Chapter 28 Reading ICCEN DAMUNA COMPELET HAUSA NOVELS BY RABIAT FULANI.docx Arewa Novels

ICCEN DAMUNA COMPELET HAUSA NOVELS BY RABIAT FULANI.docx

Author :  Rabiat Fulani Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   28 / 40

81K to 84K   out of 117.2K words

ina son zuwa gidan best.

Dan bana zuwa ko ina iyakacina makaranta.

Mama na tambaya, tace sedai na tambayi baffan.

Koda na faɗa masa kuɗin mota kawai ya bani.

Angel na shirya dan tamin rakiya.

Koda na fito mama ƙaremin kallo take, se kuma tace naje na saka kwalli da powder.

Ayya mama nikam kwalliyan me zanyi, hakan ma isa, na faɗa ina ɓata rai.

Toh kiyi zaman ki kawai ba yanda na iya haka nasaka kwallin amman ban saka powder ba.

Yawwa koke fa mace babu kwalli ai ba mace bace.



********* ********** *********

A bakin titi ya saukeni me napep din a kafa nake karasawa gidan ta.

Buzuwa! Buzuwa!! Juyowa nayi banga me kira na ba, se wata mata mara kyan gani dana gani a baya na.

Dauke kaina nayi kawai naci gaba da tafiya.

Buzuwa ta kara kira na.

Tsayawa kawai nayi ina kallon ta, a raina ina jin kaman nasanta.

Baki ganeni ba ko ? Bosslady ce fa.

Mamaki, tsoro, firgici ne duk yasameni a lokaci ɗaya, kallon ta nake sosai ina son tabbatar da zancen ta.

Kidena mamaki buzuwa.

Kalli yanda na koma, babu komai a cikin rayuwar bariki da bijirewa iyaye se nadama da danasani mara amfani.

Tabbas nasan ko hakkin ya’yan dana lalata baze barni ba.

Bansan yara nawa naja harkar bariki ba.

Yau ki kalle ni kiga yanda na zama.

Kawata ce, tace min akwai wani Alhaji me kuɗi nazo muje, na bita saboda na yarda da ita.

Tabbas buzuwa na samu kuɗi, amman na samo cuta.

Hiv ce ta maidani haka, duk kudin dana samu ya tafi a magani.

Ban karu da komai a bariki ba buzuwa.

Kuka take sosai tana bani labari.

Ni kaina da take bawa labarin kuka nake.

Sosai na kara tsorata da lamarin duniya.

Yanzu me kike anan ?

Gidan karɓar sadaka nazo.

Innallilahi wa’inna ilaihir’raji’un!!!

Kawai nake maimaita wa.

Bansan dame zan temaka miki ba, amman zo muje.

Har gidan best mukaje da ita nace ta jira ni a kofar gidan ina zuwa.

Da sallama na shiga tana zaune ita da little suna kallo, ganin a yanda na shigo mata a birkice ne yasa ta ajiye little tana tambayar ko lafiya.

Idan kina da cash ki bani Please.

Cewa tayi batada kudi bai wuce dubu biyu ba, nace bazaiyi ba, saboda haka ta bani atm nata na tafi zuwa wajen me POS.

Dubu ashirin na ciro na mika mata nayi mata kwatancen gidan mu “ki samu kizo gidanmu zamuyi magana.

Har ƙasa ta tsugunna tana min godiya.

Sallama na mata na koma cikin gidan.



********* ********* *********

Kuka sosai nake wa best.

Ina bata labarin boss lady.

Ke yanzu tausayin ta kike ji ? Ta tambaya tana Taɓe baki

Sosai best! Na fada ina hawaye.

Mezaki mata yanzu, zan temaketa watakila nima Allah ya temake ni.

Tayaya?

Naji yaya Ahmad yace kyauta suke bada maganin, toh kinga zan iya sawa ya temake ta.

Ke ture ta maganar taimako yanzu, shin kin lura da ya Ahmad yana sonki kuwa ??? Dafe kirji nayi ina kallon best baki bude, sai kuma nayi dariya nace bakida hankali ke wlh, wane irin so kuma ?

Dukan cinyata tayi tace “ke wlh da gaske nake miki fa!!!!!

Bugun ƙirjina ne ya karu, tunanuka ne suka fara gilma min a rai.

Ayi min afuwa yau page din ba tsawo sosai a karba da hakuri

Mu hadu a page 28

Taku har kullum Rabi’atu Fulani.

Talla!

💫

Talla!!

💫

Talla!!!

💫

💫

ALIYU HAIDAR ( THE LION

🦁

)

💫

Paid Book...

By

Rabi’atu Fulani....

&

Ubeera.....

Happy New Year Update......

A zaune suke suna wa junansu wani sanyayyen kallo, wanda duk wanda yaga yanda suke kallon, yasan sun nutse sosai a cikin kaunar junan su.

Gajiya tayi da irin kallon da yake mata dole yasa tayi ƙasa da idon ta.

Lovely!!!!! Taja sunan sosai tana marairaice masa.

Seda ya sauke ajiyar zuciya.

Sannan yace only! Bansan taya zan fara tunanin rayuwa babu ke ba, wallahi ina sonki sosai fiye da yanda tunani zai kawo a rai!

Murmushi ta masa, “ka kwantar da hankalinka lovely babu abinda ze faru insha Allah sai alkhairi.

Bai ce komai ba kawai yayi murmushi, yana jin wani masifaffiyar kaunarta tana ratsa bargo da jijiyarta.

Hira suka cigaba da yi mai daɗi wacce kai kana jin yanda suke tattaunawa zaka san yanda masoya biyun suke bala’in son junansu!!!

Hira suke cike da nishadi da farin ciki a tare da su.

Chan dai ya kira sunan ta:

“Only!

“Na’am my champ” ta amsa masa cikin wata kasalalliyar murya wacce Saida ta kara kashe masa jiki, duba da irin yanda ya sauke wata sassanyar ajiyar zuciya.

“Kina ganin yara nawa Yakamata ace Mun haifa idan muka yi aure ?

Saida ta dan yi jimmm kafin tace “uhmm yara nawa kake so to kai ranka ya daɗe ? Ta maida masa da tambaya.

Saida ya danyi jimmm kafin yace Ni gaskiya ban wani cika son yara ba, saboda bana son hayaniya kamar yara biyu ko uku sun isa.

“Angama ranka ya daɗe... Zaɓinka shine zaɓin Ma’eesha!

Tsara zaman aurensu suka cigaba da yi da yaran da zasu haifa sunayensu da inda zasu zauna da karatun yaran da komai.

Wayarta ce tayi ringing.... Bloody taga an rubuta da manyan baƙi, batare da ta daga ba ta kalleshi tace special lecturer ya shiga yanzu, naga Maryam ta kirani.

Kamar ƙaramin yaro haka ya taɓe fuska, saboda gaskiya bai ji daɗin katse musu hira da akayi ba.

“Ayyyahh Babe am! Zamuyi waya ai anjima, kuma kaga lecturer dinnan bashida kirki sannan test zaiyi mana bana son nayi missing.”

“Shikenan muje na taka miki zuwa bakin theater ɗin.

Suna tafe suna hira irin ta masoyan da suka shaku da junansu, har suka ƙaraso bakin theater ɗin, yayi mata sallama ya juya wajen motarsa yaja ya tafi tana daga masa hannu.

Saida taga yayi nisa sannan ta juya ta shiga theater ɗin.

Tana shiga Maryam ta harareta “Juliet ai da karki shigo ki tsaya sai malam yazo” ta karasa maganar tana harararta.

Kafin tayi magana malamin ya shigo dole taja bakinta tayi shiru kafin ya korata waje tayi asarar test din.

******** ******* *******

Kallonsa take cikin tsana me ƙarfi kafin tace:

“Haidar wallahi na tsaneka bazan taba iya rayuwar aure da kai ba, tun kwanaki nake fada maka haka baka gane ba, wallahi idan zaka zo kofar gidannan namu sau dubu kalmata bazata taba canjawa ba.

Tana gama fadar haka ta juya zata shiga gida, taji ya riko hannunta.

Tana juyowa batayi wata-wata ba ta daukeshi da mari tare da nuna shi.

This is Last Warning, karka sake dora kazamin hannunka koda a jikin hijab Dina bare a jikina idan ba haka ba zakayi nadama wacce batada iyaka!!

Zubewa yayi a kasa a gabanta batare da ya saki hannun nata ba, shadda ce Getzna a jikinsa fara karr da ita, ɗinkin tazarce amma hakan bai dameshi ba, bai ma san da ya zube a gabanta ba.

“Ina rokonki da girman Allah dan girman soyayyar da kike min, badan halina ba, Karki rabu dani....!!” Hawaye ne ya fara zuba a idanunsa wanda ya tilasta masa yin shiru.

Kallonsa tayi da wani murmushi a fuskarta sam babu alamun tausayinsa a idanunta.

“Waye ya taba ce maka ina sonka ? Wace soyayya ce haka a tsakaninmu da har kake haɗani da girmanta ? Haidarr!! Shin zaka iya fada min lokacin da Ni da bakina na furta maka cewa ina sonka ? Kai yanzu kana tunanin akwai mutumin da na tsana a duniya sama da kai ? Ka manta duk abinda kayi min ta hanyar lalata min jiyata ? Kuma saboda yanzu hankalinka ya gushe har kake tunanin cewa zan iya mantawa na fada soyayya da kai ? Kayi kuskure saleem! Idan duk maza sun kare a duniyar nan babu abunda zai saka ni Humairah na fada soyayya da kai! Wannan shine last warning din da zanyi maka, koda wasa karka sake zuwa kofar gidannan idan ba haka ba zan yi maka wulakancin da har ka mutu bazaka manta dani ba!!!

Tana fadar haka ta juya ta shige gida tana tushe bakinta saboda kar kuka ya kubce mata, kukan da take kokarin yi ba wai na rasa saleem bane ko wani abu, face na tuna irin wulakanci da tozarcin da saleem da iyayensa suka yiwa abbanta da kuma ita.

Har yanzu ta tuna sai taji hawaye sun cika zuciyarta......

Shin wane laifi haidar yayiwa Ma’eesha da har tayi masa wannan mummunar tsanar ??

Shin wane wulakanci iyayensa suka yiwa mata iyayen da yasa bazata iya yafe masa ba ??

Shin me ya juya wannan zazzafar soyayyar da suke wa juna zuwa kiyayya ??

Shin Ma’eesha zata janye maganarta ta kin auren haidar ta dawo ta aureshi ?

Shin haidar ya rasa Ma’eesha ne har abada ??

Shin waye haidar ??

Shin wace Ma’eesha ??

Duk amsar wannan tambayoyin suna cikin littafi Mai suna Haidar ( the lion

🦁

)

Zamu fara posting nasa in Sha Allah new year jan.

Labari ne da yasha banban da irin labaran da kuka saba karantawa.

Domin a cikin labarin zaku hadu da cin amana, yaudara, fansa, mamaki, takaici, da sauransu.

Labari ne wanda aka haɗa kwakwalwar marubuta wajen samar dashi, saboda jin dadinku.

Goyon bayanku muke bukata.

Zamu saka lambar wayar wanda za’a tuntuba daga zarar mun fara posting nasa, domin masu bukatarsa su biya su karanta cikin aminci.

Karku manta taku har kullum ce Rabi’atu Fulani......

Nagode

🥰

💫

❣️ ICEN DAMUNA

💫

❣️

BY

RABI’ATU (FULANI)

Young talented writers association (YOTA)

A har kullum ina Jinjina gareki garkuwata mahaifiyata Abar alfaharina





Sadaukarwa ga aminiyata Daya tilo

Amina muhammad haruna

Maman xhara

🤍

Wannan shine rubutuna na farko... Wanda ya kasance True Life story ne da ya faru a labarin wata baiwar Allah....



Yanda na fara lafiya Allah yabani ikon kamallashi lafiya

🙏





FULANI

TRUE LIFE STORY.....

💫

❣️ ICEN DAMUNA

💫

❣️

PAGE 27

Zamana a gidan best, zan iya cewa kaso 40 a cikin damuwa ta, ta ragu sosai.

Bata barina na zauna ni kadai, ko yaushe muna tare, dataga nayi shiru zata zauna tana tuno min duk rayuwar mu ta baya.

Haneep kansa hakuri kawai yayi yabar mu tare, gaba daya ya hakura da kwana tare da ita, tare muke kwana da ita da little.

Naji dadin zaman gidan sosai.

Lokacin da zan koma gida senaji tamkar kar natafi, a haka mukayi sallama cike da kewa da kuma begen junan mu.

A ranar dana koma gida, baffa yabani foam na cike na makaranta.

Da yamma na cewa mama ta kiramin ya Ahmad.

Tana fara ringing ya daga.

Yana ganin kiran yaji a jikin sa itace.

Hello yayana.

Uhm ykk ? Alhamdullah.

Daman, daman

Daman me? Bakomai ma. Ina faɗan hakan na kashe wayar.

Jujjuya wayar hannun sa yake, yasan haka kawai bazata kira shi ba dole seda dalili.

Office dinsa kawai ya rufe ya tawo gidan su.

Bayan sun gama gaisawa da mama yace mata yunwa yake ji.

Abinci ta kawo masa ya zauna yaci abincin sa hankali kwance.

Mamah dan Allah zan bata sako a mota.

Kai da kanwar ka.

Murmushi kawai yayi.

Zama mukayi acikin motar sa.

Meyasa kika kirani?

Babu komai.

Buzuwa!

Lumshe idona kawai nayi, na manta rabon da wani ya kira ni da wannan sunan gaba ɗaya.

Yar buzuwa magana nake fa.

Murmushi ne ya subuce min ban shirya ba, jin yanda yayi maganar.

Oya fadamin meyafaru kinji yar kanwata.

Makaranta zan fara zuwa, kuma kawai na hau kame kame.

Shikenam toh tunda bazaki iya fadamin ba, tafi gida.

Ka gaida umma da suhailat.

Zasuji.

“ Bansan meyasa nake jin kunyar sa ba, yanzu wallahi.

Mai da sabulu nake so irin wanda ya taba kawomin saboda tabon jiki na, amman narasa ta yanda zan faɗa masa.

Da daddare ina zaune naga humaira nata kwalliya.

Bandai ce mata komai ba, har ta gama.

Waya aka mata ta mike zata fita.

Ina zaki ? na tambayeta ina kallonta.

Sallama ake dani a waje!

Sosai nake kallon ta, zance fa ? Ah lallai yan matan mama ta girma ashe se aure.

Dariya kawai tayi ta fice.

Acikin raina nake mata addu’a, Allah ya tsare ta.

Washe gari da yamma, sega ya Ahmad a gidan mu, banma san zezo gidan ba.

Yanda nake a haka na fito ban saka komai ba.

Jakar hannun sa ya miƙomin , ga wannan na rubuta miki komai a jiki, ni zan wuce.

Sallama yayi wa mama sannan ya juya ya tafi.

Buɗe jakar nayi wani murmushi ne ya subuce min, ina fito da kayan ciki, mayuka ne da shower gel da sabulu, se wadan su magunguna.

Kotaya ya gane abin da nake so?

Banyi sati biyu ina amfani da abubuwan ba jiki na yafara dawowa daidai.

Koda baffa yayi maganar makaranta mama ce tace ya dan kara mana lokaci.

Yau ina zaune ya Ahmad yazo wajen mama, bansan ya sukayi da shiba, kawai tace natashi na shirya na bishi.

Toh kawai nace ina tunanin ina kuma zamu je.

Sosai nayi mamaki ganin unguwar da na zauna muka nufa tare da shi.

Kallon sa nake amman yayi tamkar be san ina kallon saba.

A kofar gida na, muka tsaya.

Bansan meyasa naji wata matsananciyar fargaba ta rufe niba.

Banason ki fara sabuwar rayuwa da hakkin kowa akanki, kin nemi yafiyar Kowa banda shi, dan haka shima ya kamata ki nemi yafiyar sa.

Kaina kawai na gyada masa.

Sannan ya fita a motar, knocking be jima a tsaye ba aka bude.

Nidai naga yana magana amman bansan dawa yake Maganar ba, se kuma ya nufo motar.

Sakko muje.

Kunya nake ji fa.

Ganin ba fuskan yi masa rigima kawai na fito.

Har cikin gidan muka shiga da sallama.

Wata ce ta amsa mana, sannan tace mu shiga.

Yace ku jirasa yanzu ze fito.

Ina jin sallamar sa nayi kasa da kaina, wata matsananciyar kunyarsa ce ta rufe ni.

Tamkar babu abinda ya faru yace sumayya babu magana.

Kasa kawai na sakko na haɗe hannaye na, kaina a kasa na fara magana a hankali.

Bani da bakin da zan baka hakuri akan duk abubuwan dana aikata maka, amman dan Allah kayi hakuri ka yafemin, Allah yasaka maka fiye ma da yanda ni na kuntata maka, dan Allah ba danni ba.

Ya isa haka sumayya, dan adam baya tsallake wa ƙaddarar sa, na yafe miki duniya da lahira.

Amman zan iya baki shawara ?

Kaina kawai na gyada masa.

Ki kula kodan gaba, su iyaye duk abinda suka nuna basa so, ka hakura da shi yafi maka Alkhairi.

Yanzu kalli yanda kika koma, da kinwa iyayen ki biyayya da duk haka ne faru dake ba.

Bawai ina faɗa miki haka dan baki zauna dani ba a’a ina faɗa miki dan ɗa na kowa ne.

Allah ya kiyaye gaba yasa hakan ya zamar miki darasi anan gaba.

Sosai ya Ahmad yayi masa godiya, nima namasa godiya.

Matar sa ya kara kira muka kara gaisawa sannan muka yi masa sallama muka wuce.

Ko a mota nasiha yaci gaba damin sosai kuma nasihar ta shi ta shiga jiki na.

A kofar gida ya saukeni sannan ya wuce ko gidan be shigaba.

Koda na shiga, tun kafin mana ta tambaye ni na faɗa mata duk yanda mukayi.



********* ********* *********

Lafiya kalau na fara zuwa islamiyya, bani da matsala kodan nasaka wa raina karatun zanyi ne bansani ba amman sosai nake gane karatun.

Bana kula kowa a ajin mu, abinda ya kaini shi kawai nake yi.

Duk yanda mutum yake son shiga jiki na,

28 / 40