SO MAHADIN RAYUWA COMPLETE HAUSA NOVELS PDF BY BILKISU Z YAU.txt

Author :  Bilkisu Z Ya'u Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   8 / 31

21K to 24K   out of 90.7K words

dad'i idan ina jinka a irin wannan yanayin ko, kodai in juyo in dawo ne nima jina nake kamar mara lafiya Amir ashe haka nisa da masoyi ke haifar da rad'ad'in jiki da na zuciya."



Amir ya katseta ta hanyar fad'in " ki daina fad'in maganar dawowa mana Amira kowa ya ganki yana murna kice kuma zaki juyo, tunda dai kin riga da kin kai lafiya to nagode wa Allah, mu yi hak'uri na d'an lokacin da zaki yi ki dawo, yanzu dai ki shiga gida ki huta Anjima zan sake kiranki," nan suka yi sallama ya ajiye wayar ya fad'a cikin bayi domin yin wanka, ita kuwa Amira tana fitowa daga cikin motar idanun 'yan gidan gaba d'aya yana kanta, ta k'ak'aro fara'a ta k'arasa wajensu, sister d'inta ta fara rungumeta suna murna, sai suka rungume juna da Dad d'inta, sannan yace mata " dawa kike ta waya ne haka my daughter?" Amira tace " Dad wata friend d'ita ce, ta saki Dad d'inta da sauri saboda sanin halinshi na tambayoyi zai iya sake jeho mata wata tambayar taje ta rungume Mum d'inta sannan ta je gaban Uncle kawunta wato mahaifin wadda za'ai bikinta shima ta rungume shi ya shafa kanta tare da sa mata albarka, sannan suka d'unguma dukkansu suka shiga ciki.



Wanka ta fara yi a k'erarren d'akin da yake mallakinta tamkar aljannar duniya, sannan ta shirya suka fito tare da sister d'inta, direct dining table suka wuce aka ci aka sha, daga nan suka dawo babban falo suka zauna ana ta hira, ita dai Amira ba wata walwala sosai banda eh ko a'a bata cewa komai, hankalinta yana wajen tunanin Amir, sisternta ce ta kalleta tace " wai Amira ya naga duk kin canza ne, ina lura dake fa ko abincin kirki baki ci ba," Dad dake jinsu shima yake kallon Amira yace " kin rigani magana ne nima abinda nake so in tambaya kenan, kamar daughter bata farin ciki da ganinmu. "



Amira zata yi magana kenan sai ga kiran Amir, tashi ta yi tace musu zata je ta d'an kwanta a d'aki, bata jira taji me zasu ce mata ba ta haye sama cikin sauri.



Amira ta d'aga kiran shi tare da karawa a kunne ta fad'a gado tace " kamar kasan kai nake tunani, Amir yai murmushi sannan yace "ai zuciyoyin mu had'e suke da juna," sun dad'e suna waya kiran sallah ne kad'ai ke dakatar da su daga jin muryar junansu.



Har aka kira sallar issha'i suka je suka yi sannan suka dawo suka cigaba da dosa wayarsu, suna cikin wayar ne sistern ta ta shigo tana fad'in yau ina kusa dake sister na a d'akin ki zan kwana," Amira ba don ranta yaso ba tai dariyar yak'e tace mata " to kar dai ki cikani da surutunki malama," sister tace " dan ma kin samu, daga yau ne ai gobe ke kad'ai zaki kwana ni ina tare da k'awayena."



Amir yana jinsu dan basu katse wayar ba, Amira tace mishi ya hau WhatsApp su cigaba da magana.



Nan da nan suka bud'e datan su, suka cigaba da magana a yayin da sister d'inta ta gaji da surutunta Amira bata kulata sai ta hak'ura ta k'yaleta har bacci ya kwasheta.



Su kuma suka cigaba da chat d'insu, Amira tace _"Amir d'ina gaskiya bazan iya cigaba da jure rashinka ba ko abinci fa na kasa ci, har 'yan gida sun gane akwai abinda ke damuna."_



AMIR _"To ko in zo ne?"_



AMIRA _"Amir Dad d'ina nake ji, murd'd'd'en mutum ne, baya so muna kula samari har sai mun kammala karatu, amma kazo tunda shagalin biki ake ba matsala na san yanda zan yi ba wanda zai gane komai."_



AMIR _" na shiga uku! ni yanzu ya zanyi ni da nake so na mallake ki kwanan nan yanzu in aka kasani fa, tunda kince da matsala zuwana to kiyi hak'uri ki bari har ki dawo."_



AMIRA _"gaskiya bazan iya cigaba da hak'urin jure rashinka ba, yini d'aya ma kenan har na rame, ka taho gobe ko kuma wallahi ni na dawo goben."_



AMIR _"to shikenan insha Allah goben ina hanya."_



AMIRA _"to shirya kayanka sai mu cigaba da waya tunda uwar surutu tai bacci, nafi so in cigaba da jin muryarka."_



Suka yi sallama na 'yan mintuna ya had'a kayanshi sannan ya kwanta yana kwanciya ya jawo waya zai kirata sai ga kiran Amiran ya shigo, yai murmushi ganin yanzu damuwarta a kanshi tana nema ma ta zarce tashi, ya d'aga kiran tare da kara wayar a kunne, haka suka kwana basu runtsa ba sai da asuba bayan sun yi sallah sannan ta barshi ya kwanta shima saboda kar bacci ya sace shi ya makara tahowa wajenta.



Washe gari wajen shida dai-dai Amir ya shirya, ya fito tare da kulle ko ina na gidan sannan yaje tasha ya hau mota suka d'auki hanya sai Abuja.



Duk bayan mintuna sai Amira ta kira taji suna dai-dai ina, bayan awanni da suka d'auka suna tafiya suka k'araso tashar Abuja, ya kira Amira tare da shaida mata ya k'araso gashi a tasha, zaune take ana mata lalle sai gani suka yi ta tashi zumbur tare da zuwa ta wanke lallen sannan tai hanyar d'akin Mum d'inta, Amarya na k'wala mata kira tana tambayar ina zata, ita kuwa fad'i take tana zuwa har ta shiga d'akin Mum d'in.



Key d'in motar Mum ta d'auka tana fad'in "Mum bari inje in dawo," bata jira taji me zata ce ba ta fice ta fad'a motar ta figa da gudu sai hanyar tashar Abuja.



Ko da isarta tasha ta hango shi, domin ma kusa da shi ta faka, ta saukar da glas d'in motar tare da yin hon, d'ago kanshi Amir ya yi suka yi ido hud'u da Amira, cikin sauri ya taso ya nufota, itama kasa jurewa tayi ta fito daga motar suka rungume juna suna hawayen farin ciki, kowannensu d'auke da murmushi a fuskar sa, ganin idanun mutane na kansu yasa suka shiga mota suka bar wajen sai hanyar gida.



Suna isowa Amira tai fakin d'in motar ta baya ba tare da ta shigo da ita cikin gidan ba, suka fito suka bi wata b'oyayyar hanya ta baya, suka bud'e wata k'ofa sukaita tafiya har Allah ya sada su da d'akin Amira ba tare da kowa ya gansu ba.



Suna shiga ta maida k'ofar ta rufe tare da sa makulli ta kulle ta ciki, suka zauna sunata hirar yaushe gamo, Amir yace " Amirana har kin rame," Amira tace " wallahi kuwa nesa da kai kamar yin nisa da rabi na jikina ne, kuma kaima ka rame amma baka kaini rama ba."



Dakatar da surutun ta yi ta hanyar mik'ewa tace mishi tana zuwa, ta fita taje ta d'auko musu abinci suka ci, suna ci suna hira.



Haka suka kasance a cikin gidan da dare ne kad'ai yake b'oyewa ya kwana a d'akinta tana k'asa yana saman gado, da rana kuwa shiga yake cikin 'yan biki ayi hidima da shi, amma yawanci ma sunfi tafiya bayan gidan su su zauna sui ta hira har abinci a nan suke ci komai a nan suke yi, aita nemanta in buk'atar hakan ta taso bata nan, se dai in sun dawo ta gilla musu k'arya, kullum a can suke wuni in sun tashi su bi ta k'ofar baya su shige d'aki, kuma Allah ya taimake su har yau babu wanda ya gane abinda ke faruwa.



Yau Alhamis, tashin Amira kenan daga bacci agogon d'akin ta kalla k'arfe tara na safe, zaro idanu tayi sannan ta kai dubanta kan gado wayam Amir baya nan, ta je bakin k'ofar bayi ta k'wank'wasa shima shiru, ta bud'e ba Amir a ciki, ta shiga kicin ta duba nan ma wayam baya ciki, hankalin Amira fa ya fara tashi, ta fito daga cikin d'akin ta bi ta baya ta dudduba duk inda suke zama duk babu alamun shi, hankalin Amira fa ya kai k'ololuwar tashi, kuka ta fashe dashi tana tunanin ina Amir ya tafi gashi ba wanda ya sani a garin, komawa cikin d'akinta ta yi ta d'akko mayafi ta yafa tare da zarar makullin motar Mum da ta gaje mata take hawa tunda ta dawo, ta fito ta babban falo sam ta kasa natsuwa, ta fito tana hawaye, tazo ta wuce ta gaban su Dad duk suna zaune a falo zata fita Dad ya k'wala mata kira, yace " ina zakije?" ina harga Allah bata ji shi ba hankalinta yai gaba, ta fad'a mota taja ta tafi, haka taita bi lungu da sak'o na unguwar tana dubawa ko Allah zaisa ta ganshi amma ina, maida motar gida ta yi ganin wasu guraren ba damar kutsawa da mota, ta sake fitowa a k'asa, duk ta fita hayyacinta kuka sosai take yi tana cikin tafiya sai ta hango shi zaune a wurin da bazata tab'a mantawa da shi ba har abada domin kusa da gidansu ne wurin ta can baya inda wani dad'ad'd'en gidan marayu ke wurin, lokacin tana yarinya nan ne wajen zaman su, har Amira ta k'ara so wajen bai san da ita ba, sai da ta dafa kafad'arsa tare da jijjigashi sannan ya dawo daga duniyar tunanin da ya lula.



Kallonta ya yi tare da yi mata murmushi, zama Amira ta yi kusa da shi tare da rungume shi ta fashe da kuka sannan tace " meyasa ka fito ba tare da na sani ba, yanzu da wani abu ya same ka fa, Amir d'ina bazan tab'a iya jure rayuwar da babu kai a cikinta ba, dan Allah karki barni, kuma karka sake yin nesa da ni."



Amir ya d'ago ta tare da share mata hawayen idanunta, idanunta duk sun kumbura ya kalleta yace " wa ya fad'a miki zamu rabu, insha Allah na kusa mallakarki ma a matsayin matar aurena da zarar kin gama karatunki, kuma abinda yasa na fito saboda naga kina bacci ne, kuma ban yi tunanin zaki tashi da wuri haka ba saboda nasan jiya mun dad'e muna hira bamu kwanta da wuri ba shiyasa, amma kiyi hak'uri tuba nake bazan k'ara ba," ya k'arashe maganarsa tare da rik'e kunne.



Rarrashin Amira ya yi, sannan suka tashi suka juyo da niyyar komawa gida suka ga Dad da su Mum tsaye a kansu suna musu wani irin kallo, Dad ya kalli Amira cikin d'aga murya yace "ke Amira waye wannan," ya k'arashe maganarsa tare da nuna Amir da hannu, ba Amir da Amira ba hatta ni Bk sai da na razana da ganin iyayen Amira a wajen, hakan yasa na yarda komai nawa na runtuma a guje sai gidan su Bloodynah kai tsaye bayi na shige na fara zawayi na fargaba.










_shin ya zata kasance? ku biyoni muje_












*πŸ…±K CEπŸ˜˜πŸ’‹*
πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜
*SO MAHA'DIN RAYUWA!*
πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜πŸ’˜





RUBUTAWA
*BILKISU Z. YA'U (πŸ…±K)*
```(Autar marubuta)```





SADAUKARWA GA:
*MAMAN LABYB*
```(Mamie) ```







*πŸ‡ΈπŸ‡¦ZAMAN AMANA WRITER'S*
```(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah) ```πŸ€œπŸ€›






*SANARWA!!!πŸ—£ ina makaranta litattafan Hausa? to ku saurara da kyau kuji,πŸ‘‚ shahararriyar marubuciyar littafin SHARRIN ASHQEEY mai suna RUKAYYAT BINT DAWUD (QUEEN RUKEEY) ta sake gangamo muku gingimemen labarinta mai suna JARRABAWAR RAYUWA, kar ku sake kuyi sakaci a barku a baya, sunan littafin JARRABAWAR RAYUWAAAA*







*Wallahi ina matukar jin dad'in comment d'inku, ina yinku fiye da duk wani tunani naku, Allah ya barmin ku masoyana😍😘*






*TABBAS SO MAHA'DI NE NA RAYUWA, DOMIN YAKAN ZAMA SILAR GYARA RAYUWAR WASU, A YAYIN DA YAKE ZAMA SILAR GURB'ATA NA WASU, SO TSANI NE NA TUSHEN GINA KYAKKYAWAR RAYUWA IN KA YI DACE DA MASOYI NA K'WARAI, SO YANA ZAMA NASARA GA RAYUWAR WASU A YAYIN DA YAKE ZAMA FA'DUWA KO KOMA BAYA GA RAYUWAR WASU SO YAKAN KASHE WASU RAYUKAN, A YAYIN DA YAKE BAWA WASU DAMAR CIGABA DA RAYUWA, SO RAYUWA CE, AMMA WASU LOKUTAN MUTUWA CE, DUK WANDA YA K'ULLA SO A RAI TO TABBAS YA K'ULLA HARDA ABU BIYU WATO FARIN CIKI DA BAK'IN CIKI, SANNAN LOKUTA DA DAMA KUMA MAFI YAWANCI SOYAYYA TAKAN MAKANTAR DA MASOYA TA YANDA BASA GANE DAI-DAI DA RASHINSA, IDAN KAI DACEN SO NA GASKIYA TO TABBAS RAYUWA NA D'OREWA CIKIN FARIN CIKI DA WALWALA BAYAN JURE DUKKANIN WANI RU'DANI.*








PAGE 60 to 65






Zuru-zuru suka yi dukkanin su, a yayin da Amira ta fara inda-inda, sai Dad ya sake yi mata tsawa tare da tambayarta waye wannan, Amira ta dake domin kar mahaifinta ya gane akwai wani abu da take b'oye mishi, ta kalli Dad tana d'an murmushi tace " Dad abokin karatuna ne wannan, duk k'ok'arin da nake yi kusan shine sanadi saboda yana taimaka min sosai a karatuna, kuma yazo mana biki ne zuwanshi ma kenan."



Dad jin an sako karatu a ciki sai ya sassauta fushinsa don shi mai son yaga yaranshi na maida hankali ga karatu ne sosai, amma duk da haka be gama yarda da maganarta ba saboda sunga lokacin da ta wuce tana hawaye.



Dad yace " ku biyoni muje gida," daga haka be sake cewa komai ba suka juya suka tafi, suma su Amira suka bisu a baya har suka iso har cikin babban falo inda kowa ya samu waje ya zauna.



Amir yabi kowanne daga cikin 'yan gidan ya gaishe su, sannan Dad ya cewa d'aya daga cikin yaran gidan su kaishi d'akin bak'i ya huta, Amir ya bi bayansa suka fice daga d'akin, sannan Dad ya dawo da kallon shi ga Amira yace " Amira karfa ki manta mu iyayenki ne ba sa'anninki ba da zakiy mana wasa da tunani, idan biki yazo ina kayanshi tunda da sauran kwanakin yin bikin, kuma meyasa kika fita kina kuka har na kiraki baki ji ba?"



Amira tace "Dad lokacin da na fita ina kuka fad'amin yai wata Friend d'ina ta rasu shiyasa hankalina ya tashi har kuka ga na fito ina hawaye, jakarshi kuma tana cikin mota."



Dad yace "amma ai ba da mota muka ga kin fita ba," Amira gabanta ya fad'i, saboda ta tuna ta dawo da motar gida, ta kalle shi sannan tace " Dad kenan, ai ba ni kad'ai na fita ba da driver ne, kuma sauka muka yi anan inda kuka ganmu nace drivern ya k'ara so kafin mu taho muma."



Sai a lokacin Dad d'in Amira ya numfasa, sannan yace "to shikenan ya kyauta da yazo mana biki, kuma tunda kin cemin yana taimakon ki kan karatunki zan yi mishi godiya, se dai kar ki kuskura na ji sab'anin wannan zancen kuma," Amira tace " to Dad," Dad yace "yanzu ki tashi kije ki sa a kai mishi abinci da abin sha sai ki bashi wuri ya huta, anjima idan ya fito sai mu yi magana dashi."



Amira ta tashi cike da farin cikin yau Allah ya k'waceta hannun Dad d'inta.



Tun daga ranar Amir bai sake kwana d'akin Amira ba, yanzu kulawarshi ma ba iya Amiran kad'ai ba ta tsaya harda iyayenta da 'yan uwanta, hakan ya k'ara basu damar sakewa sedai ba kamar da ba saboda yanzu basa keb'ewa suyi hira kamar da saboda idanun mahaifin Amira da wasu daga cikin 'yan gidan dake kansu, sedai ko yaushe suna mak'ale a waya da kuma chat.



Bayan ansha biki na kece raini an kai Amarya d'akinta ranar Litinin Amir yace zai juyo ya dawo, bayan ya had'a kayansa yazo falo ya duk'a bayan ya gaisheda Dad da kawunta sannan yace musu shi zai koma, Amira na zaune kusa da Dad d'inta sai aika wa Amir da harara take a fakaice.



Dad yace " ai tunda an k'are shagalin bikin kawai Amira itama ta shiga ta shirya ta bishi su koma tare, cike da farin ciki mara misaltuwa ta mik'e cikin sauri duk aka bita da ido ganin yanda ta mik'e d'in, tai saurin b'oye murnarta ta d'an b'ata rai sannan tace " gaskiya Dad ni ban gaji da ganinku ba, ka bari after five or six day's na koma makarantar."



Dad yace " a'a daughter tashi ki shirya an gama biki me zaki zauna kiyi kuma, kuma mu dama ai bazaki tab'a gajiya da ganinmu ba, oya tashi maza ki shirya," haka ta tashi tana bubbuga k'afa ita a dole bata son komawa, sai da ta kai bakin k'ofa ta juyo suka had'a idanu da Amir ta d'an yi tsallen farin ciki tare da kashe mishi ido d'aya sannan ta fad'a d'aki da sauri.



Amir ya sauke idanunshi yana murmushi a yayin da Dad ke k'ara yi mishi godiya tare da rok'on shi kan k'ara kulawa da karatun su da na Amiran.



Kowa na d'akin yai tsit, hatta kawun Amira mamaki suke yanda suka san duk tsattsauran ra'ayi da dokoki kan yaran gidan da Dad d'in yake amma ya iya yarda ya amince Amira ta bi Amir su koma kamaranta tare, duk sun k'osa su tafi kowa ya fara antayo mishi tambayoyin dalilinshi na yin haka, shi kuwa Dad yana lura da yanayin su duka, murmushi kawai ya yi.



Ba'a d'auki wasu dogon lokaci ba sai ga Amira itama janye da jakarta, d'aya daga cikin security's d'in gidan ne ya karb'i jakarsu ya fice dasu yasa a mota, sannan suka tashi gaba d'aya harda su Dad aka rakosu har bakin motocin da zasu kaisu tashar jirgi.



Sallama suka yi da kowa na gidan sannan suka shiga mota, suka fice daga gidan inda sauran motocin ke mara musu baya.



Bayan fitarsu kawu ya kalli Dad yace "amma yaya yau ka bawa kowa mamaki a gidan nan, yanda kake da tsattsauran ra'ayi kan kowa musamman matan gidan nan akan samari amma yau kai da kanka kake basu damar tafiya tare."



Dad yai murmushi sannan yace "tun ranar da Amir ya shigo gidan nan nake lura dashi, kuma nasa

8 / 31