Author : LASHMINZY Category : Romantic Hausa Novels
Page 85-86
''''''''Kamar yadda kuka sani yau monday kuma yau su Amatu zasu fara zuwa school. Da misalin ƙarfe bakwai na safe na shiga part ɗin Amatu, WoW masha Allah kawai na iya furtawa saboda kyan datayi, "sanye take da dogon hijabi me hannu har ƙasa wanda ko kayan datasa ba'a gani, "hijab ɗin yasha guga sosai kuma kalar maroon ne kamar yadda safar ƙafarta ke kalar maroon a yayinda kafaɗarta ke saɓe da handbag baƙi mekyau."Fuskarta kuwa ko ban faɗawa me karatu ba ya san tana cikin tsantsar farinciki.
A hankali Abdulrahman ke saukowa daga saman bene kamar wanda baison taka ƙasa shima ya shirya cikin manyan kaya wanda suka zauna dam a jikin shi, sai kuma baƙar jakar shi dake rataye a kafaɗar shi. Tun daga saman bene suke aikawa junan su da saƙon soyayya ta cikin ido har ya sauko ya ƙaraso wurinta. Murmushi ya sakar mata cikin zolaya yace iyee yau su baby za'a fara ɗauƙar lectures ya ƙarasa faɗar maganar yana mai yi mata dariya.
"Pillow ta ɗauko ta jefeshi dashi a yayinda ya kauce yana mata dariya, "cike da shagwaɓa ta faɗi zauna saman kujera tana bubbuga ƙafa a ƙasa wai sai ta faɗawa ammie. Cikin marairaice mata ya ƙaraso wurinta ya duƙa a gabanta yace sorry baby na kinga har kin ɓata kwalliyar taki ko, "ya faɗa yana mai shafo fuskarta.
Ita kuma harara ta banka mashi gami da cewa wace irin kwalliya nayi kai dama daƙyar kabari na shafa common powder?? Ɗan bata rai yayi yace toh so kike in bari kiyi kwalliya kowane ƙato ya kalle mun ke? Shuru tayi masa sai yace toh tashi mu tafi karmu makara.
Nan ta miƙe tsaye yaja hannunta suka fito.
A ɓangaren ameerah ma ta shirya tsaf itama sanye take da hijabi har ƙasa, "a bakin ƙofa suke tsaye ameerah na cewa ita fa ta gaji da ɓoye-ɓoyen da akewa amatu ya kamata a fito fili a faɗa mata. Abdul yace ameerah me kikeci na baka na zuba ne wai? Idan lokaci yayi zamu faɗa mata.
Ni yanxu matsala ta ita ce makarantar ku ɗaya da Abdulraman, "wallahi lokacin da nake faɗawa abdulrahman makarantar ku ɗaya da inda yake lecturing saida yayi kusa sakin fitsari saboda tsoro, kuma..... "Ameerah ta katse shi tace toh ku faɗa mata gaskiya mana kafin ta gane da kanta man. Abdul yace hmmm bazaki taɓa ganewa ba, "ameerah tace miye bazan gane ba??
""""Babu wata ɓoye-ɓoye Abdul yace muna zargin amatu nada juna biyu saboda yanayin ta da muka gani, "kuma abunda yasa muka jinkirta faɗa mata gaskiyar lamarin shine muna son sai mun tabbatar da in cikin ne da ita sai mu faɗa mata, kinga hakan da mukayi shine mafita dan nasan kodan albarkacin ɗan shi dake jikinta zata iya haƙura suci gaba da zaman su.
Ajiyar zuciya Ameerah tayi tace eh gaskiya wannan hakane toh amma yanzu wa zai kaimu school?? Murmushi yayi mai sauti haɗe da shafo kumatun ta yace sweet ameerah kenan kedai kawai mu tafi zaki ga abunda zai faru. Girgiza kanta kawai tayi tabi bayan shi.
A daidai parking slot suka tarar da Amatu da Abdulrahman, "suna ƙarasowa suka gaisa, Abdulrahman kuma ya ɗan matsa nesa dasu ya ƙara waya a kunne, sedai banji abunda yace ba kawai naga ya dawo wurin su, kallon su gabaɗayan su yayi sannan ya dawo da kallon shi zuwa ga Amatu yace ayi mun afuwa yanzu aka kirani wai an kawo emergency nan asibiti inyi sauri.
Duk da cewar taso ace shi zai fara kaita makaranta ranta bai ɓaci ba saboda tasan yanayin aikin su kuma aiki ne na samu lada, da fara'arta tace tau ai babu komai kayi sauri ka tafi. Toh yace yana kallon abdul yace hey bro ka kula mun da matas kaji ya ƙarasa faɗar maganar yana mai kashe mashi ido
"Shima abdul fakar su yayi ya ɗaga wa abdulraman babban yatsar shi 👍🏻 alamar yayi daidai kenan.
Nan Abdulrahman ya shige motar shi ya wuce suma suka take mashi baya sedai ba hanya ɗaya sukabi ba. Suna tafe suna hira har suka iso cikin makarantar, "inda abdul bai wuce ba sai daya nuna wa kowaccen su department ɗinta da kuma hall ɗinda zasuyi lecture kan ya tafi.
"Zaune suke a wani haɗaɗɗen ƙaton hall wanda cike yake da ɗaruruwan mutane sedai abu mafi burgewa shine duk yawan jama'ar dake ciki baisa zafi ba saboda akwai AC dakuma fankoki masu bawa hall ɗin iska.
Wuri ɗaya suka zauna saboda bayan abdul ya siyo musu timetable sai yaga ai suna da lecture yanxu kuma duk wuri ɗaya zasuyi. Duk da ba abu ɗaya suke karanta ba amma yawaicin courses ɗin ma tare zasuyi shi.
"Zaune suke ko waccen su da joting note a gabanta sun mayar da hankalin su kan lecturer.
'Bayan abdul ya saukesu, zai fita kenan har ya kai gate sukaci karo da Abdulrahman na shirin shigowa, "saukar da glass dukan su sukayi haɗe da sakarwa junan su murmushi sannan kowa ya kama gaban shi.
"Da misalin ƙarfe huɗu na yamma su Amatu suka fito daga lectures, tsaye suke a bakin hall ɗin suna magana da wasu ƴan mata guda biyu, "ɗaya daga cikin su ce ke cewa gaskiya ya kamata suje su siyo handout dan haka akayi da koyarwa basu da shi suma ƴan matan yau suka fara zuwa.
Eh gaskiya dan ni wallahi banji daɗi ba kowa da handout a gaban shi mu kuma mun zuba na mujiya muna kallon malami, "ameerah ta faɗa cikin nuna damuwa, "Zaliha tace toh me kuke jira kawai mu tafi. Nan suka kama hanyar zuwa minimart dan siyan handout sedai sunayi suna tambaya har suka gano wurin.
Ko waccen su ta siya sannan suka bi hanyar dawowa, suna cikin tafiya ne Amatu ta hangi wata mota sak data abdulrahman, dan ita ta ɗauka ko shine sai ganin kawai tayi motar ta wuce su da gudu. Ameerah kuma bata lura ba dan hankalinta na kan su zaliha da suke hira tana faɗa musu ai taga students handbook wasu rules and regulations idan ka gani sai kayi dariya, shine Ameerah ke cewa tana so
"Amatu da sai yanxu hankalinta ya dawo kansu tace gaskiya nima ina so saboda karmu karya dokar makaranta, "sai nazifah tace ai su bari gobe tunda safe suje su anso, "Amatu tace daman ansowa akeyi ba siya ba?? Zaliha tace eh mana da zarar kinje da ID card ɗinki na school zasu baki.
Toh kawai Amatu tace tayi saurin ɗaukar wayar ta dake ringing, cikin sanyin murya tace ai na ɗauka ko Abdulrahman ne zai mayar damu gida shida ke cikin makarantar, "daga can ɓangaren da take waya yace a'a ai tun ɗazu nayi waya dashi yace idan na fito asibiti inzo in ɗauke ku inku tashi, "owk tau bakomai sai kazo ta faɗa haɗe katse kiran.
Ameerah da hankalinta ke kan Amatu tunda ta fara waya tace yaya dai? Amatu ta amsa ta tace cewa gashi nan zuwa ɗaukar mu. Ameerah ta amsa da toh.
Nan suka samu wuri suka zauna zaliha da hafsat kuma hostel suka wuce dansu kwana sukeyi. Basu wani daɗe a wurin ba sai ga Abdulrahman yazo da irin motar da amatu ta gani, "hakan kuwa ba ƙaramin damuwar tayi ba dan suna cikin mota sai datayi magana Abdulrahman da ameerah suka kalli juna ta madubi sai ameerah tace kin dai ga irin motar amma bashi bane, "Abdulrahman ya ƙara da cewa nida nake asibiti ina naga sararin zuwa makarantar ku? Shine ai ameerah ta faɗa.
"Nan suka kawar da zancen suka ɗauko hirar school ɗinsu suna bawa Abdulrahman labarin abubuwan da suka gani.
Har suka iso gida.
A gajiye Amatu ta cire zumbulelen hijabin ta haɗe da faɗawa saman kujera, "ɗan hutawa kaɗan tayi ta shiga kitchen tasha ruwa, "Abdulrahman kuwa daman ɗaki ya wuce dan ajiye jakar shi. Bayan ya aje ne ya ɗauki wayar shi ya fara dialing number Abdul, "cikin ɗan ƙanƙanin lokaci ya ɗauka, yace ɗan uwa yane? Abdulrahman ya bashi labarin abunda Amatu tace na ta ganshi kuma da gaskiya shi ɗin ne dan shima ya gansu kuma babu halin ya koma shiyasa dayayi kusan isowa wurin su yabawa motar wuta duk cewar tana da tinted ba mai iya kallonshi.
Abdul yace gaskiya wata rana za'a iya samun matsala kawai ka ɗauƙeta ka kaita asibiti a aunata, idan harya tabbata da gaske tana da juna biyu tau shikenan idan ma bata dashi ya zama dole a faɗa mata gaskiya. Abdulrahman yace tana mun kallon likitan ne zan kaita asibiti a aunata?? Cike da damuwa abdul yace af hakane fah tau yanzu ya za'ayi kenan??
Abdulrahman yace nima kaina ya ƙulle amma bari idan ka dawo mayi magana, "abdul yace toh, daga nan ya katse kiran.
Tashi yayi daga zaunen da yake ya shiga toilet ya watso ruwa sannan ya shafa vasilin, dan yanzu yabar shafa duk wani mai me kamshi ko turare saboda Amatu. Yana cikin zura ƴar farar jallabiyar sa kenan sai gata ta shigo sanye cikin doguwar rigar yadi mara nauyi........
Comment
Share
[3/9, 4:43 PM] Lashminzy😎: 💫🌞💫🌞💫🌞💫
*RUDANI*
💫🌞💫🌞💫🌞
Story & written by
Lashminzy
💥GÕLDÊÑ"S WRÌTÊRS
ÀSSÔÇÎÃTÎÒÑ💥
'''vote me on wattpad @lashminzy'''
Masoyana ina sonku da ƙaunar ku a duk inda kuke, kuma masu turo saƙonni ina jindaɗi sosai ngd, Allah yabar mu tare ❤ ONE LOVE
Page 87-88
""""Ƙarasowa tayi wurin shi ta taya shi sanya rigar sannan taja hannun shi suka fito palour, ta zaunar dashi a gaban abincin data jera musu nan tsakiyar palour. Shi kuma binta kawai yake da ido kan ta zauna ya janyota jikin shi yace baby kina ji dani wallahi. Ɗan murmushi tayi tace toh inban kula dakai ba wazai kula mun dakai, "ko so kake inyi banza dakai wata ta ƙwace mun kai??
Ƙyalƙyacewa da dariya yayi yace haba baby ai karki damu babu wacce ta isa ta ƙwace maki ni saboda zuciya ɗaya nake dashi kuma tuni na daɗe da mallaka wa matata farinciki na shi. "Murmushi tayi me sauti haɗe da rufe fuskarta da tafukan hannunta cikin zuciyarta tana jin wani irin son mijin nata na ƙara shigar ta.
Shima murmushin yayi ya jaye hannunwan ta daga fuskarta ya riƙesu ya manna mata kiss a goshi kan ya saketa ya ɗan marairaice fuska yace "baby haƙuri na ya ƙare plsss ayi yau" ya ƙarasa faɗar maganar yana mai langaɓar da kai. Shuru tayi masa duk da tasan bata kyauta amma ita karan kanta batasan dalilin da yasa bata son ya kusance ta ba.
"""Iskar bakin shi ya fesa mata a fuska dan yadda yaga ta faɗa duniyar tunani, duk da ba wasa yake mata ba dan ya kwantar mata da hankali yace "baby muci abinci wasa nake maki", sai a sannan ta ɗago kanta ta kalleshi cike da jin tausayin shi, "toh kawai tace ta fara serving ɗinshi, yana bata tana bashi har suka kammala cin abincin
Kwashe plates ɗin tayi takai kitchen ta wanke su kan ta dawo palour kamar yadda ta saba, zama tayi saman cinyar shi haɗe da langwaɓar da kanta bisa ƙirjin shi
'"Cikin sigar shagwaɓa harda wani ɗan shafa gemunsa tace plss ya Abdul ka kaini gidan ammie! dan tunda akayi auren su sau biyu kawai ta taɓa zuwa, na biyun ma baiko san taje ba, sai daya dawo gida ya tarar batanan.
Aikuwa na yahau dokin mulki yayu fushi da ita, haƙuri kam yasha harya gaji amma fur yaƙi, "abu kamar wasa da dare yayi rufe ƙofar dakinsa yayi, "da safiya tayi Amatullahi taje ta faɗawa Abdulraheem, nan ya tasata a gaba sukaje suka sameshi, yayi ta bashi haƙuri kafin ya haƙura. Kuma yajawa Amatu kunne akan ko nan da can zata tafi ta nemi izinin mijinta kafin taje idan ba haka ba mala'iku zasu dinga tsine mata.
Harda ɗan guntun hawayenta ta duƙa gaban Abdulrahman ta roƙeshi gafara yace ai babu komai ya wuce kawai yayi hakan ne danta gane kuskurenta. Daga nan sukaci gaba da zaman su kamar yadda suka saba. Kuma tun ranar bata ƙara cewa zata gidan ammie ba sai yau
"Cike da jin kasalar shafar shi da takeyi yace indai kina son na bari kije gidan ammie toh sai kin bani hakki na, idan kuma ba haka ba sai kiyi sha zamanki, "mutsu mutsu ta farayi a jikinshi wanda ba ƙaramin tayar mashi da hankali tayi ba. Cije lips inshi yayi na ƴan sakanni kan ya saki yace kin yadda??
"Kamar jira yake ta bashi amsa ya sungume sai bedroom dinshi ya kaita, can tsakiyar gado ya kwantar da ita kan ya cire jallabiyar shi ya faɗa saman ruwan cikinta, "sai data ɗanyi ƴar ƙara jinshi a saman ta, "babu wani ɓata lokaci yafara kissing dukan sassan jikinta, "sai nishi yake still yana kan romancing ɗinta, "ita kuma sai wani turje masa take daga bisani kuma taci gaba da mayar mashi da martani dan wasu irin saƙonni yake aika mata dasu wanda baki bazai iya faɗan su ba.
Ganin abun nasu na shirin makantar dani yasa nabaro musu ɗakin 🙈
******
''Yau ta kama weekend, kowa yana gida yana hutu amma banda su Amatu da suka fita ziyara saboda sun kwana biyu basuyi ba kuma babu lokacin zuwa saboda makaranta shiyasa yau da yake weekend suka fita duk tare da mazan su. Gidan su amatu suka fara zuwa da gidan aunty hajara kan sukazo gidan mummyn Abdulrahman, bayan sun gama hirar su ne sukazo gidan ammie.
Nan suka babbaje anata hira kai kace ba surukkai bane saboda ammie zama tayi cikinsu ana ta hira ciki kuwa harda samha data biyo su sai kuma su marasa kunyan mazajen nasu. kaddai kuso kuga Abdulrahman ba kunya ba tsoron Allah, rungume yake da Amatu tun shigowar su, sai da ammie tayi mashi magana kan ya saketa yana wani cin magani.
Hira suke gwanin sha'awa ga ammie tayi musu tarba na musamman dan tasan da zuwan su, "zama sukayi a tsakiya palour anata hira ana dariya da kuma ƴan tsokane-tsokane, "ana cikin hakane Amatu ta fara kakarin amai, "da gudu ta shiga toilet ɗin ƙasa tafara kwaranyo amai, sai data kai kusan tsawon minti biyar kan aman ya tsaya, Abdulrahman sai sannu yake mata, suma gabaɗayan su suna bayanta suna jero mata sannu.
"Ammie ce ta shigo toilet ɗin taja hannunta suka haura sama, "Abdulrahman yabi bayan su aiko ammie na ganin shi aika mashi da hararan ya biyosu zai gane, "cike da jin haushi ya koma palour ya zauna kamar wani maraya, "Abdul kuwa sai dariya yake mashi, "ameerah kam duk hankalinta ya tashi gashi tana son tabi ammie kuma tana tsoron kar yadda ta hana mijinta ya bita itama ta hanata shiyasa kawai ta nemi wuri ta zauna tana jiran fitowar su.
Ɗakinta ammie takaita ta zaunar da ita saman gado, cikin kulawa tace ƴata yaushe kika fara wannan aman ne?? Amatu ta sunnar dakai ƙasa tace jiya na fara shi, ammie tace mijinki ya sani? Gyaɗa kai tayi alamar a'a, ammie tace to meyasa baki faɗa mashi ya kaiki asibiti ba?? Cikin rashin sanin amsar da zata bata tayi shuru.
Ƙura mata ido ammie tayi na ɗan wani lokaci tana nazari dan tun shigowar ta gidan ta lura da yanayinta, sai kuma yanzu dataga zahiri amma ɗuka da haka bata gasgata abunda take tunani ba. "sai kawai ta fita daga ɗakin, bada jimawa ba sai gata ta dawo da waya a kunnenta, sai dai banji abunda tace ba naga ta aje wayar ta koma wurin Amatu.
A palour kuma kowa jiran fitowar ammie yake, Abdulrahman kuwa yadda kukasan zaune yake saman ƙaya haka ya matsu baiga lafiyar babyn shi ba. Suna nan zaune a haka sai ga wata ƴar dattijuwan mata wadda zata kai sa'ar ammie, "sanye take da fararen kaya riga da wando, da alama dai nurse ce.
Gaishe su kawai tayi ta haura sama, gabaɗayan su suka zaba mata na mujiya👀 a yayinda take haurawa sama.......
Ayi hƙr da wannan
Comment
Share
[3/10, 4:14 PM] Lashminzy😎: 💫🌞💫🌞💫🌞💫
*RUDANI*
💫🌞💫🌞💫🌞
Story & written by
Lashminzy
💥GÕLDÊÑ"S WRÌTÊRS
ÀSSÔÇÎÃTÎÒÑ💥
'''vote me on wattpad @lashminzy'''
Page 89-90
""""Da sallamar ta ta shiga ɗakin ammie, daga ciki ammie ta amsa mata haɗe da tarbo ta ta ida shigowa ɗakin. Batare da sun tsaya wani dogin bayani ba dan ammie ta sanar da Its komai, "sai kawai ta umarci Amatu data kwanta saman gado, ba musu ta kwanta akan lafiyayyen gadon ammie da yasha gyara. Wasu ƴan gwaje-gwaje tayi mata da allura sannan ta bata wata ƴar kwalba tace taje tayi fitsari a ciki.
Bada jimawa ba sai gata ta dawo, ta miƙawa matar kwalbar, "murmushi matar tayi bayan ta gama karewa fitsarin kallo sedai bata ce komai ba. Ammie da duk ta matsu bataji sakamako ba tace Dr zaynab yadai ko ansamu ne? Dr zaynab tayi murmushi tace eh hajiya insha Allah shine amma sai natafi da wannan kwalbar asibiti na duba saboda mu ƙara tabbatar wa. Cike da murna ammie ta hau yi mata godiya sannan ta ɗauko wasu maƙudan kuɗi tasa mata a jaka. Dan tasan halin Dr zaynab indai hannu da hannu ta miƙa mata baza ta amsa ba.
""Amatullahi kuwa sandarewa tayi kamar mota mai remote ta zura musu ido sai yadda akace tayi takeyi, "bayan ammie ta sallami Dr ne ta juyo kan amatu tace ƴata ina fatan yanzu ba abunda yake damunki? Eh yanxu daidai nake jina kawai bakina ne bayamun daɗi, ammie tace "owk tau ga wannan ki tsotsa ni zan sauka ƙasa in samar maki abunda zakici kinji ta ƙarasa faɗar maganar haɗe da miƙa mata vitamin c ɗin da Dr ta kawo.
Tana miƙa mata ta fice daga ɗakin, har takai bakin ƙofar fita ta juyo ta kalli amatu tace karki fita yanzu zan turo maki su Ameerah, Amatu da fara'a ta amsa da toh. Ammie na ta fita ta miƙe