JALALUDEEN BOOK COMPELET HAUSA NOVELS PDF AYUSHER MUHD.doc

Author :  Ayusher Muhammad Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   10 / 37

27K to 30K   out of 109.4K words

Jalal ya bita da kallo sannan yacema matar ta fita, abokanan aikinsa suka kalleshi sukace ina taje?

Ido ya runtse sannan yace ina zuwa yai waje da sauri, dubata yafarayi tundaga office d'insu sai dak bai ganta ba, tunanin gun da suke zama ne ya fad'omai dasauri ya karasa gun elevator ya tab'a sai dai abin haushi tana kasa hakan yasa kawai ya wuce beni yafara hawa da sauri, matatakalar nada yawa sosai amma sam bai kula ba yana isa yai saurin karasawa kofar ya bud'e, tare da duba inda take zama, a zaune ya ganta ta had'e kai da gwiwa tana kuka ita kanta batasan meke damunta ba sai dai abu d'aya daya bata haushi katseta da Jalal yai tana magana, Jalal ya karaso gabanta ya tsugun na, cikin sanyin murya yace " me kike anan?"
D'ago jajjayen idanunta tai ta kalleshi cike da mamaki yace kuka? Meya saki kuka?

Harara ta makamai sannan tasa hannu ta share hawayenta jiyai zuciyarsa ba dad'i yace " Haushi kikaji? D'an ta rik'eni?"
Cikin masifa tace " Yama za'ai ka d'inga bari mata na tab'aka?"

Yace " kin kula kuwa? Bafa da saninta bane."
Cikin abin kuka tace " kare mata zakai? Bayan ina ganinta? Tashi ka bani guri tunda kare mata zakai, daga yanzu kuma bazan kara damuwa ba in wata ta tab'aka."

Murmushi yai yace " Don't tell You are jealous? "
Da sauri tace " ni? Inji wa? Akan me zanyi kishin?"
Ya kara sakin murmushi sannan yace " haka ne bayan na san kin tsaneni."
Nan ma da sauri ta kalleshi tace " nidin? Injiwa? Waya fad'ama na tsaneka?"


Kasa yai dakai yana murmushi idanunsa ne suka kai kan kafarta da alama takalmin yajima dunduniyarta ciwo garin sauri ko gudu datai d'azu, hannu yasa ya zare mata takalmin kafarta, kallansa tai cike da mamaki tace " menene?"
D'agowa yai tare da had'e rai yace " gudu kike d'azu?"

Kai tad'aga tare da kallan sa, iska ya d'an furzar yace " in zaki d'inga gudu kidaina sa irin takalmin nan gashi kinjima kanki ciwo."

Murmushi ta saki sannan tai kasa dakai ahankali tace "are u worried about me? "

D'agowa yai ya kalleta nan suka kurama juna ido a hankali ta lumshe ido, Jalal ya kura mata ido shikam bai tab'ajin abinda yakeji a wannan lokacin yana tsirgamai ba, itama idanun data lumshe jitake kamar me, wani irin so ne ke tsirga mata.

Ajiyar zuciyar da Jalal yai ne yasa ta bud'e ido ta kalleshi yace " nabar wayata a office nasan za'a nemeni bari naje mu karasa, ko zakizo mu koma?"

Tace " inafa zan koma bayan na gamajin kunya." Murmushi yai sannan yace " karkisa takalminki ki bari sai na dawo zan taho da plaster."

Kai ta d'agamai nan ya juya yai gaba.

Kallo ta bishi da shi basai ta tambaya ba soyayya ce ke yawo da ita, yau ta tabbatar da hakan dan ita kad'ai tasan metaji da taga mace tana neman jan ra'ayin Jalal, ajiyar zuciya tai tace " My First Love?" Da sauri ta rufe fuskarta da hannayenta alamar kunyar kanta take.




Jalal na komawa suka shiga tsokanarsa meye tsakaninsu, had'e fuska yai yace " meye tsakaninmu kuwa? Kufa kun iya gulma bana kuma san haka, aiki mukeyi muyi mu rabu banasan a d'inga sako personal matters aciki." Jin haka yasa sukai shiru nan suka cigaba.


Basu wani dade ba suka gama, da sauri Jalal yai waje..........


Da sauri ya fita yaje ya siyo plaster ya koma ciki, saidai yana zuwa cikin zumud'i ya bud'e kofar tare da shiga, sai dai abin daya bashi mamaki ba Seemah ba alamarta nan ya shiga duba gun sam batanan kansa ya shafa tare da cewa ina taje? Waya ya d'aga ya k'irata sai dai wayar a kashe take, juyawa yai ya fito.










? *NWA*





@&



?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 2? 0?



Nan ya sauko yana tafe yana nemanta, sai dai sam bai ganta ba, gangarawa yai yaje Office d'in Habib ya bude tare da kallan Sagir, Sagir na ganinshi ya mik'e tare da cewa shigo mana Jalal, nan Jalal ya karasa tare da mikamai hannu, suna gaisawa amma yana waige waige, Sagir ya kalleshi tare da zare hannunshi yace " Jalal me kake nema?"
Kallansa yai yace " Na'am? Kawai nazo mu gaisa ne."

Nagode kwarai, abin ya ban mamaki baka tab'a ko zuwa inda nake ba sai dai ni na nemeka amma yau da kanka? Sagir ya fad'a tare da zama, Jalal yajuya yace bari na wuce ai mun gaisa, ya fad'a yana kallan office d'in Habib.

Sagir yace nagode Jalal, har yakai kofa ya juyo yace" Chairman shi kad'aine a office?"

Da mamaki Sagir ya kalleshi yace shikad'aine zaka shiga ku gaisa ne? Da sauri yace no, na tambaya ne kawai.
Yana gama fad'ar haka yai waje.


Jalal na rufo kofar yai ajiyar zuciya yace ina taje? Nan ya cigaba da nemanta gajiya yai da yawo ya samu wata kujera ya zauna yana d'an maida numfashi, ya d'an dade kafin ya koma inda suka saba zama, yana bud'e kofar ya karasa jiki a sanyeye zuwa inda take zama, sai dai abin mamaki jiyai ance " Deen ka dawo?"

Da mamaki ya kalleta idanunwansa cike da tambayoyi karasa wa yai inda take tsaye ta jingina da bango tana kallansa, kusa da ita yaje ya saki ajiyar zuciya yace " ina kika je? Kinsan neman da namiki kuwa?"

Wani sansanyar murmushin kauna ta saki sannan tace " naji dad'i daka nemeni."

Had'e rai yai sannan ya lankwaso babban yatsansa dana kusa dashi ya d'ana mata a goshi da sauri tasa hannu agun ta kalleshi kamar zatai kuka cikin shagwab'a tace me kuma nai?

Hararar wasa ya mata sannan yace " tambaya kike? Ina kika je? Kika sani nemanki?"

Gun takara sosawa sannan ta matsa daga jikin bangon tace suprise!!!

Kallan gun data matsa yai kwali ne mai fad'i a jiki akwai hoton pizza sai kuma ledar da yana hango lemon kwallin dake ciki, kallanta yai yace " nameye?"

Kai ta girgiza sannan ta zauna ta mai alama da hannu ya zauna nan ya zauna yana kallanta yace " menene?"

Hararsa tad'anyi tace "lunch zamuyi kafin in tafi." Murmushi ya saki sannan yace " abinda kika sauka yi kenan?"

Tace " eh so nake muci abinci tare." Kallanta yai sannan yace next time in zamuci abinci nizan siya banaso kid'ingayin abinda namiji ya kamata yai."
Aranta tace ina gani ba hali gareka ba yaza'ai in d'inga d'aurama wahala.
Sai alokacin ta tuna meya ce mata yanzu.

Ido tad'an rufe sannan tace " next time in zamuci? Kana nufin ba wannan bane last kenan? "

Ehem gyaran murya yai bai magana ba, Had'e rai tai tare da bud'e pizza sannan ta gutsira ta mik'amai sannan nan ya ansa suka fara ci, ta kalleshi tace Deen what are we?


Kallanta yai shima jikinsa yai sanyi cikin sanyin murya yace "we? Kodayake I think munzama we?"
Jiyai tace me kake cewa? Tafad'a tare da bud'e mai lemon ta mik'amai ya ansa tare da kallanta mantawa tai taci abinci da hannun kawai ta rufe idannunta, yaji ne ya shigar mata ido ta saki wani kara, tare da kokarin goge idannun da sauri Jalal ya rik'e hannun da take kokarin kaiwa sannan yai saurin kurbar ruwa ya kuskure bakinsa sannan ya matso a hankali ya fara hura mata idan da yajin ya tab'a, batasan sanda ta ware idanun ba, sam jitai yajin ya tafi kallansa take idannu a bud'e zuciyarta kuwa sai bugawa take da karfin gaske, karkatar da kai yai sannan yagyara zamansa, yace " u are soo clumsy taya zaki......."
Ganin yanda take kallanshi yasa ya hura mata ido yace Kallanfa? Da sauri ta mik'e tsaye d'an jitake kamar bazata iya numfashi ba ta mik'e tana bubuga kirjinta, da sauri Jalal shima ya mik'e yaje gabanta ya kalleta tare da cewa menene kikeyi hakan? Idanunta ta zaro tana kallanshi sannan ta runtse idonta tad'anyi baya daga inda yake, da mamaki ya kalleta yace " Mekike hakan?"

Juyawa tai sannan ta zauna agunta nad'azu tace " kawai nidai kad'an dingayin nesa dani."

Kallanta yai da mamaki yace " Bangane ba? Bakyaso inzo kusa dake? Ko me kike nufi?"

Seemah a hankali ta d'ago ta kalleshi tace " bafa haka nake nufi ba."

Fuskarsa ya matso kusa da tata ya shiga jujuya kai itakam jitai numfashinta ya d'auke, idanuwansa kawai take kallo? Yad'an daga sannan yace " kince bakyason inzo kusa dake amma idanunki sun nuna kinaso me kenan?"

A hankali tai ta furzar da iska tana cewa "Cool Down Seemah." Kallanta yai sannan ya d'au pizza ya kara ci, sai da ya gama ya matso kusa da ita tare da kamo kafarta ya ciro plaster d'in daya siyo ya sa mata a gun dataji ciwon nan, itakam kallanshi kawai takeyi, d'agowa yai yace ba fita zakuyi ba? Kallansa tai tace karfe nawa? Agoggon hannunsa ya duba yace 1 nima tashi zanyi inje mosque, nan ya mike tare da gutsirar katuwar pizza ya tura mata a baki yace " ba kallo ba kice abinci kije kar yayanki yai ta jiranki."

Ya juya ya fara tafiya, sai dayai d'an nisa ya juyo yace kuma ki kunna wayarki.

Ya juya ya fita, kallo ta bishi da shi jitai shakuwa ta zo mata, cire abinda yasa mata a baki tare da kara wata shakuwa, juice d'in ta d'auka tasha sannan ta baza tagumi tace " Seemah ya zakiyi? Haka ake soyayya ko kuma nawa ne hakan?"

Sama ta kalla hasken rana yasa tai saurin yin kasa da kanta, tace dole inyi tambaya kila ko ciwon zuciya gareni ko wani abun.


Tagama cin abinci sannan ta sa ragowar a leda ta mik'e.





Habib bayan sunyi Sallah ya kira wayar Seemah a kashe nan ya tura Sagir yaje ya dubo office d'in ko tana can.

Yana shiga ya tadda ta idar da sallah itama yace " madam ana jiranki."
Nan ta mik'e tare da cewa to, nan ta fito.



Sun shiga mota, Habib ya kalli Seemah yace " Kanwata me kike tunani?" Juyowa tai tace " Yaya baka tunanin wani abun zai kara faruwa ko? Ina tsoron kar abinda yafaru agidansu Hajiya ya kara faruwa.



Kallanta yai jiki a sanyaye ya sa hannu akanta yace " karki damu Seemah insha Allah ba abinda zai faru." Tace ka fad'ama dad zamune? Yace a'a ai ba sai na fad'amai ba in zamu gaida 'yan uwa, tace to.










? *NWA*



@&
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?
=?>? *J?9?9??*=?>?
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?






Na *AYUSHER MUHD*




No. 2? 1?




A wani katon gida suka tsaya, mai gadin da sauri ya bud'e motar tare da mika gaisuwa, sunyi parking sannan Habib ya kalli Seemah yace muje ko? Kallansa tai idanunta sunyi raurau kai ya d'aga mata alamar it's okay.
A hankali ta zuro kafarta ta fito, nan suka jero tare da nufar gidan.

Bayan sunyi knocking aka zo aka bud'e wata yarinya ce wanda a haife batafi Seemah ba, tana ganin Habib ta saki fara'a tace " Yaya Habib yau kaine a gida?"

" Tafi shan ni ba ruwana dake ai." Ya fad'a tare da shiga, Seemah na biye dashi.
Matsawa tai d'aya gefen tace " Haba yayana na kaina ai nasan bazaka iya fishi da ni ba."

Kunnenta ya kama tasa kara tare da cewa yaya Habib da zafi fa? Seemah ce ta kalleshi ta saki fuska tace " kai yaya Habib daga isowa sai a fara da cin zali? Amata hakuri."
Sakinta yai yace " kinci darajar kanwata mai daraja."
Kallan Seemah tai tace " badai mai darajar nan wannan sakaliyar kanwar taka ba.....?"

Hararar da Habib ya maka mata ne yasa tai shiru kallam Seemah yai yace " kyaleta kanwata wannan da kika ganta batajin magana."

Jisukai ance lale maraba da Habibullah, juyawa sukai inda maganar ke fitowa, wata babbar macece wanda kana ganinta kasan takai misalin shekara 50, sai dai tasha kayanta ta kuma d'aura d'ankwali abinta dagwas, fara'a ce sosai a fuskarta Habib ma fuska ya saki sosai ya ja hannun Seemah suka karasa gunta, zama tai suma suka karasa suka zauna a kusa da ita a kasa, Habib ne ya gaida ita sannan Seemah, ta amsa tare da cewa " Zara na neman hanaka hutawa ko?"

Kallan wacce aka kira da Zara yai yace ai Ummy wannan yarinyar tana bukatar bulala a gurina.


Dariya suka saki dukansu, Ummy tace tashi ki kira Abbanku, nan ta mike tana cewa yaya habib zanzo Allah, amma sai yaya Ammar yazo kasar.

Da mamaki Seemah ta kalleta Ammar? Habib ne yace " Gwara ma kizo d'an Allab ba wai saboda Ammar ba kinfi kowa sannan yace bayayi dake."

Da sauri ta karasa b'angaren Abba fuska a had'e, tana dawowa, Abba na shigowa, Abba shima ya taho yana farinciki, Ummy yaji tace " Habib wannan fa? D'an ban tab'a ganinta ba?"
Murmushi Habib yai yace " Kanwa tace Seemah." Ummy ta maimaita Seemah? Seemah?
Abba dake tsaye idanunsa suka tashi daga farin ciki, su ka kad'a sukai jaa, sunan yake maimaitawa a ransa da kuma abinda ya faru a baya, abinda ya ruguzama kaninsa rayuwa ya kuma tada hankali duk zuri'arsu suka zama abin nuni ga duniya, yana tsaye Zara tace "Abba yaka tsaya anan?"

Juyowa sukai dukansu suka kalleshi Habib ya saki Murmushi ya mik'e tare da tahowa gunsa, Ummy kam tunda taji sunan itama jikinta yai sanyi, shiru tai kawai tana kallan Seemah.

Habib na zuwa kusa da Abba ya kama hannunsa tare da cewa " Abba na dade banzo gaisuwa ba ko?"

Kallansa Abba yai idanunnan jawur, zaiyi magana sukaji ance " Hello My Ummy Ur Son is back." Gaba d'aya kowa ya juya ya kalli kofa, saurayine da baifi su Ammar ba sai dai yasha kayan nigogi kana ganinshi kaga saurayin dake ji da kansa, idanunsa nakaikan Habib ya karaso da sauri yace "Hello Bros long time no see"

Baki Habib ya saki sannan ya kalleshi daga sama har kasa yace " Zaid kanannan a yanda kake, nikam yaushe zaka girma?"

Baki yad'an karkata irin salon ' yan gayo maza d'in nan zaiyi magana idanunaa suka kai kan Seemah da sauri yakarasa kusa da ita ya matsa daf da ita yana kare mata kallo, itama kallansa tai tare da kokarin matsawa, mikewa yai yace Wow ummy she is just my type.

Idanu Seemah ta zaro tare da kallansa, Zaid ya kanne mata ido d'aya dasauri tai kasa da kanta, gun Abba ya koma yace " Abba kumin aure please, nan da 1 week inasan auran yarinyarcan."

Cikin tsawa Abba yace " Ashe haryanzu zaid bazakai hankali ba? Daga ganin yarinya kawai kafara min zancen banza? Kasanta ne? Ko kasan tsatson ta?"


Kowa sai daya tsarata a falon.

Cikin rashin fahimta da raahin jin dad'i Habib yace " Abba baka tambayeni ba ai, Kanwatace fa, Seemah."

Abba ya kalleshi cikin bacin rai sai kuma ya juya ya koma ciki da sauri, Habib ya bishi da kallo, Seemah kam tumda take yauce rama ta farko da tsawa ta girgizata, jitai idanunta sun ciciko, Zara ta kalleta tace " Yaya Habib Gimbiyarku na neman yin kuka da alama bata sabajin tsawa ba."

Da sauri Habib ya taho, Zaid yasa gudu ya rigashi zuwa, kusa da ita yakara zama shima kamar me shirin kuka yace " Babyna kiyi hakuri, haka sirikinki yake sai dai nima na dade banga b'acin ransa haka ba, but karki damu tunda ni inasanki zan kareki daga komai."


Matsawa Seemah tai baya kad'an tana mai kallan mekakeyi hakan? Ummy ce tace " Zaid ka bari mana." Tafad'a tare da mikewa tace Habib inasan ganinka.

Nan suka juya, Zara ta girgiza kai tace Seemah ina tausaya mikk kin had'u da cingam d'an manne, itama ta mik'e ta bar falon.


Zaid ya kara matsowa gun Seemah yace " Babyna nasha wahala gurin nemanki,meyasa kika wahalar dani sai yau kika bayyanamin kanki?"


Seemah ta kalleshi da mamaki tace " ni kuma? A ina ka tab'a ganina?"

Jitai ya damko hannunta yakai saitin zuciyarsa yace " anan baby na."

Da sauri ta fizge hannunta tare da nik'ewa tace " Banasan haka."
Shima mikewa yai yace me kikeso to? Fad'amim in miki cikin gaggawa.

Harara ta makamai tace " Zaid kake ko? To bari kaji nifa ba ka ra gareni ba, sannan ba tsoro gareni ba, wannan abin da kakemin bakomai bane illa sallon yaudara ta samari masu ji dakansu, saidai me? Am sorry d'an na riga na gano lagwanka, bakuma na tunanin hakan zaiyi tasiri a guna."


Kallanta yakeyi kawai tana gama magana ya fad'i zaune rugub ya sa hannu a kirjinsa yace " wow! Kaiiii!!! I really like ur boldness, Baby na."
Harararsa takara yi sannan taj hanyar waje.





Habib nezaune a falon ummy, ta kalleshi tace " Habib kad'au yarinyar nan kubar gidan nan tun kafin Abbans Zara ya kara fitowa, dan banaji abin zaizo da sauki, kallanta yai yace " dab Zaid yace yanasanta ko me?"

Ido ta runtse tace " kaidai

10 / 37