Author : Rabiat Fulani Category : Romantic Hausa Novels
Seda ya sauke ajiyar zuciya.
Sannan yace only! Bansan taya zan fara tunanin rayuwa babu ke ba, wallahi ina sonki sosai fiye da yanda tunani zai kawo a rai!
Murmushi ta masa, “ka kwantar da hankalinka lovely babu abinda ze faru insha Allah sai alkhairi.
Bai ce komai ba kawai yayi murmushi, yana jin wani masifaffiyar kaunarta tana ratsa bargo da jijiyarta.
Hira suka cigaba da yi mai daɗi wacce kai kana jin yanda suke tattaunawa zaka san yanda masoya biyun suke bala’in son junansu!!!
Hira suke cike da nishadi da farin ciki a tare da su.
Chan dai ya kira sunan ta:
“Only!
“Na’am my champ” ta amsa masa cikin wata kasalalliyar murya wacce Saida ta kara kashe masa jiki, duba da irin yanda ya sauke wata sassanyar ajiyar zuciya.
“Kina ganin yara nawa Yakamata ace Mun haifa idan muka yi aure ?
Saida ta dan yi jimmm kafin tace “uhmm yara nawa kake so to kai ranka ya daɗe ? Ta maida masa da tambaya.
Saida ya danyi jimmm kafin yace Ni gaskiya ban wani cika son yara ba, saboda bana son hayaniya kamar yara biyu ko uku sun isa.
“Angama ranka ya daɗe... Zaɓinka shine zaɓin Ma’eesha!
Tsara zaman aurensu suka cigaba da yi da yaran da zasu haifa sunayensu da inda zasu zauna da karatun yaran da komai.
Wayarta ce tayi ringing.... Bloody taga an rubuta da manyan baƙi, batare da ta daga ba ta kalleshi tace special lecturer ya shiga yanzu, naga Maryam ta kirani.
Kamar ƙaramin yaro haka ya taɓe fuska, saboda gaskiya bai ji daɗin katse musu hira da akayi ba.
“Ayyyahh Babe am! Zamuyi waya ai anjima, kuma kaga lecturer dinnan bashida kirki sannan test zaiyi mana bana son nayi missing.”
“Shikenan muje na taka miki zuwa bakin theater ɗin.
Suna tafe suna hira irin ta masoyan da suka shaku da junansu, har suka ƙaraso bakin theater ɗin, yayi mata sallama ya juya wajen motarsa yaja ya tafi tana daga masa hannu.
Saida taga yayi nisa sannan ta juya ta shiga theater ɗin.
Tana shiga Maryam ta harareta “Juliet ai da karki shigo ki tsaya sai malam yazo” ta karasa maganar tana harararta.
Kafin tayi magana malamin ya shigo dole taja bakinta tayi shiru kafin ya korata waje tayi asarar test din.
******** ******* *******
Kallonsa take cikin tsana me ƙarfi kafin tace:
“Haidar wallahi na tsaneka bazan taba iya rayuwar aure da kai ba, tun kwanaki nake fada maka haka baka gane ba, wallahi idan zaka zo kofar gidannan namu sau dubu kalmata bazata taba canjawa ba.
Tana gama fadar haka ta juya zata shiga gida, taji ya riko hannunta.
Tana juyowa batayi wata-wata ba ta daukeshi da mari tare da nuna shi.
This is Last Warning, karka sake dora kazamin hannunka koda a jikin hijab Dina bare a jikina idan ba haka ba zakayi nadama wacce batada iyaka!!
Zubewa yayi a kasa a gabanta batare da ya saki hannun nata ba, shadda ce Getzna a jikinsa fara karr da ita, ɗinkin tazarce amma hakan bai dameshi ba, bai ma san da ya zube a gabanta ba.
“Ina rokonki da girman Allah dan girman soyayyar da kike min, badan halina ba, Karki rabu dani....!!” Hawaye ne ya fara zuba a idanunsa wanda ya tilasta masa yin shiru.
Kallonsa tayi da wani murmushi a fuskarta sam babu alamun tausayinsa a idanunta.
“Waye ya taba ce maka ina sonka ? Wace soyayya ce haka a tsakaninmu da har kake haɗani da girmanta ? Haidarr!! Shin zaka iya fada min lokacin da Ni da bakina na furta maka cewa ina sonka ? Kai yanzu kana tunanin akwai mutumin da na tsana a duniya sama da kai ? Ka manta duk abinda kayi min ta hanyar lalata min jiyata ? Kuma saboda yanzu hankalinka ya gushe har kake tunanin cewa zan iya mantawa na fada soyayya da kai ? Kayi kuskure saleem! Idan duk maza sun kare a duniyar nan babu abunda zai saka ni Humairah na fada soyayya da kai! Wannan shine last warning din da zanyi maka, koda wasa karka sake zuwa kofar gidannan idan ba haka ba zan yi maka wulakancin da har ka mutu bazaka manta dani ba!!!
Tana fadar haka ta juya ta shige gida tana tushe bakinta saboda kar kuka ya kubce mata, kukan da take kokarin yi ba wai na rasa saleem bane ko wani abu, face na tuna irin wulakanci da tozarcin da saleem da iyayensa suka yiwa abbanta da kuma ita.
Har yanzu ta tuna sai taji hawaye sun cika zuciyarta......
Shin wane laifi haidar yayiwa Ma’eesha da har tayi masa wannan mummunar tsanar ??
Shin wane wulakanci iyayensa suka yiwa mata iyayen da yasa bazata iya yafe masa ba ??
Shin me ya juya wannan zazzafar soyayyar da suke wa juna zuwa kiyayya ??
Shin Ma’eesha zata janye maganarta ta kin auren haidar ta dawo ta aureshi ?
Shin haidar ya rasa Ma’eesha ne har abada ??
Shin waye haidar ??
Shin wace Ma’eesha ??
Duk amsar wannan tambayoyin suna cikin littafi Mai suna Haidar ( the lion
🦁
)
Zamu fara posting nasa in Sha Allah new year jan.
Labari ne da yasha banban da irin labaran da kuka saba karantawa.
Domin a cikin labarin zaku hadu da cin amana, yaudara, fansa, mamaki, takaici, da sauransu.
Labari ne wanda aka haɗa kwakwalwar marubuta wajen samar dashi, saboda jin dadinku.
Goyon bayanku muke bukata.
Zamu saka lambar wayar wanda za’a tuntuba daga zarar mun fara posting nasa, domin masu bukatarsa su biya su karanta cikin aminci.
Karku manta taku har kullum ce Rabi’atu Fulani......
Nagode
🥰
💫
❣️ ICEN DAMUNA
💫
❣️
BY
RABI’ATU (FULANI)
Young talented writers association (YOTA)
A har kullum ina Jinjina gareki garkuwata mahaifiyata Abar alfaharina
❤
️
Sadaukarwa ga aminiyata Daya tilo
Amina muhammad haruna
Maman xhara
🤍
Wannan shine rubutuna na farko... Wanda ya kasance True Life story ne da ya faru a labarin wata baiwar Allah....
Yanda na fara lafiya Allah yabani ikon kamallashi lafiya
🙏
☺
️
FULANI
TRUE LIFE STORY.....
💫
❣️ ICEN DAMUNA
💫
❣️
PAGE 25
Banyi aune ba naji duka ta ko ina ta fuska ta ciki, ya Khalil ne shida karuwarsa suka rufeni da duka kamar Allah ya aikosu, ita tana dukana shima yana yi, naga dai abun ba na hankali bane, ban san sanda na saka dukkan karfina na hankada karuwar tasa ba, aikuwa ta fada ta bayan kujera ta wuntsila kanta ya bugu da tiles din falon.
Ya Khalil yana ganin haka yayi kanta da sauri saboda ihun da ta ƙwalla, kafin ya juyo kaina tuni nayi cikin daki da gudu na rufe da key na bar key din a jiki, zama nayi a kasa ina gursheƙen kuka, kai kace mama aka aiko min ta mutu!.
Ji nake wani abun ya tokare min makoshi, takaici baƙin ciki har da kishi ma, mamaki nake ta ya za’ayi ya Khalil ya kawo min wata banzar mace har cikin gidan aurena ? Kuma wai da wata kazamar karuwa zai hadu yana dukana ? Nidin ? Sai kace ba ammatan ya Khalil ba ?.
Ji nayi ya Khalil yana buga kofar da dukkan karfinsa, nayi kamar ban jishi ba, sai kuma naji shiru, bayan kamar minti uku naji ya dawo yana ƙoƙarin buɗe ɗakin da wani mukullin, nan ma dai yaji yaki shiga saboda na bar key dina a jikin kofar.
“Wallahi ko kizo ki buɗe kofar nan ko kuma idan na kamaki sai na lahira ya fiki jin daɗi” Cikin hargowa yake fadar hakan.
“Idan har ka kamani Dan Allah karka barni da rai ka aikawa da iyayena gawata, mara imanin banza mara imanin wofi, kuma wallahi yanda kaci amanata Allah sai ya bi min hakkina” ina fadar haka na fashe da wani irin kuka wanda kai kana jin haka zaka san me kukan daga kasan ransa yake kukan.
“Sumayya Ni kike zagi ?
Eh na zaga ɗin, kuma Wlh ka fitar min da wannan karuwar daga gidana tun kafin na sake fitowa nayi mata abunda bazata taba mantawa dani ba, cikin kuka nake fadar haka, wanda nasan cewa ko karen hauka ne ya cijeni bazan iya fita yanzu na hadu da yaya Khalil ba, dan yanda yake dukan cikina ya tabbatar min da cewar neman rayuwata yake da ta ɗan cikina, a daya bangaren na raina kuma ina jin tabbas zan iya aikatawa wannan karuwar abinda na kudurta a raina.
“Ke kin isa ki kira wata da karuwa ? Ko kin manta asalinki ne ? Kafin ma aje ga wannan ita ai bata da aure! Amma ke kin manta lokacinda da aurenki kika daukeni kika kai gidan mijinki ? Har kan gadonki kika kaini, ko kin manta ne ?!!!!
Sakkk naji nayi, Ni ya Khalil yake wa wannan gorin ? Ni yake fadawa magana haka ? Idan har aka ce ya Khalil zai taba yi min gori haka ko mama ce ta fada bazan yarda ba, kai impact ma mama ta fada din ban yarda ba, tunda tace ya Khalil ba sona yake ba, amma na nuna inaaa nipah ya Khalil yana sona, wani tunani ne ya keto min ƙwaƙwalwata,
Wata rana ya Khalil ya kunsa min takaicinsa na dawo gida ina kuka, na samu mama tana zaune tana tsintar shinkafa a tsakar gida, ina shigowa na fada jikinta na fashe da kuka.
“Mama meyesa ya Khalil zaiyi min haka.....???
Me Khalil din yayi miki ? Ta fada tana ajiye shinkafar da take tsinta.
“Mama Khalil ya daina Sona, da wata na ganshi dazu kuma yanzu nayi masa magana bai ma damu ba, sai ma cewa yayi wai shi ai mijin mace hudu ne, ina fadar haka na kara fashewa da wani irin kuka.
“Sumayya! Ni na haifeki saboda haka dole na fada miki gaskiya, Khalil bazai taba aurenki ba! Idan ma ya aureki wata ran zai goranta miki, Khalil baya sonki, zan iya rantse miki akan hakan, a yanda na fahimta da yanda yake miki gadara ji yake kamar alfarma ma yake miki soyayyar da yake dake.
“Sumayya!! Ki sani duk abinda ake fada akanki yana dawowa kunnena, yanda ake aibata soyayyarku da yanda ake muku kallon kuna fasikanci tare yana dawo min, ban taba daukar hakan ba saboda nasan ƴata bazata taba cin amanar yardar da nayi mata ba, amma dai ki sani zuciya, yau da gobe tun bana ɗauka zan iya ɗauka.
Idan da zan baki shawara ki ɗauka da sai nace ki rabu da Khalil!!!!
Ɗaga kaina nayi na kalli mama nace “mama bazan iya rayuwa ba shi ba! Shine zaɓin raina, ina masa son da bazan iya rayuwa babu shi ba! Ina fadar haka na maida kaina na kwantar a jikinta.
Murmushi mama tayi ta cigaba da shafa kaina “ke a tunaninki yanzu Khalil yana sonki ? Mutumin da baya tsoron ɓacin ranka ai baya sonka.
“Mama fa yana Sona, kawai dai dan sabanin da ake samu ne irin na soyayya.
“Sumayya ba baki nake miki ba amma dai mafi girman kuskuren da zakiyi a rayuwarki shine auren Khalil dan Khalil ba sonki yake ba!!!
Ina jin ta fadi haka na tashi daga jikinta tsam ina tura baki na shige daki.
“Mama na fara nadama!!!! Na fadi haka ina kuka bayan abinda ya wakana tsakanina da mama ya dawo min.
Kuka nake sosai, da gaske nadama ta fara kamani, nadama nake me ƙarfin gaske, ina jiyo ya Khalil yanata surfa min gori iri iri da kuma bakaken maganganu amma ban bi ta kansa ba. Yanzu ta kaina nake dan wani irin nauyi naji ƙirjina ya fara yi ga ciwon kai, kuka nake tun ina iya yi har muryata ta dushe, dag ƙarshe dai daina jiyo maganar ya Khalil nayi wanda da alama ya fita.
A wajen bacci ya daukeni nima ba shiri.
********** ********** *********
Best ta tambayi ya haneep akan maganar ko yanada sani a Lagos ?
Saidai yace bai san kowa ba, amma a abokansa akwai wa’yanda suka sani, amma ta bari gobe sai suje su samu mama akwai maganar da Zasu tattauna.
Washe gari da safe zai fita wajen karfe tara ya ɗauki best suka tafi gidan mama, a lokacin bappa bai jima da fita ba.
Bayan an gaisa little tana jikin mama, sai ya haneep ya fara magana “mama! A yandai ban san wani wanda muke tare dashi a Lagos ba, saidai a abokaina baza’a rasa wa’yanda suke da wa’yanda suka sani a Lagos ba, ko wa’yanda suke da ido, idan ana so zan iya tuntubarsu su tayamu duba, saidai wani hanzari ba gudu ba.
Sumayya aure take yi acan Lagos ba wani abun ba, idan har muka saka wani ya bibiyar mana ita hakan zai taba mata mutuncinta, duk yanda zamuyi masa bayanin cewa aure take bazai yarda ba, zai ɗauka ta tafi yawon shashancine saboda haka nan gaba Wannan abun zai iya taba mata mutuncinta da na yaranta zuwa gaba aure ma sai yayi mata wuya, kin san rayuwar nan yanzu kiwon mutum ake ba dabba ba, a shawarce a matsayina na danki mama kuma yaya a wajen Sumayya kamar yanda kika dage da addu’a kuma kika saka ana hakan to mu cigaba da yi, Allah maji rokon bawansa ne tabbas zai amsa rokonmu zai juyo da hankalinta gida.
Gyada kai mama tayi dan tabbas sai yanzu ta hango abunda haneep ya hango mata, barin ma dai yanda aka sakawa rayuwar ƴarta Idanu a unguwar nan cewa zasuyi an nemota a lagos a wajen shashanci.
Cigaba da kwantar mata da hankali yayi har Saida ta gamsu da cewar ba sai an nemo Sumayya ba, sai bayan ƙarfe goma ya tafi uzurinsa ya bar best a gidan mama akan ta cigaba da kwantar mata da hankali idan ya tashi daga kasuwa zai biyo su tafi.
********* ********* ***********
Wata gigitacciyar yunwa ce ta tasheni ba shiri na farka, agogon dakin na kalla naga karfe sha daya na dare, da sauri na jawo ragowar abincina na fara ci, saidai ba shi da yawa saboda haka ina gama ci na fara tunanin yanda zan sake dafa wani.
Ina nan zaune sai Wajen sha biyu da rabi naji fitar ya Khalil tare da yarinyar nan, inajin yana mata magana akan kar ta dawo gobe zai kirata da kansa.
Yana fita na fito na kulle gidan na shiga kitchen dan kar ma ya dawo ina girki.
Idan ba Idona ne ke min gizo ba sai nace gaba daya babu shinkafa gas ya taho karewa sannan ga taliya ma bata wuce carton daya ba gaba daya dai abincin bazai wuce sati Daya ba, a yanda nakeda cin abincinnan sosai.
Dafawa nayi na dawo na bude gidan sannan na shige daki na kulle.
Saida na gama ci na koshi saina fara tunanin yanzu idan abincinnan ya kare ya zan yi ?
Sadakina ne ya fado min a rai! Ranar da aka daura min aure aka bani sadakina a hannu a hanya muna hanya na bawa ya Khalil sadakin akan ya ajiye min ( Ni ga ƴar daɗi soyayya ) yanzu kuwa nasan da wuya ya bani sadakina, amma dai zan gwada tambayarsa.
Sai Wajen shida ya shigo ya kwanta yana bacci a falo, daga kofar dakina na zauna ina jiran ya tashi, ban fi minti talatin ba kuwa ya tashi yin fitsari, yana tashi yaga Nima na mike tsaye, bai kalleni ba yayi hanyar banɗaki.
“yawwa nace ba!
Idan ya waigo ya kalleni to bangon dakin ya kalleni, shigewa daki yayi na tsaya a wajen ina kunkuni.
Bai jima ba naga ya dawo, zai koma kan kujera ya kwanta nace “yawwa nace maganar sadakina da na baka ajiya lokacin muna hanyar zuwa nan, inada bukatarsu.
Saida yaja iska kafin yayi min reply dan har na fidda ran ce wani abun sai kuma naji yace “kin daukeni wanda bai san abinda yake ba ko ? Uban waye zai ciyar dake bayan ba jin maganarsa kike ba ? Ko kin ɗauka ban san kina bude kitchen ki dafa abinci ba ? To kin dafa sadakinki, sisi bazan baki ba, sannan joy da kika jiwa ciwo na kaita asibiti anyi mata dressing shima a cikin sadakinki, Naira biyar bazaki samu ba, kuma ki fice min daga nan kafin na tashi.
Kuka na zube a wajen ina yi kamar wata yarinya, ganin ya tashi ya nufo inda nake ba shiri na gudu daki na rufo ƙofa, ina cikin dakin ina zuba masa Allah isa.
Tunani na fara yi kenan ya zanyi yanzu ? Da me zan ceci kaina da dan ciki daga wannan yunwar ? Anan ina zaune ina tunani bacci dai ya sake daukata.
********* ********** *********
Haka rayuwa ta fara turawa a haka har Saida na cinye abincin gidan gaba daya sannan hankalina ya kara tashi, ba wanda na sani a garinnan bare na nemi taimako gashi bana da waya.
Maman Uche ce ta fado min a raina yau yana bacci a Ɗakinsa n fito na jawo kofata na mayar na rufe kamar akwai mutum a ciki, lallabawa nayi na fice daga gidan har Saida naje gidan Maman Uche.
Ina shiga ta tareni da murna “yalinya mai cau yau kece a house dina ( da yake hausarta bata gama cika ba kuma sannan da