karfi yana maimaitawa cikin farin ciki had'e da zub da hawaye yana cewa "Amira ce, wallahi Amirata ce, ko cikin miliyoyin mutane Amira wallahi zan shiga in zak'uloki, cikin sauri ya yunk'ura da niyyar zuwa wajenta, se dai abinda ya gani ya sakashi tsayawa cak, wani mutum ya gani ya fito daga b'angaren driver ya bud'e mata motar ta fito.



Tana fitowa yaga wannan mutumin yai mata magan ta bashi amsa fuskar nan ta-ta a d'aure ba alamar fara'a, suna tsaye wata yarinya wadda bata fi sa'ar Amiran ba ta tunkaro wajensu tana dariya, bayan ta k'araso suka gaisa yaji tace "Amira saura minti biyar fa a shiga lecture, nima ke na tsaya jira mu shiga tare tunda mukai waya naji kince min gaku nan nake juranki.



Amira ta kalleta tace "muje," Nura ya kalli "wannan yarinyar yace "Anisa ki kulamin da matata da kyau dan Allah," Amira tace "to insha Allah," suka yi sallama da shi ya fad'a cikin motarsa, yai mata key, ya ja ya tafi.



Duk abubuwan nan da suka faru duk a kan idanun Amir ne, kuma yaji duk abinda sukace, ya k'ara tabbatarwa da tabbas Amirarsa ce, amma abinda be gane ba shine waye wannan mutumin, kar dai Amira amanarsa taci ta sake yin wani auren? ganin su Amiran sun juya sun tafi yasa ya fito cikin sauri yana binsu a baya har saida yaga inda suka shiga.



Waje ya samu ya zauna inda duk wanda zai fito daga wajen zai ganshi, amma shi yana d'an nesa da wajen, bayan kamar wajen awa d'aya yaga anata fitowa d'aya bayan d'aya, hakan ya bashi tabbacin cewa lallai sun gama lecture d'in nasu, yana nan zaune can sai gasu sun fito ita dai da wannan yarinyar wadda yaji an kira da Anisa, rakiya yaga taiwa Amiran har wajen parking suna jiran k'arasowar mijin nata, basu dad'e ba kuwa sai gashi ya shigo, cikin sauri

24 / 31