Chapter 24 Reading ICCEN DAMUNA COMPELET HAUSA NOVELS BY RABIAT FULANI.docx Arewa Novels

ICCEN DAMUNA COMPELET HAUSA NOVELS BY RABIAT FULANI.docx

Author :  Rabiat Fulani Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   24 / 40

69K to 72K   out of 117.2K words

yarinya mai kyau take kirana ).

Murmushi nayi nace yau na kawo miki ziyara ne Maman Uche.

Kama hannuna tayi muka shiga daki, nan muka zauna muna dan hira sama sama saboda ba fahimtar hausarta nake sosai ba Ni kuma ba turanci na iya ba bare broken, Dan turancin nawa baiyi kwari ba, ina dai ji amma bana iya mayarwa shima broken din dan kadan nake ji bana iya mayarwa.

Can na nisa nace “maman Uche anan garin waye kika sani mai Siyan kayan daki ?

“Kece zaki siyar ? Ta tambayeni da hausarta ba daɗi.

Nace eh!

Okay ina siya Ni nan da kika gani komai da ruwana, me zaki siyar muje gidan ki nuna min ?

“Ah ah! Na fada ina zare Idona, ai idan mijina yasan zan siyar miki sai ya kusa yankani, gobe weekend nasan zai fita da safe zuwa inda yake zuwa ban san dai ina yake zuwa ba, idan ya fita zan zo nayi miki magana sai muyi sauri kije ki siya.

Da wannan yarjejeniyar na bar gidanta dan bana son jimawa kar ya Khalil ya tashi mu hadu.

Har na dawo bai tashi ba, na shige cikin daki, dan abinda na ciyo a gidan Maman Uche ne ya rikeni a wannan daren, amma zuwa safiya kamar anyi min sata a cikina, dan wata azababbiyar yunwa nake ji inata lekensa ta taga har Saida ya fita wajen bakwai na safe, yana fita Nima na dauki mayafina sai gidan Maman Uche da sauri muka zo na nuna mata deep freezer din dakina, matar nan saboda kanwar barauniya ce saita siya dubu arba’in, wacce idan lafiya lafiya ne saita kusa ɗari, ban damu ba haka na siyar mata, na kwashi kudi naje na siyi carton din taliya uku da kuma kayan mai da yaji sannan nayo refilling na gas, ( a duniya ba abinda take burgeni sama da taliya da manja ko farin mai ) gaba daya kuɗin da ya rage min a hannu bai kai dubu biyar ba.

Bayan kwana uku na kuma kiranta ta kuma Siyan kayan kallona na cikin daki, dalilin da yasa nake bata kayan dakina saboda nasan ba shigowa yake ba, bazai san na siyar ko ban siyar ba.



******** ********* *********

Haka rayuwa ta dinga turawa Saida ya zamana na siyar da komai na dakina saboda yunwa, kawai katifa ce yanzu a dakin sai kayan ruwa, gadon ma na siyar katifa nake yar wa na kwanta wardrobe Dina ma na siyar kayana suna Ghana must go. Tsakanina da ya Khalil ba magana, saina yi sati ban ganshi ba, bai damu da cina ko sha na ba, sau biyu a tsakankani yanzu yana dukana kuma muguntarsa na fuskanci idan zai dakeni cikina da kaina yake hari, shiyasa na samawa kaina lafiya na daina bari muna haduwa, Maman Uche yanzu ita na ɗauka yar uwa a garinnan, har kuɗi yanzu tana iya bani idan yaso saimu warware a cinikayyar da muke.

Cikina yanzu yana kan wata na bakwai, ya girma ya fito sosai, yanzu na rage bacci abinci ne dai har yanzu ban daina ci ba, saidai karuwa ma da cin yayi, dan yanzu lokaci daya ina iya cinye taliya daya ko sama da haka ma, yanzu ina dafa taliya leda uku ne, a wunin rana daya nake cinyeta.

Waya kuwa na gaji da nema, wani abun Allah kuma har yanzu banyi tunanin Siyan waya da kuɗin da nake samu ba, ( a wannan lokacin na yarda da cewa yunwa tana iya canja mutum gaba daya ta canja masa mindset, )

Kwana biyu yanzu abincina ya dauki hanyar karewa na koma lallabawa, a da ina cin leda uku yanzu na koma cin leda daya da rabi zuwa biyu, ba’ayi nisa ba, shima abincin ya kare gaba daya, wunin yau ruwa nake ta sha saboda ban san me zan siyar ba yanzu na siyi abinci, ji nayi ina niyyar mutuwa da raba hanya na dauki hanyar gidan Maman Uche muka je ta duba plasma din falo ko zatayi mata ( bahaushe yace da rigimar ciki gwamma ta waje, da wannan tunanin nayi wannan kasadar ).

Mun gama ciniki ta siya dubu ashirin da biyar ta bani kudina casss tasa yaronta ya dauki plasma aka ya dora muna juyawa muka ga mutum a tsaye a bakin kofa da jaka a rataye a kafadarsa yana kallonmu...........!!!!!!!

Tirƙashi jama’a ammatan shalelenta fa ta zama barau....barau.....

🤭

Ba ruwana kar team Sumayya suce na kirata barauniya,

Mu hadu a page 26 in Allah ya yarda nice taku har kullum Rabi’atu Fulani.

Talla!

💫

Talla!!

💫

Talla!!!

💫

💫

ALIYU HAIDAR ( THE LION

🦁

)

💫

Paid Book...

By

Rabi’atu Fulani....

&

Ubeera.....

Happy New Year Update......

A zaune suke suna wa junansu wani sanyayyen kallo, wanda duk wanda yaga yanda suke kallon, yasan sun nutse sosai a cikin kaunar junan su.

Gajiya tayi da irin kallon da yake mata dole yasa tayi ƙasa da idon ta.

Lovely!!!!! Taja sunan sosai tana marairaice masa.

Seda ya sauke ajiyar zuciya.

Sannan yace only! Bansan taya zan fara tunanin rayuwa babu ke ba, wallahi ina sonki sosai fiye da yanda tunani zai kawo a rai!

Murmushi ta masa, “ka kwantar da hankalinka lovely babu abinda ze faru insha Allah sai alkhairi.

Bai ce komai ba kawai yayi murmushi, yana jin wani masifaffiyar kaunarta tana ratsa bargo da jijiyarta.

Hira suka cigaba da yi mai daɗi wacce kai kana jin yanda suke tattaunawa zaka san yanda masoya biyun suke bala’in son junansu!!!

Hira suke cike da nishadi da farin ciki a tare da su.

Chan dai ya kira sunan ta:

“Only!

“Na’am my champ” ta amsa masa cikin wata kasalalliyar murya wacce Saida ta kara kashe masa jiki, duba da irin yanda ya sauke wata sassanyar ajiyar zuciya.

“Kina ganin yara nawa Yakamata ace Mun haifa idan muka yi aure ?

Saida ta dan yi jimmm kafin tace “uhmm yara nawa kake so to kai ranka ya daɗe ? Ta maida masa da tambaya.

Saida ya danyi jimmm kafin yace Ni gaskiya ban wani cika son yara ba, saboda bana son hayaniya kamar yara biyu ko uku sun isa.

“Angama ranka ya daɗe... Zaɓinka shine zaɓin Ma’eesha!

Tsara zaman aurensu suka cigaba da yi da yaran da zasu haifa sunayensu da inda zasu zauna da karatun yaran da komai.

Wayarta ce tayi ringing.... Bloody taga an rubuta da manyan baƙi, batare da ta daga ba ta kalleshi tace special lecturer ya shiga yanzu, naga Maryam ta kirani.

Kamar ƙaramin yaro haka ya taɓe fuska, saboda gaskiya bai ji daɗin katse musu hira da akayi ba.

“Ayyyahh Babe am! Zamuyi waya ai anjima, kuma kaga lecturer dinnan bashida kirki sannan test zaiyi mana bana son nayi missing.”

“Shikenan muje na taka miki zuwa bakin theater ɗin.

Suna tafe suna hira irin ta masoyan da suka shaku da junansu, har suka ƙaraso bakin theater ɗin, yayi mata sallama ya juya wajen motarsa yaja ya tafi tana daga masa hannu.

Saida taga yayi nisa sannan ta juya ta shiga theater ɗin.

Tana shiga Maryam ta harareta “Juliet ai da karki shigo ki tsaya sai malam yazo” ta karasa maganar tana harararta.

Kafin tayi magana malamin ya shigo dole taja bakinta tayi shiru kafin ya korata waje tayi asarar test din.

******** ******* *******

Kallonsa take cikin tsana me ƙarfi kafin tace:

“Haidar wallahi na tsaneka bazan taba iya rayuwar aure da kai ba, tun kwanaki nake fada maka haka baka gane ba, wallahi idan zaka zo kofar gidannan namu sau dubu kalmata bazata taba canjawa ba.

Tana gama fadar haka ta juya zata shiga gida, taji ya riko hannunta.

Tana juyowa batayi wata-wata ba ta daukeshi da mari tare da nuna shi.

This is Last Warning, karka sake dora kazamin hannunka koda a jikin hijab Dina bare a jikina idan ba haka ba zakayi nadama wacce batada iyaka!!

Zubewa yayi a kasa a gabanta batare da ya saki hannun nata ba, shadda ce Getzna a jikinsa fara karr da ita, ɗinkin tazarce amma hakan bai dameshi ba, bai ma san da ya zube a gabanta ba.

“Ina rokonki da girman Allah dan girman soyayyar da kike min, badan halina ba, Karki rabu dani....!!” Hawaye ne ya fara zuba a idanunsa wanda ya tilasta masa yin shiru.

Kallonsa tayi da wani murmushi a fuskarta sam babu alamun tausayinsa a idanunta.

“Waye ya taba ce maka ina sonka ? Wace soyayya ce haka a tsakaninmu da har kake haɗani da girmanta ? Haidarr!! Shin zaka iya fada min lokacin da Ni da bakina na furta maka cewa ina sonka ? Kai yanzu kana tunanin akwai mutumin da na tsana a duniya sama da kai ? Ka manta duk abinda kayi min ta hanyar lalata min jiyata ? Kuma saboda yanzu hankalinka ya gushe har kake tunanin cewa zan iya mantawa na fada soyayya da kai ? Kayi kuskure saleem! Idan duk maza sun kare a duniyar nan babu abunda zai saka ni Humairah na fada soyayya da kai! Wannan shine last warning din da zanyi maka, koda wasa karka sake zuwa kofar gidannan idan ba haka ba zan yi maka wulakancin da har ka mutu bazaka manta dani ba!!!

Tana fadar haka ta juya ta shige gida tana tushe bakinta saboda kar kuka ya kubce mata, kukan da take kokarin yi ba wai na rasa saleem bane ko wani abu, face na tuna irin wulakanci da tozarcin da saleem da iyayensa suka yiwa abbanta da kuma ita.

Har yanzu ta tuna sai taji hawaye sun cika zuciyarta......

Shin wane laifi haidar yayiwa Ma’eesha da har tayi masa wannan mummunar tsanar ??

Shin wane wulakanci iyayensa suka yiwa mata iyayen da yasa bazata iya yafe masa ba ??

Shin me ya juya wannan zazzafar soyayyar da suke wa juna zuwa kiyayya ??

Shin Ma’eesha zata janye maganarta ta kin auren haidar ta dawo ta aureshi ?

Shin haidar ya rasa Ma’eesha ne har abada ??

Shin waye haidar ??

Shin wace Ma’eesha ??

Duk amsar wannan tambayoyin suna cikin littafi Mai suna Haidar ( the lion

🦁

)

Zamu fara posting nasa in Sha Allah new year jan.

Labari ne da yasha banban da irin labaran da kuka saba karantawa.

Domin a cikin labarin zaku hadu da cin amana, yaudara, fansa, mamaki, takaici, da sauransu.

Labari ne wanda aka haɗa kwakwalwar marubuta wajen samar dashi, saboda jin dadinku.

Goyon bayanku muke bukata.

Zamu saka lambar wayar wanda za’a tuntuba daga zarar mun fara posting nasa, domin masu bukatarsa su biya su karanta cikin aminci.

Karku manta taku har kullum ce Rabi’atu Fulani......

Nagode

🥰

💫

❣️ ICEN DAMUNA

💫

❣️

BY

RABI’ATU (FULANI)

Young talented writers association (YOTA)

A har kullum ina Jinjina gareki garkuwata mahaifiyata Abar alfaharina





Sadaukarwa ga aminiyata Daya tilo

Amina muhammad haruna

Maman xhara

🤍

Wannan shine rubutuna na farko... Wanda ya kasance True Life story ne da ya faru a labarin wata baiwar Allah....



Yanda na fara lafiya Allah yabani ikon kamallashi lafiya

🙏





FULANI

TRUE LIFE STORY.....

💫

❣️ ICEN DAMUNA

💫

❣️

PAGE 26

Ya Khalil ne a tsaye a kofar dakin, nan da nan jikina ya fara rawa, kamar an kafeni a wajen naji kafafuna suna rawa kuma na kasa guduwa.

“Wacece wannan”? Maman Uche ta tambaya da hausarta mara daɗi tana nuna min ya Khalil.

Wata tsawa ya Khalil ya daka mata cikin broken yace “ubanki ne! Me ya kawoki gidana ? Barauniya ce ke ?

Maman Uche yar duniya ce, saboda haka tsawarsa ba ta bata tsoro ba, a tsanake ta kalleshi tace “Ni ba barawo bane kaya akayi min talla nazo siya, saboda haka karka sake kirana barawo.

Ya Khalil karasowa yayi cikin dakin, nunawa Maman Uche hanya yayi “bi nan kafin na saka police su kama min ke su kulle.

Maman Uche tana jin maganar police ta dauki hanyar waje bayan ta karbi kudinta da ta bani, yaronta kuma ya ajiye plasma din.

Kusa dani yazo ya saka hannu ya ɗago wuyana, idanuna ne suka firfito saboda naji shaƙar da yayi min, Saida ya ga na galabaita sannan ya saukeni, kallona yake cikin tsana.

“Dan ubanki yaushe kika fara min sata a gidannan ? Cikin hargowa yake maganar.

Kakarin amai nake na kasa magana.

Ban san me ya tuna ba, naga ya tashi ya shiga dakina, ai sai ji nayi cikina ya ɗuri ruwa, ba shiri na yunkura da dukkan karfina na nufi hanyar waje, saidai kafin na kai ga fita daga gidan ya biyoni yasa ƙafa ya taɗoni na fadi rub da ciki.

Dukana yake yi tun ina iya kuka har Saida na daina gane komai, cikina kawai yake duka, fuskata kuwa duk ya farfasata, Saida yaga na daina ganewa sannan ya tsallakeni ya shige cikin gidan.



********* ********** **********

Buɗe Idona nayi na tsinci kaina a asibiti, Maman Uche ce a kusa dani, sai wata nurse a tsaye a kaina.

Sannu suka fara yi min, amma kallonsu kawai nake iya yi.

Sai dare likita yazo a lokacin ban jima da tashi daga wani bacci ba.

Dubani ya sake yi sannan yayi min sannu ya fita.

Sai Wajen karfe tara sannan Maman Uche tazo min da abinci ta dubani.

Labari ta fara bani, ta manta wayarta ne akan kujera da ta zauna muna ciniki shine ta dawo ɗauka saita sameni a halin da nake ciki, shine ta shiga tayiwa mijina magana amma bai kalleta ba, shine ta fita ta nemo taimako ta kawoni asibiti, yanzu kwanana biyu a asibiti, ana jiran farfadowata ne sai ayi min aiki a cire abinda yake cikina, ana jiran kuma mijina yazo ya saka hannu ko babana domin a yi min theater, saidai da kamar wuya ace ɗan cikina yana raye, saidai wani iko na Allah a cewar likitoci.

Hawaye ne suka fara zubo min masu zafi, zuciyata ce take tafarfasa, ban taba jin tsanar wani mutum a duniya ba yanzu kamar Khalil.

Ashe masoyi zai iya rikiɗewa ya koma maƙiyi ? Ashe ya Khalil zai iya wulakantani haka ? Ashe ya Khalil zai iya tozartani ? Ashe ya Khalil zai iya kasheni ? Ashe ya Khalil dama ba ya sona ? Ashe ? Ashe ? Ashe ? Tambayoyi ne a raina maƙil wanda na rasa me bani amsarsu sai wanda nakeda tambayar akansa.

A ranar kwana nayi ina kuka saboda zafin abinda ya Khalil yayi min, yanzu shikenan ɗan da na ƙwallafa rai a kansa ya khalil ya kashe min shi ?

Ba’ayi min aikin ba sai wata washe garin, an ciro ɗa namiji amma ba rai kamar yanda likitoci suka fada, an bani shi na rungume yaron a ƙirjina ina jin wani sonsa yana ratsani, na sha kuka sosai yaro mai kyau kamar babansa.

Ba abinda zan ce da Maman Uche dan ta daukeni kamar ƴar cikinta, ta kula dani a asibitin nan sosai, ta kashe kuɗi akaina har na rasa bakin yi mata godiya ita da mijinta, anan ne nasan ashe ta taba zaman arewa tana yabonmu mutanen kirki ne mun yi mata halacci shiyasa itama ta kyautata min jin dadin abinda akayi mata.

Satina biyu a asibitin amma kullum saita kawo min abinci.

A ranar da na cika sati biyu ne ya Khalil yazo asibitin, ina kallonsa na ɗauke kai kamar yanda shima yayi, wata tsanarsa nake ji a raina mai kyau, ji nake a duniya yanzu banada maƙiyi kamarsa.

Takarda kawai ya ajiye min a jikina ya juya ya fita daga ɗakin.

Ban bi ta kanta ba na cigaba da tunanin da nake, amma lokaci zuwa lokaci hankalina yana kan takardar ina son budewa.

Waya naga an ajiye min again a saman takardar, daga kaina nayi na sake kallan wayar, wayata ce ya Khalil ya dawo ya ajiye min, ya kuma sake juyawa ya fita bai ce komai ba.

Yana fita na jawo takardar na fara karantawa “𝑁𝑖 𝑖𝑏𝑟𝑎ℎ𝑖𝑚 𝐾ℎ𝑎𝑙𝑖𝑙 𝑛𝑎 𝑠𝑎𝑘𝑖 𝑚𝑎𝑡𝑎𝑡𝑎 𝑆𝑢𝑚𝑎𝑦𝑦𝑎 𝐴𝑏𝑢𝑏𝑎𝑘𝑎𝑟 𝑠𝑎𝑘𝑖 𝑢𝑘𝑢!!!!!

Na rasa me zanyi a wannan lokacin! Murna zanyi ko bakin ciki ?

Hawaye naji suna zubo min masu ɗumi a fuskata, nidai gashi nan ina jina sakayau ba bakin ciki ba farin ciki kuka nayi ta yi sai Wajen karfe sha biyu na dare sannan nayo alwala nazo na tada sallah, sai Wajen asuba sannan na hakura na zauna ban jima ba aka tada sallar asuba na tashi nayi sallar asuba, a wannan lokacin dai ko Sarkin sata bacci yayi kadan ya saceni, wayata na jawo na kunna.

Fuskar wayar na kalla, hotona ne da na best akan lock screen wallpaper, akan home screen kuma hoton ya Khalil ne, ba shiri na shiga na canjashi da wani.

Phone call history Dina nake ta kalla a raina Ni kaina kunyar kiran gida nake, na rasa wa zan kira! Mama ko best ko ya Ahmad ? Ko kuwa humairah ? Shahada nayi na danna kiran best dan ita kadai ce zata fahimceni kuma bazata taba guduna ba.

********* ********** **********

Kamar a mafarki take jin ringing na wayarta, bata jima da

24 / 40